Funtua Post

Funtua Post Funtua Post
Dandalin kawo ingantattun labarai daga Funtua da sauran sassan Najeriya. Muna tabbatar da gaskiya tare da sahihanci a kowanne labari.

WhatsApp=08166055055

🥣 Tambayar dare daga Funtua PostWane abinci ne ake dafa muku a gida da kuka gaji da cinshi? 😅🍽️Akwai irin wancan abincin...
06/07/2025

🥣 Tambayar dare daga Funtua Post

Wane abinci ne ake dafa muku a gida da kuka gaji da cinshi? 😅🍽️

Akwai irin wancan abincin da idan ka hango shi a kitchen, har a zuciyarka zakaji Ka ƙoshi kafin a gama dafa shi? 😩😂

Faɗi naki/naka a comment 👇

Wani mummunan hatsarin mota da ya faru da safiyar yau Lahadi a kan hanyar Zaria zuwa Kano ya yi sanadiyyar rasa rayukan ...
06/07/2025

Wani mummunan hatsarin mota da ya faru da safiyar yau Lahadi a kan hanyar Zaria zuwa Kano ya yi sanadiyyar rasa rayukan mutane 21.

Hatsarin ya afku ne da misalin 8:23 na safe a Kasuwar Dogo, Dakatsalle, inda wata motar bas kirar Toyota Hummer (KMC 171 YM) ta yi karo da tirela kirar DAF (GWL 422 ZE), kamar yadda FRSC ta jihar Kano ta tabbatar.

Bincike ya nuna cewa direban bas ɗin ne ya yi aron hanya, wanda hakan ya haifar da mummunan gobara da ta lakume motocin biyu tare da kone mutane da dama kurmus.

Allah ya jikansu da rahma. 🤲

Jigo a jam’iyyar PDP na jihar Katsina kuma dan siyasa mai tasiri daga karamar hukumar Bakori, Hon. Abubakar Tsoho, ya fi...
05/07/2025

Jigo a jam’iyyar PDP na jihar Katsina kuma dan siyasa mai tasiri daga karamar hukumar Bakori, Hon. Abubakar Tsoho, ya fice daga jam’iyyar PDP.

Bayanai sun nuna cewa matakin nasa na ɗaya daga cikin sauye-sauyen siyasa da ake ci gaba da gani gabanin zaben 2027.

📌 Za mu bibiya domin jin inda zai dosa.

'Yan jam’iyyar haɗaka na jihar Katsina sun shiga sirrin shirin kwace mulki a zaben 2027.A zaman da ya gudana a ofishin H...
05/07/2025

'Yan jam’iyyar haɗaka na jihar Katsina sun shiga sirrin shirin kwace mulki a zaben 2027.

A zaman da ya gudana a ofishin Hon. Dr. Jamilu Lion da ke Abuja, sun halarta:

Sen. Ahmad Babba Kaita

Hon. Aminu Makera

Hon. Jamilu Lion

Hon. Abubakar Salisu ASAS

Shin jam’iyyar ADC na da karfin girgiza kujerar Gwamna Dikko Radda a 2027?

Faɗi ra’ayinka👇

Hon. Sani Aliyu Danlami (Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Katsina ta Tsakiya) ya karɓi bakuncin wasu daga cikin matasa...
05/07/2025

Hon. Sani Aliyu Danlami (Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Katsina ta Tsakiya) ya karɓi bakuncin wasu daga cikin matasan da ya samar wa aiki a Hukumar Kashe Gobara ta Gwamnatin Tarayya.

Sun kai masa ziyara a gidansa da ke cikin garin Katsina yau Asabar, domin nuna godiya.

Kungiyar Masu Kishin Harshen Hausa da Al’adunta ta ƙasa ta naɗa Sabi’u Abdu a matsayin shugaban reshen jihar Katsina.Wan...
05/07/2025

Kungiyar Masu Kishin Harshen Hausa da Al’adunta ta ƙasa ta naɗa Sabi’u Abdu a matsayin shugaban reshen jihar Katsina.

Wannan na cikin sanarwar da shugaban ƙungiyar na ƙasa, Auwal Yazeed Muhammad Matawalle, ya fitar a Juma’ar nan 4 ga Yuli, 2025.

Kafin wannan naɗi, Sabi’u Abdu ya shahara a matsayin ɗaya daga cikin masu fafutukar bunƙasa harshen Hausa, tare da gyara kura-kuran da ke barazana ga harshen da al’adun Hausawa.

Kungiyar ta taya shi murna tare da fatan Allah ya ba shi ikon sauke nauyin da ke kansa cikin nasara da gaskiya.

