Hasken Arewa

Hasken Arewa Domin Samun Sabbin Labaru Masu Inganci Na Gida Nijeriya dakuma Kasashen Ketare, Kucigaba da Kasancewa da Shafin Hasken Arewa (Haske Maganin Duhu).
(1)

14/08/2026
Idan Kasamu Damar Ganawa da Jarumar Tiktok Auta Autar mama, Wane Shawara Zakabata. Kurubutamana a Comment Section 👇👇👇👇👇👇...
14/08/2026

Idan Kasamu Damar Ganawa da Jarumar Tiktok Auta Autar mama, Wane Shawara Zakabata. Kurubutamana a Comment Section 👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇

‎TIRƘASHI: "Duk Ofishin Ƴansandan Da Aka Nemi Ka Biya Kuɗin Beli Kar Ka Bayar, Ka Fita Ka Kira Sufeto Janar Na Ƴansanda"...
14/08/2026

‎TIRƘASHI: "Duk Ofishin Ƴansandan Da Aka Nemi Ka Biya Kuɗin Beli Kar Ka Bayar, Ka Fita Ka Kira Sufeto Janar Na Ƴansanda", In Ji Kakakin Rundunar
‎
‎Kakakin Rundunar Ƴansandan Najeriya, CSP Anietie Okokon, ya gargaɗi jama’a da ka da su biya kuɗi domin samun belin wanda aka k**a a kowane ofishin ƴansanda a faɗin ƙasar nan.
‎
‎A cewar sanarwar da Premier Radio Kano ta wallafa, Dokin Ƙarfe TV ta ruwaito, Iniedu ya ce idan aka nemi mutum ya biya kuɗin beli a ofishin ƴansanda, ya fita daga wajen cikin nutsuwa sannan ya kira babban ofishin rundunar domin kai rahoton lamarin.

Wakakeyiwa Fatan Samun Nasaran Cin Zaben Kujeran Gwamnan Jahar Gombe. A. Professor Isa Ali Pantami B. Dr. Jamil Isiyaku ...
07/08/2026

Wakakeyiwa Fatan Samun Nasaran Cin Zaben Kujeran Gwamnan Jahar Gombe.

A. Professor Isa Ali Pantami
B. Dr. Jamil Isiyaku Gwamna

DA ƊUMI-ƊUMI: Davido Da Bashir Ahmad Sun Yi Musayar Kalamai Masu Zafi Kan Zaɓen Osun Da Kyautar GrammyFitaccen mawakin N...
07/08/2026

DA ƊUMI-ƊUMI: Davido Da Bashir Ahmad Sun Yi Musayar Kalamai Masu Zafi Kan Zaɓen Osun Da Kyautar Grammy

Fitaccen mawakin Najeriya, Davido, da tsohon hadimin Shugaban Ƙasa kan kafafen sada zumunta, Bashir Ahmad, sun yi musayar kalamai masu zafi a shafin X (tsohon Twitter), lamarin da ya jawo hankalin jama'a.

Lamarin ya fara ne bayan Davido ya yi tsokaci kan wani saƙon da mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Bayo Onanuga, ya wallafa game da tattaunawar Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke. A martaninsa, Davido ya rubuta cewa: "I was there live! I witnessed history!!!"

Sai dai Bashir Ahmad ya mayar da martani, inda ya ce ya adana saƙon a matsayin hujja, yana mai cewa idan sak**akon zaɓen gwamnan Osun na ranar 15 ga Agusta bai tafi yadda Davido ke fata ba, zai dawo ya tunasar da shi wannan rubutu.

Davido ya mayar da martani da cewa Bashir Ahmad ya samu ƙuri'u 16 kacal a zaɓen fidda gwani da ya taɓa shiga. Bashir Ahmad kuma ya ƙalubalanci Davido da tambayar yawan kyaututtukan Grammy da ya taɓa lashewa duk da yawan zaɓen da aka yi masa.

