Karaduwa Post

Karaduwa Post Domin Samun Labaran Duniya Gamida Nishadantar Ba Tareda Chin Mutumchi Kowa Ba.

An Kammala Aikin Rangadin Kananan Hukumomi (34) Dake Fadin Jihar Domin Duba Ayyukan Shuwagabannin Kananan Hukumomi.Kwami...
20/11/2025

An Kammala Aikin Rangadin Kananan Hukumomi (34) Dake Fadin Jihar Domin Duba Ayyukan Shuwagabannin Kananan Hukumomi.

Kwamitin kananan hukumomin da masarautu na majalisar dokokin jihar Katsina karkashin jagoranci Hon. Ibrahim Danjuma Machika, ɗan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Sabuwa, Ya kammala aikin rangadi kananan hukumomin (34) dake fadin Jihar, Domin duba ayyuka ƙananan hukumomi da karamar hukumar Musawa, Matazu, da Rimi, A ranar Laraba 19/11/2025.

Ayyukan da gwamnatin jihar ta bada umurnin aiwatar a fadin kananan hukumomi (34) dake fadin jihar karkashin jagorancin gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa Phd. CON.,

Inda kwamitin ya fara ziyarartar karamar hukumar Musawa, ya duba aikin gyaran asibitin cikin garin Kurkujan, Aikin gyaran asibitin garin Danjanku, da aikin hanyar ruwa, aikin katange makabartar garin Sabon-Layi, Duba aikin ruwa Mai tsayin gaske a cikin garin Musawa, Aikin gyaran sakatariyar karamar hukuma,

Tareda Wasu muhimman kayayyaki da siya zai rabawa al'umma domin dogara dakai, an duba motocin da Aka baida umarnin a siyawa shugaban kansiloli da mataimakin shugaban karamar hukuma, kuma Sun duba aikin gina Macanization Center Wadanda Aka gina domin ajiye motocin aikin gona, da dai sauran su.

Sai kwamitin ya wuce karamar hukumar Matazu, ya duba aikin gyaran asibitin garin Dissi, da aikin hanyar ruwa ta garin Faras, Sai duba aikin hanyar ruwa cikin garin Matazu, Sai aikin gyaran sakatariyar karamar hukuma karo na na farko, da aikin gina (Metrological center),Dake cikin karamar hukumar, Daga karshe Sun duba, motocin da Aka siyawa shugaban kansiloli da mataimakin shugaban karamar hukuma, da sakatare,da aikin gina (Macanization Center) wadanda Aka gina domin ajiye motocin aikin gona da dai sauran su.

Daga karshe kwamitin ya ziyayarci karamar hukumar Rimi, Inda ya duba aikin gyaran Masallacin garin Ika, da aikin hanyar ruwa cikin garin Kadandani, Duba aikin gadar garin Iyatawa, da aikin asibiti, aikin gyaran Makarantar firamare ta garin, sai Aikin gyaran hanyar ruwa ta garin Tardami ,Daga karshe sun duba motocin da Aka baida umarnin a siyawa shugaban kansiloli da mataimakin shugaban karamar hukuma, kuma Sun duba aikin gina Macanization Center Wadanda Aka gina domin ajiye motocin Aikin Gona, da dai sauran su.

Tawagar kwamitin sun hada Hon. Sale Magaji Ruma dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Sandamu, Hon. Abubakar Suleiman Tunas Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Ingawa, Hon. Shu'aibu Wakili Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Kafur, Hon. Zaharaddeen Isah dan majalisar Mai wakiltar Kurfi da jami'an tsaro da yan jarida.

~Karaduwa Post

DA DUMI-DUMI: Hukumar sojan ruwan Najeriya ta bayyana ranar da za'a gudanar da jarrabawar daukar ma’aikata (Batch 38)Sas...
20/11/2025

DA DUMI-DUMI: Hukumar sojan ruwan Najeriya ta bayyana ranar da za'a gudanar da jarrabawar daukar ma’aikata (Batch 38)

Sashen bunkasa samar da ayyukanyi ta jihar Katsina karkashin jagoranci Hon. Malam Yau Ahmed Nowa Dandume, Na sanar da alummr jihar Katsina da cewa, Hukumar sojan ruwan Najeriya (Nigerian Navy) ta bayyana ranar da za'a gudanar da jarrabawar daukar ma’aikata (Batch 38) ga duk masu nema da s**a kammala rajista cikin nasara.

