GANYE 24

GANYE 24 Jaridar GANYE 24 Naku Mai Albarka Domin Kawo Maku Sahihan Labarai Da ɗumi-ɗumin Su (Breaking News).

SANARWA!!! Za A Gudanar Da Gasar Karatun Al-Qur’ani Ta Nana Asma’au A Ganye Jihar AdamawaKwamitin shirya gasar karatun A...
21/05/2026

SANARWA!!! Za A Gudanar Da Gasar Karatun Al-Qur’ani Ta Nana Asma’au A Ganye Jihar Adamawa

Kwamitin shirya gasar karatun Al-Qur’ani Mai Girma ta “Nana Asma’au Qur’anic Recitation Competition” reshen jihar Adamawa, ya gayyaci daukacin al’umma zuwa wajen halartar gasar karatun Al-Qur’ani karo na uku da za a gudanar a karamar hukumar Ganye da ke jihar Adamawa.

A cewar kwamitin, za a gudanar da gasar ne daga ranar 22 zuwa 24 ga watan Mayu, shekarar 2026, inda ake sa ran mahalarta daga sassa daban-daban za su nuna kwarewarsu wajen karatu da haddar Al-Qur’ani Mai Girma.

Kwamitin ya bayyana cewa, manufar shirya gasar ita ce kara bunkasa ilimin addinin Musulunci tare da karfafa matasa da yara wajen koyon Al-Qur’ani da aiki da koyarwarsa.

Haka kuma, kwamitin ya yi kira ga masu hannu da shuni da sauran jama’a da su bayar da gudunmawa domin tallafawa gudanar da wannan gagarumin aiki na alkhairi.

Kwamitin ya kara da cewa, masu bukatar karin bayani ko wadanda ke son bayar da tallafi za su iya tuntubar su ta lambobin wayar da aka tanada domin hakan.👇🏼

Account N0: 0-0-0-3-2-5-2-1-0-3
Account N-a-m-e: Nana Asma'u Quranic Recitation Competition Yola
B-a-n-k: Taj Bank.

Lambobin waya:
08131368022
08066165820

Shari’a: Kwankwaso Ya Fallasa Wadanda S**a Kai Sunansa Majalisar Dokokin Amurka Domin A Saka Masa TakunkumiJagoran jam’i...
12/05/2026

Shari’a: Kwankwaso Ya Fallasa Wadanda S**a Kai Sunansa Majalisar Dokokin Amurka Domin A Saka Masa Takunkumi

Jagoran jam’iyyar NNPP kuma tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana cewa wasu “makiya na cikin gida” ne s**a kai sunansa zuwa Majalisar Dokokin Amurka domin neman a saka shi cikin jerin wadanda za a kakaba wa takunkumi kan batun aiwatar da Shari’a a Kano.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne yayin wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Arise TV, inda ya ce abin mamaki ne yadda ake alakanta shi kai tsaye da rikicin da ya shafi dokar Shari’a, alhali kuwa tsarin ya samo asali ne tun daga jihar Zamfara kafin Kano ta bi sahu.

A cewarsa, lokacin da aka fara batun aiwatar da Shari’a a Kano a shekarar 2000, bai yi gaggawar amincewa da kudirin ba sai bayan ya gudanar da nazari mai zurfi tare da tuntubar malamai, shugabanni da masana harkokin doka.

Kwankwaso ya kara da cewa wasu mutane ma sun nuna rashin jin dadi a lokacin saboda yadda ya dauki lokaci kafin ya rattaba hannu kan dokar, yana mai cewa an bi duk hanyoyin doka da tsarin dimokuradiyya kafin dokar ta fara aiki a Kano.

Rahotanni daga Amurka sun nuna cewa wasu ‘yan majalisar dokokin kasar sun gabatar da wani kudiri mai suna Nigeria Religious Freedom and Accountability Act 2026, wanda ke neman a kakaba takunkumi ga wasu mutane da kungiyoyi bisa zargin take hakkin addini.

Sai dai magoya bayan Kwankwasiyya sun yi watsi da batun, suna masu cewa akwai siyasa a ciki, musamman ganin yadda zaben 2027 ke kara matsowa. Wasu daga cikin magoya bayan nasa sun bayyana cewa ana kokarin bata sunan Kwankwaso ne a idon kasashen duniya domin rage masa karbuwa a siyasar Najeriya.

