Karaduwa Post

Karaduwa Post Domin Samun Labaran Duniya Gamida Nishadantar Ba Tareda Chin Mutumchi Kowa Ba.

Hon. Dauda Danladi Mahuta ya bayyana alhini da jimami bisa rasuwar Hajiya Hauwa (Maijeddah), uwargidan Shugaban Ma’aikat...
16/04/2026

Hon. Dauda Danladi Mahuta ya bayyana alhini da jimami bisa rasuwar Hajiya Hauwa (Maijeddah), uwargidan Shugaban Ma’aikatan Gidan Gwamnatin Jihar Katsina, Hon. Abdulƙadir Mamman Nasir Andaje.

Tsohon Sakataren Mulki A Ƙaramar Hukumar Dandume Jihar Katsina Hon. Dauda Danladi Mahuta ya mika sakon ta’aziyyarsa ga Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, da iyalan marigayiyar, tare da daukacin al’ummar Jihar Katsina bisa wannan babban rashi da ya girgiza zukata.

Hon. Dauda Ya bayyana marigayiyar a matsayin mace ta gari mai kyawawan halaye, wadda ta rayu cikin mutunci da hidima ga iyali da al’umma. Ya ce rasuwarta babban gibi ne da za a dade ana jin irinsa.

Hon. Dauda Danladi Mahuta ya roƙi Allah Maɗaukakin Sarki da Ya jikanta da rahama, Ya gafarta mata kura-kuranta, Ya sa Aljannatul Firdausi ta zamo makomarta. Haka kuma, Ya bai wa iyalanta da daukacin al’umma haƙurin jure wannan rashi.

“Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un.”

DA DUMI-DUMI: Jami'an Tsrao Sun K**a Daya Daga Cikin Shugaban 'Ýan Biñďiģà, Kachalla Auta, Tare Da Mai Dakinsa.Rahotonni...
16/04/2026

DA DUMI-DUMI: Jami'an Tsrao Sun K**a Daya Daga Cikin Shugaban 'Ýan Biñďiģà, Kachalla Auta, Tare Da Mai Dakinsa.

Rahotonni Dake Fitowa Na Cewa Sojojin Nijeriya Sun K**a Daya Daga Cikin Shugaban 'Ýan Biñďiģà, Kachalla Auta, Tare Da Mai Dakinsa A Jihar Gombe Bayan Sun Tsero Daga Jihar Filato

Daga: Sani Bello Bature

Wannan Itace: Ta zo na ɗaya a gasar shigar mutunci ta kasar Sierra Leone na gabatar da nasiha a lokacin gasarGasar mai t...
16/04/2026

Wannan Itace: Ta zo na ɗaya a gasar shigar mutunci ta kasar Sierra Leone na gabatar da nasiha a lokacin gasar

Gasar mai taken "Dress Like A Muslima" ta faro ne tun 2019 inda mata ke yin shigar mutunci a zaɓi gwana.

Kuna goyon bayan a ƙirƙiri irin wannan a kasar nan?

TIRƘASHI: "An samu layin waya 'Sim Cards' guda 28 a wajen Yan Damfara masu muryar tsofi da sunan Malamai ko Aljanu"Inji-...
16/04/2026

TIRƘASHI: "An samu layin waya 'Sim Cards' guda 28 a wajen Yan Damfara masu muryar tsofi da sunan Malamai ko Aljanu"

Inji- Mai magana da yawun yansandan Kano Abdullahi Kiyawa

Me zaku ce?

Marafan Dandume ya aike da sakon ta’aziyyar rasuwar matar shugaban ma’aikatan gidan gwamnatin KatsinaMai Girma Alhaji La...
15/04/2026

Marafan Dandume ya aike da sakon ta’aziyyar rasuwar matar shugaban ma’aikatan gidan gwamnatin Katsina

Mai Girma Alhaji Lawal Ibrahim Danmumuni (Marafan Dandume)” shugaban ƙungiyar MARAFAN DANMUMUNI SUPPORT DIKKO 2027 Ya aike da saƙon ta’aziyya ga shugaban ma’aikatan gidan gwamnatin Jihar Katsina, bisa rasuwar matarsa, Hajiya Maijidda Abdulkadir Mamman Nasir Andaje.

