Arewa Media Watch

Arewa  Media Watch News Media Company

OPA Ta Soki Naɗin Amupitan a Matsayin Shugaban INEC, Ta Ce Cancantarsa Ba Ta Kai Ya Riƙe Hukumar Zaɓe BaOdua People’s As...
28/11/2025

OPA Ta Soki Naɗin Amupitan a Matsayin Shugaban INEC, Ta Ce Cancantarsa Ba Ta Kai Ya Riƙe Hukumar Zaɓe Ba

Odua People’s Assembly (OPA) ta fito fili ta bayyana rashin gamsuwarta da nadin Joash Ojo Amupitan, SAN, a matsayin sabon Shugaban INEC, tana cewa wannan nadin na iya zama barazana ga sahihancin zaɓe da kwanciyar hankali na demokradiyya a Najeriya.

A cikin sanarwar da Richard Olatunji Kayode ya fitar, OPA ta ce kasar tana fuskantar mawuyacin hali na rashin amincewa da sak**akon zaɓe, don haka wajibi ne INEC ta samu shugaba mai gaskiya, kwarjini da cikakken tarihin tsayuwa kan adalci wanda duka wannan halayen Amupitan bai cika su ba.

Kungiyar ta goyi bayan ƙungiyar kwararrun lauyoyi sama da 1,000 (ALDRAP), wadda ta riga ta yi tir da nadin, tana cewa akwai bayanan da ke nuna alakar siyasa tsakanin Amupitan da Ministan Abuja, Nyesom Wike, wasu majiyoyin ma na zargin yaron Wike ne, alakar da OPA ta ce na iya haifar da shakku game da ikon Amupitan na yin aikin da bai dace ba.

OPA ta yi gargadin cewa duk wani shugaban INEC da ke da inuwa ko kusanci da manyan ‘yan siyasa ba zai iya gina sahihin tsarin zaɓe ba. Ta ce idan aka yi watsi da waɗannan korafe-korafe, za a iya sake fadawa cikin rikici, rashin tabbas da asarar amincewar jama’a ga INEC.

Ta bukaci Majalisar Dattawa da ta yi amfani da mukamin amincewa cikin gaskiya, ba tare da siyasa ta shige ciki ba, domin kare demokradiyyar Najeriya.

A ƙarshe, OPA ta kira kungiyoyin farar hula, matasa, lauyoyi da ‘yan jarida su kasance masu sa ido, su kare muradun kasa, domin a samar da INEC da za ta yi aiki bisa gaskiya, ba tare da fargaba ko tsoron siyasa ba.

NDYC Ta Caccaki Wike da INEC Kan Yunkurin Rusa Dimokuraɗiyyar NajeriyaƘungiyar Niger Delta Youth Congress (NDYC) ta yi t...
25/11/2025

NDYC Ta Caccaki Wike da INEC Kan Yunkurin Rusa Dimokuraɗiyyar Najeriya

Ƙungiyar Niger Delta Youth Congress (NDYC) ta yi taron ’yan jarida domin bayyana damuwa kan yadda Ministan FCT, Nyesom Wike, da kuma yadda INEC ke nuna rashin adalaci game da sak**akon gangamin PDP na Ibadan ke zama babbar barazana ga dimokuraɗiyyar Najeriya.

NDYC ta zargi Wike da amfani da muƙaminsa wajen tsoma baki cikin jam’iyya, tayar da rikici, tsoratarwa da kokarin tilasta ra’ayinsa, abin da ke yi wa tsarin dimokuraɗiyya mummunar illa. Ta ce halayensa na nuna girman kai, raina doka da neman iko su na iya tarwatsa ƙasa.

Kungiyar ta roki Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gargaɗi Wike, ya tunasar da shi cewa shi bawa ne na jama’a, ba sarki ba.

A bangaren INEC kuwa, NDYC ta nuna damuwa kan yadda take jan kafa wajen tabbatar da zababben shugaban PDP Kabiru Turaki, tana nuna fifiko ga Damagum. Ta ce wannan ya tauye adalci, ya kuma lalata amincewar jama’a da hukumar zabe.

