Karaduwa Post

Karaduwa Post Domin Samun Labaran Duniya Gamida Nishadantar Ba Tareda Chin Mutumchi Kowa Ba.

DA ƊUMI-ƊUMI: 'Yan sanda sun yi zama na Musamman kan wa'azin Lawan TriumphRundunar 'yan sandan jihar Kano ta gayyaci Mal...
11/07/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: 'Yan sanda sun yi zama na Musamman kan wa'azin Lawan Triumph

Rundunar 'yan sandan jihar Kano ta gayyaci Malamin domin zama da shi game da ƙorafe-ƙorafen jama'a akan wa'azinsa, wanda ya jawo cece-kuce a kafafen yaɗa labarai.

A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ta Kano Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, ƴansandan sun ce duk da cewa malamin yana da ƴancin faɗin albarkacin bakinsa, to amma "muna da hurumin ganin mun tabbatar da an yi komai bisa doka da oda.

Rundunar ta buƙaci Al'umma da su kaucewa duk wani abu da zai haifar da tarzoma a Kano da kuma bukatar duk wani mai korafi da ya kai gabanta maimakon ɗauka doka a hannu.

DA DUMI-DUMI: Ga Damar Koyon Sana'a Ga Matasa: Yayin Da Sanata Muntari Dandutse Ya Kammala Cibiyar Koyon Sana’o’i a Gari...
11/07/2025

DA DUMI-DUMI: Ga Damar Koyon Sana'a Ga Matasa: Yayin Da Sanata Muntari Dandutse Ya Kammala Cibiyar Koyon Sana’o’i a Garin Musawa

Sanatan shiyyar Funtua Jihar Katsina Mai Girma Sanata Muntari Muhammad Dandutse, ya kammala aikin gina Cibiyar Koyar da Sana’o’i ta zamani da ke cikin ƙaramar hukumar Musawa, Jihar Katsina.

Wannan cibiya tana ɗaya daga cikin muhimman ayyukan raya kasa da Sanatan ya aiwatar, da nufin tallafa wa matasa wajen koyon sana’o’i, rage zaman banza da kuma ƙara yawan ayyukan yi a yankin.

A cewar masu lura da al’amuran yau da kullum, cibiyar za ta taka muhimmiyar rawa wajen inganta rayuwar matasa, tare da basu damar samun dogaro da kai ta hanyar sana’o’in hannu daban-daban.

Rahotanni sun tabbatar da cewa aikin gina cibiyar ya kammala gaba ɗaya, kuma ana sa ran za a fara amfani da ita nan ba da jimawa ba.

Mazauna yankin Shiyyar Funtua sun bayyana jin daɗin su da godiya bisa wannan gagarumin aikin ci gaba da Mai Girma Sanata Muntari Dandutse ya kawo.

~Dandutse Media Reporters

"Ni Ba Siyan Mota GLK Ba Ne Damuwata"_-Cewar Jarumar Tiktoķ. Eshert Aleeyu, Bayan Ta Gina Katafaren GidaMenene Ra'ayin K...
11/07/2025

"Ni Ba Siyan Mota GLK Ba Ne Damuwata"_-Cewar Jarumar Tiktoķ. Eshert Aleeyu, Bayan Ta Gina Katafaren Gida

Menene Ra'ayin Ku?

11/07/2025

LIVE:🔴 Inauguration State Agency For Mass Education Board Members, By KT ST, Ministry Of Basic And Sec. Education At MBASE Conference Hall Katsina.

"Lokacina Duka na Al'ummar Kasa ta ne, Bani da Loƙacin Halartar Wani Taron Liyafa -Inji- Ibrahim TraoréShugaban Kasar bu...
11/07/2025

"Lokacina Duka na Al'ummar Kasa ta ne, Bani da Loƙacin Halartar Wani Taron Liyafa -Inji- Ibrahim Traoré

Shugaban Kasar burkina faso Ibrahim Traoré Ya ƙi karɓar gayyatar hukuma zuwa kasar Amurka, Ya ce a halin yanzu yana cike da aiki na hidimtawa al’ummar Burkina Faso, kuma bai da lokaci don wata liyafa ko taron diflomasiyya.

Me za ku ce?

Daga Shafin Dan Jarida

ABIN BURGEWA: Yadda Wasu Daga Cikin Iyayenmu Yan Fansho S**a Fara Jin Saukar Alert ,Bayan Kammala Taron Kaddamar Da Biya...
11/07/2025

ABIN BURGEWA: Yadda Wasu Daga Cikin Iyayenmu Yan Fansho S**a Fara Jin Saukar Alert ,

Bayan Kammala Taron Kaddamar Da Biyansu Kudin Fansho Da Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf Yayi Da Yammacin Jiya.

