Funtua Online Media Reporters

Funtua Online Media Reporters Funtua Online Media Reporters..Call 08029225724 for advertisement, Ceremonies and more.

Kungiyar MTK Ta Raba Tallafin Abinci Ga Marasa Lafiya a Asibitin Dan Dutse Funtua.A ranar Asabar 28/6/2025.kungiyar jin ...
03/07/2025

Kungiyar MTK Ta Raba Tallafin Abinci Ga Marasa Lafiya a Asibitin Dan Dutse Funtua.

A ranar Asabar 28/6/2025.
kungiyar jin kai mai zaman kanta Mutaimaki Kanmu Da Kanmu Support Organization (M T K) ta gudanar da rabon abinci ga marasa lafiya a Asibitin Dan Dutse, dake cikin karamar hukumar Funtua Jihar Katsina.

A cewar shugaban kungiyar, Malam Mustapha Abdul wanda kuma shine shugaban gidauniyar Arbyan Charitable Foundation wannan tallafi na daga cikin shirin kungiyar na rage radadin rayuwa ga marasa galihu, musamman masu fama da cututtuka a cibiyoyin lafiya.

Mun zo nan domin mu nuna cewa muna tare da jama'a musamman wadanda ke cikin mawuyacin hali a Asibitoci. Wannan tallafi wani bangare ne na aikace-aikacen jin kai da muke gudanarwa a fadin jihar Katsina," in ji Mustapha Abdul yayin rabon abincin.

Tallafin ya ƙunshi kayayyakin abinci da aka raba kai tsaye ga marasa lafiya da ke kwance a asibitin lamarin da ya haifar da farin ciki da godiya daga bakin iyalai da jami'an lafiya.

Wannan dai ba shi ne karo na farko da kungiyar M T K ke irin wannan aiki ba. Kungiyar na da tarihin gudanar da ayyukan jin kai a fannoni da dama, ciki har da ilimi, lafiya, da rage talauci, musamman a yankin Funtua da sauran sassan jihar Katsina.

Yan Takarar Shugabancin N U T Funtua Sun Kai Ziyarar Neman Goyon Baya.Tawagar Yan takarar shugabancin kungiyar Malamai t...
24/06/2025

Yan Takarar Shugabancin N U T Funtua Sun Kai Ziyarar Neman Goyon Baya.

Tawagar Yan takarar shugabancin kungiyar Malamai ta Najeriya (NUT) reshen Karamar Hukumar Funtua karkashin Jagorancin Comrade Yahaya Yarima sun kai ziyarar neman goyon baya da addu’o’i ga manyan jami’an ilimi da kuma Fadar Mai Martaba Sarkin Maska Hakimin Funtua.

Ziyarar ta gudana cikin natsuwa da kwanciyar hankali inda tawagar ta bayyana manufofinta na samar da sabuwar tafiya mai inganci a harkokin kungiyar N U T da kuma bunkasa ilimi.

Tawagar ta fara da kai ziyara ofishin Mukaddashiyar Sakatariyar Ilimi ta Funtua Hajiya Maryam Babajo inda s**a gabatar da takaitaccen bayani kan burinsu da tsare-tsarensu na gina sabuwar kungiyar da ke kishin Malamai da ci gaban ilimi.

Daga nan s**a ci gaba da kai ziyara ga wasu manayan jami’an hukumar ilimi da s**a hada da:

Malam Lawal Aliyu Dan Mairo Babban Jami’in Ma’aikata (PPO)
Malam Tijjani Daraktan Tsare-tsare, Bincike da Kididdiga (PRS).
Malam Sani Abdulhamid Jami’in Fasaha.
Alhaji Babangida Ma’aikacin Sashen Kudi.
Daraktan Tabbataccen Ingancin Koyo (Zonal Quality Assurance), Funtua.

Haka kuma tawagar ta samu tarba a fadar Mai Martaba Sarkin Maskan Katsina Hakimin Funtua Alhaji Sambo Idriss Sambo A Gidansa dake Funtua inda s**a gaishe shi sannan s**a nemi addu’ar Sanya albarka daga masarauta domin samun nasara a zaben da ke tafe.

