GUDI MEDIA TV

GUDI MEDIA TV Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from GUDI MEDIA TV, TV Channel, Gadaka.

04/06/2026

Ai ko biri ne mai kuɗi gwara ki ɗauka.

Gwamnan jihar Agadez Janar IBRA Boulama ya sanar cewa wasu matafiya sun rasu a yankin iyakar Nijar da Mali da Aljeriya t...
04/06/2026

Gwamnan jihar Agadez Janar IBRA Boulama ya sanar cewa wasu matafiya sun rasu a yankin iyakar Nijar da Mali da Aljeriya tazarar km 80 a yammacin Asamaka.

Bayanan farko farko sun yi nuni da cewa babbar motar da ke dauke da mutunen da aka kyasta cewa sun haura 40 ta yi batan kai a dokar daji lamarin da ya haddasa karancin ruwan sha abin nufi sun mutu ne sanadiyar ishurwa.

Shugaban karamar hukumar Arlit laftana kanal Almoustapha Ousmane ya jagoranci wata tawwagar jami'ai domin tantance zahirin abin da ya faru.

A cewar wasu shaidu motar ta taso ne daga kauyen Telhandek da ke a km 300 da iyakar Nijar dauke da wasu 'yan kasar a kan hanyar zuwa gida domin shagulgulan sallar layya kafin dreban ya yi batan Kai a hamada.

Motar ta lalace ba kuma ruwan Sha a wani lokacin da ake fuskantar matsanancin yanayin zafi.

A kalla mutane 49 ne aka yi jana'izar su a wurin da abin ya faru a cewar ofishin Gwamnan Agadez yayin da wasu mutane 2 daga cikin fasinjojj s**a tsira da ransu.

Tinubu zai nada ɗiyar shugaban hukumar NDLEA mukami a Nijeriya Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya miƙa sunan Dr. Z...
04/06/2026

Tinubu zai nada ɗiyar shugaban hukumar NDLEA mukami a Nijeriya

Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya miƙa sunan Dr. Zainab Marwa ga Majalisar Dattawa domin tantancewa a matsayin mamba a Hukumar Gudanarwar Hukumar Raya Yankin Neja Delta (NDDC), inda za ta wakilci shiyyar Arewa maso Gabas.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito naɗin na da nufin cike gurbin da aka samu sakamakon murabus ɗin tsohon mamba a hukumar, Hon. Abdulrazak Namdas.

Wanda ya ajiye mukaminsa a ranar 30 ga Maris, 2026, domin mayar da hankali kan burinsa na tsayawa takarar gwamnan Jihar Adamawa.

Fika/Fune wane ɗan takara zaka bai wa kuri'ar ka a zaɓen 2027?APCADCYPPGUDI MEDIA TV
04/06/2026

Fika/Fune wane ɗan takara zaka bai wa kuri'ar ka a zaɓen 2027?

APC
ADC
YPP

GUDI MEDIA TV

TIRƘASHI; Yadda aka rubuta kalmar "BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM" a jikin fostan wani ɗan takaran gomna a jam'iyyar ADC na ...
04/06/2026

TIRƘASHI; Yadda aka rubuta kalmar "BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM" a jikin fostan wani ɗan takaran gomna a jam'iyyar ADC na jihar Katsina.

Me zaku ce?

GUDI MEDIA TV

04/06/2026

Da na ba wa saurayi hakuri gwara na rabu dashi.

An tsaurara tsaro a Fadar Shugaban Ƙasa (Villa) sakamakon barazanar zanga-zangar da Omoyele Sowore ke shirin jagoranta. ...
04/06/2026

An tsaurara tsaro a Fadar Shugaban Ƙasa (Villa) sakamakon barazanar zanga-zangar da Omoyele Sowore ke shirin jagoranta. Wannan zanga-zangar na da nufin neman a ceto ɗalibai da malamai da aka sace a jihar Oyo.

Rahotanni sun bayyana cewa hukumomin tsaro sun jibge jami’ai a muhimman wurare da ke kewaye da Villa domin tabbatar da tsaro da kuma dakile duk wani abin da ka iya tayar da hankali yayin gudanar da zanga-zangar.

04/06/2026

Wane hali yanayin rashin wutan nepa ya jefa ku a inda kuke?

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya buƙaci masu neman takara da s**a shiga zaɓen fidda gwani na ja...
04/06/2026

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, ya buƙaci masu neman takara da s**a shiga zaɓen fidda gwani na jam’iyyar da su amince da sakamakon zaɓen tare da haɗa kai domin ƙarfafa jam’iyyar.

Obi ya bayyana hakan a taron NEC na jam’iyyar da aka gudanar a Abuja, inda ya ce samun masu nasara da waɗanda ba su yi nasara ba abu ne na al’ada a dimokuraɗiyya.

Ya kuma ce NDC za ta fara rangadin jihohi domin ƙarfafa mambobi da yaɗa manufofinta, tare da mai da hankali kan magance matsalolin Najeriya.

A nasa ɓangaren, shugabannin jam’iyyar sun yi kira ga masu korafi da su ci gaba da mara wa jam’iyyar baya, yayin da NEC ta amince da shirin amfani da kaɗa ƙuri’a ta lantarki a zaɓukan cikin gida nan gaba domin ƙara gaskiya da rage rikice-rikice.

Punch/ Facebook

Alhazzan Jihar Kebbi (426) daga Ƙananan Hukumomin Koko-Besse, Aliero, Bunza, Kalgo, HSS da KGO sun sauka a Filin Jirgin ...
04/06/2026

Alhazzan Jihar Kebbi (426) daga Ƙananan Hukumomin Koko-Besse, Aliero, Bunza, Kalgo, HSS da KGO sun sauka a Filin Jirgin Sama na Sir Ahmadu Bello dake Birnin Kebbi a yau Alhamis 4-6-2026 da misalin karfe 10:10 na safe

Nagari FM B/Kebbi 📷

Address

Gadaka

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when GUDI MEDIA TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category