Jewel Multimedia

Jewel Multimedia Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Jewel Multimedia, Media/News Company, Gombe.

Jewel Multimedia Services

A modern media platform dedicated to telling stories that create impact through news, digital communication, and community development.

DA DUMI-DUMI: Ali Nuhu ya zama Ambasadan kamfanin ABBA PANTAMI DATA LTD, bayan kulla yarjejeniyar Naira miliyan 30 na ts...
25/12/2025

DA DUMI-DUMI: Ali Nuhu ya zama Ambasadan kamfanin ABBA PANTAMI DATA LTD, bayan kulla yarjejeniyar Naira miliyan 30 na tsawon shekara guda

ABBA PANTAMI DATA LTD ya sake rage muku farashin Data zuwa Naira 500 akan kowane 1GB, ku hanzarta ku sauke Application din, domin ku more garabasa.

Duk wanda ya sayi Data mai 30DAYS a Application din ABBA PANTAMI DATA LTD to sai tayi kwanaki 30 sannan za tayi Expired. Akwai bambanci tsakanin Expired da kuma karewa.

Matukar kuna amfani da Application din ABBA PANTAMI DATA LTD da zaran ka hadu da matsalar network ko makalewar kudi kana yiwa customer care dinsu magana anan take zasu gyara maka.

Idan baka taba amfani da Application din ba ka gwada, idan ka dade baka yi amfani dashi ba ka sake gwadawa a yanzu domin tabbatar da ingancin shi.

Kuyi Download din Application din ABBA PANTAMI DATA ta wannan link din a PlayStore da kuma AppStore

👇👇
Ga link din PlayStore
https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.com.abbapantamidata.app

Ga link din AppStore
https://apps.apple.com/us/app/abba-pantami-data-ltd/id6744061271

Mai bukatan karin bayani, ya tuntubi daya daga cikin customer care ta WhatsApp;
09138275183
08126081967
07046868000

Abba Sani Pantami
07061347599

Jega Ya Gargadi Matasa Su Shiga Siyasa Ko Najeriya Ta Fuskanci Hatsarin Mulkin DanniyaDaga Muhammad Chigari KumoTsohon S...
05/12/2025

Jega Ya Gargadi Matasa Su Shiga Siyasa Ko Najeriya Ta Fuskanci Hatsarin Mulkin Danniya

Daga Muhammad Chigari Kumo

Tsohon Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Farfesa Attahiru Muhammadu Jega, ya yi kira mai ƙarfi ga matasan Najeriya da su ƙara shiga harkokin siyasa, yana jan hankalin cewa ƙasar na iya karkata zuwa mulkin danniya idan matasa ba su tashi tsaye ba.

Farfesa Jega ya yi wannan gargadi ne a jiya yayin gabatar da takarda mai taken “Zabe da Kyakkyawan Mulkin Dimokuraadiyya a Najeriya” a taron jawabin ilimi da Jami’ar Tarayya ta Kashere (F*K) ta shirya a dakin taronta na Multipurpose Hall.

Ya ce matsalolin mulki da Najeriya ke fuskanta a yau na da alaƙa kai tsaye da matasa, kasancewar su ne ginshikin cigaban kasa. Ya jaddada cewa rashin shiga harkokin siyasa da zabe na barin fagen siyasa a hannun mutanen da ke neman moriyar kansu maimakon cigaban kasa baki ɗaya.

A nasa jawabin, Babban Editan Premium Times, Dapo Olorunyomi, ya soki yadda ake gudanar da zaben fidda gwani ta hanyar kuɗi da kuma dogaro da kotuna wajen tantance sak**akon zabe. Ya ce irin wadannan dabi’u na rage amincewar jama’a ga tsarin dimokuraɗiyya, yana mai cewa babban kalubalen siyasar ƙasar shi ne tabbatar da cewa tsarin zabe yana amfanar da al’umma.

Mataimakin Shugaban Jami’ar Tarayya ta Kashere, Farfesa Umar Pate, wanda ya bude taron, ya bayyana shi a matsayin muhimmin mataki ga jami’ar da ƙasar, musamman a lokacin da ake neman sabunta dimokuraɗiyya da gina cibiyoyin gwamnati masu ƙarfi. Ya ce taken taron ya dace da halin da ƙasar ke ciki a yanzu.

Farfesa Pate ya kara da cewa jami’o’in gwamnati suna da muhimmiyar rawa wajen gina matasa masu ƙwarewa da kuma wayar da kan jama’a kan dimokuraɗiyya da shugabanci nagari.

Shugabannin jihohin Gombe da Taraba sun aika da sakonnin gaisuwa ta hannun Chiefs of Staff dinsu.

