Daily News Hausa

Daily News Hausa Daily News Hausa, is a licensed Nigerian newspaper company dedicated to delivering verified news and entertainment content in the Hausa language."
(3)

INNALILLAHI WA'INNAH ILAIHIR RAJ'IUNAllah ya yiwa Dan Makoyon Gombe rasuwa. Muna Addu'ar Allah ya jikanshi da Rahama, id...
15/08/2025

INNALILLAHI WA'INNAH ILAIHIR RAJ'IUN

Allah ya yiwa Dan Makoyon Gombe rasuwa. Muna Addu'ar Allah ya jikanshi da Rahama, idan tamu tazo Allah yasa mu cika da imani Yaa Hayyu Yaa Qayyum.

BAUCHI: Gwamna Bala Mohammed Ya Nada Dan Asalin China a Matsayin Mai Ba da Shawara Kan Tattalin ArzikiGwamnan Jihar Bauc...
15/08/2025

BAUCHI: Gwamna Bala Mohammed Ya Nada Dan Asalin China a Matsayin Mai Ba da Shawara Kan Tattalin Arziki

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed, ya ɗauki matakin da ba kasafai ake samu ba, ta hanyar naɗa wani dan asalin kasar China a matsayin mai ba shi shawara na musamman kan harkokin tattalin arziki.

Wannan naɗa ya nuna ci gaba da buɗaƙar siyasa da tattalin arziki da gwamnatin jihar ke yi tare da ƙoƙarin jawo masu zuba jari daga kasashen waje domin inganta tattalin arzikin jihar.

Dalibai Sama da 450,000 ne S**a Amfana daga Lamunin Karatu Daga Gwamnatin Tarayya – Ministan Yaɗa LabaraiMinistan Yaɗa L...
15/08/2025

Dalibai Sama da 450,000 ne S**a Amfana daga Lamunin Karatu Daga Gwamnatin Tarayya – Ministan Yaɗa Labarai

Ministan Yaɗa Labarai da wayar da kan Jama’a, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa sama da dalibai 450,000 a Najeriya sun amfana da lamunin karatu daga Asusun lamunin Ilimi na Najeriya (NELFUND) karkashin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu. Ministan ya yi wannan bayani ne a taron tattaunawa da ’yan ƙasa ( ) da aka gudanar a fadar gwamnatin Enugu.

Ya ce shirin ya biyo bayan manufofin Renewed Hope Agenda na Shugaban ƙasa domin samar da damar ilimi ga kowa, tare da sauƙaƙa wahalhalun kuɗi da dalibai ke fuskanta.

Idris ya kuma bayyana cewa akalla mutane 90,000 sun amfana daga shirin bada lamuni na “Consumer Credit Scheme”, tare da ƙarfafawa matasa da ’yan kasuwa ta hanyar samar da kuɗaɗe ga masana’antu da ƙananan sana’o’i.

Ya yi kira ga matasa da ’yan kasuwa da su yi amfani da waɗannan damammaki domin bunƙasa tattalin arzikin yankinsu da ƙasar baki ɗaya.

DA DUMI-DUMI: Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Cibiyar Maganin Ciwon Daji a EnuguGwamnatin Tarayya ta tabbatar da samar da wata...
15/08/2025

DA DUMI-DUMI: Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Cibiyar Maganin Ciwon Daji a Enugu

Gwamnatin Tarayya ta tabbatar da samar da wata cibiyar kula da cutar ciwon daji a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Najeriya (UNTH) da ke Ituku-Ozalla, jihar Enugu.

Ministan Yada Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya jagoranci mambobin Tawagar Sadarwa ta Ƙasa a ziyarar da s**a kai cibiyar, inda s**a duba irin kayan aiki da hanyoyin da ake bi wajen kula da marasa lafiya.

Cibiyar na daga cikin kokarin gwamnatin tarayya na inganta lafiyar 'yan kasa da kuma saukaka wahalhalun da marasa lafiya ke fuskanta wajen neman magani.

TARON MAULIDI A JAMI’AR ALIKO DANGOTE: Tunawa da Manzon Allah (SAW)Kungiyar Muslim Sufi Movement of Nigeria reshen Jami’...
14/08/2025

TARON MAULIDI A JAMI’AR ALIKO DANGOTE: Tunawa da Manzon Allah (SAW)

Kungiyar Muslim Sufi Movement of Nigeria reshen Jami’ar Aliko Dangote University of Science and Technology, Wudil, ta shirya babban taron Maulidin Annabi Muhammadu (SAW) a ranar Alhamis.