Ranar Jarrabawa: Asabar, 29 ga Nuwamba 2025.

Lokacin Isa: 7:00 na safe (dai-dai),

Wuraren Jarrabawa: Cibiyoyi 30 da aka kebe a fadin kasa

Za'a Iya duba cikakken bayani, ko jerin Sunayen, da ka’idojin jarrabawa:
recruitmentpastquestions.com/nigerian-navy-…

Zaku Samu Tambayoyi & Amsoshin Jarrabawar Sojan Ruwa 👉 recruitmentpastquestions.com/product/nigeri…

Daga: Shamsu Wapa Dandume
Media Aide To S.A Employment Promotion
Katsina State

~Karaduwa Post

ABU BAI DADI BA: Yadda Fusatattun mutane sun yi ruwan duwatsu ga ayarin Motocin Gwamnan Neja Umaru Bago a ziyararsa zuwa...
19/11/2025

ABU BAI DADI BA: Yadda Fusatattun mutane sun yi ruwan duwatsu ga ayarin Motocin Gwamnan Neja Umaru Bago a ziyararsa zuwa ƙaramar hukumar Bida.

Me zakuce?

19/11/2025

AN ZO WAJEN: Wasu fusatattun matasa a garin Bida na jihar Niger sun jefi Gwamnan jihar Niger Muhammad Umar Bago da duwatsu

An fara kenan, amma wannan dabi'ar na jifan Shugabanni da ake ganin sun gaza ba mai kyau bane, madadin jifa da Duwatsu ku jefe su da addu'ah sai tafi tasiri

Allah Ka shiryar da shugabannin mu!

Daga: Datti Assalafiy

Gwamnatin Tarayya Ta Tura Ƙarin Jami’an Tsaro Don Murƙushe Ta’addanci – Ministan Yaɗa LabaraiGwamnatin Tarayya ta tabbat...
19/11/2025

Gwamnatin Tarayya Ta Tura Ƙarin Jami’an Tsaro Don Murƙushe Ta’addanci – Ministan Yaɗa Labarai

Gwamnatin Tarayya ta tabbatar da kudurinta na ƙara tsananta yaki da ta’addanci da aikata laifuka a sassa daban-daban na ƙasar, bayan jerin hare-haren da s**a faru kwanan nan.

A wani taron manema labarai da aka gudanar a Radio House, Abuja, ranar Laraba 19 ga Nuwamba, 2025, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar dan Jama’a, Mohammed Idris, ya bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ɗaga matakin sha’anin tsaro zuwa matsayi mafi girma domin kare rayuka da dukiyoyin ‘yan ƙasa.

Ministan ya miƙa sakon ta’aziyyar Shugaban Ƙasa ga iyalai da al’ummomin da abin ya shafa, yana mai bayyana kashe babban hafsan soji, sace dalibai a Jihar Kebbi da harin da aka kai cocin Eruku a Kwara a matsayin “abu mai muni” game da barazanar da ƙasar ke fuskanta.

Ya ce Shugaba Tinubu ya dage tafiyarsa zuwa taron G20 a Afirka ta Kudu da wasu tarukan ƙasashen waje, domin mai da hankali kan batutuwan tsaron cikin gida. Haka kuma ya umarci rundunonin soji da ‘yan sanda su tura ƙarin jami’ai zuwa Eruku da yankin ƙaramar hukumar Ekiti ta Jihar Kwara.

Ministan ya ƙara da cewa: “Jami’an tsaronmu sun samu umarni na musamman wajen ceto daliban makarantar Kebbi da gaggawa, tare da tarwatsa duk wata hanyar sadarwa ta ‘yan ta’adda a faɗin ƙasa.”

A cewar Idris, Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, na can Birnin Kebbi bisa umarnin Shugaban Ƙasa, yana ganawa da Gwamnan Jihar Kebbi, shugabannin tsaro, sarakunan gargajiya, da iyalan daliban da aka sace.

