Daily News Hausa

Daily News Hausa Daily News Hausa, is a licensed Nigerian newspaper company dedicated to delivering verified news and entertainment content in the Hausa language."
(1)

DA DUMI-DUMI: Gwamnan jihar Gombe ya bawa tsofaffin ma'aikatan jiha da na kananan hukumomi Naira biliyan 8.2 na giratuti...
04/11/2025

DA DUMI-DUMI: Gwamnan jihar Gombe ya bawa tsofaffin ma'aikatan jiha da na kananan hukumomi Naira biliyan 8.2 na giratuti. Ya kuma bawa dalibai Naira biliyan 1.5 na Scholarship.

YANZU-YANZU: Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima Ya Tafi Brazil Don Halartar Taron Sauyin Yanayi na COP30Mataimakin...
04/11/2025

YANZU-YANZU: Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima Ya Tafi Brazil Don Halartar Taron Sauyin Yanayi na COP30

Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, ya tashi zuwa Brazil domin wakiltar Najeriya a taron Majalisar Dinkin Duniya kan sauyin yanayi, COP30.

Ziyarar ta fito ne daga kokarin Najeriya na taka rawa wajen tattauna hanyoyin magance sauyin yanayi da kare muhalli, tare da bada gudunmawa ga cimma manufofin kasa da kasa wajen rage hayaki mai gurbata yanayi da bunkasa ci gaban dorewa.

Shettima zai shiga tattaunawa da shugabannin kasashen duniya kan dabarun rage tasirin dumamar yanayi, bunkasa sabbin hanyoyin samar da mak**ashi mai tsafta, da kuma karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashe wajen kiyaye muhalli.

Najeriya na daga cikin kasashen da ke fuskantar kalubale na sauyin yanayi, musamman matsalolin ambaliyar ruwa da fari, wanda hakan ya sanya wakilcin kasa a irin wannan taro ya zama mai matukar muhimmanci.

04/11/2025

🥹🥹🥹

゚viralシ

Yaudarar Trump Wajen Amfani da Najeriya Don Ceto Makomar Siyasar Sa a AmurkaRubutawa: Aliyu SambaAkwai wata tsohuwar ka’...
04/11/2025

Yaudarar Trump Wajen Amfani da Najeriya Don Ceto Makomar Siyasar Sa a Amurka

Rubutawa: Aliyu Samba

Akwai wata tsohuwar ka’ida a ilimin siyasa da ake kira “Diversionary Theory of War”, wadda ke bayyana cewa wasu gwamnatoci na iya shiga cikin rikicin wasu ƙasashe ko ƙirƙirar barazana daga waje don karkatar da hankalin jama’a daga matsalolin cikin gida. Wannan dabarar tana taimakawa wajen haɗa kan al’umma da dasa musu kishin ƙasa, musamman idan gwamnati na fuskantar rikice-rikice ko rarrabuwar kawuna a cikin gida.

Wannan ne ainihin abin da ake gani Shugaban Amurka Donald Trump ke aikatawa a halin yanzu, amfani da Najeriya a matsayin abar lakacewa hanci don ya samu hanyar ceto kansa daga matsalolin cikin gida da kuma tabbatar da tasirinsa a idon magoya baya.

Dalilai Masu Tabbatar da hakan sun haɗa da:

1. Rikicin Cikin Gida da Majalisar Wakilai (House of Representatives). Trump yana cikin matsananciyar takaddama da Majalisar Wakilai ta Amurka, duk kuwa da cewa jam’iyyarsa ta Republican ke da rinjaye. Sabani kan kasafin kuɗi, ikon mulki, da tsoma baki cikin harkokin majalisa sun haifar da rabuwar kawuna a cikin jam’iyyar. Wannan ya rage masa iko, ya kuma bar shi cikin yanayi da ke buƙatar ya samo sabuwar hanya don dawo da martaba da haɗin kai a cikin jam’iyyarsa.

Ta fuskar dabarar “Diversionary Strategy”, irin wannan yanayi yakan sa shugabanni su kirkiri barazana daga waje don jawo hankalin jama’a su manta da rikicin cikin gida. A wannan karon, Trump ya zabi Najeriya a matsayin abin zargi ta hanyar kirkirar labarin cewa ana kisan kare dangi ga mabiya addinin Kirista a kasar, wani ikirari da ba shi da tushe ko hujjar da za ta iya tabbatar da shi.

