Karaduwa Post

Karaduwa Post Domin Samun Labaran Duniya Gamida Nishadantar Ba Tareda Chin Mutumchi Kowa Ba.

WATA SABUWA: "Peter Obi Zai Koma PDP Don Takarar Shugabancin Kasa a 2027 –Inji-Ali Modu Sheriff Tsohon Gwamnan Jihar Bor...
28/07/2025

WATA SABUWA: "Peter Obi Zai Koma PDP Don Takarar Shugabancin Kasa a 2027 –Inji-Ali Modu Sheriff

Tsohon Gwamnan Jihar Borno, Sanata Ali Modu Sheriff, ya tabbatar da cewa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a zaben 2023, Peter Obi, na shirin komawa jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) domin yin takarar shugaban kasa a zaben 2027.

Ya bayyana hakan ne yayin wata hira da ya yi da Channels Television a daren Litinin.

“A game da wannan siyasa, su (ADC) babu su a cikin lissafi. Bayanai da nake da su sun nuna cewa ko da yaushe daga yanzu, Peter Obi zai koma PDP kuma zai tsaya takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar,” in ji shi.

A baya-bayan nan, dattijo kuma daya daga cikin wadanda s**a kafa PDP, Farfesa Jerry Gana, ya bayyana cewa jam’iyyar ta fara tattaunawa da Peter Obi da wasu fitattun ‘yan siyasa daga Kudu gab da zaben 2027.

Farfesa Gana, wanda ya taba rike matsayin Ministan Yada Labarai, ya ce PDP na kokarin sake gyara kanta kuma tana nazarin abubuwan da s**a faru a zabukan fidda gwani na baya domin daukar sabbin matakai.

Jita-jitar dawowar Obi PDP ta kara karfi bayan rahotanni sun bayyana cewa jam’iyyar na iya bai wa yankin Kudu tikitin shugaban kasa a 2027.

Hakan ya kara kara da wutar rade-radin ne bayan Mataimakin Sakataren Yada Labarai na PDP na kasa, Ibrahim Abdullahi, ya bayyana Peter Obi a matsayin “muhimmin jigo” ga jam’iyyar.

DA DUMI-DUMI: Shugaban ƙaramar hukumar Malumfashi Jihar Katsina Hon: Muntari Abdullahi, ya bada kyautar sabbin motoci bi...
28/07/2025

DA DUMI-DUMI: Shugaban ƙaramar hukumar Malumfashi Jihar Katsina Hon: Muntari Abdullahi, ya bada kyautar sabbin motoci biyu ga mataimakinsa da shugaban kansilolin ƙaramar hukumar.

Kyautar motocin wanda shugaban yabayar yau ɗaya ga mataimakin,sa Hon: Muntari Ado Dayi, ɗayar kuma ga shugaban ƙansiloli Hon: Nura Musa Imam, dukka bisa umarnin mai girma gomna ne da yasa a basu dan saukaka musu aiki da hidundumun ofishin su.

Daga: Kamala Bala Kamalancy

KAJI RABO: A karon farko an samu mutumin da bai taɓa cin haram ba a ma'aikatan gwamnati a Najeriya.Na kafa kwamitin da z...
28/07/2025

KAJI RABO: A karon farko an samu mutumin da bai taɓa cin haram ba a ma'aikatan gwamnati a Najeriya.

Na kafa kwamitin da zai riƙa bincikata a matsayina na Shugaban Kotun Kula da Ɗa’ar Ma’aikata a Najeriya kuma ni ban san daɗin gado ko katifa ba a ƙasa nake kwana tsawon shekaru 35 dana shafe ina aikin gwamnati, yanzu har nayi ritaya ko mota ban da ita.

Motar office ɗina ma ƙarfe 4 na yamma na yi nake ajeye ta in hau motar haya zuwa gida, tunda nake ban taɓa ci haram ba—In ji Barista Mainasara Umar Kogo k**ar yadda ya bayyana a firarsa da sashin Hausa na RFI

Muna fatan Allah ya ƙaro mana irinsu a Najeriya

AURE MARTABA: Kyawawan Hotunan Ango Abdul Jalil Da Amaryarsa Nana AminatuAllah Ya Kawo Kazantar Ɗaki!Hotuna 📸:kapital_sh...
28/07/2025

AURE MARTABA: Kyawawan Hotunan Ango Abdul Jalil Da Amaryarsa Nana Aminatu

Allah Ya Kawo Kazantar Ɗaki!

