GDK TV

GDK TV Wannan gidan talabijin din, mun bude ta ne domin fadakar da al'umma, wayarwa, da nishadantarwa.

Da Dumi-Dumi: BUK ta zaɓi Farfesa Haruna Musa a matsayin sabon shugaba Jami'ar Bayero ta Kano, ta zabi Farfesa Haruna Mu...
01/07/2025

Da Dumi-Dumi: BUK ta zaɓi Farfesa Haruna Musa a matsayin sabon shugaba

Jami'ar Bayero ta Kano, ta zabi Farfesa Haruna Musa a matsayin sabon shugaban jami'ar.

Musa ya zama shugaban ne bayan jami'ar ta gudanar da zaɓe tsakanin ƴan takarar kujerar a yau Talata a harabar jami'ar.

Ga jerin yadda sakamakon zaɓen ya kasance:

1. Farfesa Haruna Musa = 853
2. Farfesa Mahmoud Umar Sani = 367
3. Farfesa Muhammad Sani Gumel = 364
4. Farfesa Adamu Idris Tanko = 161
5. Farfesa Bashir Muhammad Fagge = 18

HOTUNA: Tawagar Dr. Abdullahi Umar Ganduje a birnin Madinah inda zasu halarci jana'izar Alh Aminu Ɗantata bayan sallar l...
01/07/2025

HOTUNA: Tawagar Dr. Abdullahi Umar Ganduje a birnin Madinah inda zasu halarci jana'izar Alh Aminu Ɗantata bayan sallar la'asar a yau.

An kafa kwamitin da zai ba da shawarar yadda za a kirkiri karin masarautu a jihar BauchiGwamnan jihar Bauchi Bala Mohamm...
01/07/2025

An kafa kwamitin da zai ba da shawarar yadda za a kirkiri karin masarautu a jihar Bauchi

Gwamnan jihar Bauchi Bala Mohammed ya amince da kafa wani kwamiti mai mutune 41 domin duba shawarwarin da s**a shafi kirkiro sababbin masarautu da za su ba da damar a nada karin sarakuna, hakimai da magaddai a a fadin jihar.

Yadda tawagar Gwamnatin Shugaba Tinubu ta mika sakon ta'aziyyarta ga iyalan marigayi Alh. Aminu Dantata a garin Madina
30/06/2025

Yadda tawagar Gwamnatin Shugaba Tinubu ta mika sakon ta'aziyyarta ga iyalan marigayi Alh. Aminu Dantata a garin Madina

Jirgin Rano Air ya gamu da matsalar inji a sararin samaniya Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Ƙasa (NCAA) ta dakat...
30/06/2025

Jirgin Rano Air ya gamu da matsalar inji a sararin samaniya

Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Ƙasa (NCAA) ta dakatar da jirgin Rano Air daga tashi daga Sakkwato zuwa Kano biyo bayan matsalar injin da ta faru lokacin yana sararin samaniya.

Daraktan hulɗa da jama'a da kare hakkin fasinjoji na NCAA, Michael Achimugu, ya ce jirgin Rano Air mai lamba 5N-BZY ya samu matsala a ɗaya daga cikin injinan sa yayin da yake sararin samaniya, amma matukin jirgin ya sauke shi lafiya.

Ya bayyana cewa an ga hayaki daga injin jirgin, wanda ya sanya aka gaggauta aiwatar da matakan tsaro, kuma NCAA ta dakatar da jirgin daga sake tashi har sai an kammala bincike.

“Jirgin Rano mai lamba 5N-BZY ya samu matsala a injin na 1. An lura da hayaki a cikin ɗakin fasinja da inda matuki ke zaune. An kunna na'urar lumfashi. An ɗauki dukkan matakan tsaro da s**a dace kafin sauka.

" Hayakin daga baya ya gushe. Matukin jirgin ya saukar da jirgin lafiya ba tare da wata matsala ba,” in ji Achimugu a cikin wata sanarwa da ya fitar a yau Litinin.

