Hausa Explorer

Hausa Explorer Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Hausa Explorer, Media/News Company, Garki Abuja Nigeria, Garki.

Domin samun labarin Al’ajabi, siyasa, Tsaro da hirarraki masu ƙayatarwa daga kowa ne lungu da saƙo na fadin duniya ku kasance da shafin mu na Hausa Explorer

zaku iya kiranmu a Wannan Lambar :090..............

29/07/2025

Majalisar Wasanni ta Kungiyar Tarayyar Afirka, wato African Union Sports Council, ta kai ziyara ta musamman ga shugaban Kungiyar Wasannin Sojojin Afirka OSMA da ke Abuja, domin tattaunawa da neman hadin gwiwa wajen bunkasa harkokin wasanni a nahiyar Afirka.

28/07/2025

Yadda Jagororin Sabuwar Tafiyar ADC a shiyar Arewa Maso Yamma s**a gudanar taron zaben wakilancin shugabancin Jam'iya Naka A Birnin Abuja.
Wakilan Jihohin Kano, Kaduna, Katsina, Kebbi,Jigawa, Zamfara, Sokoto.

25/07/2025

Taron masu ruwa da tsaki na karamar hukumar Gwoza dan lalubo mafita game da rikicin ta'addancin boko haram da ya addabesu.

JARUMA UMMI NUHU Rayuwar ɗan adam cike take da darussa da wa’azi. Wannan ya bayyana sosai a cikin wata hira da Hadiza Ga...
25/07/2025

JARUMA UMMI NUHU

Rayuwar ɗan adam cike take da darussa da wa’azi. Wannan ya bayyana sosai a cikin wata hira da Hadiza Gabon ta yi da tsohuwar fitacciyar jarumar fina-finan Hausa, Ummi Nuhu, wadda ta shahara sosai a zamaninta, amma yanzu ta bayyana cikin kuka da nadama.

A cikin hirar, Ummi Nuhu ta bayyana cewa yanzu tana cikin tsufa, ba ta da lafiya kuma ba ta da aure b***e ‘ya’ya da za su kula da ita. Ta ce duk damar da ta samu a lokacin da take cikin ƙuruciya ta rasa su ne saboda ta bijire wa aure tana bin rudanin duniya da jin daɗin wucin gadi. Yanzu masu lasanta sun bar ta, kuma idan ta je wani wuri kamar Abuja, babu wanda ke kula da ita kamar da.

Abin da ya fi tayar da hankali shi ne lokacin da rashin lafiya ya kwantar da ita a gadon asibiti tana fama da wahala har tana yin fitsari da ƙashi a kwance, sai ta yi tunanin inda ace tana da yara sune zasuyi hidima da ita amma ba ta haifa su ba saboda kin yin aure. Wannan ya sa nadamar ta fi ta kowacce mace girma, domin lokaci ya kure mata.

Wallahi wannan labari ya cika da darasi mai girma. Akwai mata da dama musamman a cikin masana’antar fina-finan Hausa da ke jinkirta aure ko ma gujewa gaba ɗaya domin su biye wa shagala da halayen da ba su da amfani. Amma lokaci na tafiya, kuma wata rana da za a buƙaci kulawa da tausayi daga iyali da ‘ya’ya sai su rasa su.

A karshe, wannan ya zama babban darasi ga kowace yarinya da ke tunanin bariki da shagala shi ne mafita. Duniya mai wucewa ce, kuma aure da iyali su ne garkuwar mace daga kunci na rayuwa idan lokaci ya ja.

Allah Ka ba mu ikon gamawa da duniya lafiya, Ka tsare mu daga nadamar da ba ta da amfani.

25/07/2025

Shin ashe har yanzu akwai Masu Bautar Dodo a Najeriya ?

17/07/2025

Yadda Jami'an tsaro s**a kame wasu mutane dake hanyar Zuwa karbo 'yan uwansu da akayi garkuwa dasu fiye da kwanaki 70 a Garin Dan Magori dake yankin karamar hukumar Bungudu jihar Zamfara.

Masha Allahu an basu damar zuwa dawo da 'yan uwansu.

Asusun Kula da Lafiyar Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ya bukaci gwamnatin Jihar Borno da ta ci gaba da bayar d...
17/07/2025

Asusun Kula da Lafiyar Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ya bukaci gwamnatin Jihar Borno da ta ci gaba da bayar da gudunmawarta ga Asusun Ciyar da Yara (Child Nutrition Fund CNF), wani asusu na musamman da aka kafa don yakar matsanancin rashin gina jiki a yankin arewa maso gabas.

Babban jami’in UNICEF a ofishin Maiduguri, Mista Joseph Senesie, ne ya yi wannan kiran a ranar Laraba, 16 ga Yuli, a Maiduguri yayin da yake mika katunan abinci na musamman guda 2,254 (Ready-to-Use Therapeutic Food RUTF) ga gwamnatin jihar Borno.