Hotuna 📸:kapital_shot

Hon. Ibrahim Danjuma Machika Ya Sake Neman A Gina Babbar Asibitin (General Hospital) A Karamar Hukumar Sabuwa, Domin Ing...
28/07/2025

Hon. Ibrahim Danjuma Machika Ya Sake Neman A Gina Babbar Asibitin (General Hospital) A Karamar Hukumar Sabuwa, Domin Inganta Harkokin Lafiya Al'umma.

Ɗan Majalissa mai Wakiltar ƙaramar hukumar Sabuwa Jihar Katsina Hon. Ibrahim Danjuma Machika, Ya gabatar da ƙudurin tuni ga ɓangaren zartaswa, in da ya nemi Gwamnati da ta faɗaɗa gami da daga Darajar ƙaramar asibitin garin Sabuwa zuwa Babban Asibitin Jiha (General Hospital), Ranar Litinin July 28th, 2025.

A nashi jawabin, yace ƙaramar hukumar Sabuwa, tana da yawan Al’umma, kuma rashin Babban Asibitin na cikin abinda ke damun ƙaramar hukumar, mayar da Asibitin Babba, zai sauƙaƙawa Al’ummar garin, sannan ya haɓɓaka harkar neman lafiya, duba da wannan na cikin ƙudurorin da Gwamnatin Malam Dikko Umaru Radda PhD, ta sanya a gaba

Ƙudurin ya samu goyan baya da ga mambobin Majalissar, in da Kakakin Majalissa, Rt. Honourable Nasir Yahaya FISS, ya bada umarni da a turashi zuwa ga ɓangaren zartaswa, domin ayi duba akai.

Hotuna📸KTHA

ADALIN SHUGABA: "Tabbas Gwamna Abba K. Yusuf Na Daban ne A cikin Gwamnonin Ƙasar Nan"Daga Abubakar Shehu Dokoki .Biyo ba...
28/07/2025

ADALIN SHUGABA: "Tabbas Gwamna Abba K. Yusuf Na Daban ne A cikin Gwamnonin Ƙasar Nan"

Daga Abubakar Shehu Dokoki .

Biyo bayan Cece-kuce da nuna halin da makarantun Jihar Kano suke ciki, wanda dan Bello yayi, jama'a dayawa sun tofa albarkacin bakinsu, wasu sun s**an matakin na dan Bello wasu suna zagi, da maganganu dai kala-kala.

Kwatsam sai akaga Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ziyarci ɗaya daga cikin waɗannan Makarantun da ake ƙorafi akansu, ko kunsan menene ya Burgeni Gameda matakin da Gwamnan ya ɗauka?

Bakowanne mutum ne yake yarda da idan anyi kuskure, tabbas kuskure bane, karɓar gyara yanada wahala koda acikin yan uwanmu talakawa, bare kuma Gwamna guda, wanda yake da ikon samun hanyoyin wanke gwamnatin sa, k**a daga jaridu da muƙarraban gwamnati, amma Abba bai zaɓi wannan hanyar ba.

Da yawa fa wasu acikin gwamnatin wannan matakin baiyi musu daɗi ba, wasu burinsu a fito a ƙaryata, wasu burinsu ace an k**a Dan Bello an nuna masa ƙarfin gwamnati, wasu burinsu a ƙyalesu Suyita kare gwamnati, amma ina! Gwamna Abba Kabir Yusuf bai zaɓi wannan hanyar ba.

Tabbas Kanawa sunyi dacen gwamna daidai da zamani, wanda koda wasa yaji matsala nan take zakaga yaje wajen ɗaukar mataki, jama'a dole muyi masa uzuri kowa yasan yadda gwamnati take, bakowanne gwamna ne yake sanin irin wannan matsalar ba, saboda faɗi da girman gwamnati, gakuma yan komai kayi daidai ne na cikin gwamnati , na tabbata kasancewar gwamna Abba yana Bibiyar al'amuran social media, hakan yana taimaka masa matuƙa wajen magance wasu matsalolin.

