Arewa Media Watch

Arewa  Media Watch News Media Company

Ƙungiyoyin fararen hula daga Arewacin Najeriya da kuma kudancin kasar nan sun jaddada kiran cewa dole Elrufa'i ya fuskan...
26/02/2026

Ƙungiyoyin fararen hula daga Arewacin Najeriya da kuma kudancin kasar nan sun jaddada kiran cewa dole Elrufa'i ya fuskanci dukkan tuhume-tuhumen da ake masa, babu wani tsohon shugaba da yafi karfin doka ko waye shi.

Abubuwan daya aikata lokacin da yake kan karagar mulki tun daga kwace kadarorin al'umma, take hakkin dan'adam, k**a mutane ba gaira ba dalili, ya zama dole yanzu ya fuskanci hukuncin abinda ya aikata.

Daga Nura Jamilu
Shugaban masu rajin kare demokradiyya na Kaduna

Ina Ka Ke Lokacin Da El-Rufai Ke Gallazawa Mutane Da Sace Dukiyar Al'ummar Jihar Kaduna ~ KVU Ta Caccaki Atiku Abubakar ...
25/02/2026

Ina Ka Ke Lokacin Da El-Rufai Ke Gallazawa Mutane Da Sace Dukiyar Al'ummar Jihar Kaduna ~ KVU Ta Caccaki Atiku Abubakar

Ƙungiyar Kaduna Voices United (KVU), wadda ta yi fice wajen tabbatar da anyi gaskiya, riƙon amana da adalci a harkokin mulki, ta yi martani kan kalaman da Atiku Abubakar da yayi dangane da tsare tsohon gwamnan Kaduna State, Nasir El-Rufai.

KVU ta bayyana cewa duk da cewa damuwa kan lafiyar El-Rufai abu ne mai muhimmanci, akwai tambaya kan dalilin da ya sa irin wannan ƙwazo wajen neman gaskiya da rikon amana bai bayyana ba a lokacin da yake kan mulki, lokacin da ake ta zarge-zargen sa da cin hanci, tauye haƙƙin jama’a da kuma amfani da iko wajen tsoratar da masu adawa. A cewarsu, nuna damuwa yanzu kaɗai na iya zama misali na son zuciya da rashin daidaito a siyasa.

Ƙungiyar ta jaddada cewa El-Rufai na fuskantar tuhume-tuhume masu tsanani daga Department of State Services (DSS), wanda ya shigar da ƙara uku a Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja. Tuhume-tuhumen sun shafi zargin sa da yin satar bayanan waya ba bisa ƙa’ida ba, rashin kai rahoton bayanan da aka ce ya samu, da kuma jefa tsaron ƙasa cikin haɗari, zarge-zargen da s**a samo asali daga wata hira da ya yi a tashar Arise TV inda ya yi iƙirarin samun damar sauraron wayoyin mai bawa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro.

Haka kuma, yana ƙarƙashin bincike daga Economic and Financial Crimes Commission (EFCC) kan zargin karkatar da kuɗaɗen jama’a da s**a kai kimanin naira biliyan 432, ciki har da kuɗaɗen da ake alaƙantawa da wasu manyan ayyuka k**ar na layin dogo na Kaduna. Bugu da ƙari, Independent Corrupt Practices and Other Related Offences Commission (ICPC) na bincike kan zargin cin zarafin ofis da kuma take dokokin saye da bayar da kwangila.

KVU ta bayyana cewa waɗannan zarge-zarge ba ƙananan batutuwa ba ne, domin sun shafi tsaron ƙasa, dukiyar jama’a, da kuma amincewar al’umma ga shugabanci. Don haka, ƙungiyar ta yi gargadin cewa yunƙurin wanke El-Rufai daga waɗannan matsaloli kafin kammala bincike da shari’a zai iya tauye tsarin dimokuraɗiyya da ƙa’idar cewa babu wanda ya fi ƙarfin doka.

