Funtua Online Media Reporters

Funtua Online Media Reporters Funtua Online Media Reporters..Call 08029225724 for advertisement, Ceremonies and more.

23/08/2026

To Fa! "Mai Girma Gwamna Kana Abin da Ya Dace, Amma Shugabannin Kananan Hukumomi Suna Bata Abin”

'Mai girma Gwamna, kana abin da ya dace, amma shugabannin ƙananan hukumomi na ɓata abin, sannan kansilolinka ɗauki-ɗaura ne. Jeka ka duba inda kansilolin na gaskiya suke, irin waɗanda ake zaɓa da kuri’a. Da yanzu sun cire shugabannin ƙananan hukumomi...”

— Inji Hon. Sanusi Aliyu Waziri.

Kungiyar Wazobiya Youth Progressive Forum Ta Kaddamar da Sabbin Shugabanninta a FuntuaA ranar Lahadi, 23 ga Agusta, 2026...
23/08/2026

Kungiyar Wazobiya Youth Progressive Forum Ta Kaddamar da Sabbin Shugabanninta a Funtua

A ranar Lahadi, 23 ga Agusta, 2026, kungiyar Wazobiya Youth Progressive Forum ta gudanar da babban taro tare da kaddamar da shugabanninta na reshen Ƙaramar Hukumar Funtua, ƙarƙashin jagorancin Ishaq El-Yakub.

An gudanar da taron ne a harabar Tudun Wada Primary School, Funtua, inda matasa da manyan baki daga kabilu da harsuna daban-daban s**a halarta.

Manufar kafa kungiyar, a cewar wadanda s**a shirya taron, ita ce ƙarfafa haɗin kai tsakanin matasa, samar da zaman lafiya da fahimtar juna, tare da haɗa kan al’ummomi daban-daban da ke zaune a Ƙaramar Hukumar Funtua, ciki har da Hausawa, Yarabawa, Inyamurai da Fulani — wato WAZOBIYA.

Da yake jawabi a wajen taron, Majin Garin Funtua, Alhaji Nuhu Aliyu, ya fara da godiya ga Allah, sannan ya bayyana cewa kafa irin wannan kungiya babban alheri ne.

Ya yaba da matakin da matasan s**a ɗauka, tare da ba da shawarwari kan yadda kungiyar za ta ci gaba da samun nasara. Ya ce daya daga cikin abubuwan da ke kawo cikas ga ci gaban al’umma a wannan zamani shi ne son kai, yana mai jaddada cewa matasa su ne ginshiƙin al’umma.

Ya yi kira ga matasa da su ci gaba da irin wannan ƙoƙari na haɗa kan jama’a, sannan ya tabbatar da cewa ƙofarsa a bude take ga kungiyar a duk lokacin da suke buƙatar shawarwari ko taimako.

Shi ma Dokajin Funtua ya gode wa Allah, sannan ya yi kira ga mahalarta taron da su kasance masu girmama lokaci.

Ya bayyana cewa Allah ne Ya halicci dukkan mutane, kuma da Ya so, da Ya halicci mutane gaba ɗaya a kan kabila ɗaya da addini ɗaya. Sai dai hikimar Allah ta sa aka samu al’ummomi da kabilu daban-daban.

Ya ce kasancewar kungiyar ta ƙunshi matasa daga kabilu da harsuna daban-daban abin alfahari ne, tare da addu’ar Allah Ya ƙara haɗa kan al’umma.

Tsohon ES na Ƙaramar Hukumar Funtua ya bayyana cewa kowace kungiya tana buƙatar mambobinta su kasance masu ƙoƙarin raya ta da kansu domin samun ci gaba mai ɗorewa.

Shi ma Salisu Fa’ida ya nuna godiyarsa ga Allah, tare da bayyana muhimmancin irin wannan haɗin kai da ake samu tsakanin matasa.

Ya yaba da ƙoƙarin kungiyar wajen haɗa kan matasa daga kabilu da harsuna daban-daban, yana mai cewa irin wannan haɗin kai na da matuƙar muhimmanci wajen samar da zaman lafiya da ci gaban al’umma.

A nasa jawabin, Dr. Nura ya bayyana cewa kafa kungiyar Wazobiya mataki ne mai kyau wajen ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kai a tsakanin al’ummar Funtua.

Ya yi kira ga al’umma da masu ruwa da tsaki da su riƙa tallafa wa kungiyar domin ta samu damar cimma manufofin da aka kafa ta a kansu.

Sarkin Matasan Funtua, Malam Babawo, wanda shi ne wanda ya kafa kungiyar, ya gode wa Allah bisa wannan nasara da aka samu.

Ya bayyana cewa nasarar da kungiyar ta samu ba tasa kaɗai ba ce, sai dai sakamakon gudunmawa, shawarwari da goyon bayan da ya samu daga manya da sauran masu ruwa da tsaki.

Shugabar bangaren mata ta kungiyar ta gode wa Allah, sannan ta bayyana cewa kafa Wazobiya Youth Progressive Forum ya ƙara samar da wata kafa ta haɗa kan al’ummomi daban-daban da ke zaune a Ƙaramar Hukumar Funtua.