Wanene Yafi burgeku acikinsu, gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf kokuma Dan Bello ?

Allah Ya ƙara kawo mana Cigaba mai ɗorewa, AMEEN .

SHAWARA: 'Ya k**ata hankalin mai saran kaba ya koma ga rina!Lokaci ya yi da za mu faɗawa kanmu gaskiya, Kasar Nijeriya m...
28/07/2025

SHAWARA: 'Ya k**ata hankalin mai saran kaba ya koma ga rina!

Lokaci ya yi da za mu faɗawa kanmu gaskiya, Kasar Nijeriya musamman ta Arewa gyaran tarbiyya shi ne babban abun da take buƙata, matuƙar ba mu samu wayewar kan yadda za mu mu'amalanci juna ba, har abada ba wani abun kirki da za mu iya ƙulla wa yayi tasiri'

'Saɓanin ra'ayi ba illa ba ne ballantana ya zama abun gaba ko ƙullatar juna'

Karatu ne ga mai hankalin ganewa!

Shawarar Matashin Dan Jarida Mai Aiki A Kasar China Nura Ishaq Banye Ga Matasan Najeriya

28/07/2025

Domin Tabbatar Jaridar Karaduwa Post, Ta Al'umma Ce
Ka Zaɓi Wani Aiki Ka Bamu Zamuyi,
Bamu Da Bangare
Wajen Aiki..

TALLAFI: Abin Burgewa Gwamnan Jihar Yobe Mai Mala Buni Ya Shirya Kaddamar da Gwangwaje Al'ummarsa Da Sabon Tallafin Noma...
28/07/2025

TALLAFI: Abin Burgewa Gwamnan Jihar Yobe Mai Mala Buni Ya Shirya Kaddamar da Gwangwaje Al'ummarsa Da Sabon Tallafin Noma na Shekara Bana

A wani yunkuri na ci gaba da bunkasa harkar noma da karfafa gwiwar manoma a karkara, Mai Girma Gwamnan Jihar Yobe, Hon. (Dr.) Mai Mala Buni, CON, zai kaddamar da wani sabon Babban Shirin Tallafin Noma domin kakar noman shekarar 2025.

Za'a gudanar da wannan muhimmiyar kaddamarwa gobe Talata, 29 ga Yuli, 2025 a filin wasa na August 27 Stadium da ke Damaturu, da misalin karfe 2:00 na rana.

Wannan sabon shiri na bana yana ci gaba ne da matakin da Gwamna Buni ya dauka a bara, inda ya kaddamar da babban shirin tallafin noma mai darajar naira biliyan 14 (₦14bn) domin bunkasa samar da abinci, samar da ayyukan yi da kuma karfafa zaman kace wando ga al’ummar jihar.

Shirin bana na 2025 zai kara daukaka wannan tsari, inda za a raba sabbin kayan aikin noma, traktoci, taki, injinan noma na hannu don karfafa noma na zamani a cikin kananan hukumomi 17 na jihar.

Gwamnatin Gwamna Buni na ci gaba da jajircewa wajen inganta noma a matsayin ginshikin tattalin arziki, ci gaban karkara, da rage talauci, musamman a wannan lokaci da kasar ke fuskantar kalubalen rashin wadataccen abinci.

Yusuf Ali
Focal Person
Digital and Strategic Communications

"Ina sane da wani ƙaton otel da tsohon ɓarawon Kano wato Abdullahi Gandollar ya gina kuɗinshi zai iya gyara duka makaran...
28/07/2025

"Ina sane da wani ƙaton otel da tsohon ɓarawon Kano wato Abdullahi Gandollar ya gina kuɗinshi zai iya gyara duka makarantun Kano"-Inji Sowore

Fitaccen dan Jarida Mai rajin samar da Shugabanci nagari a Najeriya, Omoyele Sowore Ya Zargi Dr. Abdullahi Umar Ganduje da gina wani katafaren Otel na gani na fada.

