Karaduwa Post

Karaduwa Post Domin Samun Labaran Duniya Gamida Nishadantar Ba Tareda Chin Mutumchi Kowa Ba.

Iran ta cire tuta, Iran na ƙera jiragen yaƙi marasa matuƙa (Shaheed) guda 400 a kowace rana, A halin yanzu tana da kiman...
07/01/2026

Iran ta cire tuta, Iran na ƙera jiragen yaƙi marasa matuƙa (Shaheed) guda 400 a kowace rana,

A halin yanzu tana da kimanin jirage marasa matuƙa 80,000 a sahun gaba masu shirin shiga fagen daga.

Nan da Karshen Wannan wata adadin jiragen Yakin Shasheed zai haura zuwa dubu 165,500.

Hasashe ya nuna cewa Iran zata zama ƙasar da ta fi kowacce yawan masu sarrafa jiragen yaƙi marasa matuƙa a duniya. Wannan aiki ya gudana ne da taimakon kasar Rasha.

Hotunan Yadda Mabiya Shi'a a Najeriya s**a gudanar muzaharar Fatimiyya, Domin tuna ranar da aka haifi Sayyada Zahrah (S....
07/01/2026

Hotunan Yadda Mabiya Shi'a a Najeriya s**a gudanar muzaharar Fatimiyya, Domin tuna ranar da aka haifi Sayyada Zahrah (S.A) a garin Soba ta jihar Kaduna, A ranar talata 6/01/2026.

Hotuna :📸Journalist Moh'd

Rasha ta aika sako ga Amurka, bayan kwace jirgin Ruwanta a Iyakar Venezuela.Ministan Harkokin Wajen Rasha, a wani sako d...
07/01/2026

Rasha ta aika sako ga Amurka, bayan kwace jirgin Ruwanta a Iyakar Venezuela.

Ministan Harkokin Wajen Rasha, a wani sako da ya aika, bayan ƙwace jirgin ɗaukar man fetur na Marinera da Amurka ta yi, ya ce:

“Rasha na buƙatar Amurka ta tabbatar da an yi wa ’yan ƙasar Rasha da ke cikin jirgin Kyakkyawar mu’amala ta jin ƙai da nuna mutuntawa, tare da basu cikakken haƙƙoƙinsu, ciki har da haƙƙinsu na komawa ƙasarsu ta Rasha ba tare da wata Sharaɗi ba.”

HOTO📸 Abdul Journalist 1

TIRKASHI: Jerin Gidajen Alfarma 57, Otal-otal, Da Sauran Kayayyakin da Aka Kwace Daga Tsohon AGF Malami A Cikin Zargin D...
07/01/2026

TIRKASHI: Jerin Gidajen Alfarma 57, Otal-otal, Da Sauran Kayayyakin da Aka Kwace Daga Tsohon AGF Malami A Cikin Zargin Da Ake Mai Na Karkatar Da Naira Biliyan 8.7.

HOTUNA 🖼️Madugun Darikar Kwankwasiyya Dakta Rabiu Musa Kwankwaso, Yakai ziyarar girmamawa ga fitaccen ɗan kasuwa kuma ma...
07/01/2026

HOTUNA 🖼️Madugun Darikar Kwankwasiyya Dakta Rabiu Musa Kwankwaso, Yakai ziyarar girmamawa ga fitaccen ɗan kasuwa kuma mai aikin jinkai.

’Yan bindiga sun sace ɗan jaridar daukar hoto Umar Iyale a Kaduna’Yan bindiga sun sace Umar Iyale, gogaggen ɗan jaridar ...
07/01/2026

’Yan bindiga sun sace ɗan jaridar daukar hoto Umar Iyale a Kaduna

’Yan bindiga sun sace Umar Iyale, gogaggen ɗan jaridar daukar hoto, a unguwar Danhonu II da ke cikin Millennium City a Jihar Kaduna.

Rahotanni sun ce ’yan bindigar sun sace Iyale, wanda ke fama da wata rashin lafiya da ba a bayyana ba, a daren ranar Litinin da misalin karfe 9:00 na dare, daga gidansa.
An ce yana gida shi kaɗai a lokacin da maharan s**a shiga s**a tafi da shi.

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, Mansir Hassan, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce rundunar ta kaddamar da aikin ceto domin kubutar da ɗan jaridar.

~Karaduwa Post

WATA SABUWA: Mun samu labarin cewa jami’an tsaron DSS sun rabe a kofar gidan yarin kuje suna jiran Abubakar Malami ya zo...
07/01/2026

WATA SABUWA: Mun samu labarin cewa jami’an tsaron DSS sun rabe a kofar gidan yarin kuje suna jiran Abubakar Malami ya zo fitowa bayan samun beli su sake k**a shi - Zargin Ofishinsa

07/01/2026

"Tunda Akayi Jihar Katsina Ba'a Taɓa Gwamna Irin Malam Dikko Umar Radda Ba"_-Inji- GM Usman Rabi'u Mahuta.