A ƙarshe, ƙungiyar ta buƙaci gwamnatin tarayya ta tabbatar da bin doka da oda wajen tsarewa da shari’ar El-Rufai, tare da bayyana gaskiya game da halin da yake ciki. Sun kuma yi kira ga shugabannin siyasa da su guji nuna son kai, su fifita gaskiya da adalci sama da alaƙar siyasa, domin tabbatar da cewa Najeriya ta samu shugabanci mai tsafta da rikon amana.

Sa hannun
Yusuf Dama'i
Secretary KVU

Ka Daina Siyasantar Da Harkokin Tsaron Kasa ~ Martanin Nigerian Unite Ga Atiku Abubakar Kalaman Atiku Abubakar na cewa i...
24/02/2026

Ka Daina Siyasantar Da Harkokin Tsaron Kasa ~ Martanin Nigerian Unite Ga Atiku Abubakar

Kalaman Atiku Abubakar na cewa idan wani abu ya samu tsohon gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai gwamnatin tarayya za a ɗorawa laifi ko alhakin haka, ya nuna wani salo na siyasa da muka saba gani a Najeriya, siyasar neman tausayin jama'a domin kauce wa fuskantar shari’a. Irin wannan magana k**ar yunƙuri ne na matsa lamba ga hukumomi, maimakon a bar doka ta yi aikinta.

Sai ɗan siyasa ya gama satar dukiyar ƙasa yayin da yake karagar mulki, amma da zarar hukumomi sun fara bincikensa sai ya bijiro da rashin lafiya don kaucewa tuhuma, to wannan wasan kwaikwayon dole yazo karshe a wannan lokacin. Domin wannan kiran na ka a wannan lokacin ba komai illa neman mafaka ta siyasa don biyan bukatar kanku bakomai ba.

A ƙasarmu, ya zama ruwan dare duk lokacin da ake tuhumar ‘yan siyasa, sai su bayyana kansu a matsayin marasa lafiya domin neman beli ko sassauci. Amma da zarar sun samu damar fita, sai mu gan su suna halartar taruka, suna tafiya ko’ina cikin ƙoshin lafiya. Wannan dabi’a ta sa jama’a s**a fara tambayar gaskiyar ikirarin rashin lafiyar da ake yi a irin waɗannan lokuta.

Saboda haka, a yanzu ba daidai bane yayin da Elrufa'i ke fuskantar tuhuma daga hukumomi a bijiro da maganar rashin lafiya don nema masa bail, wannan cin dunduniyar doka ne, haka kuma kashe goben ƙasa ne.

Idan akwai tuhuma a kan El-Rufa’i, abin da ya dace shi ne ya fuskanci shari’a k**ar kowane ɗan ƙasa. Babu wanda ya fi ƙarfin doka, kuma babu wanda ya k**ata a ba shi kariya ta siyasa domin guje wa bincike ko tuhuma. Adalci ba ya aiki da barazana ko tausayi, yana aiki ne da gaskiya da hujja.

Lokaci ya yi da za a daina amfani da lafiyar mutum a matsayin garkuwa ta tserewa fuskantar tuhuma a gaban kuliya manta sabo. Najeriya za ta samu ci gaba ne kawai idan muka yarda cewa kowa babba ko ƙarami dole ya amsa idan an tuhume shi. Doka ta fi kowa, kuma dole ta yi aiki akan kowa.

A cikin hotunan nan dake kasa za ku ga yadda yan siyasa ke rainawa mutane hankali a duk lokacin da suke fuskantar tuhuma daga hukumomi a kasar nan.

Sa hannun
Mustapha Basiru
Shugaban Nigerian Unite

Ƙungiyoyin Matasa Daga Jihar Kaduna Sun Yi Kira Ga EFCC Da Su Binciki Elrufa'i Haɗakar ƙungiyoyin matasa daga jihar Kadu...
16/02/2026

Ƙungiyoyin Matasa Daga Jihar Kaduna Sun Yi Kira Ga EFCC Da Su Binciki Elrufa'i

Haɗakar ƙungiyoyin matasa daga jihar Kaduna sun yi ƙawanya a hukumar EFCC yau yayin da tsohon gwamnan jihar ke karɓar gayyatar da hukumar tayi masa kan zarge-zargen cin hanci da rashawa a lokacin mulkinsa.

