23/08/2026
Kungiyar Wazobiya Youth Progressive Forum Ta Kaddamar da Sabbin Shugabanninta a Funtua
A ranar Lahadi, 23 ga Agusta, 2026, kungiyar Wazobiya Youth Progressive Forum ta gudanar da babban taro tare da kaddamar da shugabanninta na reshen Ƙaramar Hukumar Funtua, ƙarƙashin jagorancin Ishaq El-Yakub.
An gudanar da taron ne a harabar Tudun Wada Primary School, Funtua, inda matasa da manyan baki daga kabilu da harsuna daban-daban s**a halarta.
Manufar kafa kungiyar, a cewar wadanda s**a shirya taron, ita ce ƙarfafa haɗin kai tsakanin matasa, samar da zaman lafiya da fahimtar juna, tare da haɗa kan al’ummomi daban-daban da ke zaune a Ƙaramar Hukumar Funtua, ciki har da Hausawa, Yarabawa, Inyamurai da Fulani — wato WAZOBIYA.
Da yake jawabi a wajen taron, Majin Garin Funtua, Alhaji Nuhu Aliyu, ya fara da godiya ga Allah, sannan ya bayyana cewa kafa irin wannan kungiya babban alheri ne.
Ya yaba da matakin da matasan s**a ɗauka, tare da ba da shawarwari kan yadda kungiyar za ta ci gaba da samun nasara. Ya ce daya daga cikin abubuwan da ke kawo cikas ga ci gaban al’umma a wannan zamani shi ne son kai, yana mai jaddada cewa matasa su ne ginshiƙin al’umma.
Ya yi kira ga matasa da su ci gaba da irin wannan ƙoƙari na haɗa kan jama’a, sannan ya tabbatar da cewa ƙofarsa a bude take ga kungiyar a duk lokacin da suke buƙatar shawarwari ko taimako.
Shi ma Dokajin Funtua ya gode wa Allah, sannan ya yi kira ga mahalarta taron da su kasance masu girmama lokaci.
Ya bayyana cewa Allah ne Ya halicci dukkan mutane, kuma da Ya so, da Ya halicci mutane gaba ɗaya a kan kabila ɗaya da addini ɗaya. Sai dai hikimar Allah ta sa aka samu al’ummomi da kabilu daban-daban.
Ya ce kasancewar kungiyar ta ƙunshi matasa daga kabilu da harsuna daban-daban abin alfahari ne, tare da addu’ar Allah Ya ƙara haɗa kan al’umma.
Tsohon ES na Ƙaramar Hukumar Funtua ya bayyana cewa kowace kungiya tana buƙatar mambobinta su kasance masu ƙoƙarin raya ta da kansu domin samun ci gaba mai ɗorewa.
Shi ma Salisu Fa’ida ya nuna godiyarsa ga Allah, tare da bayyana muhimmancin irin wannan haɗin kai da ake samu tsakanin matasa.
Ya yaba da ƙoƙarin kungiyar wajen haɗa kan matasa daga kabilu da harsuna daban-daban, yana mai cewa irin wannan haɗin kai na da matuƙar muhimmanci wajen samar da zaman lafiya da ci gaban al’umma.
A nasa jawabin, Dr. Nura ya bayyana cewa kafa kungiyar Wazobiya mataki ne mai kyau wajen ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kai a tsakanin al’ummar Funtua.
Ya yi kira ga al’umma da masu ruwa da tsaki da su riƙa tallafa wa kungiyar domin ta samu damar cimma manufofin da aka kafa ta a kansu.
Sarkin Matasan Funtua, Malam Babawo, wanda shi ne wanda ya kafa kungiyar, ya gode wa Allah bisa wannan nasara da aka samu.
Ya bayyana cewa nasarar da kungiyar ta samu ba tasa kaɗai ba ce, sai dai sakamakon gudunmawa, shawarwari da goyon bayan da ya samu daga manya da sauran masu ruwa da tsaki.
Shugabar bangaren mata ta kungiyar ta gode wa Allah, sannan ta bayyana cewa kafa Wazobiya Youth Progressive Forum ya ƙara samar da wata kafa ta haɗa kan al’ummomi daban-daban da ke zaune a Ƙaramar Hukumar Funtua.
Ta ce hakan ne ya sa aka sanya wa kungiyar suna WAZOBIYA, domin ya zama alamar haɗin kan al’ummomi da kabilu daban-daban.
Wasu daga cikin mahalarta taron sun tofa albarkacin bakinsu cikin harsuna daban-daban, inda s**a bayyana farin cikinsu da kafa kungiyar.
Sun ce irin wannan kungiya za ta taimaka wajen ƙara fahimtar juna, haɗin kai da zaman lafiya tsakanin matasa da sauran al’ummomin da ke zaune a Ƙaramar Hukumar Funtua.
Taron ya samu halartar manyan baki, matasa da wakilan al’ummomi daga kabilu da harsuna daban-daban da s**a haɗu ƙarƙashin Wazobiya Youth Progressive Forum, domin ƙarfafa zumunci, haɗin kai da zaman lafiya a tsakanin al’umma.