Taron ya samu halartar ɗalibai da malamai, inda aka yi tunawa da haihuwar Manzon Allah (SAW) tare da karfafa soyayya da bin koyarwarsa. An gudanar da karatun Alƙur’ani, wa’azi, da addu’o’i na musamman domin zaman lafiya da ci gaban ƙasa.

Taron ya kasance wani mataki na inganta tarbiyya da fahimtar addini a tsakanin matasa, musamman a cikin muhallin ilimi.

Sheikh Kabiru Gombe Ya Samu Sabuwar Sarauta a Jihar TarabaHakimin Lau, Alhaji Abdullahi Ibrahim na Chindo, ya naɗa babba...
14/08/2025

Sheikh Kabiru Gombe Ya Samu Sabuwar Sarauta a Jihar Taraba

Hakimin Lau, Alhaji Abdullahi Ibrahim na Chindo, ya naɗa babban sakataren ƙungiyar Izala, Sheikh Muhammad Kabir Haruna Gombe, da sarautar Modibbon Lau.

An bayyana wannan karramawa a matsayin alamar girmamawa da yabawa da gudummawar malam Kabiru Gombe wajen wa’azi da faɗakarwa, musamman a fannin addini da ci gaban al’umma.

DA DUMI-DUMI: Dan Bello Ya Samu Sarautar “Sarkin Yakin Talakawan Najeriya”Majalisar Malamai Mahaddata Al-Qur’ani ta karr...
14/08/2025

DA DUMI-DUMI: Dan Bello Ya Samu Sarautar “Sarkin Yakin Talakawan Najeriya”

Majalisar Malamai Mahaddata Al-Qur’ani ta karrama ɗan gwagwarmaya Bello Galadanci (Dan Bello) da sarautar Sarkin Yakin Talakawan Najeriya, bisa jajircewarsa wajen kare muradun al'umma da tsayawa wajen wanzar da adalci.

An bayyana cewa wannan lambar girma wata alama ce ta girmamawa da goyon bayan da yake samu daga jama’a, musamman a tsakanin matalauta da talakawa da ya dade yana rajin kare hakkokinsu.

Majalisar zartarwa ta ƙasa Ta Dakatar da Kafa Manyan Makarantu har tsawon shekaru 7 don Inganta Wanda Ake DasuMajalisar ...
14/08/2025

Majalisar zartarwa ta ƙasa Ta Dakatar da Kafa Manyan Makarantu har tsawon shekaru 7 don Inganta Wanda Ake Dasu

Majalisar zartarwa ta ƙasa (FEC) ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta amince da sanya takunkumin shekaru bakwai kan kafa sabbin manyan makarantu na gaba da sakandare na tarayya a faɗin ƙasar. Wannan ya haɗa da jami’o’i, kwalejojin fasaha da kwalejojin ilimi. Ministan Ilimi, Tunji Alausa, ya bayyana cewa matsalar da ake fuskanta a fannin ilimi yanzu ba ta samun damar shiga makarantu ba ce, sai dai yawan maimaita kafa sababbin makarantu ba tare da isasshen kayan aiki da ma’aikata ba, wanda ke rage ingancin ilimi da lalata darajar da ɗaliban Najeriya ke da ita a idon duniya.

Alausa ya ce akwai jami’o’i na tarayya 72, na jihohi 108, da masu zaman kansu 159, haka kuma akwai irin wannan yawaitar a kwalejojin fasaha da na ilimi, gami da wasu cibiyoyi kamar monotechnics, kwalejojin noma, na kiwon lafiya da makamantansu. Ya bayyana cewa a wasu makarantu adadin ɗaliban da ke nema ya ragu ƙwarai. Haka ma a kwalejojin fasaha 295 da kwalejojin ilimi 219, inda wasu daga ciki basu samu ɗalibi ko ɗaya ba, lamarin da ke nuna asarar kuɗaɗe da rashin inganci.

Ya ce akwai misali daga arewacin ƙasar inda wata jami’ar tarayya ke da ƙasa da ɗalibai 800 amma tana da ma’aikata fiye da 1,200, wanda ya kira da abinda ba zai ɗore ba. Bisa haka, gwamnati ta dauki matakin takaita kafa sababbin makarantu domin maida hankali wajen inganta waɗanda ake da su, ta hanyar ƙara ƙarfin su, gyara kayan aiki da samar da ƙwararrun malamai. Ya ce manufar ita ce a ƙara ingancin ilimi, don tabbatar da cewa ƙasashen duniya na ci gaba da girmama digirorin Najeriya.