Matasan sun bayyana cewa, ya zama wajibi tsohon gwamnan ya tsaya ya fuskanci tuhume-tuhumen da ake masa, kar ya mayar da abun siyasa, domin babu wanda yafi karfin bincike idan ana tuhumarsa.

Matasan sun jaddadawa EFCC cewa, dole a gudanar da bincike mai zurfi akansa, idan har ba shi da laifi su sallameshi, amma idan aka sameshi da laifi to a hukunta shi k**ar yadda hukumar take hukunta kowa.

Daga Muhammad Abdullahi
Shugaban kungiyoyin matasan jihar Kaduna

Kogunan Gusau Shine Amsa A Jihar Zamfara 2027A yau Jihar Zamfara na bukatar shugaba nagari, mai hangen nesa, mai tausayi...
09/02/2026

Kogunan Gusau Shine Amsa A Jihar Zamfara 2027

A yau Jihar Zamfara na bukatar shugaba nagari, mai hangen nesa, mai tausayi ga talaka, kuma wanda ya san halin da al’umma ke ciki.

Ba kowa ba ne zai iya ɗaukar wannan nauyi, sai mutumin da Allah ya horewa baiwa da basira, kwarewa, da kuma kishin jama’a. Daga cikin irin wadannan mutane, sunan Kogunan Gusau ya fito fili ba tare da shakka ba.

Kogunan Gusau mutum ne da ya shahara wajen taimakon jama’a, gina al'umma, da tsayawa tsayin daka wajen kare muradun al’umma. Tarihinsa ya nuna cewa shi shugaba ne mai sauraron jama’a, wanda ke da fahimtar matsalolin tsaro, tattalin arziki, ilimi da walwalar al’umma. Ba wai kawai a iya magana ya tsaya ba, faɗa da aikatawa sunanshi.

A tsawon lokaci, Kogunan Gusau ya nuna jajircewa, hakuri da kwarewa a harkokin shugabanci da siyasa. Yana da fahimta mai zurfi game da jihar Zamfara daga karkara zuwa birane, kuma yana da zuciyar haɗa kan jama’a ba tare da nuna bambanci ba. Wannan shi ne irin shugabancin da Zamfara ke nema a wannan lokaci mai muhimmanci.

Muna kira gare ka, Kogunan Gusau, da ka amsa kiran al’umma. Ka tsaya ka fafata domin karɓar kujerar Gwamnan Jihar Zamfara a 2027 insha Allahu, domin mutane da dama sun yarda kai ne mutumin da ya dace da wannan aiki.

Zamfara na bukatar shugaba mai tsoron Allah, gaskiya, hangen nesa da kuma karfin gwiwar kawo sauyi, kuma wadannan siffofi suna tare da kai.

Allah Ya taimaka, Ya ba da nasara, kuma Ya sanya abin da ya fi alheri ga Jihar Zamfara da al’ummarta.

An Jaddada Jagoranci Nagari Da Yaƙi Da Shan Miyagun Ƙwayoyi a Babban Taron Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya "CNG" a...
16/01/2026

An Jaddada Jagoranci Nagari Da Yaƙi Da Shan Miyagun Ƙwayoyi a Babban Taron Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya "CNG" a Sakkwato

Ƙungiyar Coalition of Northern Groups (CNG) ɓangaren ɗalibai ta samu gagarumar nasara wajen shirya laccar bai ɗaya da aka gudanar a Kwalejin Ilimi ta Shehu Shagari da ke Sakkwato.

An gudanar da laccar ne ƙarƙashin jagorancin Mai Martaba HRH Farfesa Sambo Wali Junaid (Wazirin Sakkwato), inda manyan masu jawabi s**a yi jawabai masu armashi kan batutuwa masu muhimmanci da s**a shafi kyakkyawan jagoranci nagari, illolin shan miyagun kwayoyi, da kuma mummunan tasirin "Hate speech" a makarantun gaba da sakandare da ma al’umma baki ɗaya.

Taron ya samu halartar ɗalibai masu yawa daga fannoni daban-daban, abin da ke nuna yadda matasa ke da ƙwazo da sha’awar rungumar kyawawan ɗabi’u, haɗin kai da jagoranci nagari.