Dalilin da ya sa aka ɗage jana'izar marigayi Aminu Dantata Ministan yaɗa labarai Mohammed Idris ne ya tabbatar wa da BBC...
30/06/2025

Dalilin da ya sa aka ɗage jana'izar marigayi Aminu Dantata

Ministan yaɗa labarai Mohammed Idris ne ya tabbatar wa da BBC ɗage jana'izar sakamakon rashin isar gawar marigayin a kan lokaci zuwa birnin Madinah.

Ya ce akwai ƙa'idoji da Gwamnatin Saudiyya ta shimfiɗa kan yadda za a shigar da gawar, domin yi mata jana'iza a ƙasar, inda zuwa yanzu ake ci gaba da cike-ciken takardu tsakanin Gwamnatin da iyalan mamacin.

Mohammed Idris ya ce idan an kammala za a ɗauko gawar daga Dubai zuwa Saudiyya.

Gwamnan Kano ya jagoranci tawogar Kano da Jigawa zuwa halartar jana'izar Dantata a Madina Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abb...
30/06/2025

Gwamnan Kano ya jagoranci tawogar Kano da Jigawa zuwa halartar jana'izar Dantata a Madina

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya tashi daga Filin Jirgin Sama na Malam Aminu Kano, inda yake jagorantar wata babbar tawaga domin halartar jana’izar fitaccen attajiri kuma dattijon kasa, marigayi Alhaji Aminu Alhassan Dantata, a birnin Madina mai alfarma, da ke Kasar Saudiyya.

Marigayin ya rasu da safiyar Asabar a birnin Abu Dhabi na Hadaddiyar Daular Larabawa.

Wannan bayanin na cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar.

Tawagar tana dauke da Sarkin Kano, Khalifa Muhammadu Sanusi II, Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Umar Namadi, tsohon gwamnan Jigawa Barr. Ali Sa’ad Birnin Kudu, da wasu manyan jami’an gwamnati da fitattun dattawan jihar.

Da ya ke jawabi kafin tafiya daga filin jirgin sama, Gwamna Yusuf ya bayyana marigayi Dantata a matsayin “uba ga mutane da dama, wanda kyautatawarsa da kishinsa ga dan Adam s**a wuce kima da iyaka.”

Gwamnan ya jaddada cewa halartar tawagar Kano a jana’izar da za a gudanar a Madina na nuni da irin girmamawa da godiya da al’ummar Kano ke da ita ga marigayin da irin gudummawar da ya bayar a rayuwarsa.

Ana sa ran jana’izar za ta ja hankalin wakilan jihohi da na gwamnatin tarayya, ‘yan uwa da abokan arziki, masana addini da masoya daga sassa daban-daban na duniya, dukkansu domin yin addu’a da neman gafara ga marigayin.

Mazauna karamar hukumar Isa dake jihar Sokoto sun nuna damuwarsu kan barazanar da fitaccen dan binidigar Bello Turji.Maz...
29/06/2025

Mazauna karamar hukumar Isa dake jihar Sokoto sun nuna damuwarsu kan barazanar da fitaccen dan binidigar Bello Turji.

Mazauna karamar hukumar sun roki gwamnatin jihar da hukumomin tsaro da su ba su kariya cikin gaugawa.

Wani mai aski, Abubakar Isa, ya bayyana lamarin a matsayin abin tayarda hankali, yana mai tambayar yadda mai laifi zai iya yanke hukunci ga ‘yan kasa masu bin doka da oda.