Masu sharhi kan harkokin siyasa na ganin wannan batu na iya kara jawo muhawara tsakanin bangarorin siyasa a Arewa, musamman a daidai lokacin da ake ci gaba da tattaunawa kan hadakar jam’iyyun adawa da shirye-shiryen zaben 2027.

Daga: Daily True Hausa

12/05/2026
DA ƊUMI-ƊUMI: An Fara Raba Riguna Da Kuɗi Naira Dubu Goma Ga Matasa Domin Taron Tarbar Ɗan Takarar Gwamnan Jihar Gombe A...
30/04/2026

DA ƊUMI-ƊUMI: An Fara Raba Riguna Da Kuɗi Naira Dubu Goma Ga Matasa Domin Taron Tarbar Ɗan Takarar Gwamnan Jihar Gombe Aminu Yuguda (AG) Wanda Zai Gudana A Yau Alhamis.

Ko me kuka fahimta?

Al’ummar ƙaramar hukumar Ganye da ke jihar Adamawa na ci gaba da bayyana damuwa kan matsalar rashin ingantaccen hanyar s...
25/03/2026

Al’ummar ƙaramar hukumar Ganye da ke jihar Adamawa na ci gaba da bayyana damuwa kan matsalar rashin ingantaccen hanyar sadarwa ta kiran waya da ke addabar yankin da kewaye.

Rahotannin da GANYE 24 MEDIA ta samu daga mazauna yankin sun nuna cewa matsalar ta daɗe tana ci gaba, musamman a baya-bayan nan, inda suke fuskantar tangarda wajen yin kira ko karɓar kira, musamman a wasu lokuta na rana da dare. Wasu daga cikin mazauna sun ce sau da yawa dole sai sun matsa zuwa wasu wurare kafin su samu damar yin kira cikin sauƙi.

Mazauna yankin sun bayyana cewa matsalar na shafar harkokinsu na yau da kullum, ciki har da kasuwanci, sadarwa tsakanin iyalai, da kuma harkokin gaggawa. Sun ce a lokutan da ake buƙatar kiran gaggawa, kamar lokacin rashin lafiya ko haɗari, rashin network na iya janyo babbar illa.

Haka kuma, wasu matasa da ‘yan kasuwa sun koka cewa matsalar na rage musu damar gudanar da sana’o’insu da s**a dogara da sadarwa, musamman a wannan zamani na fasaha.

Al’ummar yankin na kira ga hukumomin da abin ya shafa da kamfanonin sadarwa da su gaggauta ɗaukar matakan gyara, domin samar da ingantaccen network da zai sauƙaƙa rayuwar jama’a tare da bunƙasa tattalin arziƙin yankin.

Sai dai zuwa yanzu ba a samu wata sanarwa kai tsaye daga kamfanonin sadarwa ba dangane da matsalar a yankin.

HUBBUL QUR’AN TV Na Farin Cikin Gayyatar Ku Zuwa Wajen Taron Ta Na Shekara-shekara Da Ta KeyiMuna farin cikin gayyatarku...
23/03/2026

HUBBUL QUR’AN TV Na Farin Cikin Gayyatar Ku Zuwa Wajen Taron Ta Na Shekara-shekara Da Ta Keyi

Muna farin cikin gayyatarku zuwa ga, Annual National Qur’anic Conference

Wanda zai gudana Kamar haka 👇👇

🗓 Rana: 24th March, 2026
⏰ Lokaci: 10:00am – 4:00pm
📍 Wuri: Muhammadu Inuwa Yahaya Multipurpose Hall, Dukku

Wannan taro zai haɗa manyan malamai da masu karatun Al-Qur’ani domin faɗakarwa, ilmantarwa da ƙarfafa zumunci tsakanin al’umma.

🤲 Kada ku bari a baku labari ku zo ku amfana!

