Hausa Explorer

Hausa Explorer Idan musa sake abunda ba dai-dai.

Burinmu shine kawo wani abu dake da amfani ko kyawonji da gani kuma da zasu ilimantar ko jan hankalin masu bibiyarmu, zaku iya turo mana labaranku ko kuma wani abu da kuke son mu wallafa maku a wannan number 08087136710.

Ministan Tsaro, Mohammed Abubakar Badaru ya ce Najeriya ta sake jaddada kudirinta na hana yaduwar mak**an nukiliya tare ...
26/09/2025

Ministan Tsaro, Mohammed Abubakar Badaru ya ce Najeriya ta sake jaddada kudirinta na hana yaduwar mak**an nukiliya tare da kira ga ƙasashen duniya da su gaggauta fara tattaunawa kan yarjejeniyar Fissile Material Cut-off Treaty (FMCT).

Ministan ya yi wannan kira ne a taron ministocin ƙasashen da ke goyon bayan FMCT a New York, inda ya ce hana kera kayan nukiliya zai hana yaki mara iyaka, ya kuma ƙarfafa yarjejeniyar hana yaɗuwar mak**an nukiliya.

Ya bukaci kasashen duniya su dauki mataki, musamman da wannan shekarar ke cika shekaru 80 da harin Hiroshima da Nagasaki.

Najeriya ta kuma tuna rawar da Afirka ta taka wajen hana mak**an nukiliya ta hanyar yarjejeniyar Pelindaba, tare da neman irin wannan tsari a duniya baki ɗaya.

Badaru ya ce rage mak**an nukiliya zai ba da damar amfani da albarkatun kasa a bangaren lafiya, ilimi da cigaban tattalin arziki, tare da goyon bayan shirin Renewed Hope Agenda na Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

25/09/2025

Yadda aka gudanar da Taron Jana'izar Binne Kare Wizzy a kano.

Wasu gungun matasa a jihar Kano sunyi taron jana'izar tare da binne karensu mai suna Wizzy a safiyar yau Alhamis, bayan yamútu a daren jiya Laraba.

Matasan 'yan karamar hukumar Kabo sun shaku da karen matuka, haka tasa s**ayi jimamin rasuwar tasa.

KNC Hausa

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya umurci shugaban hukumar zaɓe ta ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, da ya gaggauta t...
24/09/2025

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya umurci shugaban hukumar zaɓe ta ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, da ya gaggauta tafiya hutu kafin ƙarshen wa’adinsa. Rahotanni sun ce wannan mataki ya samo asali ne daga abin da aka bayyana a matsayin cin amana ga gwamnatin APC da ta naɗa shi.

Majiyoyi sun ce gwamnan Imo, Hope Uzodimma, ya zargi Yakubu da ƙoƙarin rajistar sabbin jam’iyyu da kuma marawa wani ɗan takara baya a zaɓen gwamnan jiharsa.

Matakin ya kawo cikas ga ayyukan INEC, inda aka soke muhimman taruka da jam’iyyu da kungiyoyin farar hula. Ana saran nan gaba kaɗan Shugaba Tinubu zai gabatar da sunan sabon shugaban INEC ga majalisun dokokin Najeriya.

Sai dai wani binciken kwa-kwafin Sahara Reporter ya nuna tsohon gwamnan Delta, James Ibori, na ƙoƙarin tura abokinsa, Moses Ogbe, domin ya zama sabon shugaban INEC, duk da dogon tarihin zargin maguɗin zaɓe da ake danganta da shi tun shekarun 2003 da 2007.

Idan za'a iya tunawa Farfesa Yakubu ya hau kujerar shugaban INEC a shekarar 2015 bayan naɗin tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari.

24/09/2025

Ministan Tsaron Najeriya, Dr. Mohammed Badaru Abubakar, ya bukaci Ɗaliban da s**a kammala karatu a kwalejin horar da yakin sama dake Makurdi su rungumi kirkira da hangen nesa wajen fuskantar barazanar tsaron da kasar nan ke fama dashi.

