07/08/2026
DA ƊUMI-ƊUMI: Davido Da Bashir Ahmad Sun Yi Musayar Kalamai Masu Zafi Kan Zaɓen Osun Da Kyautar Grammy
Fitaccen mawakin Najeriya, Davido, da tsohon hadimin Shugaban Ƙasa kan kafafen sada zumunta, Bashir Ahmad, sun yi musayar kalamai masu zafi a shafin X (tsohon Twitter), lamarin da ya jawo hankalin jama'a.
Lamarin ya fara ne bayan Davido ya yi tsokaci kan wani saƙon da mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Bayo Onanuga, ya wallafa game da tattaunawar Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke. A martaninsa, Davido ya rubuta cewa: "I was there live! I witnessed history!!!"
Sai dai Bashir Ahmad ya mayar da martani, inda ya ce ya adana saƙon a matsayin hujja, yana mai cewa idan sak**akon zaɓen gwamnan Osun na ranar 15 ga Agusta bai tafi yadda Davido ke fata ba, zai dawo ya tunasar da shi wannan rubutu.
Davido ya mayar da martani da cewa Bashir Ahmad ya samu ƙuri'u 16 kacal a zaɓen fidda gwani da ya taɓa shiga. Bashir Ahmad kuma ya ƙalubalanci Davido da tambayar yawan kyaututtukan Grammy da ya taɓa lashewa duk da yawan zaɓen da aka yi masa.
A ƙarshe, Davido ya ce ba ya auna nasara da kyauta guda ɗaya, yana mai cewa nasararsa tana cikin cika manyan filayen wasa, biliyoyin sauraron wakokinsa, tasirinsa a duniya da kuma yadda mutane ke rera wakokinsa a nahiyoyi daban-daban. Haka kuma ya soki Bashir Ahmad, yana mai cewa duk da goyon bayan gwamnati, bai samu isasshen goyon bayan jama'a a siyasa ba.
Musayar kalaman ta ci gaba da jawo cece-kuce a kafafen sada zumunta, inda magoya bayan ɓangarorin biyu ke bayyana ra'ayoyinsu kan lamarin.
Ganye24