A cewar Sowere, Girman Otel din zai iya gyara makarantun jihar Kano gaba ɗaya.

Dan jaridar Ya bayyana haka ne cikin wani rubutu da Ya wallafa a shafinsa na Facebook da cewa "Ina sane da wani ƙaton otel da tsohon ɓarawon Kano wato Abdullahi Gandollar ya gina. Wannan otel kuwa tana da titin Ƙasa, inji Sowere.

KAJI KO: Tsohon Gwamnan Jihar Adamawa Sen Bindow Jibrilla ya yi rajista ya karbi katinsa na ADC a Garin Mubi dake Jihar ...
28/07/2025

KAJI KO: Tsohon Gwamnan Jihar Adamawa Sen Bindow Jibrilla ya yi rajista ya karbi katinsa na ADC a Garin Mubi dake Jihar Adamawa.

DA DUMI-DUMI: Gwamnatin Tarayya Ta Yabi Super Falcons A Matsayin Zakarun AfrikaGwamnatin Tarayyar Najeriya a yau ta shir...
28/07/2025

DA DUMI-DUMI: Gwamnatin Tarayya Ta Yabi Super Falcons A Matsayin Zakarun Afrika

Gwamnatin Tarayyar Najeriya a yau ta shirya kyakkyawar tarba ga 'yan ƙwallon mata, wato Super Falcons, bayan dawowar su daga Rabat, babban birnin ƙasar Morokko, inda s**a lashe gasar Kofin Afrika na Mata ta CAF ta shekarar 2024 a matsayin zakarun Afrika.

A cikin wata sanarwa, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana nasarar a matsayin fiye da cin gasar wasanni kawai, yana mai cewa, “nasarar wata shaida ce ta jajircewa, ƙwazo, da ƙarfin gwiwar 'yan Nijeriya wadda Super Falcons ta nuna.”

Da yake jawabi a madadin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da Gwamnatin Tarayya, Ministan ya yaba wa 'yan wasa, da masu horaswa da tawagar ma'aikatan su bisa jajircewar su da sadaukarwar su.

Ya ce: “Kun zamo abin koyi ga matasa a Nijeriya, kuma kun nuna irin tasirin da wasanni suke da shi wajen haɗa kan jama’a da kuma ƙarfafa gwiwa.”

Ya ƙara da cewa gwamnatin Tinubu tana da cikakken ƙudiri wajen ci gaba da saka jari a fannin wasanni da tallafa wa ‘yan wasa, ta hanyar samar da ababen more rayuwa da matakan da za su ba su damar yin fice.

Yayin da Super Falcons ke shigowa Abuja, ministan ya buƙaci 'yan Nijeriya da su fito su tarbi ƙungiyar a lokacin tafiyar da za su yi daga ƙofar birnin Abuja zuwa Dandalin Eagle har zuwa Fadar Shugaban Ƙasa, inda za a karɓe su a hukumance.

“Super Falcons sun ɗaga tutar Nijeriya sama, sun kuma kawo farin ciki ga miliyoyin ‘yan ƙasa. Barkan ku da dawowa, zakarun Afrika!” inji shi.

A ranar Asabar dai Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Super Falcons ɗin murna kan nasarar da s**a samu a gasar.

A takardar sanarwa wadda Mai ba Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Yaɗa Labarai, Mista Bayo Onanuga, ya rattaba wa hannu, Tinubu ya ce, "Gagarumar nasarar da Super Falcons s**a samu a daren yau a Rabat, inda s**a zo daga 'yan sahun baya s**a buge Marokko da ke da ƙarfi kuma a gaban 'yan kallo masu shauƙi, alama ce ta jan halin da 'yan Nijeriya suke da shi.

"Tare da aiki tukuru, sadaukarwa da jajircewar, kun cimma nasarar da ƙasar nan take fatan samu kuma take addu'a a kai. Ƙasar nan tana sa ran yin kyakkyawar tarba ga gwarzayen mu. Muna murna! Nijeriya tana ɗokin ku."

Address

Funtua

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Karaduwa Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share