14/11/2025
TIRKASHI: Trump Ya Yi Martani Kan Salon Barkwancin ’Yan Najeriya Duk da Rikice-Rikicen Duniya
Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana ’yan Najeriya a matsayin “mutane manya” wadanda “ko da me ya faru sai sun juya shi barkwanci.”
Da yake magana yau da safe yayin wata ganawa da tawagar Najeriya a Amurka, Trump ya ce:
“Najeriya ita ce ƙasar da idan ta ji labarin yaƙi, suna fara barkwanci! Abin mamaki ne. Mutane nagari ne, amma ba su ɗauki komai da muhimmanci komai sai su juya shi wasan barkwanci.”
Shugaban ya bayyana mamakinsa kan yadda yawancin ’yan Najeriya suke fuskantar manyan matsalolin duniya da dariya maimakon firgici ko ruɗani. “Ban taɓa ganin irin haka ba. Sauran ƙasashe s**an firgita. Najeriya kuwa suna yin barkwanci. Abin dariya ne, amma kuma wani irin hauka ne,” in ji Trump cikin dariya.