25/07/2025
JARUMA UMMI NUHU
Rayuwar ɗan adam cike take da darussa da wa’azi. Wannan ya bayyana sosai a cikin wata hira da Hadiza Gabon ta yi da tsohuwar fitacciyar jarumar fina-finan Hausa, Ummi Nuhu, wadda ta shahara sosai a zamaninta, amma yanzu ta bayyana cikin kuka da nadama.
A cikin hirar, Ummi Nuhu ta bayyana cewa yanzu tana cikin tsufa, ba ta da lafiya kuma ba ta da aure b***e ‘ya’ya da za su kula da ita. Ta ce duk damar da ta samu a lokacin da take cikin ƙuruciya ta rasa su ne saboda ta bijire wa aure tana bin rudanin duniya da jin daɗin wucin gadi. Yanzu masu lasanta sun bar ta, kuma idan ta je wani wuri kamar Abuja, babu wanda ke kula da ita kamar da.
Abin da ya fi tayar da hankali shi ne lokacin da rashin lafiya ya kwantar da ita a gadon asibiti tana fama da wahala har tana yin fitsari da ƙashi a kwance, sai ta yi tunanin inda ace tana da yara sune zasuyi hidima da ita amma ba ta haifa su ba saboda kin yin aure. Wannan ya sa nadamar ta fi ta kowacce mace girma, domin lokaci ya kure mata.
Wallahi wannan labari ya cika da darasi mai girma. Akwai mata da dama musamman a cikin masana’antar fina-finan Hausa da ke jinkirta aure ko ma gujewa gaba ɗaya domin su biye wa shagala da halayen da ba su da amfani. Amma lokaci na tafiya, kuma wata rana da za a buƙaci kulawa da tausayi daga iyali da ‘ya’ya sai su rasa su.
A karshe, wannan ya zama babban darasi ga kowace yarinya da ke tunanin bariki da shagala shi ne mafita. Duniya mai wucewa ce, kuma aure da iyali su ne garkuwar mace daga kunci na rayuwa idan lokaci ya ja.
Allah Ka ba mu ikon gamawa da duniya lafiya, Ka tsare mu daga nadamar da ba ta da amfani.