Badaru wanda Babban Hafson tsaron Najeriya Janar Christopher Musa ya wakilta Ya jaddada cewa yaki da ta’addanci, garkuwa da mutane da sauran laifuka na bukatar dabaru na zamani da hadin kai tsakanin kasashe. Haka kuma, Babban Hafsan Sojin Sama, Air Marshal Hasan Bala Abubakar, ya gargadi Daliban da su tashi tsaye wajen yaki da ta’addanci cikin gaggawa.

An yaye kimanin Ɗalibai 29 bayan makonni 37 na karatu, inda Cdr PC Onah ya lashe kyautar zakara da mafi kyawun sak**ako. Wannan yaye ya zama mataki na kara gina shugabannin tsaro masu iya kare martaba da tsaron kasa.

Zaku iya Ganin yadda taron ya kasance a cikin bidiyo.

21/09/2025

A kashe ‘yan bindiga 10, gobe 20 za su fito- Kachalla Ummaru

Shahararren jagoran ‘yan bindiga, Kachalla Ummaru, ya gargadi jami’an tsaro cewa kashewa ba zai kawo karshen ta’addanci ba. A cewarsa, idan aka kashe ‘yan bindiga 10, 20 za su sake fitowa, idan aka kashe 30, fiye da hakan za su bayyana a birane da karkara.

Ya bayyana haka ne yayin taron sulhu tsakanin ‘yan bindiga da dattawan al’umma a Matazu LGA, Jihar Katsina.

Ummaru ya jaddada cewa hanyar da ba ta amfani da karfi (non-kinetic) ita ce kadai mafita.

Dattawan al’umma sun bukaci duka bangarorin da su rungumi gaskiyar sulhu domin samun zaman lafiya.

🎥:

Shin Atiku ne zai bar ADC ko su Obi da El-rufai ne zasu fita zuwa wata Jam'iyyar?Ga cikakken Labarin a Comment 👇
13/09/2025

Shin Atiku ne zai bar ADC ko su Obi da El-rufai ne zasu fita zuwa wata Jam'iyyar?

Ga cikakken Labarin a Comment 👇

Gwamnatin Abba Gida-Gida cike ta ke da barayi:ICPC ta bankado ₦1.17 biliyan da aka biya a watan Nuwamba 2023 don kwangil...
13/09/2025

Gwamnatin Abba Gida-Gida cike ta ke da barayi:

ICPC ta bankado ₦1.17 biliyan da aka biya a watan Nuwamba 2023 don kwangilar bogi.
Kwamishinan Raya Karkara da Al’umma, Abdulkadir Abdulsalam, ya amsa da kansa cewa shi ya rattaba hannu.

An biya kuɗin nan ta hannun Bureau de Change — daga asusun gwamnatin Kano aka cire, aka maida dala har $1 miliyan aka mikawa shugaban Fadar Gwamna, Abdullahi Rogo, a Abuja.

ICPC ta riga ta kwato ₦1.1 biliyan, amma wannan kawai ɓangare ne na babbar satar ₦6.5 biliyan da ake bincike a kai.

Dan Bello yace: “Lokacin da makarantu ke ruɓewa da asibitoci ke bushewa, shugabanni suna kwaɓar kuɗin jama’a cikin jakar barayi.”

Ministan Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, ta bayyana cewa ba ta ji haushi ba kan zanga-zangar da ma’aikatan ma’aik...
13/09/2025

Ministan Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, ta bayyana cewa ba ta ji haushi ba kan zanga-zangar da ma’aikatan ma’aikatarta s**a yi, inda s**a nemi a sauke ta saboda ƙin biyan bukatunsu na jin daɗin a wajen aiki.

Ta faɗa hakan ne a ganawar town hall da aka gudanar a Cibiyar Ƙasa ta Ci gaban Mata a ranar Juma’a, bayan ma’aikatan sun kulle ta daga shiga ofis a ranar Laraba 10 ga Satumba, suna rera wakokin haɗin kai.