A yau mutane da dama na amfani da kalmar:"Zamanin ya canza" a matsayin garkuwa don ɓoye rashin kunya, rashin tarbiyya, d...
05/07/2025

A yau mutane da dama na amfani da kalmar:
"Zamanin ya canza" a matsayin garkuwa don ɓoye rashin kunya, rashin tarbiyya, da watsi da kyawawan dabi’u.

Amma fa gaskiyar tambaya ita ce:
Shin zamanin ne ya lalace, ko halin mutane ne s**a lalata zamanin?

Faɗi gaskiyar ra’ayinka a comment👇

Gwamnatin Shugaba Tinubu Na Tattaunawa Kan Dawo Da Tallafin Mai Gwamnatin tarayya karkashin shugaba Bola Ahmed Tinubu na...
04/07/2025

Gwamnatin Shugaba Tinubu Na Tattaunawa Kan Dawo Da Tallafin Mai

Gwamnatin tarayya karkashin shugaba Bola Ahmed Tinubu na duba yiwuwar dawo da tallafin mai ko kuma duba hanyoyin da za su saukaka farashin man fetur a kasar nan.

Rahotanni sun bayyana cewa gwamnati ta fara tuntubar masana da masu ruwa da tsaki a harkar albarkatun mai domin gano mafita mai dorewa ga wahalhalun da 'yan kasa ke fuskanta sakamakon tsadar man fetur.

Wani jami’in gwamnati ya tabbatar da cewa “ba lallai a kira shi dawo da tallafi kai tsaye ba, amma ana nazarin yadda za a rage wa talaka raɗaɗin hauhawar farashin mai”.

Kamar yadda kowa ya sani, cire tallafin mai a shekarar 2023 ya haifar da karin farashi a kowane sashe na rayuwa – daga sufuri zuwa abinci. Wannan ne yasa gwamnatin ke kokarin yin gyara don rage wa jama’a nauyi.

📌 Me kuke tunani?
Dawo da tallafi, ko a nemo wata dabara da zata rage farashi?

MUTANEN AREWA MASU ABIN MAMAKIA daidai lokacin da rayukan 'yan Arewa suke salwanta a wasu jihohin Arewa irinsu Sokoto, K...
04/07/2025

MUTANEN AREWA MASU ABIN MAMAKI

A daidai lokacin da rayukan 'yan Arewa suke salwanta a wasu jihohin Arewa irinsu Sokoto, Katsina, Zamfara da Borno wanda ya kamata muyi ta yayatawa domin a dauki mataki..

Amma sam wannan bai damemu ba, abinda muka mayar da hankali a daidai wannan lokaci da jinanen 'yar Arewa suke kwarara shine musu da jayayya akan cewa tsakanin motar Mawaki Rarara da ta Naziru Sarkin waka wacce ta fi tsada?

Ance wai Naziru ya sayi mota ta sama da kudi Naira Miliyan dari biyar, akace wai ta fi motar Rarara tsada, akan wannan ake ta musu da jayayya har ya zama abin trending a Facebook

Ni banga wani abin burgewa anan ba, idan motar Naziru ta fi na Rarara tsada to sai me?, abin da ya kamata ayi musu ma a kai shine tsakanin Mawaki Rarara da Naziru Sarkin Waka wa yafi amfani da damarsa wajen taimakon talakawa?

Inda zamu sa su a mizani na adalci Rarara ya fi naziru amfanar da al'ummah, a yanzu bani da wata alaka da Rarara, kuma bana ra'ayin siyasarsa, na taba alaka dashi farkon lokacin da ya fara yiwa Buhari waka a 2015, har ma ya nemi nambar wayata yake kirana mu gaisa a wancan lokaci

Lokacin da ya kirkiri wani website da yake tura wakokinsa ni ya fara yiwa magana domin na tallata masa a Facebook, kuma haka akayi na tallata a wancan lokaci, duk da ni bana ra'ayin wakoki da kide-kide irin na zamanin mu, amma saboda soyayyar Buhari na tallata masa

A yanzu ina ganin yadda Rarara yake fitar da kudade ya sayi abinci masu yawa ya raba wa bayin Allah kyauta, abinda ban taba gani Naziru Sarkin waka yayi ba kenan, gaskiya ko kusa ba za'a kwatanta kirkin Rarara da na Naziru ba, Rarara ya fishi kyauta da tallafawa mabukata nesa ba kusa

A yanzu ma nayi wannan tsokacin ne saboda ina free babu wani update mai ma'ana da zanyi, mu dawo kan matsalolin da s**a addabemu a Arewa don Allah

Ubangiji Allah Ka yaye mana matsalolin da suke addabarmu a Arewa

Datti Assalafiy

Address

Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Funtua Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Funtua Post:

Share