NDYC ta jaddada cewa sak**akon taron Ibadan halastacce ne, kuma INEC dole ta tsaya kan doka ba tare da shiga hannun masu son murde sak**akon siyasa ba don biyan buƙatar Wike.

Ta kuma bayyana cewa halayen Wike ba sa wakiltar mutanen Niger Delta gaba ɗaya.

A ƙarshe, NDYC ta ce za ta ci gaba da kare dimokuraɗiyya da doka, domin Najeriya ta fi kowane mutum girma, kuma duk wanda ya yi barazana ga tsarin mulki dole a tsawatar masa.

Da hannun
Comr. Israel Uwejeyan, National Coordinator, NDYC

22/11/2025

INEC's Shameful Bias

It’s now clear that INEC under this new chairman has abandoned neutrality and is gradually turning into Wike’s personal agency. The same INEC that spoke with confidence on Arise News on November 11 is now contradicting itself just to please Wike.

This sudden turnaround shows dangerous bias, a deliberate attempt to weaken the PDP and serve selfish political interests. A national institution should not dance to the tune of one politician, yet this INEC chairman seems ready to destroy credibility at all cost.

Tsayuwar Daka a Ibadan: Yadda Kauran Bauchi, Dauda Lawal da Makinde S**a Ceto Mutuncin Jam'iyyar PDPA babban taron da ja...
21/11/2025

Tsayuwar Daka a Ibadan: Yadda Kauran Bauchi, Dauda Lawal da Makinde S**a Ceto Mutuncin Jam'iyyar PDP

A babban taron da jam’iyyar PDP ta gudanar a Ibadan ranar Asabar da ta gabata, an ga wani sabon salo na shugabanci da jajircewa wanda ya tabbatarwa ‘yan Najeriya cewa PDP har yanzu tana da waɗanda za su tsaya tsayin daka domin kare darajarta.

A cikin waɗanda s**a fito fili wajen nuna wannan kwazo, akwai Kauran Bauchi, wanda ya jagoranci aikin gyara da tsaftace jam’iyya da tsantseni. Tsayuwarsa wajen korar masu tada zaune tsaye a ciki, musamman waɗanda ke aiki da boyayyun manufa don rusa jam’iyyar daga cikin gida, ya zama abin yabo da koyi. A gaskiya, Kauran Bauchi ya zama ginshiƙin da ya hana jam’iyyar durkushewa.

Baya ga haka, Gwamnan Zamfara Dr. Dauda Lawal ya nuna irin kishinsa ga dimokuraɗiyya. Goyon bayansa ga sahihin tsari da adalci a cikin jam’iyya ya karfafa gwiwar mambobi da magoya baya, ya tabbatar masu cewa PDP na da shugabanni da ba za su lamunci karya ko shisshigi ba.

A bangaren Seyi Makinde, Gwamnan jihar Oyo, ya ba da cikakken gudunmawa wajen tabbatar da cewa taron Ibadan ya kasance sahihi, kuma cikin tsarin da ya dace. Makinde ya tabbatar da cewa jam’iyya ta gudana bisa ka’ida, ba tare da batan batu ko rikice-rikice ba, aikin da ya kara tabbatar da cewa PDP jam’iyyar da take da ni’imar shugabanni masu hangen nesa.

A tare, waɗannan manyan shugabanni uku sun yi abin da ake kira ceto martabar PDP, tare da dawo da yarda da kwarin gwiwar jama’a. Sun nuna cewa jam’iyyar adawa ba ta mutu ba, kuma ba za ta mutu ba, muddin akwai shugabanni irin su Kauran Bauchi, Dr. Dauda Lawal da Seyi Makinde.

A Ibadan, PDP ta sake tsayawa kan kafafunta kuma hakan ya sake busawa dimokuraɗiyya a rai.

