Karaduwa Post

Karaduwa Post Domin Samun Labaran Duniya Gamida Nishadantar Ba Tareda Chin Mutumchi Kowa Ba.

DA DUMI-DUMI: Gwamna Dikko Raɗɗa Ya Karɓi Jiga-Jigan Jam'iyyar PDP Waɗanda S**a Sauya Sheka Zuwa Jam'iyyar APC A Kananan...
26/09/2025

DA DUMI-DUMI: Gwamna Dikko Raɗɗa Ya Karɓi Jiga-Jigan Jam'iyyar PDP Waɗanda S**a Sauya Sheka Zuwa Jam'iyyar APC A Kananan hukumomi Funtua Da Bakori Karkashin Sanata Muntari Dandutse.

Mai girma gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umar Raɗɗa PhD. CON. Ya karɓi jiga-jigan jam'iyyar adawa ta PDP waɗanda s**a sauya sheka zuwa jam'iyyar APC a kananan hukumomin Funtua da Bakori karkashin jagorancin dan majalisar dattijan tarayyar Nijeriya mai wakiltar shiyyar Funtua Sanata Muntari Mohammed Dandutse, Taron da ya gudana a dakin taro na gidan gwamnatin jihar a ranar Juma'a 26/09/2025

A jawabin mai girma Gwamnan Malam Dikko Umar Raɗda, yayi godiya ga jagororan da s**ayi wannan aiki domin ganin an kawo sauyi da cigaba musamman sanata Muntari Dandutse da Hon. Musa Adamu Funtua da sauransu, Ya bayyana wannan a matsayin abin ya kamata kowanne wanda yake da mukami ko matsayi yayi a wannan lokacin,

Daga karshe ya bayyana farin cikinsa matuka ganin yadda aka samu haɗuwar kai tsakanin yan siyasa a kananan hukumomin Funtua da Dandume, dafatan cigaba da samun hadin kai tsakanin junan domin samun makoma ta gari.

Da yake tofa albarkacin bakinsa sanata mai wakiltar shiyyar Sanata Muntari Mohammed Dandutse, ya bayyana yadda wannan shugabanni da s**a shiga a jam'iyyar APC yanzu s**a zama wata katanga mai amfani ga al'umma tun abaya, ya bayyana su matsayin mutane masu mutunci da sanin ya kamata da abinyi waɗanda zasu taimakawa al'umma ba masu roko da banbaɗanci ba, daga karshe yayi fatan sake haɗuwar kawunan al'ummar yanki baki daya.

Taron ya samu halartar shugaban jam'iyyar APC Alhaji sani Muhammad JB Daura, Kwamishina ma'aikatar lafiya Hon. Musa Adamu Funtua Mai baiwa gwamna shawara akan harkokin siyasa Hon. Umar Yau Gwajo-gwajo, Hon. Turaji mai baiwa gwamna shawara akan samar da ayyukanyi Hon. Malam Yau Ahmad Nowa Dandume, Hon. Sani Adamu Funtua, Tsohon ɗan majalisar dokokin Hon. Haruna Goma, da sauran shugaban jam'iyyar APC da na tsohuwar jam'iyyar PDP Kafin su dawo Jam'iyyar APC da sauran jami'an tsaron da yan jarida.

DA DUMI-DUMI: Alamu Sun Nuna wa, Shuwaganni Duniya Na fushi da Shugaban ƙasar Isr@'ila.Hotunan sun nuna Firayim Ministan...
26/09/2025

DA DUMI-DUMI: Alamu Sun Nuna wa, Shuwaganni Duniya Na fushi da Shugaban ƙasar Isr@'ila.

Hotunan sun nuna Firayim Ministan Isr@’ila, Benjamin Netanyahu, yana jawabi a gaban ɗakin taro kusan babu kowa bayan yawancin ƙasashe sun yi ficewa daga wajen zaman Majalisar Dinkin Duniya a New York, ranar Juma’a.