Ministan ya kuma yi watsi da ƙoƙarin da wasu ke yi na bai wa rikicin fassarar addini, yana mai cewa matsalolin tsaro a Najeriya sun shafi musulmi da kirista, da kabilu daban-daban.

“A wannan lokaci, haɗin kan ƙasa shi ne kayan aikinmu mafi ƙarfi,” in ji shi. “Dole ne mu guji ƙiyayya da rarrabuwar kawuna. Abokan gaba na gaskiya su ne ‘yan ta’adda da miyagun da ke ƙoƙarin tayar da hankalin ƙasa.”

Ya jaddada matsayin Najeriya a matsayin ƙasa mai addinai daban-daban, inda ‘yancin bauta ke cikin kundin tsarin mulki. Ya kuma kira jama’a da su tallafa wa jami’an tsaro, yana mai tabbatar da cewa ana ci gaba da gudanar da ayyukan tsaro domin ganin an kubutar da ɗaliban da aka sace tare da dawo da zaman lafiya a yankunan da abin ya shafa.

Hotunan Yadda Fitaccen Dan kwallon Duniya Cristiano Ronaldo, Ya gana da Shugaban Kasar Amurka Donald Trump a Fadar white...
19/11/2025

Hotunan Yadda Fitaccen Dan kwallon Duniya Cristiano Ronaldo, Ya gana da Shugaban Kasar Amurka Donald Trump a Fadar white House yau Laraba.

A taron majalissar ɗinkin duniya (UN) mawaƙiyar America "Nicki Minaj" tace:Kiristoci na fuskantar kisan kiyashi a Nigeri...
19/11/2025

A taron majalissar ɗinkin duniya (UN) mawaƙiyar America "Nicki Minaj" tace:

Kiristoci na fuskantar kisan kiyashi a Nigeria 🇳🇬, ana koresu daga gidajensu, ana ƙona dukiyarsu da wuraren ibadarsu

Nicki Minaj ta godewa shugaban America "Donald Trump" sannan tayi kira da a ɗauki matakin gaggawa domin kare 'yancin addini da adalci
-------------------------

Shin kuna sauraren waƙoƙin "Nicki Minaj"?

- Amatsayinka na musulmi idan kana sauraren waƙoƙin wannan matar, kayi gaggawa ka gogesu, kayi deleting album ɗinta daga wayarka

- Kayi unfollow ɗinta a duk shafukan sada zumunta

- Ka nemi tsarin Allah daga sharrin munafukan mutane masu neman jefa ƙiyayya acikin zaman lafiyan wannan ƙasar tamu (Nigeria)

Daga: Alhassan Mai Lafia

Sashen bunkasa samar da ayyukan yi karkashin jagorancin Hon. Ya'u Ahmad Nowa Dandume, ta ziyarci karamar hukumar Dutsin-...
19/11/2025

Sashen bunkasa samar da ayyukan yi karkashin jagorancin Hon. Ya'u Ahmad Nowa Dandume, ta ziyarci karamar hukumar Dutsin-ma da wasu kananan hukumomi hudu da suke makwabtaka da ita.

A ranar Laraba 19 watan Nuwamba, shekarar 2025 Sashen bunkasa samar da ayyuakan yi ta jihar katsina karkashin jagorancin Hon. Ya'u Ahmad Nowa Dandume, takai ziyarar wayar da kan matasa game da ayyuka masu damara a kananan hukumomin Dutsin-ma,Kurfi,Batsari,Safana,Danmusa.

Hon. Ya'u Ahmad Nowa Dandume wanda shine mai baiwa gwamnan jihar katsina shawara kan samar da ayyukan yi, yayi ma matasa bayani dalla-dalla akan muhimmancin wannan ma'aikata.

Ya kuma kara da cewa wannan ma'aikata ba akan bunkasa gami da samar da ayyukan yi kawai ta tsaya ba, harda neman guraben karatu a makarantun koyon sana'o'i irin su (Katsina Youth Craft Village) makarantar koyon sana'a dake garin onatcha da kuma makarantar koyon tukin jirgin ruwa.