Marigayiyar ta rasu ne bayan fama da gajeruwar rashin lafiya, lamarin da ya jefa iyalanta da ma al’umma cikin alhini.

A cikin saƙon ta’aziyyar da ya fitar, ya bayyana rasuwar a matsayin babban rashi, yana mai jajanta wa mijinta da sauran iyalai da abokan arziki, tare da addu’ar Allah ya jikanta da rahama, ya gafarta mata kura-kuranta, ya kuma ba waɗanda ta bari haƙurin jure wannan rashi.

Haka kuma, ya miƙa gaisuwa da ta’aziyyarsa ga Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda, da ma’aikatan fadar gwamnatin jihar, bisa wannan rashi da ya shafi gwamnati da al’umma baki ɗaya.

Gwamnatin Tarayya Ta Kulla Yarjejeniyar Dalar Amurka Biliyan Daya Da Kamfanin Karfe Na IndiyaGwamnatin Tarayya ta rattab...
15/04/2026

Gwamnatin Tarayya Ta Kulla Yarjejeniyar Dalar Amurka Biliyan Daya Da Kamfanin Karfe Na Indiya

Gwamnatin Tarayya ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya (MoU) da wani babban kamfanin sarrafa karafa na kasar Indiya mai suna Rashmi Metaliks Group, domin zuba jarin dalar Amurka biliyan daya (kimanin naira triliyan 1.5) a cikin shekara uku.

Ministan Raya Fannin Karfe, Prince Shuaibu Abubakar Audu, shi ne ya jagoranci tawagar Najeriya zuwa birnin Kolkata na kasar Indiya, inda aka kulla wannan yarjejeniya bayan ya ziyarci masana’antar kamfanin.

Cikin wata sanarwa da Shugabar Sashin Yada Labarai na Ma’aikatar, Salamatu Jibaniya, ta fitar ranar Talata, Minista Audu ya bayyana matakin a matsayin gagarumin ci gaba da zai taimaka wajen farfado da fannin karfe a Najeriya.

Ministan ya ce wannan jari zai bunkasa masana'antu a kasar nan, ya samar da ayyukan yi ga dimbin matasa, sannan ya rage dogaro da shigo da karafa daga kasashen waje, wanda hakan zai taimaka wajen adana kudaden kasashen waje.

Yayin rangadin da ya gudanar a masana’antar, Prince Audu ya jinjina wa yadda kamfanin ke amfani da fasahar zamani da kuma tsarin aiki mai inganci, inda ya ce hakan abin koyi ne ga Najeriya wajen inganta harkar karfe.

Ministan ya kara da cewa Najeriya na da burin daina zama kasar da ke fitar da danyen ma'adinai kawai, inda take kokarin komawa kasar da ke sarrafa su da kanta. Ya bayyana cewa Najeriya na da sama da tan biliyan uku na danyen karfe (iron ore) masu inganci.

"Muna da danyen karfe mai ingancin kashi 67 cikin dari, kuma kudin da ake kashewa wajen sayen karfe a Najeriya duk shekara ya kai dalar Amurka biliyan 10," in ji shi.

Ya kara da cewa Najeriya na da burin zama matattarar karfe a nahiyar Afirka, tare da shirin samar da tan miliyan 10 na danyen karfe duk shekara kafin zuwa shekarar 2030.

A nasa bangaren, Mataimakin Shugaban Kamfanin Rashmi Metaliks Group, Mista Sunil Patwari, ya yabawa kokarin Najeriya na farfado da fannin karfe, inda ya bukaci gwamnati ta ba su dukkan goyon bayan da ya dace don tabbatar da nasarar ayyukan da ke kunshe a yarjejeniyar.