“Muna shan wahala a kasarmu, ba za mu iya cigaba da rayuwa cikin barazana daga Turji ba," in ji Abdullahi Isa

Gobe Litinin Za'a Binne Alh. Aminu Dantata A Madina:A gobe Litinin ne za’a gabatar da gawar marigayi Alh Aminu Dantata a...
29/06/2025

Gobe Litinin Za'a Binne Alh. Aminu Dantata A Madina:

A gobe Litinin ne za’a gabatar da gawar marigayi Alh Aminu Dantata a baban Masallacin Madinah domin yi masa Jana‘iza bayan amincewar da hukumomin kasar Saudiyya s**ayi, kamar yadda iyalan Marigayin s**a bayyana.

Allah yagafarta masa

Za a binne Dantata a Madina kamar yadda ya bar wasiyya - Iyali Iyalin marigayi Alhaji Aminu Dantata da ya rasu a jiya Ju...
28/06/2025

Za a binne Dantata a Madina kamar yadda ya bar wasiyya - Iyali

Iyalin marigayi Alhaji Aminu Dantata da ya rasu a jiya Juma'a a Dubai sun bayyana cewa ya bar musu wasiyya cewa a binne shi a birnin Madina, Saudi Arebiya.

Majiyoyi daga iyalin marigayin sun gabatar da cewa ya bada wasiyyar a binne shi kusa da mai dakin sa a Madina.

Hakazalika Majalisar Malamai ta Jihar Kano ta sanar da sanarwar gudanar da sallar jana'iza ga a marigayi Aminu Dantata a yau Asabar.

A wata sanarwa da ta fitar, majalisar ta ce za a yi salatun ga'ib, wato sallar mamaci ba tare da gawar tana nan ba.

Za a yi sallar a masallacin Umar Bin Kattab dake Dangi a birnin Kano a yau Asabar da misalin karfe 2 na rana.

Sanarwar ta yi kira ga al'umma da su yi tururuwa don gudanar da sallar da kuma addu'a ga mamacin.

INNALILAHI WA INNA ILAHI RAJI'UUN!Allah ya yi wa shahararren mai kudin nan dan asalin jihar Kano Alhaji Aminu Alhassan D...
28/06/2025

INNALILAHI WA INNA ILAHI RAJI'UUN!

Allah ya yi wa shahararren mai kudin nan dan asalin jihar Kano Alhaji Aminu Alhassan Dantata rasuwa da misalin karfe 3:am a birnin Abu Dhabi.

Yanzu-yanzu Allah madaukakin sarki ya karbi rayuwar shahararren mai kudin nan dan asalin jihar Kano Alhaji Aminu Alhassan Dantata.

Abubakar Dalori Ya Maye Gurbin Ganduje a Matsayin Shugaban Riko na Jami'ar APC Bayan SaukarsaBayan murabus ɗin Dr. Abdul...
27/06/2025

Abubakar Dalori Ya Maye Gurbin Ganduje a Matsayin Shugaban Riko na Jami'ar APC Bayan Saukarsa

Bayan murabus ɗin Dr. Abdullahi Umar Ganduje daga kujerar Shugaban Ƙasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Hon. Abubakar Dalori ya zama sabon Shugaban riko na jam’iyyar.

Dalori, wanda ya kasance Mataimakin Shugaban Ƙasa (Mai wakiltar Arewa) na jam’iyyar APC, yanzu shine zai jagoranci al’amuran jam’iyyar har zuwa lokacin babban taro da aka tsara zai gudana a watan Disamba na shekarar 2025.

Ganduje ya ajiye aikinsa a ranar Juma’a, 27 ga Yuni, saboda matsalolin Rashin lafiya, lamarin da ya zo ba tare da wani hasashe ba. Wannan ya buɗe kofar jagoranci na wucin gadi, inda Dalori zai kula da tafiyar da jam’iyyar a halin yanzu.

A matsayin sabon Shugaban riko, Dalori zai sa ido wajen tabbatar da ɗa’idaiton cikin gida, shiryawa babban taron jam’iyya, da kuma tabbatar da zaman lafiya tsakanin ɓangarori daban-daban na APC.

Address

Gadaka

Telephone

+2348082396404

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when GDK TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category