Mutane Sama Da Dubu 900,000 Ne S**a Rabauta Da Lamunin Inganta Sana’o’i A Nijeriya, Cewar Gwamnatin TarayyaGwamnatin Shu...
11/07/2025

Mutane Sama Da Dubu 900,000 Ne S**a Rabauta Da Lamunin Inganta Sana’o’i A Nijeriya, Cewar Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta bada tallafi da lamunin inganta sana’o’i ga sama da ‘yan Najeriya 900,000 ta hanyar shirin ‘Presidential Conditional Grant and Loan Scheme’, domin tallafawa ‘yan kasuwa kanana, masu sana’o’i, da matasan ‘yan kasuwa a fadin kasar.

Ministan Watsa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ne ya bayyana hakan a taron Gwamnonin APC da Kwamishinonin Watsa Labarai na jihohin s**a yi a Minna, Jihar Neja. Ya kuma ce sama da dalibai 300,000 suna amfana da sabon tsarin lamunin karatu, wanda ke tabbatar da cewa babu wani matashi da zai rasa damar zuwa jami’a saboda rashin kudin makaranta.

Gwamnatin Tarayya ta kuma sanya hannu kan shirin bunkasa noma da masana’antun sarrafa amfanin gona, ta hanyar kara wa Bankin Noma karfi da Naira tiriliyan 1.5 domin bai wa manoma da ‘yan kasuwa a bangaren noma jari. A bangaren bunkasa matasa da basira, gwamnatin ta ware Naira biliyan 75 don tallafa wa kananan masana’antu da masu sana’a, sannan ta ware Naira biliyan 120 da aka tanada domin horar da masu sana’ar hannu da fasaha, da nufin tallafa wa matasa miliyan 10 a fadin kasa.

Har ila yau, shirin Three Million Technical Talent (3MTT) na bai wa matasa damar koyon fasahar zamani, inda aka kaddamar da cibiyar 3MTT a Kano kwanan nan. A bangaren kirkire-kirkire da tattalin arzikin, gwamnati ta samar da Creative Economy Development Fund (CEDF) wanda ke bayar da tallafi har zuwa $100,000 ga masu kasuwanci, tare da karin tallafi daga Naira 500,000 zuwa Naira miliyan 2 ga matasa ta hanyar Nigeria Youth Investment Fund.

DA DUMI-DUMI: NAOWA Ta Tallafa wa Matan Sojoji da Zawarawan Jaruman Sama da 1,500 a AbujaƘungiyar Matan Hafsoshin Sojin ...
11/07/2025

DA DUMI-DUMI: NAOWA Ta Tallafa wa Matan Sojoji da Zawarawan Jaruman Sama da 1,500 a Abuja

Ƙungiyar Matan Hafsoshin Sojin Najeriya (NAOWA) ta gudanar da shahararren taron jin ƙai ga mata fiye da 1,500 da s**a haɗa da matan sojoji da zawarun jaruman da s**a rasa mazajensu a fagen fama.

Taron wanda aka gudanar a NAOWA Events Centre da ke Asokoro, dake Abuja, ya samu halartar wakililar shugabar ƙungiyar, Hajiya Mernan Femi Oluyede, wacce ta samu wakilcin mataimakiyarta, Hajiya Bilkisu Ibrahim. An raba kayan abinci da sauran kayan tallafi ga mahalartan.

Hajiya Bilkisu Ibrahim ta jaddada cewa NAOWA na da burin karfafa gwiwar matan sojoji da zawarawa ta hanyar tallafi da juyayin da ya dace da irin sadaukarwar mazajensu. Ta kuma nanata bukatar zaman lafiya, haɗin kai da goyon bayan juna a tsakanin iyalan dakarun Najeriya.

Wasu daga cikin zawarawan da s**a amfana sun bayyana farin cikinsu da godiya ga ƙungiyar bisa wannan kulawa da taimakon da s**a ce “ya zo a kan kari.”

-----
Shin irin wannan tallafi na NAOWA yana isar da sakon da ya kamata ga iyalan jaruman da s**a sadaukar da rayukansu? Ku aiko da ra'ayoyinku.

~Fara'a TV

Hotunan Yadda Mabiya Mazhabar Shi'a S**ayi Zaman Ashura Na Shekara 1447 Tsawon Kwanaki Domin Jajanta Akan Abinda Ya Faru...
11/07/2025

Hotunan Yadda Mabiya Mazhabar Shi'a S**ayi Zaman Ashura Na Shekara 1447 Tsawon Kwanaki Domin Jajanta Akan Abinda Ya Faru A Karbala, A Karamar Hukumar Dandume Jihar Katsina.

