Gombe Focus

Gombe Focus Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Gombe Focus, Media/News Company, Gombe.

Wane Ne Ke Neman Bata Sunan NAHCON?Daga Ibrahim Baba SuuleimanZarge-zargen da ke yawo cewa Hukumar Hajji ta Ƙasa (NAHCON...
23/06/2025

Wane Ne Ke Neman Bata Sunan NAHCON?

Daga Ibrahim Baba Suuleiman

Zarge-zargen da ke yawo cewa Hukumar Hajji ta Ƙasa (NAHCON) ta kashe sama da Naira biliyan 1.64 wajen daukar nauyin matan ma'aikata yayin aikin Hajjin 2025 ba kawai ƙarya ba ce, har ma suna k**a da wani yunkuri na ganganci domin bata suna da kwarjinin hukumar da shugabancinta. Zargin da ya fi daukar hankali shi ne wanda ke cewa Shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya kwana a ɗakin otal a Hilton Makkah Suites da ke biyan $1,000 kowane dare tare da kawo ‘yan uwansa 12, wannan batu babu ƙaƙƙarfan hujja ko shaidar gaskiya a cikinsa.

Don fayyace gaskiya, manufofin NAHCON ba su ba da damar amfani da kudaden gwamnati wajen daukar nauyin tafiya ko masaukin matan ma'aikata ba. Abin da ke akwai shi ne tsarin walwala da hukumar ta amince da shi ta hannun kwamitinta, wanda ke ba ma'aikatan da ke yi wa ƙasa aiki a Saudiyya har na tsawon fiye da wata guda damar daukar matansu da kudinsu, cikin tsarin rangwame da ya kebanta. Wannan tsari bai haɗa da muhimman abubuwa ba k**ar masauki a Makka, abinci, kuɗin tafiya (BTA), da sufuri tsakanin garuruwa. Wadannan duk ma'aikacin ne ke daukar nauyinsu daga alawus dinsa.

Wannan tsari ba sabon abu ba ne a NAHCON. Hukumomi k**ar NNPC, CBN, FIRS da ma’aikatar harkokin wajen Najeriya suna da irin wannan tsari na tallafa wa ma’aikata yayin dogon aiki a ƙasashen waje. Manufar NAHCON na bin matakin da ya dace ne da dokoki da ka’idojin kasa da kasa, kuma ba ta da alaka da almundahana ko amfani da dukiyar jama’a ta hanyar da ba ta dace ba.

Yin zargin cewa ma'aikatan NAHCON ba su da ikon daukar nauyin matansu babban kuskure ne kuma magana ce ta raina hankali. Wannan magana ta son rai ne, kuma a wasu lokuta matan ma'aikatan suna taka rawar gani wajen daukar wasu daga cikin kudin tafiyarsu. Babu wani laifi ko karya doka a wannan tsarin.

Adadin kudin da aka ambata a cikin rahotannin da ke yawo an cika su da ƙarya kuma sun ginu ne a kan ƙaryar da ba ta da tushe. Rahotannin sun yi kuskure wajen ɗaukar cewa duk kudin da aka kashe iri ɗaya ne ga kowa da kowa, ba tare da la’akari da ainihin abin da wannan tsrari ya ƙunsa ba. NAHCON ta bayyana cewa abubuwan da aka haɗa a cikin wannan tsarin na matan ma'aikata sun ƙunshi takardun visa, tikitin jirgi da masauki kawai a Masha'ir da Madinah. Ma'aikatan sun san waɗannan iyakokin kuma suna shiryawa bisa haka.

Maganar cewa Shugaban ya kwana a ɗakin $1,000 a dare kuma ya kawo iyalanshi 12 ƙarya ce tsagwaron ta. Babu wata shaida ko takardar biyan kudi da ke nuna hakan daga hukumar. A hakikanin gaskiya, Shugaban ne da kansa ya dauki nauyin tafiyar matarsa ta hanyar da ya dace, kuma babu wani daga cikin iyalansa da ya halarci aikin a matsayin jami’in NAHCON. Ko visa da aka yi wa matarsa ma, ba a karkashin hukumar aka yi ba.

Har ila yau, ƙarya ce a ce matan ma'aikata sun mamaye dakunan da aka tanada wa mahajjata ko jami’an hukumar. NAHCON tana da ƙa'idoji na masauki da ake kula da su ta hanyar kwamitoci da aka ware. Duk wani sauyi ko sabani ana gyara shi nan da nan. Babu wata shaida da ke nuna an yi amfani da dukiyar gwamnati ba bisa ka’ida ba.