"Haraji Ba Azabtarwa Ba Ne, Garkuwar Cigaban Ƙasa Ne Mai Ƙarfi – Shugaban FIRS Ya Ja Hankalin ’Yan Najeriya"Shugaban Huk...
26/09/2025

"Haraji Ba Azabtarwa Ba Ne, Garkuwar Cigaban Ƙasa Ne Mai Ƙarfi – Shugaban FIRS Ya Ja Hankalin ’Yan Najeriya"

Shugaban Hukumar Tara Haraji ta Ƙasa (FIRS) ya yi kira ga ’yan Najeriya da su daina kallon biyan haraji a matsayin wata azabtarwa, yana mai jaddada cewa kuɗaɗen haraji na taka muhimmiyar rawa wajen gina manyan ayyukan raya ƙasa, inganta ilimi da kiwon lafiya, da kuma tallafawa ci gaban tattalin arziki na dogon lokaci.

Ya ce samun kyakkyawar al’adar biyan haraji muhimmin mataki ne wajen inganta cigaban ƙasa da rage dogaro da rancen waje.

~Rariya Online

UNGA 80: Kashim Shettima ya gana da Guterres tare da jaddada neman kujerar dindindin a kwamitin tsaro na MDDMataimakin s...
26/09/2025

UNGA 80: Kashim Shettima ya gana da Guterres tare da jaddada neman kujerar dindindin a kwamitin tsaro na MDD

Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima, ya gana da sakatare janar na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD), António Guterres, a zauren majalisar dake birnin New York, inda batun neman kujerar dindindin a kwamitin tsaro ya kasance kan gaba a tattaunawar.

Ganawar ta gudana ne bayan taron babban zauren Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 80 (UNGA80), inda Shettima ya gabatar da jawabin ƙasa a madadin Shugaba Bola Tinubu.

Shettima ya jaddada bukatar MDD ta ƙara tallafa wa Najeriya don cimma burinta, musamman yadda ƙasar ke sha’awar samun kujerar dindindin a kwamitin tsaro.

Batutuwan da aka tattauna

Ministan harkokin waje, Yusuf Tuggar, ya shaida wa manema labarai cewa an tattauna kan ci gaban da ake son samu wajen aiwatar da muradun ci gaba masu ɗorewa (SDGs), batun sauyin yanayi, da kuma haɗin kai don ƙarfafa dimokuraɗiyya a Najeriya da yankin Afirka.

Ya ce Guterres ya yaba da rawar da Shettima ya taka wajen jaddada bukatar Najeriya ta kujerar dindindin, tare da bayyana irin muhimmancin MDD a Najeriya, kasancewar dama ofisoshi da hukumomin majalisar da dama suna aiki a ƙasar.

Batun fasahar zamani da walwalar jama’a

Ministan sadarwa da kirkire-kirkire, Bosun Tijani, ya bayyana cewa Guterres ya nuna farin ciki da nasarar Najeriya wajen ƙaddamar da samfurin fasahar AI mai harsuna da dama (multilingual AI model) na farko a nahiyar Afirka, wanda gwamnati ta tallafa.

A cewarsa, Guterres ya bukaci Najeriya ta taimaka wa sauran ƙasashen Afirka don kada a bar nahiyar baya a fannin na’urorin fasahar (AI).

A nasa bangaren, Ministan walwala, jin kai da rage talauci, Yusuf Sununu, ya ce Shettima ya bayyana kokarin gwamnatin Tinubu wajen rage talauci da tallafawa jama’a. Ya ce gwamnati na da jadawalin al’umma da ta ƙunshi gidaje miliyan 18.9, inda aka riga aka tallafa wa sama da mutane miliyan 8.1 ta hanyar shirin bayar da kuɗin tallafi.

Sununu ya ce an kuma bayyana damuwa kan raguwar tallafin kuɗi daga wasu ƙungiyoyin MDD, ciki har da shirin WFP wanda ya tallafa wa sama da mutane miliyan 1.3 da kayan abinci.

Tabbacin goyon bayan MDD

Sakataren-janar na MDD ya tabbatar wa Najeriya cewa za ta ci gaba da samun goyon baya wajen ƙara ƙarfin ma’aikatun gwamnati, tabbatar da sahihancin bayanan al’umma, da kuma samun karin tallafi don rage talauci da inganta jin dadin jama’a.