Tun kafin taron, Farfesa Jega ya ziyarci muhimman sassa na jami’ar, ciki har da Kwalejin Kimiyyar Likitanci, dakin gwaje-gwaje na zamani, sabbin dakunan karatu da aka gina, da Gidan Watsa Labarai na jami’ar.

SRC Ta Raba Tallafi a Masaukan Daliban Jami’ar Tarayya KashereMajalisar Wakilan Dalibai ta Jami’ar Tarayya Kashere (SRC)...
02/12/2025

SRC Ta Raba Tallafi a Masaukan Daliban Jami’ar Tarayya Kashere

Majalisar Wakilan Dalibai ta Jami’ar Tarayya Kashere (SRC) ta gudanar da rabon tallafi ga daliban mazauna masaukan jami’ar, a wani mataki da aka bayyana a matsayin ci gaba wajen inganta walwalar ɗalibai da kyautata yanayin rayuwarsu. An gudanar da wannan aiki ne a ranar Litinin, 1 ga Disamba 2025.

A yayin bikin rabon kayan, Shugaban SRC, Kwamared Kabir Faizu Danyaya, ya ce wannan shiri na daga cikin ƙudurin majalisar na ganin cewa ɗalibai sun samu dukkan irin tallafi da kulawa da ya dace. Ya bayyana cewa SRC na ɗaukar walwalar ɗalibai a matsayin abin da ya fi komai muhimmanci a aikinsu na yau da kullum. Danyaya ya jaddada cewa taken su na “Ba a Bar Kowa a Baya” ya kasance mabudin ƙarfafa majalisar wajen ɗaukar matakai masu tasiri ga dalibai.

Shugaban sashen kwanan Dalibai, Dahiru Sulaiman Gwale, wanda ya karɓi kayan a madadin daliban masaukan, ya bayyana tallafin a matsayin wani abu da ya zo a daidai lokacin da ake buƙatarsa. Ya ce tsananin buƙatar kayayyakin tsafta da sauran kayan amfani na yau da kullum ya sa wannan tallafin ya zama abin jin daɗi ga dalibai, musamman duba da ƙalubalen da ake fuskanta a masaukan.

Wasu daga cikin daliban da s**a samu tallafin sun bayyana farin cikinsu tare da jinjinawa majalisar bisa ga jajircewarta. Sun ce matakin na nuna cewa majalisar na bibiyar kalubalen da dalibai ke fuskanta tare da ɗaukar matakai kai tsaye ba tare da jinkiri ba.

Kayan da aka raba sun haɗa da robar ruwa, mujajjawa (moppers), tsintsiya, sabulai, Hypo da sauran muhimman kayan tsaftace muhalli kayan da ake amfani da su akai-akai wajen tabbatar da tsafta da ingantaccen yanayi a masaukan jami’ar.

Wannan shiri dai ya ƙara ƙarfafa gwiwar daliban cewa akwai ci gaba a aikace a tsakanin shugabannin majalisar, musamman wajen kula da buƙatun ɗalibai da kuma kawo sauƙi a rayuwar su.

Ina Matafiya Wannan Hanyar A Wace Jiha Take A Nigeriya?
02/11/2025

Ina Matafiya Wannan Hanyar A Wace Jiha Take A Nigeriya?

DADUMI-DUMI: Yanzu Haka Matasan Karamar Hukumar Dukku Suna Gudanar Da Zanga-Zangar Lumana Kan Lalacewar Hanyar Titin Gom...
02/11/2025

DADUMI-DUMI: Yanzu Haka Matasan Karamar Hukumar Dukku Suna Gudanar Da Zanga-Zangar Lumana Kan Lalacewar Hanyar Titin Gombe–Dukku–Darazo

A yau, matasa da dattawa daga ƙaramar hukumar Dukku da kewaye s**a fito kan tituna domin nuna damuwa kan halin da hanyar Gombe–Dukku–Darazo ke ciki, wadda ta dade tana cikin matsanancin lalacewa.

Hanyar, wacce ke da muhimmanci wajen haɗa jihohin Gombe, Adamawa da Bauchi, ta zama barazana ga rayukan jama’a saboda ramuka, rashin kyawunta, da yawan hatsari da ke faruwa a kullum.

Masu zanga-zangar sun gudanar da ita cikin lumana, ba tare da tashin hankali ba, inda s**a ɗauki banner na takardu masu rubuce-rubuce k**ar:
- “Mu ma ‘yan Najeriya ne!”
- “Hanyar Gombe–Dukku tana kashe mu!”
- “Muna bukatar aikin gaggawa, ba alkawari ba!”