Kiran da wasu ke yi na a binciki NAHCON ta hannun EFCC yana da kyau, NAHCON ba ta da abin ɓoyewa. Ana duba asusun ta akai akai ta Ofishin Auditor-General na Tarayya kuma hukumar na bin doka wajen dukkanin harkokinta na kudi. Amma irin wadannan binciken dole ne su dogara da gaskiya ba sharri ko siyasar karya da nufin bata suna ba.

Abin takaici shi ne, bayan gudanar da aikin Hajji mafi nasara a cikin kusan shekaru 15, aikin da aka yaba masa daga kowane bangare, wasu mutane sun dage wajen bata sunan NAHCON. Shin saboda an daina salon "ta fiya ta zo" da aka saba? Ko saboda Shugaban ba ya karbar cin hanci? Ko kuma saboda malami ne kuma Sheikh mai tsantseni, wasu ke jin tsoro da jajircewarsa da adalcinsa?

Ko menene dalili, lokaci zai fayyace gaskiya. NAHCON za ta ci gaba da jajircewa wajen nuna gaskiya, rikon amana da yi wa al’ummar Musulmi ta Najeriya hidima. Wadanda ke son bata sunanta don wata manufa ta siyasa ko ta son kai, a ƙarshe za su sha kunya.

Rubutawa: Alhaji Mubarak Oyewale
Mahajjacin Hajjin 2025 daga Ilorin

Jibwis Nigeria

Siyasar Kano!Dan majalisar dattawa mai wakiltar Kano ta kudu, Sen. S A Kawu Sumaila, OFR Ph.D ya sauya sheka a siyasance...
23/04/2025

Siyasar Kano!

Dan majalisar dattawa mai wakiltar Kano ta kudu, Sen. S A Kawu Sumaila, OFR Ph.D ya sauya sheka a siyasance, inda ya bayyana komawarsa komawarsa jam'iyya mai mulkin kasa wato APC a ranar Larabar nan.

Hakan yabiyo bayan ganawarsa da shugaban ƙasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, wanda hakan ya kawo ƙarshen raɗe raɗin da ake yi na komawar tasa jamiyya mai mulki.

Sanatan ya bayyana hakan a shafinsa na Facebook.

NAHCON and State Pilgrims Boards Agree on May 9, 2025, for Inaugural Hajj FlightThe National Hajj Commission of Nigeria,...
22/04/2025

NAHCON and State Pilgrims Boards Agree on May 9, 2025, for Inaugural Hajj Flight

The National Hajj Commission of Nigeria, NAHCON, held a meeting with State Muslim Pilgrims’ Welfare Board Executive Secretaries under the Forum of States today 22nd of April 2025. The meeting is to assess level of preparedness of the State Pilgrims’ Boards.

In his Opening Speech, NAHCON Chairman Professor Abdullah Saleh Usman reminded the house that the Hajj industry is in the last lap of preparation before commencement of 2025 Hajj season. He called on the states to update NAHCON on the level each state has reached in Visa production, vaccination, bags procurement and other sundry matters.

During the meeting, honorable Commissioner Operatiions, Prince Anofiu Elegushi disclosed that Air Peace has been assigned 5,128 pilgrims cumulative from Abia state, Akwa Ibom, Anambra, Armed Forces, Bayelsa, Benue, Borno, Cross River Delta, Ebonyi, Edo, Ekiti, Enugu, Imo, Kogi, Ondo, Rivers, and Taraba

FlyNas on the other hand was allocated 12,506 pilgrims from Federal Capital Territory, (FCT Abuja), Kebbi, Lagos, Ogun, Osun, Sokoto and Zamfara states. FlyNas is bringing in nine aircraft for the operation.

Max Air is airlifting pilgrims from Bauchi, Gombe, Jigawa, Kano, Katsina, Kwara, Oyo and Plateau states. The airline promised to conclude airlift of its 15, 203 maximum by 24th of May. Two aircraft will be deployed for the operation- a B747 with 400 capacity and the second aircraft with a 560 capacity.

Umza has been allocated 10,163 pilgrims from Kaduna, Adamawa, Nasarawa, Niger and Yobe states. Umza is deploying two aircraft a B747 with 477 capacity and a B777 with 310 capacity.

The 2025 Hajj airlift distribution was calculated on a total of 43,000 pilgrims.

The Commissioner Planning Research Statistics Information & Library Services (PRSILS), Prof Abubakar Yagawal informed the house of the level of the Commission’s preparedness in terms of clinics secured in Makkah and Madinah, distribution of Yellow Cards to states and finally reminded them not to enroll pregnant women for the Hajj exercise.

The meeting further deliberated and settled on 9th of May as date of inaugural flight to be concluded by 24th of May. The inbound flight is tentatively scheduled to commence from 13th June to end by 2nd July.