Hon. Nowa ya rufe bayanin shi da kira ga matasa da su sani cewa wannan jarabawa da ake gabatarwa a yanzu akan ayyukan Immigration Service,Correctional service,Federal Fire Service, da su kula sosai domin gujewa laifin satar amsa domin yanzu zamani ya zo na'ura ce take tsaron jarabawar kuskure kadan mutum zaiyi akama shi da laifin satar amsa.

Shi kuwa wakilin kwamishinan 'yan sanda CSP Aminu Tanimu da takwaran shi wakilin shugaban hukumar kashe gobara ta kasa reshen jihar katsina ASF I Haruna Muhammad Ahmad, sunyi ma matasan bayani akan ka'idoji da kuma kalubalen da ake fuskanta a lokacin neman aiki akan yanar gizo (Online Registration) da kuma hanyoyin da za'a bi wajen magance kalubalen.

A nashi jawabin Daraktan ma'aikatar Malam Aliyu Aminu Bakori FCNA, ya bayyana illolin shan kwaya da kuma da kuma abinda take haifarwa, ya kuma kara da cewa "Kana ji kana gani aikin kayan sarki (aikin damara) zai gagare ka, sannnan kuma duk mai shan kwaya bazai taba zama cikakken mutum ba

Shi kuwa shugaban kungiyar kirstoci ta kasa reshen karamar hukumar Batsari, ya nuna farin cikin shi gami da godiya ta musamman tare da jinjina wa ga Hon. Nowa da kuma mai girma gwamnan jihar katsina Malam Dikko Umar Radda Phd,Con kan iri kokarin da suke yi wajen ganin matasan jihar katsina sun samu abinyi babu dare baba rana. Daga karshe yayi addu'a akan Allah ya kara daukaka mai girma gwamna zuwa shugaban kasa.

A cikin tawagar akwai daraktan sashen samar da ayyukanyi Malam Aliyu Aminu Bakori FCNA. (Director Employment), Daraktan kula da sashen kudi Ibrahim Garba Salmanu (DFA Employment), Ibrahim Bature Safana (DAS Employment), Khalid Al-hafiz Bakori (PRO),Da Aramaya'u Alhaji Sani (Staff Officer), Abubakar Ibrahim (Chief Driver) Tare da mataimaki na musamman Abdulbasir Ashafa (Special Assistant), Da sauran ma'aikatansa.

~Karaduwa Post

19/11/2025

BIDIYO:🎥 Tattaunawa tare da Alh. Abdulbasir Ayuba (Dogon Malam) daga karamar hukumar Musawa jihar Katsina a cikin shirin "Siyasar mu a yau".

DA DUMI-DUMI: Wasu tsoffin 'yan majalisar dokokin jihar Kano da kuma masu ci a yanzu sun mara wa Barau Jibrin baya don t...
19/11/2025

DA DUMI-DUMI: Wasu tsoffin 'yan majalisar dokokin jihar Kano da kuma masu ci a yanzu sun mara wa Barau Jibrin baya don tsayawa takarar gwamna a 2027

Me zakuce?

Hotunan Yadda Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya sauka a Birnin Kebbi domin ganawa da gwamnatin jihar Kebbi tar...
19/11/2025

Hotunan Yadda Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya sauka a Birnin Kebbi domin ganawa da gwamnatin jihar Kebbi tare da iyayen ɗalibai Mata da aka sace a Maga.

DA DUMI-DUMI: Zulum ya gana da shugaban rundunar sojin kasa ta Najeriya.Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulu...
19/11/2025

DA DUMI-DUMI: Zulum ya gana da shugaban rundunar sojin kasa ta Najeriya.

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya bayyana cewa mafi munin lokacin ta’addancin Boko Haram ya shige, ya amince da karuwar hare-haren Yan Ta'addan ƴan kwanakin nan.

Gwamna Zulum ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin ganawarsa da Shugaban Rundunar Sojin Najeriya (COAS), Laftanar Janar Shuaibu Waidi, a Maiduguri.

Address

Nasarawa Ɗandume Local Government
Funtua

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Karaduwa Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share