BABBAR HALAKA CE GA RAYUWAR MATASHI YA RINKA RAYUWA A BISA DORON KARYA Daga:Abdulbasir Ashafa Ahmad Dandume Babbar halak...
11/07/2025

BABBAR HALAKA CE GA RAYUWAR MATASHI YA RINKA RAYUWA A BISA DORON KARYA

Daga:Abdulbasir Ashafa Ahmad Dandume

Babbar halaka ce ga rayuwar Matashi ya saka rayuwar shi cikin ƙarya alhali bai da hali, amma saboda yana so sai ya burge wasu sai ya lalata rayuwar shi ta hanyar jefa kanshi cikin halaka, tare kuma da biyewa mutanen banza wanda sun yi bara'a da Allah (S.W.T) tun daga duniya har lahira.

Za kaga Matashi baya da hali anma shi burin shi dole sai ya burge mutane ta hanyar jawo ma kanshi hidimar da tafi samun shi, kuma baya so aga gazawarsa, daga nan ne lalacewa zata shigo don duk hanyar da zaibi ya samu kudi ita yake so, saboda baya bukatar ace ya gaza, wani ma daga nan ne zai hadu da mutanen da zasu jefa rayuwar shi cikin bala'in da baya iya fidda kanshi, ta hanyar sace-sace ko damfara, ko ya dunga kawalci, ko ya fada hanyar yan luwadi, abinda Allah ya halakar da wasu a baya saboda muninsa.

Shawarata a nan ita ce, ka yarda da matsayin da Allah ya aje ka, kada kayar da samun wani ya tsone maka ido ballantana har kace zaka yi wata gasa da shi, domin kuwa Allah ya riga ya ƙaddara wani sai yafi wani a cikin rayuwa, duk rashinka wani yafi ka, ka dunga yi ma Allah godiya a kowane yanayi kake sai kaga taimakonsa na ƙaruwa a gareka.

LABARI MAI DAƊI: Dakarun Sojin Najeriya na 223 Light Battalion dake Zuru sun samu nasarar daƙile harin ƴan bindiga a gar...
11/07/2025

LABARI MAI DAƊI: Dakarun Sojin Najeriya na 223 Light Battalion dake Zuru sun samu nasarar daƙile harin ƴan bindiga a garin Riɓah, da ke cikin Karamar Hukumar Danko Wasagu ta Jihar Kebbi Arewa maso Yamma.

Baya ga daƙile harin, sojojin sun hallaka yawancin ‘yan bindigar da s**a kai farmakin da mahukunta a jihar s**a tabbatar da sun kai 150, ya yin da wasu daga cikinsu s**a tsere da munanan raunukan harbin bindiga. Sama da ‘yan bindiga 400 dai ɗauke da muggan makamai s**a kai farmaki, amma an fatattake su.

An yi artabu mai tsanani tsakanin dakarun soji da ‘yan bindigar, wanda hakan ya kai ga kashe da dama daga cikinsu. Duk da cewa wasu daga cikin ‘yan ta’addan sun ɗauki gawarwakin abokan su, amma sun bar wasu a ƙasa tare da tarin makamai da aka ƙwato.

Waɗannan mutane da jami'ai s**a hallaka ana tunanin Lakur̃awà ne.

Naso a turo man video artabun amman ance sai oga ya bada umurnin a saka man.

Ƴan uwa, jami'an mu s**an faɗa mana cewar "Babu abin da muke buƙata ga al'umma face su riƙa yi mana addu'ar samun nasara a koda yaushe".

Don Allah ƴan uwa, mu ciga da saka jami'an mu cikin addu'o'in mu🙏

Allah ya ƙara ba jami'an tsaron mu nasara.

INNA LILLLAHI WA I NA ILAIHIL RAJI'UN.Anyi Awon Gaba Da Wannan Matashi Abubakar Gossima Bulangu A Garin Dutse.Wasu Mutan...
11/07/2025

INNA LILLLAHI WA I NA ILAIHIL RAJI'UN.

Anyi Awon Gaba Da Wannan Matashi Abubakar Gossima Bulangu A Garin Dutse.

Wasu Mutane A Garin Dutse Dake Jihar Jigawa Arewacin Najeriya Sun Zo Sun Yi Awon Gaba Da Matashi Abubakar Gossima Bulangu A Jiya, Inda S**a Bayyana Kansu A Matsayin Jami'an Tsaro, S**a Ce An Yi Karar Sa Ne, Saidai An Bincika Dukkanin Ofisoshin Tsaro Dake Cikin Garin Dutse Babu Labarinsa

Allah Ya Bayyana Shi Cikin Aminci!

Address

Nasarawa Ɗandume Local Government
Funtua

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Karaduwa Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share