Rahotanni sun nuna cewa kafin Ministan ya dawo gida, zai gana da takwaransa na kasar Indiya, Shri Kumaraswamy, domin kara tattauna hanyoyin hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu a fannin hakar ma'adinai da kera karafa.

HASBUNALLAH: Anyi Jana'izar Matar Shugaban Ma’aikata, Maijeddah__Gwamna Radda Ya Jagoranci Tawagar KatsinaMai girma Gwam...
15/04/2026

HASBUNALLAH: Anyi Jana'izar Matar Shugaban Ma’aikata, Maijeddah

__Gwamna Radda Ya Jagoranci Tawagar Katsina

Mai girma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, a ranar Laraba ya jagoranci wata babbar tawagar gwamnati zuwa jana’izar marigayiya Hajiya Hauwa (Maijeddah) Abdulkadir Mamman Nasir, matar Shugaban Ma’aikata na Gidan Gwamnatin Katsina.
An gudanar da sallar jana’izar a Masallacin GRA da misalin karfe 1:12 na rana, jim kaɗan bayan sallar Zuhr, inda ‘yan uwa, jami’an gwamnati, da masu jaje s**a hallara domin yi mata addu’ar bankwana.

Daga bisani, an binne marigayiyar da misalin karfe 1:45 na rana a makabartar Gidan Dawa da ke Katsina.

Malaman addinin Musulunci da sauran shugabannin addini sun gudanar da addu’o’i, inda s**a roƙi Allah Maɗaukakin Sarki (SWT) ya gafarta mata kura-kuranta, ya ba ta Aljannatul Firdausi, sannan ya ba iyalan da ta bari haƙuri, juriya da ƙarfin zuciya na jure wannan rashi.

Tawagar ta haɗa da Sakataren Gwamnatin Jiha (SSG), Abdullahi Garba Faskari; Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Katsina, Hon. Nasir Yahaya Daura.

Haka kuma akwai Babban Sakataren Sirri na Gwamna, Hon. Abdullahi Aliyu Turaji; Sanatan da ke wakiltar Yankin Funtua, Hon. Muntari Dandutse; da Shugaban Ma’aikatan Jiha, Alhaji Falalu Bawale.

Har ila yau, mambobin Majalisar Dokokin Jihar Katsina, mambobin Majalisar Zartarwa ta Jiha, Babban Alƙalin Jihar Katsina, Babban Khadi, manyan jami’an gwamnati, da sauran manyan baki daga ciki da wajen jihar sun halarta.

‘Yan jam’iyya, ‘yan uwa, abokai, da abokan hulɗar marigayiyar, tare da shugabannin al’umma da na addini, su ma sun halarta domin yi mata addu’ar samun rahama.

Yan sanda sun ƙwato wayoyin hannu kusan 200 da ake zargin an sace su, tare da wasu kayayyakin lantarki a Tarans-Nzonia.H...
15/04/2026

Yan sanda sun ƙwato wayoyin hannu kusan 200 da ake zargin an sace su, tare da wasu kayayyakin lantarki a Tarans-Nzonia.

Hukumar ‘Yan sanda a ƙaramar hukuma ta Trans-Nzoia sun k**a mutane 170 da ake zargi, ciki har da mutum biyar da aka ruwaito sun tsere daga ofishin ‘yan sanda na Kiungani a farkon wannan shekara. An kuma ƙwato wayoyin hannu kusan 200 da ake zargin an sace su, tare da wasu kayayyakin lantarki.

Kwamandan ‘yan sanda na ƙaramar hukumar, Rico Ngare, ya bayyana cewa wasu daga cikin waɗanda aka k**a ana zargin suna da alaƙa da ƙungiyoyin ‘yan daba na siyasa, yayin wani samame na tsaro da aka gudanar a ranar Talata.

Hotuna daga Osinde Obare.