A ƙarshe, Davido ya ce ba ya auna nasara da kyauta guda ɗaya, yana mai cewa nasararsa tana cikin cika manyan filayen wasa, biliyoyin sauraron wakokinsa, tasirinsa a duniya da kuma yadda mutane ke rera wakokinsa a nahiyoyi daban-daban. Haka kuma ya soki Bashir Ahmad, yana mai cewa duk da goyon bayan gwamnati, bai samu isasshen goyon bayan jama'a a siyasa ba.

Musayar kalaman ta ci gaba da jawo cece-kuce a kafafen sada zumunta, inda magoya bayan ɓangarorin biyu ke bayyana ra'ayoyinsu kan lamarin.

Ganye24

Takardar naɗin Adeniyi Adeyemi Mathew ta bogi ba ta fito daga Fadar Shugaban Ƙasa ba- Shugaban ICPC Shugaban Hukumar Yaƙ...
06/08/2026

Takardar naɗin Adeniyi Adeyemi Mathew ta bogi ba ta fito daga Fadar Shugaban Ƙasa ba- Shugaban ICPC

Shugaban Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (ICPC), Dr. Musa Adamu Aliyu, ya bayyana cewa binciken da hukumar ta gudanar ya tabbatar da cewa Adeniyi Adeyemi Mathew bai taɓa samun naɗi daga Gwamnatin Tarayya ba, kuma hukumar da ya riƙa ikirarin jagoranta mai suna "Presidential Foreign Investment Promotion Council" (PFIPC) ba ta taɓa wanzuwa a ƙarƙashin kowace doka ko umarnin gwamnati ba.

Da yake jawabi ga manema labarai a Abuja, shugaban ICPC ya ce takardar naɗin da Adeyemi ya gabatar ta jabu ce, kuma ba ta fito daga Fadar Shugaban Ƙasa ba. Ya ƙara da cewa binciken ya gano Adeyemi ya ƙirƙiri wasu hukumomi na bogi guda biyu tare da ƙirƙirar takardun doka na jabu domin buɗe asusun banki.

ICPC ta kuma bayyana cewa ba a taɓa ware ko fitar da kuɗin Gwamnatin Tarayya ga hukumar ba, kuma babu wata matsala da aka samu a tsarin aiki na Fadar Shugaban Ƙasa ko Babban Bankin Najeriya.

Hukumar ta ba da shawarar a gurfanar da Adeyemi a kotu, a hukunta jami'an gwamnati da sakacinsu ya ba shi damar gudanar da ayyukan ba bisa ƙa'ida ba, tare da aiwatar da gyare-gyaren hukumomi.

Sai dai Shugaban Hukumar ya ce har yanzu ana ci gaba da binciken dukkan ayyukansa, asusun bankinsa da kuma waÉ—anda ake zargi da haÉ—a baki da shi.

"Naƙi tayin manyan ƙungiyoyi biyu na Premier League (Chelsea da Liverpool), saboda buri na kawai shi ne in buga wa Manch...
06/08/2026

"Naƙi tayin manyan ƙungiyoyi biyu na Premier League (Chelsea da Liverpool), saboda buri na kawai shi ne in buga wa Manchester United wasa."

Cewa Youri Tielemans:

DA DUMI-DUMI: An gana tsakannin Tinubu da Khalifan Tijjaniyya na Kasa Sheikh Ibrahim Sahiru Bauchi.An yi wata Ganawar Si...
06/08/2026

DA DUMI-DUMI: An gana tsakannin Tinubu da Khalifan Tijjaniyya na Kasa Sheikh Ibrahim Sahiru Bauchi.

An yi wata Ganawar Sirri tsakannin Khalifan Tijjaniyya Sheikh Sayyadi Ibrahim Sheikh Dahiru Bauchi, Da Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu a Fadar Shugaban Kasa Dake Babban Birnin Tarayya Abuja a Jiya Laraba.