Sai dai duk da takunkumin, FEC ta amince da kafa sabbin jami’o’i masu zaman kansu guda tara wanda s**a daɗe a hukumar Jami’o’i ta kasa (NUC) kimanin shekaru shida. An kammala gina makarantun tuni da saka jarin biliyoyin naira. Alausa ya kuma ce an yi garambawul ga ka’idoji guda 350 ba sa aiki aiki a baya, kuma daga yanzu duk makarantar da za a kafa, ko ta gwamnati ko mai zaman kanta, ba zata samu amincewa ba sai ta cika sabbin sharuddan. Ya gargadi cewa idan ba a dauki mataki ba, yawan rashin aikin yi ga matasa zai ƙaru, kuma hakan zai rage tasirin digirin Najeriya a duniya.

ALLAH SARKI: Rasuwar Fatima Rabi’u Lawal: Ana Bukatar Addu’ar Rahama a GaretaInna lillahi wa inna ilaihi raji’un. Fatima...
14/08/2025

ALLAH SARKI: Rasuwar Fatima Rabi’u Lawal: Ana Bukatar Addu’ar Rahama a Gareta

Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un. Fatima Rabi’u Lawal ta rasu sakamakon haihuwa. Iyalanta da danginta sun bukaci al’umma da su sanya ta cikin addu’a, domin samun rahamar Allah da sauƙin hisabi. Allah ya gafarta mata, ya sanya Aljannah makoma.

DA DUMI DUMI: Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Buɗe Jami'ar Mata Ta Farko a NajeriyaGwamnatin tarayya ta amince da buɗe ja...
14/08/2025

DA DUMI DUMI: Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Buɗe Jami'ar Mata Ta Farko a Najeriya

Gwamnatin tarayya ta amince da buɗe jami'ar mata zalla ta farko a Najeriya, mai suna Tazkiyah University da ke Kaduna. Jami'ar wacce Sheikh Farfesa Ibrahim Ahmad Maqary ya kafa, za ta mayar da hankali kan ilimantar da mata kacokan, domin inganta rayuwarsu da ci gaban al'umma.

DA DUMI-DUMI: Manyan Fastoci 42 Da Bishop 2 Sun Karɓi Musulunci a AbujaA wani taron musamman da aka gudanar a babban ɗak...
14/08/2025

DA DUMI-DUMI: Manyan Fastoci 42 Da Bishop 2 Sun Karɓi Musulunci a Abuja

A wani taron musamman da aka gudanar a babban ɗakin taron masallacin ƙasa da ke Abuja, an samu karuwar mabiya addinin Musulunci bayan wasu manyan fastoci 42, bishop biyu, wata fasto mace da kuma sista, tare da iyalansu, sun bayyana shahadarsu.

Rahotanni sun nuna cewa waɗannan mutane sun karɓi Musulunci ne tare da shaidar cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma Annabi Muhammad (SAW) ManzonSa ne.

An shirya musu taron na musamman domin karantar da su akidu da koyarwar Musulunci har na tsawon kwanaki bakwai a wannan dakin taron, domin tabbatar da fahimtar su da kuma samun cikakken shiri wajen sauya rayuwa bisa tafarkin Musulunci.

A halin yanzu, al’umma da dama sun bayyana farin cikinsu da addu’ar samun ƙarfafa wa waɗanda s**a karɓi Musulunci, tare da roƙon Allah ya dafa musu da ƙarfafa su a sabon tafarkin da s**a dauka.

Allah ya ɗaukaka Musulunci da Musulmai.

DA DUMI-DUMI: Nasir El-Rufai Ya Bayyana A Kaduna Bayan Dogon LokaciTsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya...
13/08/2025

DA DUMI-DUMI: Nasir El-Rufai Ya Bayyana A Kaduna Bayan Dogon Lokaci

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana a cikin jihar, inda ya samu kyakkyawar tarba daga al’umma yayin wata ziyara da ya kai, bayan ɗan wani lokaci da bai bayyana a bainar jama’a a jihar ba.

Ziyarar ta jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta, inda jama’a ke tofa albarkacin bakinsu kan dawowar sa.

Address

Gombe
7979101

Telephone

+2348149675978

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Daily News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Daily News Hausa:

Share