INEC Tayi Watsi Da Buƙatar Masu Yiwa PDP Zagon Kasa, Ta Tabbatar Da Damagun a Matsayin Shugaban Jam'iyyar  PDP Daga Jimo...
19/11/2025

INEC Tayi Watsi Da Buƙatar Masu Yiwa PDP Zagon Kasa, Ta Tabbatar Da Damagun a Matsayin Shugaban Jam'iyyar PDP

Daga Jimoh Isma'il Adetunji

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta tabbatar da cewa Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa (NWC) na jam’iyyar PDP ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyya na ƙasa Kabiru Tanimu Turaki (SAN) ita ce hukuma ɗaya tilo da ta dace a doka.

INEC ta ƙi yarda da takardar bogi da wasu korarru Mohammed Abdulrahman da Samuel Anyanwu s**a aika suna kiran a dage zaben fidda gwani na gwamnan Jihar Ekiti, matakin da ya fallasa yunƙurinsu na rugujewa jam’iyyar adawa ta ƙasa ta hanyar karya doka da son zuciya.

INEC ta jaddada cewa wannan takardar da waɗannan haramtattun shugabanni s**a turo a ranar 6 ga Nuwamba, 2025, ba ta da wani inganci. Su kansu sun yi ikirarin shugabanci ne bisa ƙarya, inda s**a jingina dalilan karya na wai “matsalolin shirye-shirye” domin su kawo tangarda ga zaɓen ranar 8 ga Nuwamba.

Hukumar ta bayyana a fili cewa kawai sa hannun shugaban jam’iyya na ƙasa da sakataren ƙasa na halastattaccen NWC ne ake karɓa a hukumance.

Matakin INEC ya yi daidai da hukuncin da jam’iyyar PDP ta yanke tun farko na dakatar da Anyanwu, Abdulrahman da wasu abokan aikinsu a ranar 1 ga Nuwamba, 2025 saboda aikata laifukan karya tsarin jam’iyya, wanda ya sabawa sassan 57(3), 58(1)(a)(b)(c)(h), da 59(1) na kundin tsarin PDP (2017 da aka gyara).

Wadannan hukunci an tabbatar da su ne a babban taron jam’iyyar da aka yi a Ibadan a ranar 15 ga Nuwamba, 2025, inda aka zaɓi Barrister Tanimu Turaki a matsayin sabon shugaban jam’iyya na ƙasa, tare da tsige manyan masu tada fitina ciki har da Anyanwu, Abdulrahman, Nyesom Wike da Ayo Fayose saboda aikata manyan laifuka na tafka ayyukan adawa da jam’iyyar, ƙirƙiro bangarori, da amfani da kotu wajen rugujewa jam’iyya.

Wike Na Kawo Barazana Ga Demokradiyyar Najeriya – Ƙungiyar Nigeria Unite Ta Gargadi EUƘungiyar Nigeria Unite ta aika wa ...
14/11/2025

Wike Na Kawo Barazana Ga Demokradiyyar Najeriya – Ƙungiyar Nigeria Unite Ta Gargadi EU

Ƙungiyar Nigeria Unite ta aika wa ƙungiyar Tarayyar Turai (EU) da wasika mai zafi, tana zargin Ministan Abuja, Nyesom Wike, da haifar da barazana ga dimokiraɗiyar Najeriya ta hanyar murkushe ‘yan adawa da goyon bayan shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu domin tabbatar da wa’adi na biyu ba tare da hamayya ba.

Ƙungiyar ta ce bayan rugujewar dimokiraɗiya a Mali, Burkina Faso da Nijar, yanzu haka Najeriya ma na kan layin tangal-tangal, saboda irin matakan zaluntar ‘yan adawa da kuma amfani da cin hanci wajen tilasta sauya sheƙa.

Ta gargadi cewar idan ba a dauki mataki ba, lamarin zai iya jefa Najeriya cikin rikici, ya kawo bacewar tsaro a yankin Sahel, tare da tura miliyoyin ‘yan Najeriya zuwa Turai da Amurka a matsayin ‘yan gudun hijira.