A cewarsa, Guterres ya gode wa Shugaba Bola Tinubu da gwamnatin Najeriya baki ɗaya kan irin haɗin kai da suke bai wa MDD.UNGA 80: Kashim Shettima ya gana da Guterres tare da jaddada neman kujerar dindindin a kwamitin tsaro na MDD

Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima, ya gana da sakatare janar na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD), António Guterres, a zauren majalisar dake birnin New York, inda batun neman kujerar dindindin a kwamitin tsaro ya kasance kan gaba a tattaunawar.

Ganawar ta gudana ne bayan taron babban zauren Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 80 (UNGA80), inda Shettima ya gabatar da jawabin ƙasa a madadin Shugaba Bola Tinubu.

Shettima ya jaddada bukatar MDD ta ƙara tallafa wa Najeriya don cimma burinta, musamman yadda ƙasar ke sha’awar samun kujerar dindindin a kwamitin tsaro.

Batutuwan da aka tattauna

Ministan harkokin waje, Yusuf Tuggar, ya shaida wa manema labarai cewa an tattauna kan ci gaban da ake son samu wajen aiwatar da muradun ci gaba masu ɗorewa (SDGs), batun sauyin yanayi, da kuma haɗin kai don ƙarfafa dimokuraɗiyya a Najeriya da yankin Afirka.

Ya ce Guterres ya yaba da rawar da Shettima ya taka wajen jaddada bukatar Najeriya ta kujerar dindindin, tare da bayyana irin muhimmancin MDD a Najeriya, kasancewar dama ofisoshi da hukumomin majalisar da dama suna aiki a ƙasar.

Batun fasahar zamani da walwalar jama’a

Ministan sadarwa da kirkire-kirkire, Bosun Tijani, ya bayyana cewa Guterres ya nuna farin ciki da nasarar Najeriya wajen ƙaddamar da samfurin fasahar AI mai harsuna da dama (multilingual AI model) na farko a nahiyar Afirka, wanda gwamnati ta tallafa.

A cewarsa, Guterres ya bukaci Najeriya ta taimaka wa sauran ƙasashen Afirka don kada a bar nahiyar baya a fannin na’urorin fasahar (AI).

A nasa bangaren, Ministan walwala, jin kai da rage talauci, Yusuf Sununu, ya ce Shettima ya bayyana kokarin gwamnatin Tinubu wajen rage talauci da tallafawa jama’a. Ya ce gwamnati na da jadawalin al’umma da ta ƙunshi gidaje miliyan 18.9, inda aka riga aka tallafa wa sama da mutane miliyan 8.1 ta hanyar shirin bayar da kuɗin tallafi.

Sununu ya ce an kuma bayyana damuwa kan raguwar tallafin kuɗi daga wasu ƙungiyoyin MDD, ciki har da shirin WFP wanda ya tallafa wa sama da mutane miliyan 1.3 da kayan abinci.

Tabbacin goyon bayan MDD

Sakataren-janar na MDD ya tabbatar wa Najeriya cewa za ta ci gaba da samun goyon baya wajen ƙara ƙarfin ma’aikatun gwamnati, tabbatar da sahihancin bayanan al’umma, da kuma samun karin tallafi don rage talauci da inganta jin dadin jama’a.

A cewarsa, Guterres ya gode wa Shugaba Bola Tinubu da gwamnatin Najeriya baki ɗaya kan irin haɗin kai da suke bai wa MDD.

Hotunan Yadda Shugaban kasar Najeriya Bola Ahmad Tinubu  ya halarci bikin naɗin sabon sarkin Ibadan na 44 wato Olubadan ...
26/09/2025

Hotunan Yadda Shugaban kasar Najeriya Bola Ahmad Tinubu ya halarci bikin naɗin sabon sarkin Ibadan na 44 wato Olubadan Oba Rasheed Ladoja Yau Juma'a

INNALILAHI WA INNA ILAHI RAJI'UUN!Shugaban Karamar Hukumar Kebbe A Jihar Sokoto, Honarabul Abdullahi Yarima Ya Rasu Alla...
26/09/2025

INNALILAHI WA INNA ILAHI RAJI'UUN!

Shugaban Karamar Hukumar Kebbe A Jihar Sokoto, Honarabul Abdullahi Yarima Ya Rasu

Allah ya yi wa shugaban karamar hukumar Kebbe dake jihar Honarabul Abdullahi Yarima rasuwa, yau Juma'a.

