Dr. Shamsuddeen Dan'uwa

Dr. Shamsuddeen Dan'uwa Health Promoter. Content Creator . YouTuber. Historics. Editor. we are ready to entertain, motivate and educate people around the world.

03/05/2025

Banga Wani Abin damuwaba don Facebook ya bar Nigeria.

Shelkwatar ƴansanda ta gaiyaci Sarki Sanusi akan kisan da aka yi a hawan sallah Shelkwatar Ƴansanda Ƙasa ta gayyaci Sark...
05/04/2025

Shelkwatar ƴansanda ta gaiyaci Sarki Sanusi akan kisan da aka yi a hawan sallah

Shelkwatar Ƴansanda Ƙasa ta gayyaci Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II domin amsa tambayoyi kan wani lamari da ya faru a lokacin bikin Sallah a Kano.

Tun da fari, rundunar ƴansanda tare da sauran hukumomin tsaro a jihar sun soke duk wani hawan sallah, musamman jerin gwanon dawaki a jihar, saboda dalilan tsaro.

Sai dai a yayin da Sarkin ke tattaki domin halartar Sallar idi a filin Idi na Kofar Mata a ranar 30 ga watan Maris, an caka wa wani dan banga da ke kare sarkin wuka har lahira, yayin da wasu da dama su ka jikkata.

Bayan faruwar lamarin, wasu majiyoyi sun shaidawa DAILY NIGERIAN cewa tun da farko babban sifeton yansanda na ƙasa, Kayode Egbetokun ya umarci kwamishinan ‘yan sandan jihar da ya k**a sarkin.

Sai dai kuma majiyoyin sun ce Kwamishinan ya bayyanawa Sufeto Janar din cewa, lamarin ba shi da alaka da kin yin hawan sallah, kuma Sarkin bai yi amfani da dawakai wajen ziyartar gidan gwamnati ba k**ar yadda al’adar ta tanada.

Watakila bai IGP bai gamsu da bayanin da Kwamishinan ya yi masa ba, sai ya umurci sashen binciken asiri na rundunar da ya gayyaci sarkin zuwa Abuja domin amsa tambayoyi.

A wata wasikar gayyata da ya sanya wa hannu, shugaban sashin, CP Olajide Ibitoye, ‘yan sandan sun gayyaci sarkin da ya gurfana a gaban sashen tattara bayanan sirri na rundunar a ranar Talata 8 ga Afrilu da karfe 10 na safe.

Sai dai kuma wasu majiyoyi daga fadar Sarkin sun shaidawa DAILY NIGERIAN cewa Sarkin bai samu takardar gayyatar a hukumance ba.

31/03/2025

Eid Al-Fitr 1446H/2025M Greetings

On the occasion of Eid Al-Fitr, I am pleased to extend my warmest congratulations and sincere best wishes. I pray to Almighty Allah to accept our fasting, prayers, and good deeds and to bless the entire Muslim Ummah with goodness, prosperity, long life, good health and barakah.

💐 Wishing you a blessed Eid! 🌹

Kwamitin duba wata a Saudiyya ne ya sanar da hakan bayan shafe sa'o’i ana dubawa.Gobe Lahadi 30 ga watan Maris ce za ta ...
29/03/2025

Kwamitin duba wata a Saudiyya ne ya sanar da hakan bayan shafe sa'o’i ana dubawa.

Gobe Lahadi 30 ga watan Maris ce za ta kasance 1 ga watan Shawwal, kuma goben ne za a yi bikin Sallah Ƙarama a ƙasar.

Ƙarin bayani - https://bbc.in/4456WDE

Eman Ahmed Abdul Aty mace mafi kiba a duniya Yar Masar ce wacce ake ganin ita ce mace mafi kiba a duniya kuma mace ta bi...
26/03/2025

Eman Ahmed Abdul Aty mace mafi kiba a duniya

Yar Masar ce wacce ake ganin ita ce mace mafi kiba a duniya kuma mace ta biyu mafi nauyi a tarihi, bayan Carol Yager. An yi iƙirarin cewa nauyinta da farko ya kai kilogiram 500 (lb 1,100).

An haifi Abd El Aty a Masar kuma ta zauna a Alexandria. Iyalinta sun bayyana cewa tana da nauyin kilogiram 5 (11 lb) lokaci da aka haife ta. Ta yi fama da matsalar zazzabin thyroid kuma ta daina makaranta.

Abd El Aty ta rasu a ranar Litinin, 25 ga Satumba, 2017 da karfe 4:35 na yamma, kwanaki 16 bayan cikarta shekaru 37 da haihuwa, sak**akon cututtukan da s**a hada da zuciya da na koda, a Asibitin Burjeel, Abu Dhabi, UAE lokacin da aka kwantar da ita asibiti a watan Mayu na 2017.

LABARI CIKIN GAGGAWA 👌Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo, tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, Labour Par...
24/03/2025

LABARI CIKIN GAGGAWA 👌

Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo, tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, Labour Party's Peter Obi, da tsohon gwamnan jihar Rivers, Rotimi Amaechi, tsohon gwamna Aminu Tambuwal a ranar Litinin, sun gana a Abuja.

Tsofaffin shugabannin sun gana ne a yayin wani taro na taya tsohon gwamnan jihar Imo, Emeka Ihedioha murnar cika shekaru 60 da haihuwa.

22/03/2025
19/03/2025

Gwamnonin PDP ga Tinubu: Ka gaggauta janye dokar-ta-ɓaci a jihar Rivers

Ƙungiyar gwamnonin jam'iyyar PDP ta yi kira ga shugaban kasa Bola Tinubu da ya gaggauta janye dokar-ta-ɓaci da ya kakaba wa jihar Rivers.

Gwamnonin sun kuma nemi Tinubu da ya janye dakatarwar da ya yi wa gwamnan jihar Rivers Siminalayi Fubara da mataimakiyar sa, inda su ka kira matakin da tsantsar ganganci da rashin dacewa.

TheCable ta rawaito cewa a wata sanarwa da shugaban kungiyar, Gwamna Bala Mohammed na Bauchi ya sanyawa hannu, gwamnonin sun ce ta tabbata Tinubu ya daure wa tsohon gwamnan Rivers, Nyesom Wike gindi ya na lalata dimokuraɗiyya.

"Mun gano cewa ka ƙyale Wike yana abinda ya ga dama saboda ya na maka aiki. Wannan mataki da aka dauka akan al'ummar jihar Rivers wata barazana ce ga dorewar dimokuraɗiyya," in ji wani sashi na sanarwar.

14/03/2025

Kalli Abin al-ajabi Tare da Wanzamin nan

Soyayyar gaskiya a koyaushe tana kulawa.
13/03/2025

Soyayyar gaskiya a koyaushe tana kulawa.

Address

Farin Bene
Gobirawa
700252

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Dr. Shamsuddeen Dan'uwa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share