Fatima Sanda Usara,
Assistant Director, I&P
For
Chairman/CEO
NAHCON
22/4/2025

Babu kamshin gaskiya a zarge-zargen da ake yi min – shugaban NAHCONShugaban Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON), Farfesa Ab...
21/04/2025

Babu kamshin gaskiya a zarge-zargen da ake yi min – shugaban NAHCON

Shugaban Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON), Farfesa Abdullahi Saleh, ya ce duk zarge-zargen da ake yi masa, musamman na kin yin aiki da wasu ma’aikata a hukumar, ba gaskiya ba ne.
Farfesa Saleh ya musanta zarge-zargen da wasu ke yi masa, inda ya ce wasu rashin fahimtar ayyukan shugabannin hukumar da ma na hukumar ne ya janyo hakan.

Ya kara da cewa ikirari na ajiye ƴan kwamitin da ba na zartarwa ba na hukumar ba shi da tushe b***e mak**a.

A cewar sa, wadanda ba sa cikin kwamitin zartaswa ba su da wata tak**aimiyar rawar da zai su taka a dokance.

Jibwis Nigeria

KIWON LAFIYAƳan Najeriya na ci gaba da bayyana damuwa dangane da korafin Jami'ar Ibadan akan yadda ake samun ƙaruwar dal...
21/04/2025

KIWON LAFIYA
Ƴan Najeriya na ci gaba da bayyana damuwa dangane da korafin Jami'ar Ibadan akan yadda ake samun ƙaruwar dalibai mata da kan sayar da maniyin su ga masu buƙatar haihuwa domin samun abin masarufi.

Wannan ya biyo bayan wata wasiƙar cikin gida da Daraktan Lafiya na Jami'ar, Dakta Aderonke B. Ajayi ya rubuta, wanda yake gargadi akan matakin saboda illar dake tattare da shi. Ajayi ya ce yayin da bada kyautar maniyin kan taimaka ga mabukata wajen samun ɗa, illar sa ga ƴam matan da s**a mayar da hakan a matsayin sana'a da kuma halin kula da lafiyarsu na da girma.

Jaridar Vanguard da ake wallafawa a Najeriya ta jiyo Dakta Ajayi na kira ga ɗalibai da iyayen su da hukumomin dake kula da makarantu tare da hukumomin lafiya da su yi taka tsan tsan akan lamarin. Baya ga illar da ka iya shafar halin lafiyar ƴam matan dake sayar da maniyin su domin taimakawa marasa haihuwar, likitan ya kuma yi gargadin cewar ba'a buƙatar yin haka sama da sau uku a cikin shekara guda ko kuma sau biyar a rayuwarsu, saboda yadda hakan ka iya haifar da cutar sankara.

Ƴan Najeriya da dama sun buƙaci samar da dokar da za ta kula da wannan bangaren domin ƙare lafiya da kuma jinsin jama'a.

Copied

Duk zarge-zargen da ake min babu kamshin gaskiya a ciki, in ji shugaban NAHCON Shugaban Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON)...
21/04/2025

Duk zarge-zargen da ake min babu kamshin gaskiya a ciki, in ji shugaban NAHCON

Shugaban Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON), Farfesa Abdullahi Saleh, ya ce duk zarge-zargen da ake yi masa, musamman na kin yin aiki da wasu ma'aikata a hukumar, ba gaskiya ba ne.

Saleh ya musanta zarge-zargen da wasu ke yi masa, inda ya ce wasu rashin fahimtar ayyukan shugabannin hukumar da ma na hukumar ne ya janyo hakan.

Ya kara da cewa ikirari na ajiye ƴan kwamitin da ba na zartarwa ba na hukumar ba shi da tushe b***e mak**a.

A cewar sa, wadanda ba sa cikin kwamitin zartaswa ba su da wata tak**aimiyar rawar da zai su taka a dokance.

DA ƊUMI-ƊUMI: Fafaroma ya mutuLimamin kiristocin duniya, Pope Francis ya mutu, ya na da shekaru 88.Channels TV ta rawait...
21/04/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Fafaroma ya mutu
Limamin kiristocin duniya, Pope Francis ya mutu, ya na da shekaru 88.

Channels TV ta rawaito cewa Pope, wands a hausance ake kira da Fafaroma, ya mutu ne a yau Litinin bayan ya yi fitowa ta karshe a wani taron addu'a don ranar Easter a jiya Lahadi.

Fadar Vatican ce ta fitar da sanarwar mutuwar ta Pope, wanda ta de ya cika da misalin ƙarfe 7:35 na safiya.