"Ilimin PhD, MSc, BSc, HND, ND da NCE ba su wadatar ba, idan mutum bai san ilimin addinin Musulunci ba"-Inji-Bin Kanoma....
07/01/2026

"Ilimin PhD, MSc, BSc, HND, ND da NCE ba su wadatar ba, idan mutum bai san ilimin addinin Musulunci ba"-Inji-Bin Kanoma.

Fitaccen Malamin addinin Muslunci a Najeriya Shêikh Ahmad Umar Bin Kanoma ya bayyana cewa ilimin zamani k**ar PhD, MSc, BSc, HND, ND da NCE ba su wadatar ba, idan mutum bai san ilimin addinin Musulunci ba.

Ya ce duk wanda bai san ilimin addini ba, komai yawan takardun karatunsa, jahili ne inji shi.

Me zakuce?

Madugun adawar siyasa a Najeriya Kuma Tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar tare da tsohon sanata Dino Melaye a...
07/01/2026

Madugun adawar siyasa a Najeriya Kuma Tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar tare da tsohon sanata Dino Melaye a kasar Dubai.

Mun Shirya Tsaf Domin Karɓar Miliyoyin Baƙi Da Za Su Halarci Maulidin Sheikh Ibrahim Inyass Karo Na 40 A KatsinaBabban k...
07/01/2026

Mun Shirya Tsaf Domin Karɓar Miliyoyin Baƙi Da Za Su Halarci Maulidin Sheikh Ibrahim Inyass Karo Na 40 A Katsina

Babban kwamitin shirya Maulidin Sheikh Ibrahim Inyass, karo na arba'in wanda za a gudanar a jihar Katsina a ranar 17 ga watan Janairu na wannan shekarar ya ce shirye-shiryen sun yi nisa na karɓar bakin da ake sa ran za su halarta, wanda s**a kai sama da mutum Miliyan huɗu.

Shugaban babban kwamitin shirya Maulidin Sheikh Hadi Balarabe ya tabbatar da haka ga manema labarai a babban ofishin ƙungiyar Munazzamatul Fitiyanul Islam dake hanyar Batsari a cikin garin Katsina, yau Laraba.

Sheikh Hadi Balarabe ya kara da cewa wannan shi ne karo na ukku da jihar Katsina ke karɓar wannan babban taron Maulidin Sheikh Ibrahim Inyass kuma tun daga yau an fara gudanar da na wannan shekarar. Idan za a tuna mun taɓa karɓar a 2002 da 2016 da kuma bana, wanda an fara gudanar da taron Maulidin Sheikh Ibrahim Inyass a shekarar 1986, yau shekara 40 kenan cif da fara shi a Najeriya.

Shugaban kwamitin shiryawar, Sheikh Hadi Balarabe ya cigaba da cewa a bana a ranar 11 ga wannan wata za a fara gudanar da taron masana da kara wa juna sani na kasa da kasa, wanda za a kwashe tsawon kwanaki biyar ana yinsa, wanda masana daga kasashen duniya za su samu halarta domin gabatar da makaloli da s**a shafi rayuwar shahararren malamin Addinin Musulunci, Sheikh Ibrahim Inyass.

Haka zalika za a gudanar da babban taron Maulidin Sheikh Ibrahim Inyass a ranar 17 ga watan Nan, a filin Wasa na tunawa da Sarkin Katsina, Marigayi Muhammadu Dikko dake cikin garin Katsina, wanda za a fara da misalin karfe 8:00 na safiya zuwa karfe biyu na rana.

Malam Hadi Balarabe ya tabbatar wa mahalarta wannan gagarumin taron Maulidin cewa kwamitin ya shirya tsaf domin samar da tsaron lafiya da dukiyoyi da samar da masauki ga manyan baki da duk wani abu da ake buƙata. Muna kira ga wadannan dinbin baki na mu su zamanto masu bin doka da oda, domin an gudanar da taron lafiya an kuma tashi Lafiya.

~Focus News Hausa

DA DUMI-DUMI: Jam’iyyar PDP na shirin zama a teburin tattaunawa da Atiku Abubakar, Peter Obi da sauran jiga-jigan jam’iy...
07/01/2026

DA DUMI-DUMI: Jam’iyyar PDP na shirin zama a teburin tattaunawa da Atiku Abubakar, Peter Obi da sauran jiga-jigan jam’iyyar, domin ƙarfafa haɗin kai da sake gina jam’iyyar, domin tunkarar zaɓen shekarar 2027.

Address

Nasarawa Ɗandume Local Government
Funtua

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Karaduwa Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share