Wani daga cikin shugabannin zanga-zangar ya ce:
“Ba wai muna neman abun da bai dace ba ne; muna neman rayuka su tsira, tattalin arziki ya bunƙasa, da kuma a dawo da martabar wannan hanya wacce take jigon hulɗar kasuwanci da sufuri a Arewa maso Gabas.”

Sun kammala da kira ga gwamnati da hukumomin da abin ya shafa da su saurari ƙorafin jama’a, domin gyaran hanyar zai taimaka wajen tabbatar da tsaro, ci gaba, da haɗin kan al’umma.

Sheikh Professor Isa Ali Pantami Ya Sa An Rushe Masallacin Kofar Hakimin Pantami, Zai Gina Sabon Masallaci Na ZamaniBabb...
24/10/2025

Sheikh Professor Isa Ali Pantami Ya Sa An Rushe Masallacin Kofar Hakimin Pantami, Zai Gina Sabon Masallaci Na Zamani

Babban malamin addinin Musulunci kuma tsohon Ministan Sadarwa na Najeriya, Sheikh Professor Isa Ali Ibrahim Pantami, CON (Majidadin Daular Usmaniyya), ya bayar da umarnin rushe tsohon Masallacin Kofar Hakimin Pantami da ke cikin garin Gombe, domin gina sabon masallacin Juma’a na zamani a wurin.

Rahotanni sun tabbatar da cewa, bayan rushewar masallacin, Sheikh Pantami ya sayi gidaje uku da ke gefen masallacin, domin fadada fili da samar da isasshen wurin ibada ga jama’ar da ke halartar sallar Juma’a.

A cewar mazauna yankin, wannan aiki na Sheikh Pantami ya zama abin yabo, ganin yadda tsohon masallacin ke da ƙaramin fili da kuma cunkoso, musamman a lokutan sallar Juma’a.

Wani daga cikin mazauna unguwar, Malam Abdullahi Haruna, ya bayyana cewa wannan mataki ya nuna irin kishin da Sheikh Pantami ke da shi ga addini da al’umma.

Sheikh Pantami mutum ne da ke nuna kishin addini da kulawa da jama’a. Wannan aiki da yake yi zai taimaka wajen kawo sauƙi da kwanciyar hankali ga masu ibada. Allah ya saka masa da alkhairi,” in ji shi.

Ana sa ran sabon masallacin da za a gina zai kasance na zamani, mai ɗauke da kayayyakin more rayuwa da tsarin da ya dace da zamani ciki har da na’urorin sanyaya iska, tsarin sauti na zamani.

Wannan aikin na cikin jerin ayyukan alkhairi da Sheikh Pantami ke gudanarwa a fadin ƙasar nan, musamman waɗanda s**a shafi gina masallatai, tallafawa malamai, da taimakon al’umma ta fannoni daban-daban.

A ƙarshe, jama’ar yankin sun roƙi Allah Ya saka wa Sheikh Pantami da alkhairi, tare da jinƙan iyayensa.

HISBAH Pantami Yamma Ta Shayar Da Bayin Allah Ruwan Sanyi A Gombe A yau Juma’a, rundunar Hisbah Pantami Yamma ta gudanar...
24/10/2025

HISBAH Pantami Yamma Ta Shayar Da Bayin Allah Ruwan Sanyi A Gombe

A yau Juma’a, rundunar Hisbah Pantami Yamma ta gudanar da wani aikin alkhairi mai matuƙar jan hankali na shayar da bayin Allah ruwan sanyi (pure water) a masallatai biyu a cikin birnin Gombe.

Aikin, wanda aka gudanar ƙarƙashin jagorancin Malam Ibrahim M. Labaran, ya gudana ne a Masallacin Juma’a na Maizare (Ahajas) da kuma Masallacin Juma’a na Madina Quarters, Opposite Wuri Biriji, inda aka raba kwalaben ruwa ga masu halartar sallar Juma’a.

Rahotanni sun tabbatar da cewa mutum 660 ne s**a amfana da wannan shirin, wanda aka yi da nufin rage ƙishirwa da taimaka wa al’umma a wannan lokacin na zafi mai tsanani.

Da yake jawabi ga wakilanmu, Malam Ibrahim M. Labaran ya bayyana cewa wannan aiki wani ɓangare ne na shirye-shiryen Da’awah and Relief Organization Gombe wajen ganin an karfafa taimakon juna da ciyar da al’umma gaba.

Wannan ba kawai rabon ruwa ba ne, alkhairi ne da nufin ƙara haɗin kai da nuna kulawa ga bayin Allah. Muna fatan sauran ‘yan uwa musulmi za su yi koyi da irin wannan aiki, in ji shi.