Jerin Yan Takarar da Mukaman da Suke Nema:

1 Comr. Abdulkadir Ahmad A-K A Matsayin Chairman
2 Comr. Usman Mansir Deputy Chairman
3 Comr. Abubakar Yakubu Vice Chairman
4 Comr. Abdulkadir Salisu Jerry Vice Chairman III
5 Malam Saidu Secretary General
6 Mal. Isah Abdullahi Treasurer
7 Comr. Abubakar Sanusi Umar – Assistant Secretary General
8 Comr. Saleh Lawal – Public Relations Officer
9 Malam Nura Hashimu Financial Secretary
10 Jamilu Abashe – Auditor I
11 Comr. Yusuf Hamza Auditor Il
12 Comr. Sa’adatu Abdulkadir Welfare Officer

A jawabin karshe, Comrade Yahaya Yarima ya gode wa shugabannin da s**a karbe hannu bibbiyu.

TEAM YARIMA/AK FOR N U T CHAIRMAN FUNTUA BRANCHE.Tasamu Zaman Tattaunawa da  Yan Takarkarinta a Ranar 22/06/2025. karkas...
23/06/2025

TEAM YARIMA/AK FOR N U T CHAIRMAN FUNTUA BRANCHE.

Tasamu Zaman Tattaunawa da Yan Takarkarinta a Ranar 22/06/2025.

karkashin Jagorancin YAHAYA YARIMA DAN TAKARAR CHAIRMAN FOR N U T FUNTUA BRANCH ABDULKADIR AHMAD AK.

Kungiyar Hasken Katsina Ta Kai Ziyarar Girmamawa da Barka da Sallah Ga Dattawan Jihar KatsinaShugaban Kungiyar Hasken Ka...
13/06/2025

Kungiyar Hasken Katsina Ta Kai Ziyarar Girmamawa da Barka da Sallah Ga Dattawan Jihar Katsina

Shugaban Kungiyar Hasken Katsina (Katsina Light Project), Comrade Injiniya Musa Abdullahi tare da tawagarsa, sun kai ziyarar girmamawar Barka da Sallah ga wasu daga cikin fitattun dattawan jihar Katsina da ake kallonsu a matsayin iyayen kungiyar.

Wadanda aka kai wa ziyarar sun hada da:

1 Ubankasa Hakimin Dutsinma, Alhaji Dr. Sada Balan Gwaggo (Sada Yandaka Katsina)

2 Alhaji Tukur Ahmad Jikamshi, tsohon mataimakin gwamnan jihar Katsina

3 Alhaji Muttaqa Badaru Jikamshi, shugaban rukunin kamfanonin Hill Side Investment

A yayin ziyarar, Comrade Musa ya jaddada goyon bayan kungiyar ga ci gaban da Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda, PhD, ke samarwa a cikin shekaru biyu da s**a wuce. Haka kuma, ya bayyana kudirin kungiyar na ci gaba da wayar da kan al'umma kan manufofin gwamnatin jihar.

Mutane da dama da s**a halarci ziyarar sun bayyana ra’ayoyinsu, inda s**a yaba da irin aikin da kungiyar ke yi, tare da nuna goyon bayansu ga fadada ayyukanta a fadin jihar Katsina.

An kammala ziyarar da addu’o’i na musamman domin samun zaman lafiya a jihar Katsina, da kuma fatan alheri ga Gwamna Dikko Radda bisa jagorancinsa da yake wa jihar.

Kungiyar El-Arabian Charitable Foundation Ta Kai Ziyarar Girmamawa da Barka da Sallah a FuntuaShugaban kungiyar El-Arabi...
13/06/2025

Kungiyar El-Arabian Charitable Foundation Ta Kai Ziyarar Girmamawa da Barka da Sallah a Funtua

Shugaban kungiyar El-Arabian Charitable Foundation, Muhammad Mustapha Abdu, tare da wasu daga cikin wakilan kungiyar, sun kai ziyarar girmamawa da barka da Sallah ga wasu daga cikin fitattun dattawan Karamar Hukumar Funtua da ke jihar Katsina.