Ta ce hakan ne ya sa aka sanya wa kungiyar suna WAZOBIYA, domin ya zama alamar haɗin kan al’ummomi da kabilu daban-daban.

Wasu daga cikin mahalarta taron sun tofa albarkacin bakinsu cikin harsuna daban-daban, inda s**a bayyana farin cikinsu da kafa kungiyar.

Sun ce irin wannan kungiya za ta taimaka wajen ƙara fahimtar juna, haɗin kai da zaman lafiya tsakanin matasa da sauran al’ummomin da ke zaune a Ƙaramar Hukumar Funtua.

Taron ya samu halartar manyan baki, matasa da wakilan al’ummomi daga kabilu da harsuna daban-daban da s**a haɗu ƙarƙashin Wazobiya Youth Progressive Forum, domin ƙarfafa zumunci, haɗin kai da zaman lafiya a tsakanin al’umma.

Shuwagabannin Akwatinan Zaɓe na Unguwar Ibrahim dake cikin Karamar Hukumar Funtua, Sun Koka Kan Rashin Kulawa da Su a AP...
23/08/2026

Shuwagabannin Akwatinan Zaɓe na Unguwar Ibrahim dake cikin Karamar Hukumar Funtua, Sun Koka Kan Rashin Kulawa da Su a APC

“Sai wahala ta zo ake neman mu, amma da samu ya zo sai a guje mu” — Inji Shuwagabannin Akwatinan Unguwar Ibrahim

Shuwagabannin Akwatinan Zaɓe na Unguwar Ibrahim sun koka kan yadda s**a ce ake nuna musu ƙyama da rashin kulawa a cikin harkokin Jam’iyyar APC, musamman wajen cin moriyar dimokuraɗiyya da ayyukan jam’iyyar.

A ranar Lahadi, 23 ga watan Agusta, 2026, Shuwagabannin Akwatinan Zaɓe na Unguwar Ibrahim sun gudanar da wani taro domin bayyana damuwarsu kan yadda ake nuna rashin kulawa da su, duk da irin gudunmawar da suke bayarwa wajen tafiyar da harkokin jam’iyyar a matakin ƙasa.

Mahartan taron sun bayyana cewa, “Sai wahala ta zo ake neman mu, amma da samu ya zo sai a guje mu.” Sun ce abin takaici ne yadda wasu daga cikin waɗanda ke da mukamai a yankin ba sa bayar da isasshen tallafi ga al’umma.

Sun bayyana cewa daga cikin mutanen da suke ganin suna taimakawa al’umma akwai Alh. Lawal Abbas, Alh. Aminiu Isyaku da Hon. Aminu Halilu, inda s**a ce ban da irin wannan gudunmawar da wasu daga cikinsu ke bayarwa, ba a ganin isasshen tallafi ga al’umma daga sauran masu ruwa da tsaki.

Shuwagabannin sun kuma bayyana damuwarsu kan yadda Unguwar Ibrahim ke da zaɓaɓɓen Kansila da Supervisory Councillor, amma s**a ce suna ganin ba a yin abubuwan da s**a dace wajen tallafa wa al’umma da kuma mutanen da ke aiki tukuru domin ci gaban jam’iyyar.

Sun jaddada cewa su ‘yan Jam’iyyar APC ne kuma suna da aniyar ci gaba da mara wa jam’iyyar baya a zaɓen 2027, amma s**a yi kira ga shugabannin jam’iyyar da masu ruwa da tsaki da su dinga kula da su tare da tabbatar da cewa ana bai wa ‘yan kwamitin akwatin zaɓe muhimmiyar kulawar da ta dace.

A gefe guda, sun yaba wa Gwamnatin Jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Malam Dr. Dikko Umar Radda, PhD, bisa ƙoƙarin da take yi wajen kawo ayyukan ci gaba da inganta rayuwar al’umma.

Taron ya samu jagorancin:

Chairman: Malam Abdulgafar Suleiman
Secretary: Abubakar Ahmad
P.R.O: Sagir Danjuma (CK)

LABARI CIKIN HOTUNAYadda Aka Gudanar da Zagayen Gari na Maulidin Fiyayyen Halitta, Annabi Muhammad ﷺ, a Ƙaramar Hukumar ...
23/08/2026

LABARI CIKIN HOTUNA

Yadda Aka Gudanar da Zagayen Gari na Maulidin Fiyayyen Halitta, Annabi Muhammad ﷺ, a Ƙaramar Hukumar Funtua

An gudanar da zagayen gari na Maulidin Fiyayyen Halitta, Shugabanmu Annabi Muhammad ﷺ, a Ƙaramar Hukumar Funtua, inda al’umma s**a fito domin tunawa da ranar haihuwar Manzon Allah ﷺ tare da nuna ƙauna da girmamawa gare shi.

An gudanar da zagayen cikin yanayi na nishaɗi da salati, inda mahalarta s**a ci gaba da karanta salati da yabo ga Manzon Allah ﷺ.

