11/07/2025
Mutane Sama Da Dubu 900,000 Ne S**a Rabauta Da Lamunin Inganta Sana’o’i A Nijeriya, Cewar Gwamnatin Tarayya
Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta bada tallafi da lamunin inganta sana’o’i ga sama da ‘yan Najeriya 900,000 ta hanyar shirin ‘Presidential Conditional Grant and Loan Scheme’, domin tallafawa ‘yan kasuwa kanana, masu sana’o’i, da matasan ‘yan kasuwa a fadin kasar.
Ministan Watsa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ne ya bayyana hakan a taron Gwamnonin APC da Kwamishinonin Watsa Labarai na jihohin s**a yi a Minna, Jihar Neja. Ya kuma ce sama da dalibai 300,000 suna amfana da sabon tsarin lamunin karatu, wanda ke tabbatar da cewa babu wani matashi da zai rasa damar zuwa jami’a saboda rashin kudin makaranta.
Gwamnatin Tarayya ta kuma sanya hannu kan shirin bunkasa noma da masana’antun sarrafa amfanin gona, ta hanyar kara wa Bankin Noma karfi da Naira tiriliyan 1.5 domin bai wa manoma da ‘yan kasuwa a bangaren noma jari. A bangaren bunkasa matasa da basira, gwamnatin ta ware Naira biliyan 75 don tallafa wa kananan masana’antu da masu sana’a, sannan ta ware Naira biliyan 120 da aka tanada domin horar da masu sana’ar hannu da fasaha, da nufin tallafa wa matasa miliyan 10 a fadin kasa.
Har ila yau, shirin Three Million Technical Talent (3MTT) na bai wa matasa damar koyon fasahar zamani, inda aka kaddamar da cibiyar 3MTT a Kano kwanan nan. A bangaren kirkire-kirkire da tattalin arzikin, gwamnati ta samar da Creative Economy Development Fund (CEDF) wanda ke bayar da tallafi har zuwa $100,000 ga masu kasuwanci, tare da karin tallafi daga Naira 500,000 zuwa Naira miliyan 2 ga matasa ta hanyar Nigeria Youth Investment Fund.