05/06/2026
Reply da nayi wa wani daga cikin abokan mu a wannan kafar ta Facebook akan Kwankwasiyya.
Matsaya ta kenan akan yarfe da kokarin mayar da masoya Kwankwaso marasa daraja.
Da farko dai ni ba dan kwankwasiyya bane.
Zage-zage kuma ya danganta da tarbiyyar da mutum yayi wa kan shi a lokacin musayar magana.
Ko wane bangare akwai masu irin wannan dabi’ar, ba iya yan kwankwasiyya bane. Wata kila saboda baka tare da su ne ka kasa ganin na sauran bangarorin.
Amsar tambayar ka kuma, ga shi a taikace.
Don suna neman goyon bayan al’umma baya nufin su ja baki suyi shiru ayi musu kage da yarfe, ramawar da sukeyi ne yake wa wasu zafi kuma hakan ba laifi bane. Idan basu da zarrar fatattakar abokan adawa da baki to aya kake tunanin zasu iya jan ragamar kasar irin Nigeria.
Baka son mutum, Fine. Idan ya ki ka, bashi da laifi.
The same mutanen da ke kukan yan kwankwasiyya suna wuce gona da irin sune dai suke fara takalarsu.
Minene laifin yan kwankwasiyya don sun rama? Ko ramuwar ma kune zaku nuna musu yadda zasuyi?
NOTE: Wannan hoton kuma na dauke shi ne a shekarar 2023 a dakin wasu abokaina yan kwankwasiyya.
Ina son Kwankwaso amma babu wani dan siyasa da nake kallo a matsayin alkibilata. Sannan nayi sharing wannan reply din ne saboda mutane masu fassara irin ta kallon aibun yan kwankwasiyya ba tare da yin adalci ba su yi wa Allah su rage munafunci.