Shugaban Ƙasar Iran ya yaba da jajircewar ma’aikatan agajin gaggawaMasoud Pezeshkian, Shugaban Ƙasar Iran, ya kai ziyara...
15/04/2026

Shugaban Ƙasar Iran ya yaba da jajircewar ma’aikatan agajin gaggawa

Masoud Pezeshkian, Shugaban Ƙasar Iran, ya kai ziyara ga jami’an agajin gaggawa a ma’aikatarsu, inda ya nuna godiya da jin daɗin irin namijin ƙoƙarin da s**a yi. Ya bayyana cewa ma’aikatan lafiya da na agajin gaggawa sun nuna ƙwazo, jajircewa da gwarzantaka tun bayan yaƙin tsokanar da Amurka da Isra'ila s**a ƙaddamar kan Iran, duk da barazanar da ke fuskantar rayuwarsu.

Shugaban ya ƙara da cewa irin wannan sadaukarwa da s**a nuna ya zama abin alfahari ga ƙasar Iran, yana mai kiran su “fitattun jarumai” a lokacin wannan yaƙi.

Ziyarar ta kuma nuna yadda gwamnati ke ƙoƙarin ƙarfafa gwiwa da goyon bayan waɗanda ke aikin ceto rayuka a wannan lokaci mai wahala.

Gwamna Zulum ya jagoranci jana'izar marigayi Birgediya Janar Omo Braimah, Kyaftin Ismail, da sauran jaruman sojoji wadan...
15/04/2026

Gwamna Zulum ya jagoranci jana'izar marigayi Birgediya Janar Omo Braimah, Kyaftin Ismail, da sauran jaruman sojoji wadanda s**a rasu fagen daga.

An gudanar da Jana'iza mai cike da sosa rai a ranar yau Laraba, 15 ga Afrilu, 2026 ta marigayi Birgediya Janar Omo Braimah, Kyaftin Ismail, da sauran jaruman sojoji wadanda s**a biya babban lada a lokacin aikinsu.

An yi jana'izar, wacce aka yi ta a Makabartar Maimalari Cantonment da ke Maiduguri a Jihar Borno cikin bakin ciki, girmamawa da alhini.

DA DUMI-DUMI: Peter Obi, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar Labour (LP) a shekarar 2023, a ranar Laraba ya gana da w...
15/04/2026

DA DUMI-DUMI: Peter Obi, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar Labour (LP) a shekarar 2023, a ranar Laraba ya gana da wakilai daga ofisoshin diflomasiyya da dama a Abuja.

A cikin wani rubutu da aka wallafa a shafin X, Esther Umoh, mai ɗaukar hoton Obi, ta ce tsohon gwamnan Anambra ya gana da "wakilai daga ofisoshin diflomasiyya da dama, ciki har da Babban jakadan Burtaniya, da ofisoshin jakadancin Jamus, Kanada, da Faransa."

LABARI MAI DAƊI: Rundunar Zamfara State Community Protection Guard (ZCPG) ta tare wata babbar hanyar da ake zargin ana b...
15/04/2026

LABARI MAI DAƊI: Rundunar Zamfara State Community Protection Guard (ZCPG) ta tare wata babbar hanyar da ake zargin ana bi wajen kai kayayyaki ga ‘yan bindiga a ƙaramar hukumar Maru, inda ta k**a wani direba da aka samu da na’urorin fashewa guda 98 waɗanda ake zargin za a kai su ga ƙungiyoyin masu laifi.

Hukumomi sun kuma ƙwato kuɗi har ₦13,352,500 tare da sabbin babura guda biyu, waɗanda ake kyautata zaton suna da alaƙa da wannan aiki. Jami’ai sun bayyana wannan kamen a matsayin babban nasara a ƙoƙarin da ake yi na dakile ayyukan ‘yan bindiga a yankin.

Hotuna 📸Kautal TV

Address

Nasarawa Ɗandume Local Government
Funtua

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Karaduwa Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share