A wasu wurare da aka kai ruwan, jama’a sun bayyana farin cikinsu da godiya ga rundunar Hisbah, inda s**a ce a wannan lokaci na zafi, ruwan sanyi ya zama wata ni’ima ta musamman.

Aikin ya kuma jawo yabo daga masu ibada da mazauna yankunan Maizare da Madina Quarters, inda aka yaba da yadda rundunar ke ci gaba da shirya ayyuka masu amfani ga al’umma.

Hakika, wannan shayarwa ta zama wata gagarumar nasara ga rundunar Hisbah Pantami Yamma, kuma ta zama abin koyi ga sauran kungiyoyi masu kishin al’umma a jihar Gombe.

#

22/10/2025

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Abdulrahman Kumo, Abdulrahaman Ahmad, Arki Ibrahim Samaila, Buharee Abdullahi Dam Roni, Adamu Ibrahim, Bello Muhammad Nuhu Masu, Garba Sa'idu Kumo, Sahabo Abdulkadir, Auwal Musa Gadawo, Mohammed Idris Mancy, Hassan Haruna Umar, Comrd Muazu Manga, Abdullahi Bello Kumo, Sadiq Abdallah Gombe, Abigail Kelmi Lazarus, Muhammad Dahiru, Àhmèd Sidi Lùggèrèwò, Sulaiman Salihu Annoor, Dg Kabir Usman, Shehu Ahmad Dukku, Hassan J Muhammad, Adamu Manjas, Passman Garba Muh'd Dalori, Usman Bello Tumu, Aminu Ahmad Pantami, Real Jay, Shehu Ali, Adamu Mohammed Danjuma, Tukur Abubakar Abuu Sadeeq, Prince M A Kumo, Abdulrashid Abdullahi Kano, Sadiq Ahmad, Babanladi Saro, Ibrahim Usman Gombe, Asheer Yusuff, Muhammad Ahmad Sheikh, Rabiu Saeedu, Shanawa Kanhawa Kumo, Muhammad Musa Muhammad, Abubakar Muhammad Bappah, Kabiru Yahaya Sambo-daji, Ahmed Saleh Ibrahim, Emmanuel Fatusi, Muhammad Kwairi Waziri, Muhammad Sani Ibrahim, Abubakar Mato Kumo

LABARI MAI DADI YANZU-YANZU: Kamfanin ABBA PANTAMI DATA LTD, ya rage muku farashin Data, kowa ya duba Application dinshi...
19/10/2025

LABARI MAI DADI

YANZU-YANZU: Kamfanin ABBA PANTAMI DATA LTD, ya rage muku farashin Data, kowa ya duba Application dinshi domin more garabasa.

Hukumar Leken Asiri ta Tsaro ta Najeriya (Defence Intelligence) ta k**a wani Birgediya Janar tare da wasu jami’an soja b...
18/10/2025

Hukumar Leken Asiri ta Tsaro ta Najeriya (Defence Intelligence) ta k**a wani Birgediya Janar tare da wasu jami’an soja bisa zargin shirin kulla juyin mulki domin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Daga Sahara

Hukumar Karɓan Korafe-Korafe ta Ƙasa (PCC) reshen Jihar Gombe ta gudanar da bikin cika shekaru 50 da kafa ta a Najeriya,...
17/10/2025

Hukumar Karɓan Korafe-Korafe ta Ƙasa (PCC) reshen Jihar Gombe ta gudanar da bikin cika shekaru 50 da kafa ta a Najeriya, a ranar Alhamis, 16 ga Oktoba, 2025.

Shugaban hukumar, Comrade Bashir Funawo, ya bayyana cewa PCC na kare haƙƙin jama’a da tabbatar da adalci tsakanin ‘yan ƙasa da hukumomi.

Hukumar ta gudanar da tattaki domin wayar da kan jama’a kan yadda ake mika korafi cikin bin doka, inda mazauna Gombe s**a yaba da irin rawar da PCC ke takawa wajen tabbatar da adalci.

17/10/2025

Shugabannin Soshiyal Midiya na Hon. Usman Bello Kumo sun halarci Shirin Siyasar mu a Yau

Shugabannin soshiyal midiya na Hon. Usman Bello Kumo sun halarci shirin Siyasar mu a Yau na Jewel Multimedia, inda s**a tattauna kan dabarun ƙarfafa hulɗa da jama’a ta kafafen sada zumunta da kuma yada sahihan bayanai kan ayyuka da manufofin Hon. Kumo.

Usman Mangadu Morrison Mega No Shaking Usman Umar Mega Auwal Usman Kombani Usman Bello Tumu

Address

Gombe
1238

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jewel Multimedia posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jewel Multimedia:

Share