Nigeria Unite ta kuma bukaci EU, AU, Amurka da Birtaniya su sanya takunkumi kan Wike da dakatar da shi daga tafiye-tafiye, tare da daukar mataki kan wasu manyan alkalan ƙasar, kwamishinan ‘yan sanda Abuja da hukumar INEC, domin cewar suna sabawa dokokin siyasa da na aikinsu.

Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya Ta Soki Shirye-shiryen Zanga-zangar Neman Sakin Nnamdi KanuKungiyar Gamayyar Kungi...
19/10/2025

Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya Ta Soki Shirye-shiryen Zanga-zangar Neman Sakin Nnamdi Kanu

Kungiyar Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya (CNG) ta bayyana adawa da s**a mai tsanani kan shirin gudanar da zanga-zangar neman a saki shugaban ƙungiyar IPOB da aka haramta, Nnamdi Kanu.

CNG ta ce wannan yunkuri da wasu shugabannin siyasa da na al’ada na kabilar Igbo, da masu kiran kansu ‘yan gwagwarmaya k**ar Omoyele Sowore, ke jagoranta tare da wasu ‘yan Arewa marasa kishin ƙasa wani makirci ne na yi wa ƙasa karan tsaye da barazana ga zaman lafiya da doka.

Kungiyar ta bayyana cewa Nnamdi Kanu da IPOB sun haifar da mutuwar fiye da mutane 1,200 ciki har da jami’an tsaro sama da 400, sun ƙone ofisoshin ‘yan sanda fiye da 100, kuma sun jawo asarar dukiya da ta haura ₦450 biliyan a Kudu maso Gabas.

CNG ta tunatar da cewa tun daga 2016 Kanu ya kasance mai yada ƙiyayya, tashin hankali da rarrabuwar kai ta hanyar IPOB da rundunarsa ta ESN, inda aka kashe ‘yan Arewa da dama, aka lalata kasuwanci, tare da hana zaman lafiya.

Kungiyar ta kuma yi kira ga gwamnatin tarayya ta tabbatar da shari’ar Kanu ta tafi yadda doka ta tanada ba tare da matsin lamba na siyasa ba, tare da bukatar jami’an tsaro su hana duk wata zanga-zangar da zata kawo tashin hankali.

CNG ta gargadi ‘yan siyasa da masu daukar nauyin zanga-zangar da cewa za a bincike su, tare da kira ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu da kada ya bari a yi masa barazana wajen yin doka bisa ra’ayi ko jin kai.

A ƙarshe, CNG ta jaddada cewa sakin Nnamdi Kanu ba zai kawo zaman lafiya ba, sai dai ya kara dagula ƙasa da karya tsarin shari’a. Ƙasar da ba ta mutunta doka ba, ba za ta samu zaman lafiya ba.

Sa hannu:
Comrade Jamilu Aliyu Charanchi
Koodineta Na Ƙasa, CNG
Abuja, Najeriya

Zargin Badaƙalar Miliyan 23: Tsohon Shugaban Masu Rinjaye A Majalisar Dokokin Jihar  Borno, Hon. Idrisa Jidda, da Sa’ad ...
28/09/2025

Zargin Badaƙalar Miliyan 23: Tsohon Shugaban Masu Rinjaye A Majalisar Dokokin Jihar Borno, Hon. Idrisa Jidda, da Sa’ad Abubakar Isah Ana Zarginsu da Karɓar Naira Miliyan 23 a Badakalar Kwangila Da Aka Danganta Da Hon. Adamu Aliyu

Daga Tukur I. Tukur

Tsohon Shugaban Masu Rinjaye A Majalisar Dokokin Jihar Borno, Hon. Idrisa Jidda, tare da Sa’ad Abubakar Isah, ana zargin sun karɓi Naira miliyan 23 daga hannun Mohammad Jidda, wanda ya shigar da ƙara kan batun badakalar kwangila a Jami’ar Jos ƙarar tana hannun Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa da Sauran Laifuka (ICPC).