Hakika, laccar ta ilmantarwa ta kuma yi tasiri sosai, inda ta haɗa zukatan matasa masu burin gina kyakkyawar makoma mai ɗorewa da ci gaban al’umma.

Masu Yaɗa Ƙarya Akan Gwamnan Bauchi Ba Za Ku Yi Nasara Ba!Muna jan hankalin jama’a game da wani labari na ƙarya da ake y...
07/01/2026

Masu Yaɗa Ƙarya Akan Gwamnan Bauchi Ba Za Ku Yi Nasara Ba!

Muna jan hankalin jama’a game da wani labari na ƙarya da ake yaɗawa a kafafen sada zumunta, wanda ake zargin cewa an bai wa wata ƙungiya da ake alaƙantawa da ta’addanci kuɗi daga Gwamnatin Jihar Bauchi. Wannan labari ba shi da tushe, b***e Malama, babu hujja, kuma ƙarya ce tsagwaronta.

Babu wani lokaci da Gwamnatin Jihar Bauchi, ko Mai Girma Gwamna Sanata Bala Abdulkadir Mohammed, ya amince ko ya ba da umarnin bai wa kowace ƙungiya da ke da alaƙa da ta’addanci kuɗi, ko ta kowace hanya. Wannan zargi an ƙirƙire shi ne kawai domin ɓata suna, yaudarar jama’a, da tayar da fitina.

Muna kira ga jama’a da su yi watsi da irin waɗannan labaran ƙarya, su kuma guji yaɗa bayanan da ba su tantance ba. Gwamnatin Jihar Bauchi ta himmatu wajen tabbatar da tsaro, zaman lafiya, da bin doka da oda, tare da haɗin gwiwa da hukumomin tsaro na ƙasa.

Duk wanda ke yaɗa wannan labari na ƙarya, yana da niyyar ɓata sunan shugabanci da ya samu amanar jama’a, kuma hakan ba zai hana gwamnati ci gaba da ayyukan alheri da ci gaban jihar Bauchi ba.

Gaskiya ce za ta yi nasara a kowane lokaci.

Kungiyar Arewa Media Writers Ta Yi Kira Ga Shugaba Tinubu Da Ya Gaggauta Sauke Ministan Abuja, Nyesom Wike…Kungiyar ta c...
05/01/2026

Kungiyar Arewa Media Writers Ta Yi Kira Ga Shugaba Tinubu Da Ya Gaggauta Sauke Ministan Abuja, Nyesom Wike

…Kungiyar ta ce dole ne a dakatar da duk wani yunkuri da ke barazana ga dimokaradiyya, zaman lafiya da haɗin kan ƙasa.

Daga Kungiyar “Arewa Media Writers”

Kungiyar Marubutan Arewa "Arewa Media Writers" ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙungiyar na Ƙasa, Comr. Haidar H. Hasheem (Kano), ta nuna matuƙar damuwa tare da yin Allah-wadai da abin da ta bayyana a matsayin k**a-karya, nuna wariya da cin zarafin ‘yan ƙasa, da ake zargin Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, na aikatawa.

Kungiyar ta ce abin takaici ne yadda ake zargin Ministan da amfani da ƙarfin iko wajen cuzgunawa ‘yan Arewa da ‘yan adawa, musamman saboda banbancin ra’ayin siyasa, abin da hakan ke tauye ‘yancin ‘yan ƙasa tare da zama barazana ga tsarin dimokaradiyyar Najeriya.

A cewar ƙungiyar, ana zargin Wike da amfani da hukumar EFCC da jami’an tsaro wajen tsoratarwa da musgunawa abokan hamayya, lamarin da ke haifar da fargaba, rashin adalci da rashin amincewa ga hukumomin gwamnati.

Kungiyar Arewa Media Writers ta kuma nuna damuwa kan yadda Ministan ke yin furuci da ayyuka masu ɗauke da wariya ga al'ummar Hausawa/Fulani, inda ta jaddada zargin da Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Muhammad, ya yi a baya-bayan nan, wanda yace ya samu wata masaniya daga mai jiya mai tushe dake nuna cewa hatta hukumomin EFCC, Wike ke amfani da su wajen matsin lamba ga yan adawa, haka kuma ya tabbatar dasa hannun Ministan wajen ƙoƙarin bata masa suna ta hanyar jingina shi da zargin ɗaukar nauyin ta’addanci a kotu.