Ya jaddada cewa ci gaba da bayar da gudunmawar kudi zuwa CNF a wannan shekara zai taimaka matuka wajen kare lafiyar yaran da s**a fi fuskantar barazanar rashin lafiya da rashin abinci mai gina jiki a jihar.

Senesie ya bayyana cewa UNICEF ta mika katunan abincin ne don magance matsanancin rashin gina jiki da kuma biyan bukatun gina jiki ga yaran da abin ya shafa.

Ya kara da cewa an sayi abincin ne ta hanyar Asusun CNF.

Kwamishinan Lafiya da Walwalar Jama’a na Jihar Borno, Farfesa Baba Mallam Gana, wanda ya karɓi kayan a madadin gwamnatin jihar, ya gargadi jama’a da kada su sayar da abincin.

Gwamnati da UNICEF sun bayyana damuwa a watan Afrilu dangane da yadda ake satar kayayyakin abinci na tallafi, ana karkatar da su ko kuma ana sayar da su a kasuwa.

Ya yaba wa UNICEF bisa wannan gudunmawa. Ya ce fiye da yara miliyan biyu a arewa maso gabas na fuskantar matsalar rashin gina jiki.

17/07/2025

Rundunar Sojin Sama ta Najeriya ta bayyana aniyarta na tabbatar da cewa akalla 90% na jiragen saman ta za su kasance cikin koshin lafiya kafin ƙarshen shekarar 2025. Babban Hafsan Sojin Sama, Air Marshal Hasan Bala Abubakar, ne ya bayyana hakan a wani taron Injiniyan Jiragen Sama da aka gudanar a Abuja.

A cikin jawabin sa, ya ce hakan zai taimaka wajen ƙarfafa aiki da shirin tsaro, kuma yanzu haka rundunar na da kusan kashi 72% na jirage masu aiki. Ana kuma sa ran ƙara yawan jirage zuwa guda 49 kafin ƙarshen 2026.

Rundunar ta kuma ƙaddamar da sabon tsarin kula da lafiyar iragen sama (DALCM) don tabbatar da ingantaccen aiki daga lokacin shigowar jirgi har zuwa fitar sa daga amfani.

An samu halartar manyan kwararru da s**a gabatar da muhimman bayanai kan gyare-gyare da dabarun fasaha na zamani domin ciyar da rundunar gaba.

16/07/2025

Yadda Mallam Adam Ashaka yake Da'awar Yada Addinin Musulunci ga kristoci da littafin Bible a wasu sassa na ƙasar Najeriya.

Sakon Ranar  Yawan Jama'a ta Duniya  a 2025Taken Ranar: Ba wa Matasa Dama Su Gina Iyalan da S**a Dace a Duniya Mai Adalc...
14/07/2025

Sakon Ranar Yawan Jama'a ta Duniya a 2025
Taken Ranar: Ba wa Matasa Dama Su Gina Iyalan da S**a Dace a Duniya Mai Adalci Cike da Fata"

Ranar Yawan Jama'a ta Duniya ta bana tana jaddada muhimmancin matasa a matsayin ginshiƙin ci gaban al’umma. Yanzu ne lokacin da ya kamata shugabanni su mayar da hankali wajen samar da sahihin bayani da sabis na lafiyar haihuwa ga matasa, domin su samu damar yanke shawara da ta dace da rayuwarsu. Wannan ba kawai batun lafiya ba ne a'a batune na haƙƙinsu.

Muna kira ga gwamnati, shugabanni da ƙungiyoyi da su ƙara zuba jari a fannonin ilimi, lafiyar jiki da ta tunani, da kuma tsara manufofi da ke tallafa wa matasa. Idan aka ba matasa ilimi da dama, tare da goyon baya, za su iya zama jagororin canji a cikin al’umma.

Sako guda, murya ɗaya: Matasa na da muhimmanci a basu dama, a saurare su.

13/07/2025

Mutuwar Buhari 😭😭

An samu wata rashin jituwa tsakanin liman da mamu bayan da limamin ya sanar da cewa za'ayi Addu'ar nema wa mai girma tsohon shugaban kasa Buhari gafara, mamu s**ace bazasuyi ba.

Ina laifin Buhari a halin da kasa take ciki da har zai fuskanci irin wannan abu ?

Shin Jahilci ne ko rashin neman a zauna lafiya ?

13/07/2025

Yanzun-Yanzun: Tifa ta fada cikin gadar Flamingo dake Minna.

Ruhotanni na tabbatar da cewar Yaron motar tifar ya rasa ransa nan take yayinda diriban da wani mutum ɗaya s**a jimu.

Address

Garki Abuja Nigeria
Garki

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa Explorer posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share