Wannan batu ya fito fili ne a wata hira da mai aikin, Mr. Lawal Abubakar, wanda yake cikin rashin lafiya a gidansa da ke Dutsin-Ma, Jihar Katsina. Ya ce Hon. Idrisa Jidda ɗan’uwan mai ƙarar ne, Mohammad Jidda.

Mr. Lawal Abubakar ya bayyana cewa Hon. Idrisa Jidda, wanda a halin yanzu yake matsayin Mashawarcin Gwamna kan Harkokin Gidaje ga Gwamna Babagana Umara Zulum na Jihar Borno, ya karɓi Naira miliyan 20 daga asusun Zenith Bank na kamfanin Imanal Concept Ltd, mallakar Sa’ad Abubakar Isah wannan kuɗi na daga cikin abin da ake tuhuma da shi da aka danganta da sunan Hon. Adamu Aliyu.

Mr. Abubakar ya ce shi dai kawai ya gabatar da Hon. Adamu Aliyu ga mai kasuwancin Mohammad Jidda, ya kuma umarce shi ya sanya kuɗi a asusunsa. Bayan kwangilar ta karye, “na faɗa wa Adamu ya mayar da duk abin da aka biya shi, kuma an shaida min cewa ya mayar.”

A cewar Mr. Lawal Abubakar, Hon. Idrisa Jidda da Sa’ad Abubakar Isah sun tunkari Mohammad Jidda s**a karɓi kuɗaɗe daga kamfaninsa, Mohibba Investment Limited, s**a raba su tsakaninsu.

“Sun yaudari Mohammad Jidda suna cewa an biya Hon. Adamu Aliyu. Amma a ranar 29 ga Disamba, 2023, Alhaji Idrisa Jidda ya karɓi Naira miliyan 20 da aka shigar masa a asusun Zenith Bank daga Imanal Concept Ltd. Ina da rasit ɗin banki da zai tabbatar da hakan. Dukkanin asusun da aka yi ma’amala da su suna a Zenith Bank,” in ji Mr. Lawal Abubakar.

Ya ƙara cewa akwai ƙarin takardu da hujjoji da ke nuna wasu ma’amaloli da s**a shafi Idrisa Jidda da Sa’ad Abubakar Isah.

“Sa’ad Abubakar Isah tare da Hon. Idrisa Jidda sun taɓa haɗuwa da mai ƙarar s**a ce suna wakiltar Mr. Lawal Abubakar. S**a karɓi Naira miliyan 23 s**a raba tsakanin su. Saboda haka ya k**ata mai ƙarar ya mayar da ƙarar ne a kan Hon. Idrisa Jidda da Sa’ad Abubakar Isah (mai kamfanin Imanal Concept Ltd), ba kan Hon. Adamu Aliyu ba,” ya yi nuni.

Gwamnatin Tinubu Ta Fi Duk Gwamnatocin Mulkin Soja Muni Da K**a Karya A Tarihin Nijeriya, Inji El-RufaiTsohon Gwamnan Ji...
22/09/2025

Gwamnatin Tinubu Ta Fi Duk Gwamnatocin Mulkin Soja Muni Da K**a Karya A Tarihin Nijeriya, Inji El-Rufai

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya jefa sabon kakkausan magana kan gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, inda ya bayyana cewa wannan gwamnati ta fi kowace gwamnatin soja da Najeriya ta taba fuskanta muni da zalunci, k**ar yadda jaridar Channel Television s**a wallafa.

El-Rufai ya jaddada cewa talakawa na cikin mawuyacin hali, matsin tattalin arziki ya yi tsanani, farashin kaya ya haura sama, sannan rashin tsaro ya kara ta’azzara. Ya ce idan aka kwatanta halin da ake ciki yanzu da lokacin mulkin soja, rayuwar ‘yan Najeriya ta fi ta yanzu sauki.