A yayin ganawar Sayyid Ibrahim, ya tattauna da Shugaban Kasar Ne Akan Wasu Batutuwa Da S**a Shafi Al'ummar Nijeriya, Tare Da Mika Masa Takardar Gayyatar Maulidin Shehu Ahmad Tijjani Wanda Za a Gudanar A Ranar Lahadi a Jihar Kano..

EFCC Ta Bayyana Dalilin Daskarar da Asusun Gwamnatin Jihar OsunHukumar Yaƙi da Yi wa Tattalin Arziki Zagon Ƙasa da Laifu...
05/08/2026

EFCC Ta Bayyana Dalilin Daskarar da Asusun Gwamnatin Jihar Osun

Hukumar Yaƙi da Yi wa Tattalin Arziki Zagon Ƙasa da Laifukan Kuɗi (EFCC) ta bayyana dalilan da s**a sa ta daskarar da asusun bankin Gwamnatin Jihar Osun, tana mai jaddada cewa matakin ba shi da alaƙa da zaɓen gwamna da ke tafe a jihar.

A cikin wata sanarwa, EFCC ta ce tun daga watan Maris na shekarar 2026 take gudanar da bincike kan zargin rashin gaskiya wajen sarrafa kuÉ—aÉ—en Ecology Fund, Intervention Funds, da kuÉ—aÉ—en rabon FAAC, waÉ—anda adadinsu ya kai Naira biliyan 11.

Hukumar ta ce a yayin binciken, ta gayyaci wasu manyan jami'an gwamnatin jihar domin amsa tambayoyi, ciki har da Akanta Janar na jihar.

Sai dai EFCC ta bayyana cewa ba za ta daskarar da asusun gwamnatin ba, da ba ta lura da yadda aka fara fitar da manyan kuÉ—aÉ—e daga asusun tun daga ranar 2 ga Agustan 2026 zuwa wasu asusun kamfanoni da ake zargi. A cewar hukumar, hakan ya sa ta É—auki matakin gaggawa na dakatar da zirga-zirgar kuÉ—aÉ—en domin kare dukiyar al'umma.

Hukumar ta jaddada cewa É—aya daga cikin nauyin da doka ta É—ora mata shi ne kare kuÉ—aÉ—en gwamnati da dukiyoyin jama'a, don haka ba za ta zura ido tana kallon yadda ake karkatar da kuÉ—aÉ—en jama'a ba.

EFCC ta kuma bayyana cewa duk da tana sane da zaɓen gwamnan Jihar Osun da ke gabatowa, hakan ba zai hana ta aiwatar da ayyukan da doka ta ba ta ba. Ta ce ba zai dace ba a yi amfani da batun zaɓe a matsayin uzuri na hana ta cika aikinta.

Har ila yau, hukumar ta bayyana cewa ba Jihar Osun kaɗai take sa ido kan harkokin kuɗinta ba, domin akwai wasu jihohi da dama da ke ƙarƙashin bincikenta domin tabbatar da gaskiya, riƙon amana da amfani da kuɗaɗen jama'a yadda ya k**ata.

A ƙarshe, EFCC ta buƙaci al'umma da su yi watsi da rahotannin ƙarya da ƙoƙarin bata sunan hukumar, tana mai tabbatar da cewa tana gudanar da aikinta ba tare da nuna son kai ko bambanci ba, kuma manufarta ita ce kare muradun dukkan 'yan Najeriya da kuma hana wawure kuɗaɗen jama'a.

Wasu daga cikin matan Kannywood mafi kamun kai a tarihin masana'antar wanda kowa yana yana yabonsu Wacece gwanar ka/ki a...
05/08/2026

Wasu daga cikin matan Kannywood mafi kamun kai a tarihin masana'antar wanda kowa yana yana yabonsu

Wacece gwanar ka/ki acikin wadannan jarumai rubuta mana a comment section 👇👇

Address

Dabo Mall, Ladoke Akintola Boulevard Street, Opp FCMB Along Old CBN, Garki 2, Abuja
Garki Ii

Opening Hours

09:00 - 17:00

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hasken Arewa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hasken Arewa:

Shortcuts

Share