Ministar ta ce rikicin ya ƙara mata suna fiye da da, domin a matsayinta na 'yar siyasa ta saba da zarge-zarge da rikice-rikice. Ta ƙara da cewa, lamarin ya sa ayyukan ma’aikatar sun fara samun kulawa daga jama’a fiye da da.

Kungiyar Ƴan Kasa Masu Ƙin Aiyukan Ƴan Bindiga da Rashin Tsaro a Najeriya (CABIN) ta bai wa Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal...
12/09/2025

Kungiyar Ƴan Kasa Masu Ƙin Aiyukan Ƴan Bindiga da Rashin Tsaro a Najeriya (CABIN) ta bai wa Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal, wa’adin kwanaki bakwai domin ya bayyana inda ƴan bindiga da sauran ƙungiyoyin aikata laifi ke ɓoye a faɗin jihar.

A wata sanarwa da shugaban ƙungiyar, Kwamared Solomon Charles Abutu, ya sa hannu, CABIN ta bayyana cewa furucin da gwamnan ya yi a baya-bayan nan, inda ya ce ya san inda ƴan bindigar ke zaune, alama ce ta cewa ya zaɓi yin shiru kan manyan laifukan da s**a haddasa mutuwar dubban mutane, garkuwa da jama’a, da kuma tilasta wa al’umma barin muhallansu.

Ƙungiyar ta yi gargadin cewa idan gwamnan bai yi bayani cikin wa’adin kwanaki bakwai ba, hakan zai zama tamkar haɗin baki, kuma hakan zai haifar da manyan zanga-zanga a Zamfara, Abuja da sauran sassan ƙasar. Haka kuma, ƙungiyar za ta nemi gwamnatin tarayya ta ayyana dokar ta-baci a Zamfara domin kare rayukan al’umma.

CABIN ta nuna bacin rai cewa duk da biliyoyin naira da gwamnan ke karɓa a kowane wata a matsayin kuɗin tsaro, bai samar da sak**ako wajen kare jihar daga miyagun ba.

Ta kuma zargi gwamnan da gazawa wajen cika alkawuran da ya ɗauka ga al’ummar Zamfara da s**a zabe shi a 2023. A cewar ƙungiyar.

Bugu da ƙari, CABIN ta yi kira ga Shugaba Bola Tinubu da ya sa ido kai tsaye kan abin da ke faruwa a Zamfara, tare da ɗaukar mataki kan abin da ta kira “gagarumar sakaci a nauyin da ke wuyan gwamnati,” tana gargadin cewa halin shiru zai ƙara ƙarfafa miyagun a wasu sassan ƙasar.

An k**a wani ma’aikacin Jami’ar Tarayya da ke Bayelsa bisa zargin fyade da kuma cin zarafin yara ƙanana.Cikakken Labarin...
12/09/2025

An k**a wani ma’aikacin Jami’ar Tarayya da ke Bayelsa bisa zargin fyade da kuma cin zarafin yara ƙanana.

Cikakken Labarin na Comment 👇

Ƙungiyar Likitocin Gwamnati (Resident Doctors) a Najeriya ta fara yajin aikin gargadi na kwana 5, inda s**a rufe asibito...
12/09/2025

Ƙungiyar Likitocin Gwamnati (Resident Doctors) a Najeriya ta fara yajin aikin gargadi na kwana 5, inda s**a rufe asibitoci saboda bashin alawus da kuma bashin albashi da ba a biya ba.

Update!!Gwamnan Jihar Kebbi ya saki ɗan jaridan da aka tsare saboda fallasa mummunan halinda asibitin gwamnati take ciki...
12/09/2025

Update!!

Gwamnan Jihar Kebbi ya saki ɗan jaridan da aka tsare saboda fallasa mummunan halinda asibitin gwamnati take ciki , tare da dakatar da Kwamishinan Lafiya.

Address

Garki Abuja
Garki

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa Explorer posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share