Wannan furuci na El-Rufai ya janyo cece-kuce a tsakanin ‘yan kasa, inda wasu ke ganin ya dace a saurari wannan kira saboda gaskiyar abinda ke faruwa, yayin da wasu kuma ke kallon shi a matsayin kalaman tunzuri na siyasa.

Ko me zaku ce?

Daga Comr Haidar H Hasheem

DWI Ta Yi Allah-wadai da Zarge-zargen Banza Marasa Tushe Na Abubakar Malami Kan ’Yan Majalisar Jihar KebbiKungiyar Democ...
19/09/2025

DWI Ta Yi Allah-wadai da Zarge-zargen Banza Marasa Tushe Na Abubakar Malami Kan ’Yan Majalisar Jihar Kebbi

Kungiyar Democracy Watch Initiative (DWI) ta bayyana takaici da ƙin amincewa da ƙorafin da tsohon Ministan Shari’a, Abubakar Malami (SAN), ya shigar a kan ’yan majalisar jihar Kebbi da ke kira da a k**a shi tare da gurfanar da shi gaban doka.

A cewar kungiyar, zarge-zargen Malami cewa Gwamna Nasir Idris da shugabannin jam’iyyar APC suna shirin shigo da ’yan daba da mak**ai cikin jihar, ba su da tushe kuma manufarsu kawai ita ce tada hankalin jama’a da kawo fitina.

Kungiyar ta kuma yi nuni da cewa Malami da kansa ana zarginsa da shigo da ’yan daba daga jihohin makwabta, abin da ya haddasa rikici a Birnin Kebbi da kai hari ga ofishin APC na jihar. Wannan, a cewar DWI, ya nuna cewa maimakon ya zama mutum mai kare doka da adalci, Malami ya zamo wanda ke yada fitina da kawo rikici.

DWI ta yi kira da gaggawa ga hukumomin tsaro da Majalisar Ɗinkin Tarayya da su k**a Malami tare da gurfanar da shi domin kare zaman lafiya da mutuncin dimokuraɗiyya.

Kungiyar ta kammala da tabbatar da goyon bayanta ga ’yan majalisar Kebbi da al’ummar jihar wajen neman adalci da tabbatar da siyasa mai lumana da gaskiya.

Kisan Hakimin Dogon Daji A Zamfara Barazana Ce Ga Tsaron Ƙasa – In Ji Shugaban Arewa Media Writer’s, Comr. Haidar H. Has...
18/09/2025

Kisan Hakimin Dogon Daji A Zamfara Barazana Ce Ga Tsaron Ƙasa – In Ji Shugaban Arewa Media Writer’s, Comr. Haidar H. Hasheem

Shugaban ƙungiyar Arewa Media Writer’s, na ƙasa ya bayyana matuƙar takaici da bacin rai kan kisan gilla da ‘yan bindiga s**a yi wa Hakimin Dogon Daji a ƙaramar hukumar Tsafe ta jihar Zamfara, inda s**a yi masa yankan rago har lahira. Wannan lamari abin kunya ne ga ƙasa baki ɗaya kuma babban ƙalubale ne ga gwamnati da hukumomin tsaro k**ar yadda rahotan BBC Hausa da Leadership s**a kawo rahotan.

Wannan mummunan hari ya sake tabbatar da cewa lamarin tsaro a Arewacin Najeriya na ta ƙara tabarbarewa, inda ake ci gaba da kai hare-hare a ƙauyuka, sace jama’a, kona gidaje da gonaki, tare da hallaka shugabannin al’umma ba tare da tsoro ba. Wannan yanayi ya jefa dubban mutane cikin fargaba, gudun hijira, da rasa amincewa ga gwamnati.

Ya k**ata gwamnati ta gane cewa tsaro ba abu ne da za a siyasantar da shi ba. Tsaro shi ne ginshiƙin kowace al’umma, kuma kariya ga rayuka da dukiyoyi wajibi ne na gwamnati. Rashin ɗaukar mataki mai tsauri na iya ƙara dagula rayuwar jama’a da kuma barazana ga makomar ƙasa baki ɗaya.