Kungiyar ta bayyana cewa irin waɗannan zarge-zarge ba komai ba ne illa kiyayya ta kabilanci da siyasar adawa, wanda hakan ya saba wa ruhin haɗin kan ƙasa. Idan baku manta ba tun a lokacin da Wike ke Gwamnan Jihar Rivers, an samu rahotannin rusa masallatai, rufe shaguna da gidajen ‘yan Arewa, tare da korar su daga jihar, abin da har yanzu ke ci wa zukatan al’umma tuwo a ƙwarya.

Haka kuma ƙungiyar ta yi tsokaci kan sauke Sakataren Ilimi na Abuja, Dr. Danlami, wanda ɗan Arewa ne, inda ta ce yadda aka yi hakan ya ƙara nuna amfani da iko ba bisa ƙa’ida ba, tare da mayar da shi aiki bisa wasu sharudda.

Ba wannan kaɗai ba, kungiyar ta kuma nuna damuwa kan zargin amfani da jami’an tsaro wajen tarwatsa rikici a helkwatar jam’iyyar PDP, inda aka ce har aka yi amfani da hayaki mai sa hawaye ga wasu gwamnoni ciki har da Seyi Makinde da Bala Muhammad, lamarin da bai dace ba ga shugabanni da kundin tsarin mulki ya tanadar musu da rigar kariya.

Kungiyar Arewa Media Writers ta jaddada cewa tsarin shugabancin Najeriya bai ginu kan kabilanci, wariya ko ramuwar siyasa ba, illa adalci, daidaito da mutunta ‘yancin kowa.

A ƙarshe, Kungiyar Arewa Media Writers tana kira ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya gaggauta dakatar da duk wani yunkuri da ke barazana ga dimokaradiyya Najeriya, taka wa Ministan Abuja burki, ko kuma a sauke shi daga mukaminsa, domin kare martabar dimokaradiyya, zaman lafiya da haɗin kan ƙasa.

Arewa Media Writers za ta ci gaba da tsayawa kan gaskiya, adalci da kare haƙƙin al’umma.

✍️✍️
Comr Nura Siniya
Chairman Arewa Media Writer's Katsina Chapter

GWAMNAN JIHAR BAUCHI YA FALLASA ASIRIN MINISTAN ABUJA NYESOM WIKEMaigirma Gwamnan jihar mu na Bauchi Senator Bala Abdulk...
02/01/2026

GWAMNAN JIHAR BAUCHI YA FALLASA ASIRIN MINISTAN ABUJA NYESOM WIKE

Maigirma Gwamnan jihar mu na Bauchi Senator Bala Abdulkadir Mohammed (Kauran Daular Usmaniyyah) ya fallasa asiri na makircin da Ministan Abuja Nyesom Wike yake kulla masa da jihar Bauchi gaba daya

Maigirma Gwamna yayi wannan fallasa ne a cikin shirin Sunrise Daily na Channels TV dazu da safe, yace akwai wanda yake shirya min makirci, kuma na san shi, shine Ministan Abuja na yanzu Nyesom Wike, ya fada wa duniya cewa zai kunna wuta a jihata na Bauchi

Kauran Daular Usmaniyyah yaci gaba da cewa; na fahimci Wike ne yake bada umarni wa hukuma irin na EFCC wajen batani, yana bawa mutane cin hanci, yana sayar da filayen Abuja yana amfani dasu wajen cimma burinsa, ba sabon abu bane a gareni saboda na taba rike mukamin Ministan Abuja na shekaru 6 na san komai

Gwamnan Bauchi yaci gaba da cewa; yana da hujjoji daga majiyarsa na sirri dake EFCC wanda s**a tabbatar masa da cewa Wike ne yake tsara duk abinda yake faruwa da ‘yan adawar siyasa a Nigeria