Za a gudanar da jana'izarsa a Masallacin Alu Quarters bayan kammala Sallar Juma'a.

Allah ya jikansa da rahama!

Daga: S-bin Abdallah Sokoto

YANZU-YANZU: A karkashin umarnin Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, manyan malamai daga sassa daban-daban na jihar K...
26/09/2025

YANZU-YANZU: A karkashin umarnin Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, manyan malamai daga sassa daban-daban na jihar Kano sun fara halartar zaman Majalisar Shura, domin sauraron korafe-korafen al’ummar Musulmi kan zargin cin zarafin Annabi Muhammadu (SAW) da ake yi wa Malam Lawal Triumph.

Wannan mataki yana cikin kokarin gwamnatin Kano na tabbatar da girmama Addini, kiyaye zaman lafiya da bada dama ga malamai su tattauna cikin hikima da sanin ya kamata.

26/09/2025

KAI TSAYE: 🔴Jawabin Malam Gwamna Dikko Umar Radda Wajen Karbar Waɗanda S**a Canja Sheka Daga Jam'iyyar PDP Zuwa Jam'iyyar APC Daga Kananan Hukumomin Funtua Da Bakori, Karkashin Jagorancin Senator Muntari Dandutse, A Gidan Gwamnatin Jihar Katsina.

26/09/2025

KAI TSAYE: 🔴Wajen Karbar Waɗanda S**a Canja Sheka Daga Jam'iyyar PDP Zuwa Jam'iyyar APC Na Garin Funtua Da Bakori, Karkashin Jagorancin Senator Muntari Dandutse, A Gidan Gwamnatin Jihar Katsina.

26/09/2025

KAI TSAYE: 🔴Wajen Karbar Waɗanda S**a Canja Sheka Daga Jam'iyyar PDP Zuwa Jam'iyyar APC Daga Kananan Hukumomin Funtua Da Bakori, Karkashin Jagorancin Senator Muntari Dandutse, A Gidan Gwamnatin Jihar Katsina.

Hotunan Yadda aka gudanar da Sallar Juma'a a Masallacin Haramai na Makkah, ya yin da yanayin zafin rana ya kai digiri 38...
26/09/2025

Hotunan Yadda aka gudanar da Sallar Juma'a a Masallacin Haramai na Makkah, ya yin da yanayin zafin rana ya kai digiri 38°C.

HASBUNALLAHI😭Yanbindiga Sun Halbe Masallata Suna Tsaka da Sallar Subahi a Tsafe.Wasu ’yanbindiga sun kai mummunan farmak...
26/09/2025

HASBUNALLAHI😭Yanbindiga Sun Halbe Masallata Suna Tsaka da Sallar Subahi a Tsafe.

Wasu ’yanbindiga sun kai mummunan farmaki a safiyar Juma’a a masallacin garin ’Yandoto, karamar hukumar Tsafe, jihar Zamfara, inda s**a bindige mutane biyar har lahira a lokacin da suke tsaka da gudanar da sallar Asubahi.

Shaidu sun ce maharan sun shigo garin ne, inda s**a kutsa cikin masallaci s**a bude wuta kan-mai-uwa-da-wabi ga jama’ar da ke Sallah, wanda hakan ya jawo mutuwar mutane biyar nan take, yayin da wasu s**a samu raunuka.

Baya ga haka, rahotanni sun kuma tabbatar da cewa ’yanbindigar sun yi awon gaba da mutane da dama daga yankin, lamarin da ya kara tayar da hankulan mazauna garuruwan Tsafe da kewaye.

Da hantsin yau juma'a ne majiyoyi s**a s**a bayyanawa Majiyar Karaduwa Post, Jaridar Taskar Labarai cewar an yi wa wadanda s**a kashe din sutura, inda aka sallaci gawarwakinsu da yi masu jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanada, abin da ya sanya al’ummar garin ke cikin alhini da jimami.

Har ya zuwa hada wannan rahoton dai jami’an tsaro daga yankin ba su fitar da bayani kan lamarin ba tukunna, sai dai mazauna yankin na ci gaba da kiran gwamnati da hukumomin tsaro da su dauki matakin gaggawa domin dakile hare-haren da ke addabar al’ummar jihar Zamfara.

Address

Nasarawa Ɗandume Local Government
Funtua

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Karaduwa Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share