A wannan yanayi, muna kira da:

1. Gwamnati ta tashi tsaye da gaggawa wajen murkushe ‘yan bindiga da duk wata ƙungiya ta ta’addanci a Arewa.

2. A samar da kayan aiki na zamani ga jami’an tsaro, tare da horo da ƙarfafawa domin su iya gudanar da ayyukansu yadda ya k**ata.

3. A shimfiɗa tsare-tsare na dindindin don tabbatar da tsaro a ƙauyuka da birane.

A madadin al’ummar Arewa da ƙungiyar Arewa Media Writer’s, ina kira da a ɗauki wannan kisan da aka yi wa hakimin Dogon Daji a matsayin kira na musamman ga shugabanni a dukkan matakai, domin lokaci ya yi da za a kawo ƙarshen wannan masifar tsaro da ta addabi yankinmu.

A ƙarshe, ina addu’a ga Allah Madaukakin Sarki Ya jikan hakimin da aka kashe, Ya ba iyalansa da al’ummarsa juriya, Ya kuma dawo da zaman lafiya mai ɗorewa ga Najeriya baki ɗaya.

✍️ Rubutawa:
Comr. Haidar H. Hasheem
National Chairman, Arewa Media Writer’s

Al'umma A Jihar Imo Sun Yiwa El'rufai Tofin Alatsine, Sun Yi Watsi Da Shi Tare Da Nuna Ƙyma Da Irin SiyasarsaDaga Abdul-...
09/09/2025

Al'umma A Jihar Imo Sun Yiwa El'rufai Tofin Alatsine, Sun Yi Watsi Da Shi Tare Da Nuna Ƙyma Da Irin Siyasarsa

Daga Abdul-Azeez Suleiman

Nasir El-Rufai, tsohon gwamnan Kaduna, ya gamu da zanga-zangar ƙin karɓarsa a Owerri, Jihar Imo, lokacin da ya halarci Taron Odenigbo 2025 a Assumpta Cathedral. Jama’a sun fito da kwalaye da ƙorafe-ƙorafe, suna zarginsa da kalaman wariya kan kabilar Igbo a baya.

Wannan martani bai tsaya kan shi kaɗai ba, ya kuma fito da tsohuwar matsalar rashin haɗin kai, raunin Yaƙin Basasa, da kuma gajiyar jama’a ga shugabannin da ake ganin sun rabu da halin rayuwar talakawa.

Masu zanga-zangar har sun yi kira ga a tsawatar wa Peter Obi saboda kusancinsa da shi, abin da ya nuna cewa kowane ɗan siyasa na iya fuskantar tambaya muddin yana da alaƙa da mutanen da ake kallon masu raba kan ƙasa.

Zanga-zangar ta zama alamar cewa jama’a na da ƙarfi wajen kalubalantar manyan ‘yan siyasa, musamman a wannan zamani na kafafen sada zumunta. Darasin da ke ciki shi ne shugabanni su daina rarrabuwar kawuna, su rungumi tattaunawa, su girmama tarihi, domin kawai haka za a samu haɗin kan ƙasa mai bambance-bambance.

Jama’a Sun Yi Masa Watsi, Sun Nuna Ƙiyayya da Siyasar Rarrabuwar irin ta El'rufai, sun kuma shawarci Peter Obi da ya gaggauta nesanta kansa da El'rufai don tsira da mutuncinsa.

Address

Pantami Hurumin Da'u Quaters
Gombe

Opening Hours

Monday 06:00 - 12:00
Tuesday 06:00 - 12:00
Wednesday 06:00 - 12:00
Thursday 06:00 - 12:00
Friday 06:00 - 13:00
Saturday 06:00 - 12:00
Sunday 06:00 - 13:00

Telephone

+2348125747767

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Media Watch posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa Media Watch:

Share