Kaura yace tsohon Accountant General dinsa na jihar Bauchi yaci amanata, ni na kaishi Kotu da kaina domin a masa hukunci, daga bisani Kotu ta bada belinsa, to a yanzu Wike ne yake aiki dashi a Kotu wajen bada shaida na karya akan mukarrabaina da aka k**a

A matsayina na Gwamna wanda na rike manyan muk**ai tun daga Sanata har Minista, ina shugaban al'ummah ta ya zai kasance ina daukar nauyin ta'addanci, ana min wannan sharri ne saboda ina cikin manyan 'yan adawa

Zan bi duk matakan da s**a dace domin na kare kaina, na rubuta wa Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya takardan korafi, tare da sanar da hukumomin tsaro, kuma zan kai korafina zuwa ga hukumonin Majalisar dinkin duniya, inji Maigirma Gwamna

Sannan Gwamna Bala yace Shugaban Kasa Tinubu yana kewaye da 'yan daba, 'yan damfara wadanda suke son ha||akashi a siyasance irinsu Wike

Muna rokon Allah Ya kare jihar Bauchi daga wadanda suke neman jingina mana ta'addanci, Allah Ya sa mugun nufinsu ya kare a kansu da iyalansu kadai.

Ƙungiyar “Kano Youth For Good Governance” Ta Caccaki Sanata Rufa’i Hanga Bisa Gazawa, Raini Da Butulci A Kano Ta Tsakiya...
31/12/2025

Ƙungiyar “Kano Youth For Good Governance” Ta Caccaki Sanata Rufa’i Hanga Bisa Gazawa, Raini Da Butulci A Kano Ta Tsakiya

Ƙungiyar Kano Youth For Good Governance ƙarƙashin jagorancin Comr. Nura Sale na zargin Sanata Rufa’i Hanga da zama Sanata mafi gazawa a tarihin Kano ta Tsakiya.

Sanata wanda ya kasa kawo ko aiki ɗaya da al’umma za su nuna su ce “ga abin da ya mana”, sai dai zama a Abuja yana cin moriyar mukami tare da iyalinsa, alhali jama’ar Kano ta tsakiya na fama da talauci da rashin kulawa.

Mutumin da ya sanyawa karen gidansa sunan “Kwankwaso” akwai butulcin da ya wuce wannan, ba soyayya bane, cin mutunci ne kai tsaye ga tafiya da kuma abinda al’ummar Kano ke girmamawa, kuma hakan ya nuna a sarari cewa Sanatan ba shi da kishin jama’a ko dabi’ar girmamawa ga Kwankwaso.

Butulcin Sanata Rufa’i Hanga ya kai matakin da ya kasa taimakawa iyalan marigayi Alh. Yawale, mutumin da ya yi masa riga da wando, ya tsaya masa a lokacin bukata. Wannan hali na nuna cewa Sanatan ba ya tuna alheri, kuma bai cancanci amanar jama’a ba.

Abin mamaki shi ne yadda Sanatan ke fitowa yana zargin wasu da butulci da cin amana, har sanata ne yake da bakin cin mutuncin manyan Jihar Kano, alhali shi ne cikakken misalin abin da yake zargi na cin amana da rashin amfani.

Kano Youth For Good Governance na jaddada cewa tarihin Sanata Rufa’i Hanga ba tarihin aiki ba ne, tarihin gazawa ne, raini da cin amana irin ta siyasa.

✍️
Kano Youth For Good Governance
Comr. Nura Sale
Shugaban Kungiyar

Matasa Daga Arewacin Najeriya Sun Bukaci Tinubu Ya Sallami Ministan Tsaro Bello MatawalleƘungiyar Northern Christian You...
19/12/2025

Matasa Daga Arewacin Najeriya Sun Bukaci Tinubu Ya Sallami Ministan Tsaro Bello Matawalle

Ƙungiyar Northern Christian Youth Coalition (NCYC) ta bukaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya sallami Ministan Ƙasa na Tsaro, Dr. Bello Muhammed Matawalle, sak**akon zarge-zargen da suke nuna cewa yana da alaƙa da ta'addanci wanda tsohon hadiminsa Musa Kamarawa yayi ikirari.

