Harshen mu Hausa ne

Harshen mu Hausa ne Shafin Harshen mu Hausa ne, akwai labarai daban daban da kuma labarai dumi-dumi; kuma akwai labaran

20/07/2025

A yau ne shafin ta cika shekaru 5 akan sada zumunta ta Facebook

Muna godewa ma'abotan mu. Allah Ya kara muku karama, Amin. 🙏🤗🎉

Akan rasuwar Yarima
20/07/2025

Akan rasuwar Yarima

Allah Ya yi wa Yarima Alwaleed bin Khalid bin Talal bin Abdulaziz Al Saud rasuwa

Shafin Life in Saudi Arabia ya rawaito cewa Yariman ya rasu ne bayan ya yi doguwar suma ta tsawon shekaru 20, har ake masa laƙabi da Yariman barci.

Jama'a, shin kun san sunan tsuntsu a wannan hoto?
19/07/2025

Jama'a, shin kun san sunan tsuntsu a wannan hoto?

Gasar cin kofin Nahiyar Afirka ta mace: Tawagar ƴan matan ƙasar Najeriya masu buga kwallon kafa ta hallaka kasar Zambiya...
19/07/2025

Gasar cin kofin Nahiyar Afirka ta mace: Tawagar ƴan matan ƙasar Najeriya masu buga kwallon kafa ta hallaka kasar Zambiya da ci 5-0 a kwatal fainal

Tsohon shugaban jam'iyyar APC, Dakta Abdullahi Umar Ganduje wanda ya sauka daga shugabancin jam'iyyar APC a watan Yuni y...
19/07/2025

Tsohon shugaban jam'iyyar APC, Dakta Abdullahi Umar Ganduje wanda ya sauka daga shugabancin jam'iyyar APC a watan Yuni ya shirya tafiyar ne kwana biyar kacal da saukarsa daga muƙamin, k**ar yadda Muhammad Garba ya bayyana cikin wata sanarwa a yau Asabar, inji jaridar BBC Hausa

Jama'a, yaya kuke ganin haka?

Allah Ya yiwa tsohon Shugaba Muhammadu Buhari rasuwa a yau, Lahadi, 13 ga watan Yuli a birnin Landan Allah Ya gafarta ma...
13/07/2025

Allah Ya yiwa tsohon Shugaba Muhammadu Buhari rasuwa a yau, Lahadi, 13 ga watan Yuli a birnin Landan

Allah Ya gafarta masa da masa rahama, Amin

Labari daga ƙasar Indiya
13/07/2025

Labari daga ƙasar Indiya

Shugaban wata makaranta a Indiya ya shiga hannu bisa yi wa ɗalibai mata tsirara don gano masu yin al'ada

Ɗalibai a IndiyaAsalin hoton,Getty Images
An k**a shugaban makaranta da wata malamai mata a garin Thane da ke jihar Maharashta ta ƙasar Indiya.

BBC Hausa ta rawaito cewa ana zargin mutanen biyu ne da cire wa ɗalibai mata kaya domin duba ko suna jinin al'ada ko kuma a'a, bayan ganin ɗishi-ɗishin jini a bangon ban-ɗaki.

Ƴansanda sun ɗauki matakin ne bayan mahaifiyar ɗaya daga cikin ɗaliban kimanin 15 ta shigar da koke kan lamarin.

Makarantar na ƙunshe ne da ɗalibai kimanin 600, wadanda ke karatu daga matakin nazare zuwa sakandare.

Lamarin dai ya faru ne a ranar Talata a gundumar Shahpur na birnin Thane.

A ranar Laraba iyayen yara sun yi zanga-zanga a harabar makarantar sannan s**a buƙaci gwamnatin yankin ta hukunta masu hannu a lamarin.

Bayan haka ne ƴansanda s**a sanya ido kan mutum 8 da ake zargi, inda a yanzu s**a k**a shugaban makarantar da kuma wata malama.

Ƴansandan na zargin mutanen da cin zarafi da kuma keta mutuncin ɗaliban k**ar yadda yake ƙunshe a doka.

Bayanin ƴansanda ya nuna cewa lamarin ya faru ne tsakankanin ƙarfe 10 zuwa 12 na rana a ranar 8 ga wannan wata na Yuli, lokacin da shugaban makarantar ya tara yara mata ɗalibai na makarantar su 125 a ɗakin taro na makarantar.

Daga nan ne aka kunna masu bidiyon jinin da aka gani a ban-ɗaki, sannan aka tuhume su da ɓata bangon da jinin al'ada.