Daily Nigerian Hausa
Throgh Sani Labaran

16/01/2025

96.2K followers, 10.7K likes, 839 comments

16/01/2025

970.8K followers, 5935 likes, 135 comments

Nasarawa State Governor Dissolves SSG, Commissioners, AidesBy Sabiu AbdullahiNasarawa State Governor, Abdullahi Sule, ha...
04/01/2025

Nasarawa State Governor Dissolves SSG, Commissioners, Aides

By Sabiu Abdullahi

Nasarawa State Governor, Abdullahi Sule, has dissolved the state executive council, comprising all commissioners, and sacked the Secretary to the State Government, Barrister Muhammad Aliyu-Ubamdoma.

The decision was announced at a special emergency executive meeting in Government House, Lafia, on Friday, shortly after Vice President Kashim Shetima's one-day working visit to the state.

A top government official, who preferred anonymity, stated that Governor Sule is known for restructuring the state's administration, although the exact reasons for the dissolution are not yet clear.

This move is not unprecedented, as Sule dissolved the state executive council in 2021, citing the need for a more effective and efficient governance structure.

Governor Sule expressed his gratitude to the outgoing council members for their contributions to the state's growth and wished them well in their future endeavors.

According to a statement by Mohammed Iliyasu-Idde, permanent secretary of cabinet affairs and special services, "All the outgoing council members are to hand over the affairs of their ministries and government property in their possession to the permanent secretaries in their respective ministries while the SSG is to hand over to the permanent secretary cabinet affairs and special services."

The dissolution of the executive council has left citizens of Nasarawa State awaiting further clarification on the implications of this decision and the future direction of the state's administration.

KISHI: Miji ya kashe fasto bisa zargin mu'amala da matarsaRundunar ƴansanda a jihar Osun ta tabbatar da kisan wani fasto...
03/01/2025

KISHI: Miji ya kashe fasto bisa zargin mu'amala da matarsa

Rundunar ƴansanda a jihar Osun ta tabbatar da kisan wani fasto mai suna Sina Olaribigbe da wani miji mai kishi ya yi, bisa zargin ya na mu'amala da matarsa.

CSP Yemisi Opalola, mai magana da yawun rundunar, ta tabbatar da faruwar lamarin a jiya Alhamis a Osogbo.

Mrs. Opalola ta ce lamarin ya faru ne sa'ilin da mijin ya tarar da faston a gidan matarsa, nan fa ya caccaka masa wuƙa saboda ya yi zargin ya yi mu'amala da ita.

“Ma’auratan ba sa zaune tare amma duk da haka auren nasu bai rabu ba a hukumance.

“Faston ne dama ke shiga tsakani don sasanta rigimar su, kuma a wannan lokaci yana gidan matar ne lokacin da mijin ya zo.

“Mijin, a ganinsa, ya ɗauka faston ya na wata mu'amala ne da matarsa.

“An ce mijin ya yi aiki cikin fushi, inda ya daba wa faston wuƙa sau da dama, har ya mutu nan take,” inji ta.

Mrs. Opalola ta bayyana cewa an k**a wanda ake zargi, yayin da aka ajiye gawar faston a dakin ajiye gawawwaki na asibiti.

Daga shafin: . Sani Sabo Labaran

SABON SHUGABAN TSARO NA SOSJOJIN KASA YA KARBI RAGAMARSA.****A yaiune sabon Mukaddashin shugaban sojojin kasa na Nigeria...
01/11/2024

SABON SHUGABAN TSARO NA SOSJOJIN KASA YA KARBI RAGAMARSA.
****
A yaiune sabon Mukaddashin shugaban sojojin kasa na Nigeria Major General Olufemi ya k**a aiki biyo bayan nadashi da Shugaba Ahmad Bola Tinibu da yayi sak**akon tafiya jinya da tsohon shugaban yayi.

Shugaban Hafsan Sojojin Nigeria General Christopher Musa shine wanda yamika kundin ayyuka ga sabon shugaban, a inda yakara nuna muhimmancin cigaba da ayyukan soja batare da wani gibiba.

Musa, yacigaba da cewa shugaba Tinibune yaga dacewar zabarsa a wannan matsayi na Mukaddashi domin samun cigaba a harkar tsaro ba tare da tasgiro ba a wannan kasa.

A nashi bayani Oluyede yamika godiyarsa wa shugaba Tinibu tare da yiwa Lagwbaja's addu'ar samun lafiya.

Yakuma kara da neman hadin kan hukmar tsaro da abokan aikinsa domin samu damar sauke wannan nauyi da aka dora masa.

Kafin zamowansa wannan matsagi ya taba rike shugaban Task Force Brigade in Operation HADIN KAI. Inda yabada guddummawa sosai wajen yaki da Boko Haram a kasar.

01/11/2024

Address

Gombe

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Gombe Focus posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Gombe Focus:

Share