Allah ya bada ikon halarta

Ziyarar Mataimakin Shugaban Ƙasa: Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Adamawa ta kammala shirye-shiryen tsaroRundunar ‘Yan Sand...
22/03/2026

Ziyarar Mataimakin Shugaban Ƙasa: Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Adamawa ta kammala shirye-shiryen tsaro

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Adamawa ta sanar da kammala dukkan shirye-shiryen tsaro domin tabbatar da zaman lafiya da tsaron jama’a gabanin, yayin da kuma bayan ziyarar Mataimakin Shugaban Ƙasa da ake sa ran zai kai a ranar Litinin, 23 ga Maris, 2026.

A cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, SP Suleiman Yahaya Nguroje ya fitar, ya ce Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar, CP Dankombo Morris, ya jagoranci tsara tsare-tsaren tsaro tare da bayar da umarni ga dukkan shugabannin yankuna, DPOs, kwamandojin rundunonin musamman da shugabannin sassa domin tabbatar da aiwatar da ingantaccen tsaro.

Sanarwar ta bayyana cewa an riga an yi cikakken bayani ga jami’an tsaro tare da tura kayan aiki da jami’ai a wurare masu muhimmanci, inda aka mayar da hankali kan aikin leƙen asiri, tsaron kai tsaye, da kuma haɗin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro daban-daban.

Daga cikin matakan da aka ɗauka akwai ƙarfafa aikin tattara bayanan sirri da sanya ido a wuraren da Mataimakin Shugaban Ƙasar zai ziyarta da hanyoyin da zai bi. Haka kuma, an girke tsauraran matakan tsaro a filin jirgin sama tare da tura jami’an rundunar PMF da na yaƙi da ta’addanci (CTU).

Bugu da ƙari, rundunar ta baza jami’anta a wuraren taro, manyan gine-ginen gwamnati da sauran muhimman ababen more rayuwa, yayin da aka umarci jami’an sintiri su rika kula da manyan hanyoyi da mashigai da ficewa daga jihar, tare da ƙara yawan sintiri a cikin birnin Yola.

Har ila yau, an tanadi tsarin kula da zirga-zirgar ababen hawa domin tabbatar da tafiya cikin tsari, tare da tura ƙwararrun jami’an EOD masu gano abubuwan fashewa domin share hanya da tsaftace wuraren da za a gudanar da taruka.

Rundunar ta ce tana aiki kafada da kafada da sauran hukumomin tsaro da s**a haɗa da Sojojin Najeriya, Rundunar Sojin Sama, DSS, NSCDC, FRSC da NDLEA domin tabbatar da ziyarar ta gudana cikin lumana ba tare da wata matsala ba.

Kwamishinan ‘Yan Sandan ya kuma gargadi jami’ansa da su kasance masu bin doka da oda, ladabi da mutunta jama’a yayin gudanar da aikinsu, tare da nuna ƙwarewa da tsantseni.

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Adamawa ta tabbatar wa al’ummar jihar aniyar ta na kare rayuka da dukiyoyi, tare da kira ga jama’a da su ba da haɗin kai domin samun nasarar wannan ziyara.

ALLAHU AKBAR: Dandazon Musulmi na sallar idi a garin Bhopal dake kasar India
21/03/2026

ALLAHU AKBAR: Dandazon Musulmi na sallar idi a garin Bhopal dake kasar India

Lokacin Sallar Idi a Masallacin Idi na Izala dake Arewa da kasuwar dabbobi (Tiken Shanu) a karamar hukumar Ganye, jihar ...
19/03/2026

Lokacin Sallar Idi a Masallacin Idi na Izala dake Arewa da kasuwar dabbobi (Tiken Shanu) a karamar hukumar Ganye, jihar Adamawa.

Mai Jagorantar Sallah:
Sheikh Ahmad Gidado Ganye.

Mai Gabatar da Nasiha:
Ustaz Shu’aibu Idris Al-Ganyawiy.

Lokacin Gudanar da Sallah:
Karfe 10:00 na safe

Sanarwa daga: JIBWIS Social Media, Ganye Branch, Adamawa State

CIKIN HOTONA: Yadda Wajin Rufe Tafsirin Ramadan na Malama Zainab Ja'afar Mahmud ya kasance.
19/03/2026

CIKIN HOTONA: Yadda Wajin Rufe Tafsirin Ramadan na Malama Zainab Ja'afar Mahmud ya kasance.

Address

Ahmadu Bello Way
Ganye

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when GANYE 24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to GANYE 24:

Share