Ya Allah, Ka ƙara mana ƙaunar Manzon Allah ﷺ, Ka sanya mu cikin masu bin Sunnarsa.

🤲 Jama'a, mu yi wa Annabi Muhammad ﷺ salati.

Allahumma Salli Ala Sayyidina Muhammadin Wa Ala Alihi Wa Sahbihi Wasallam.

Funtua Online Media Reporters

Gwamna Radda Ya karbi Nadin da Aka Yi Masa a Matsayin Mai Gudanar da Yaƙin Neman Zaɓen Shugaba Tinubu a KatsinaGwamnan J...
23/08/2026

Gwamna Radda Ya karbi Nadin da Aka Yi Masa a Matsayin Mai Gudanar da Yaƙin Neman Zaɓen Shugaba Tinubu a Katsina

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya bayyana farin cikinsa tare da karɓar nadin da aka yi masa a matsayin Mai Gudanar da Ayyukan Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Shugaban Ƙasa na Jam’iyyar APC a Jihar Katsina, domin sake zaɓen Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Gwamna Radda, wanda shi ma ke neman sake zaɓe a matsayin Gwamnan Jihar Katsina, ya tabbatar wa Shugaban Ƙasa da shugabannin Jam’iyyar APC cewa a shirye yake ya jagoranci yaƙin neman zaɓe mai ƙarfi, ingantacce kuma wanda zai haɗa kowa da kowa a faɗin jihar.

Ya ce babban abin da zai fi mayar da hankali a kai shi ne haɗa kan ‘yan jam’iyya, masu ruwa da tsaki, shugabannin al’umma, matasa, mata da sauran magoya baya a cikin ƙananan hukumomi da rumfunan zaɓe 361 na Jihar Katsina, domin ƙara ƙarfafa goyon bayan Shugaba Tinubu a zaɓen da ke tafe.

Gwamnan ya nuna godiyarsa ga Shugaba Tinubu da shugabancin ƙasa na Jam’iyyar APC bisa amincewar da s**a yi da shi. Ya kuma yaba da yadda aka haɗa wasu ‘yan asalin Jihar Katsina cikin Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Shugaban Ƙasa, yana mai cewa jihar tana da kyakkyawan tarihi na samar da ƙwararrun mutane waɗanda ke taka muhimmiyar rawa a ayyukan jiha da na ƙasa.

Gwamna Radda ya bayyana kwarin gwiwarsa cewa ƙwarewa, kishin ƙasa da jajircewar ‘yan Katsina da aka sanya cikin kwamitin za su ƙara wa ƙoƙarin jam’iyyar ƙarfi, tare da taimakawa wajen cimma nasarar da ake fata ga Shugaba Tinubu da Jam’iyyar APC.

Saboda haka, ya buƙaci mambobin Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Shugaban Ƙasa daga Jihar Katsina, shugabannin jam’iyya da sauran masu ruwa da tsaki na APC a faɗin rumfunan zaɓe 361 da su ƙara kaimi wajen gudanar da ayyukansu tare da fara ƙarfafa tsarin tuntuɓar jama’a da haɗa kan magoya baya tun kafin lokacin zaɓe.

Gwamna Radda ya ce:

“Mun nuna ƙarfimmu da jajircewarmu ga Jam’iyyar APC a shekarar 2023. Wannan wata dama ce gare mu da za mu ƙara himma, mu kasance cikin haɗin kai, sannan mu tattara jama’armu domin sake zaɓen Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

“Mun shirya tsaf domin wannan aiki, kuma Jihar Katsina za ta taka cikakkiyar rawarta wajen tabbatar da nasarar Shugaban Ƙasa da kuma babbar jam’iyyarmu ta APC.”

23/08/2026

Kai tsaye daga wajen taron kungiyar wakilan akwatin zaɓe na jam'iyyar apc na Unguwar Ibrahim ward Funtua .

23/08/2026
Ministan Gidaje Eng. Muttaqa Rabe Darma ya bayyana cewa duk wani ɗan Siyasa a Jam'iyyar APC, to Gwamnan Katsina Dikko Ra...
23/08/2026

Ministan Gidaje Eng. Muttaqa Rabe Darma ya bayyana cewa duk wani ɗan Siyasa a Jam'iyyar APC, to Gwamnan Katsina Dikko Radda ne Jagoran Siyasar shi a Jihar.

Darma ya bayyana haka a hirarsa da DCL Hausa, bayan jita-jitar da ake yaɗawa game da tsamin dangantaka tsakanin Gwamnan jihar Katsina Dr Dikko Radda da Ibrahim Masari.

Da ake tambayarsa waye Jagoran Siyasar shi a Katsina, Darma ya ce “Ba Ni ba, shi kan shi Ibrahim Masarin Dikko Radda ne Jagoran Siyasar shi a jihar Katsina ” Inji shi¹

23/08/2026

With Jamilu Rabe Dan Amana – I just got recognised as one of their top fans! 🎉

Address

Funtua
MAKERAROADFUNTUA

Telephone

+2348029225724

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Funtua Online Media Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Funtua Online Media Reporters:

Shortcuts

Share