Ziyarar ta gudana cikin yanayi na girmamawa da nuna kyakkyawar alaka tsakanin kungiyar da al’ummar yankin, kuma na daga cikin ayyukan da kungiyar ke aiwatarwa domin karfafa zumunci da sada zumunta da manyan mutane a sassa daban-daban na kasa.

Daga cikin wadanda aka kai wa ziyara sun hada da, Mai girma Sarkin Maska, Alhaji Sambo Idris Sambo, Alhaji Ladan Mati Bamba, Alhaji Tukur Ahmad Jikamshi, tsohon mataimakin gwamnan jihar Katsina.

A yayin ziyarar, shugaban kungiyar ya bayyana cewa manufar wannan ziyara ita ce “karfafa alaka ta zumunci, girmama dattawan yankin da kuma mika sakon fatan alheri a wannan lokaci na bukukuwan Sallah.”

Daya daga cikin dattawan da aka ziyarta ya bayyana jin dadinsa bisa wannan ziyara, yana mai cewa irin wannan mataki yana kara dankon zumunci da hadin kai a tsakanin al’umma.

Kungiyar El Arabian Charitable Foundation ta kaddamar da bada tallafin kudi ga marasa Lafiya a cikin General Hospital da...
21/05/2025

Kungiyar El Arabian Charitable Foundation ta kaddamar da bada tallafin kudi ga marasa Lafiya a cikin General Hospital dake cikin Karamar Hukumar Funtua.

An kaddamar da bada tallafin kudi ga marasa Lafiya dake cikin General Hospital a cikin Karamar Hukumar Funtua Karkashin Jagorancin Shugaban Kungiyar Muhammad Mustapha Abdul.

A kalla Mutane 300 ne s**a amfana da tallafin kudi na Naira 5000 Wanda Kungiyar El Arabian Charitable Foundation ta bada sannan Kungiyar ta Kara da tallafawa marasa karfi da kudi don siyan Magani.

An kaddamar da bada tallafin kudi ne a Ranar Laraba 21/5/2025.

15/05/2025
Labari Cikin Hotuna Yadda Permanent member na hukumar ilimin bai daya Hon Rabi'u Idris dashi da quality assurance ta fun...
15/05/2025

Labari Cikin Hotuna
Yadda Permanent member na hukumar ilimin bai daya Hon Rabi'u Idris dashi da quality assurance ta funtua Local Government s**a kai ziyarar wani aiki.1q

Wasu Daga cikin yan Media  na Funtua tare Da hadin guiwa da wasu daga cikin mutanen gidan Hon Abdullahi Goya Zaɓaɓɓen ch...
10/05/2025

Wasu Daga cikin yan Media na Funtua tare Da hadin guiwa da wasu daga cikin mutanen gidan Hon Abdullahi Goya Zaɓaɓɓen chairman Na funtua Local government. Sun zo gaida Hon kamal Alti Dan-Malam (Wakilin matasan funtua)

Wasu Daga Cikin yan Media na Funtua tare da hadin gwiwa da wasu daga cikin mutanen Hon Abdullahi Goya Zaɓaɓɓen Chairman na Funtua local Government sun zo gaida Hon Kamal Alti dan Malam.

Bayan duba lafiyar sa shine s**ayi kira da ya kara fitowa Takarar Da Majalisar Jiha A karo Na 3 kamar yanda yayi A shekarar 2019 2023. Duba da yanda yake samun nasara.

Bayan nan sunyi mashi addua tare da fatan wannan tafiya ta zamanto anyi ta cikin Sa'a da Nasara

Sun kara da mashi addu'ar Allah ya bashi lafiya.

07/05/2025
07/05/2025

Elder Alh Mati Bamma Funtua tattaunawar shi da Funtua Online Media Reporters akan siyasar Funtua local Government.

Address

Funtua

Telephone

+2348029225724

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Funtua Online Media Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Funtua Online Media Reporters:

Share