Bayanin ya ce daga nan ne aka umarci malamai mata na makarantar su tafi da ɗaliban ban-ɗaki su cire musu kaya domin gano waɗanda ke jinin al'ada.

Lamarin, a cewar bayanin ya girgiza ɗaliban.

Wasu daga cikin iyayen sun ce yaransu sun ƙi zuwa makaranta sanadiyyar kaduwar da s**a yi.

Aliko Dangote ya yi magana akan matatar mai ta ƙasar Najeriya Jama'a, shin kun yarda da Dangote?
13/07/2025

Aliko Dangote ya yi magana akan matatar mai ta ƙasar Najeriya

Jama'a, shin kun yarda da Dangote?

Daga wurin Aure a yau, Juma'a, 11 ga watan Yuli
11/07/2025

Daga wurin Aure a yau, Juma'a, 11 ga watan Yuli

Labari akan hukumar ƴan sanda
11/07/2025

Labari akan hukumar ƴan sanda

Lauya ya maka IGP da wasu mutane a kotu bisa ƙin biyaiya ga umarnin kotun a Abuja

Wani lauya a Abuja, Yahuza Maharaz, ya shigar da kara akan raina kotu kan Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, IGP, Kayode Egbetokun, tare da Isah Yusuf Musa da wasu mutum biyu, bisa zargin kin bin umarnin kotu.

A ranar 25 ga Yuni, Mai shari’a M.A Madugu na Babbar Kotun Taraiya da ke zaune a Bwari ya bayar da umarnin wucin-gadi, inda ya bukaci ƴansanda da sauran wadanda ake kara su ci gaba da barin komai a yadda yake (status quo), kafin fara sauraron karar da Maharaz ya shigar, a madadin Pamodi Pharmacy da ke Abuja.

A cewar takardun kotu da DAILY NIGERIAN ta samu, karar mai lamba: HC/BW/CV/199/2025 ta samo asali ne daga saɓani kan yarjejeniyar haya tsakanin Pamodi Pharmacy da ke Hillcrest Shopping Complex, Lokogoma, Abuja da kuma Isah Yusuf Musa.

Karar ta hada da shi Isah Yusuf Musa, Hill Crest Estate Management Development, Rundunar Ƴansanda ta ƙasa da kuma IGP a matsayin wadanda ake kara na farko zuwa na hudu.

Yayin da ya ke yanke hukunci kan bukatar da ke dauke a takardar umarni lamba: FCT/HC/M/8303/2025, Mai shari’a Madugu ya bada umarnin cewa a tsaya a yadda ake dangane da ofishin haya mai fadin murabba’in mita 160 da ke cikin Hill Crest Shopping Complex/Mall a fili No. 102, Cadastral Zone C09, Ahmadu Bello Way, Lokogoma, Abuja FCT.”

Sai dai kuma duk da wannan umarnin kotu na ci gaba da barin komai yadda yake, wanda ya shigar da kara ya zargi Musa da bayar da umarni a yanke wutar lantarki da kuma rufe ruwan da katin sayar da maganin ke amfani shi.

Hakanan, ya zargi Mista Musa da cire takardar umarnin kotu da aka manna a jikin bangon ginin, duk da umarnin da kotu ta bayar.

Lauyan ya kuma ce rundunar ƴansanda ta gayyaci Manajan Daraktan kamfanin domin yi masa tambayoyi, abin da ya ce ya saɓa wa umarnin kotu.

A cewar saƙon kar-ta!kwana da aka turo masa, an bukace shi da ya bayyana a gaban wani kwamiti na AIG Zone 7 a uau Juma’a.

Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na ‘yansanda, Muyiwa Adejobi, bai amsa tambayoyin da wakilin Daily Nigerian ya aiko masa ba dangane da lamarin.

Menene ra'ayin ku akan haka?
11/07/2025

Menene ra'ayin ku akan haka?

Shettima ya bayyana ƙoƙarin da tsohon Ministan Shari'a Mohammed Adoke ya yi na hana Goodluck Jonathan cire shi a matsayin gwamnan jihar Borno a 2013 sai dai wasu na alakanta hakan da abin da Tinubu ya yi a jihar Rivers na dakatar da gwamna da ƴan majalisa.

Hoto: jama'a, shin kun san sunan wannan tsohon ɗan kwallon kafa?
28/06/2025

Hoto: jama'a, shin kun san sunan wannan tsohon ɗan kwallon kafa?

Address

Festac Town

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Harshen mu Hausa ne posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Harshen mu Hausa ne:

Share