16/04/2026
Hon. Dauda Danladi Mahuta ya bayyana alhini da jimami bisa rasuwar Hajiya Hauwa (Maijeddah), uwargidan Shugaban Ma’aikatan Gidan Gwamnatin Jihar Katsina, Hon. Abdulƙadir Mamman Nasir Andaje.
Tsohon Sakataren Mulki A Ƙaramar Hukumar Dandume Jihar Katsina Hon. Dauda Danladi Mahuta ya mika sakon ta’aziyyarsa ga Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, da iyalan marigayiyar, tare da daukacin al’ummar Jihar Katsina bisa wannan babban rashi da ya girgiza zukata.
Hon. Dauda Ya bayyana marigayiyar a matsayin mace ta gari mai kyawawan halaye, wadda ta rayu cikin mutunci da hidima ga iyali da al’umma. Ya ce rasuwarta babban gibi ne da za a dade ana jin irinsa.
Hon. Dauda Danladi Mahuta ya roƙi Allah Maɗaukakin Sarki da Ya jikanta da rahama, Ya gafarta mata kura-kuranta, Ya sa Aljannatul Firdausi ta zamo makomarta. Haka kuma, Ya bai wa iyalanta da daukacin al’umma haƙurin jure wannan rashi.
“Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un.”