A cikin wata sanarwa da Babban Kwamishinan ƙungiyar, Jeremaid Hudso Bako, ya fitar, ƙungiyar ta ce kira da take yi na nufin ƙarfafa gaskiya, riƙon amana, da dawo da amincewar jama’a ga gwamnati, musamman a bangaren tsaro.

Ƙungiyar ta yaba wa Shugaba Tinubu kan tsige tsohon Shugaban Hukumar NMDPRA, Farouk Ahmed, tana mai cewa hakan alama ce ta ƙoƙarin gwamnati wajen yaƙi da cin hanci da rashawa. Sai dai ta ce ya dace a yi adalci iri ɗaya ga kowa, ciki har da Matawalle.

NCYC ta jaddada cewa zarge-zargen da ake yi wa Matawalle suna da nauyi sosai, musamman ganin cewa suna da alaƙa da tsaron ƙasa da rayukan al’umma, don haka bai dace a yi shiru a kansu ba.

Ƙungiyar ta ce idan har gwamnatin Tinubu na son a san ta da gaskiya, adalci da shugabanci nagari, to ya zama dole ta ɗauki mataki cikin gaggawa kan duk wani jami’i da ake zargi da aikata abubuwan da za su iya lalata amincin ƙasa tare da sauke ƙaramin ministan da kuma gudanar da binciken gaggawa a kansa.

Odua People’s Assembly Ta Nemi Gwamnati Ta Gudanar Da Bincike Gaggawa Kan Matawalle....Zargin alaƙa da ‘yan bindiga bara...
16/12/2025

Odua People’s Assembly Ta Nemi Gwamnati Ta Gudanar Da Bincike Gaggawa Kan Matawalle
....Zargin alaƙa da ‘yan bindiga barazana ce ga tsaron Najeriya.

Ƙungiyar Odua People’s Assembly (OPA) ta nuna damuwa matuƙa kan zargin da ake yi wa Ministan Tsaron Ƙasa (State), Bello Matawalle, dangane da alaƙa da ‘yan bindiga. Ƙungiyar ta ce zargin yana da hatsari ga tsaron ƙasa da amincewar jama’a.

OPA ta buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta gudanar da bincike mai zaman kansa, tare da sanya gaskiya kuma ba tare da son kai ba, domin fayyace gaskiyar lamarin. Ta ce rashin daukar mataki zai ƙara raunana amincewar jama’a da hukumomin gwamnati, musamman a lokacin da Najeriya ke fama da matsanancin matsalar tsaro.

Ƙungiyar ta ce bayyanar wani bidiyo da ke nuna Bello Turji, shugaban ‘yan bindiga, yana kare Matawalle abin tayar da hankali ne, domin yana nuna yiyuwar haɗin kai tsakanin jami’an gwamnati da masu laifi.

OPA ta bayyana cewa duk wata alaƙa, kai tsaye ko a kaikaice, tsakanin jami’an gwamnati da ‘yan bindiga cin amanar ‘yan Najeriya ne, musamman waɗanda s**a sha wahala sak**akon rashin tsaro.

A matsayin mataki na dawo da amincewar jama’a, OPA ta buƙaci a sauke Matawalle daga muƙaminsa nan take, tare da kafa cikakken tsari na bincike mai zaman kansa. Ta kuma gargadi cewa rashin daukar mataki mai tsauri zai ƙarfafa ‘yan bindiga tare da ƙara ta’azzara rashin tsaro.

Ƙungiyar ta bukaci ‘yan Najeriya su kasance masu faɗakarwa, su kuma riƙa kira ga alhakin shugabanni, tana jaddada cewa yaƙi da ‘yan bindiga ya zama na bai ɗaya, ba tare da la’akari da siyasa ko yanki ba.

Sa Hannun
Sunday Daniel
Mai magana da yawun Odua People’s Assembly

Address

Pantami Hurumin Da'u Quaters
Gombe

Opening Hours

Monday 06:00 - 12:00
Tuesday 06:00 - 12:00
Wednesday 06:00 - 12:00
Thursday 06:00 - 12:00
Friday 06:00 - 13:00
Saturday 06:00 - 12:00
Sunday 06:00 - 13:00

Telephone

+2348125747767

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Media Watch posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa Media Watch:

Share