Dalilan Siyasa da Dabarun “Geopolitical Strategy” na Amurka

A tarihi, Amurka ta yi amfani da wannan salon wajen tabbatar da tasirinta a duniya:

• A Iraki (2003), ta kirkiri hujjar mak**an kare dangi don fara yaƙi, daga baya aka tabbatar da cewa hujjar ƙarya ce.

• A lokacin Yaƙin (Cold War), ta shiga cikin harkokin Vietnam, Chile, da Nicaragua don kare muradunta.

• Bayan harin 9/11, ta fara yaƙi da “ta’addanci” a Afghanistan da Iraki domin haɗa kan jama’ar ta.

Yanzu kuma, Trump na ƙoƙarin amfani da wannan salo wajen farfado da tasirin Amurka a Afirka, ta hanyar yin amfani da Najeriya a matsayin misali na “ƙasar da ake zargin take zaluntar Kiristoci.” Wannan ya dace da yadda yake amfani da manufarsa ta “America First”, wato kare Amurka da darajarta ta hanyar rage ƙimar wasu ƙasashe.

Dalilan da ke Tabbatar da Cewa Wannan Dabara na Nufin Kassara Najeriya Kai Tsaye;

1. Shigar Najeriya cikin BRICS:
Matakin Najeriya na shiga haɗin gwiwar tattalin arziki na BRICS (Brazil, Russia, India, China, South Africa) ya nuna ƙoƙarinta na rabuwa daga dogaro da tsarin tattalin arzikin yammacin duniya da Amurka ke jagoranta. Wannan babban juyi ne wanda ya tayar da hankalin Trump da masu ra’ayinsa na adawa da China da Rasha.

2. Goyon bayan Falasdinu: Najeriya ta bayyana matsayinta na gocewa goyon bayan kai tsaye ga Isra’ila tare da jaddada cewa tana marawa Falasdinu baya kan manufar ƙasa biyu. Wannan ya saba wa ra’ayoyin Trump wanda ya daɗe yana amfani da goyon bayan Isra’ila don samun farin jini a cikin Amurkawa.

3. Sake tsari a tattalin arziki: Tinubu ya ɗauki sabbin matakai na sake fasalin tattalin arzikin ƙasa ta hanyar sassauta canjin kuɗi, jawo jarin ƙasashen gabas, da rage dogaro da tallafin Amurka. Wannan ya zama abin da ke ɗora Najeriya a sahun ƙasashen da ke neman ‘yancin tattalin arziki, wanda ke da barazana ga tasirin Amurka a yankin.

4. Trump da dabarar ƙarya a kafafen labarai: A cikin siyasar sa, Trump ya shahara da amfani da ƙarya da bayanan yaudara (disinformation) don jawo hankalin jama’a. Zargin sa na cewa ana “kashe Kiristoci a Najeriya” ya dace da irin wannan salo, manufarsa ita ce bata sunan Najeriya, ƙirƙirar labarin tausayi, da jawo magoya baya na addinin kiristanci a Amurka.

Mu dawo mu kalli gaskiyar Abin Da Ke Faruwa.

Najeriya tana fuskantar matsalolin tsaro da ta’addanci da ke da dalilai da dama, wani lokacin bisa dalilin siyasa, wanj lokacin bisa dalilin tattalin arziki, ko kabilanci, ba iya rikicin addini kawai ba. Masu aikata laifukan ba wai suna wakiltar wani addini bane, kuma gwamnati na kokarin shawo kan matsalar a matakai daban-daban.

Don haka, zargin Trump na cewa ana yin “genocide” ga Kiristoci a Najeriya, ba wai kawai ƙarya ba ce, illa ma yana da nufin rage darajar Najeriya a idon duniya, tayar da hankali, da rage amincewar kasashen duniya da shugabancin Tinubu.

Me Ya Kamata Najeriya Ta Yi

1. Ƙarfafa huldar diflomasiyya da kasashen gabas da na BRICS, don tabbatar da cikakken ‘yanci a fannin tattalin arziki.

2. Amfani da kafafen yada labarai na duniya wajen fayyace gaskiyar lamarin tsaron Najeriya da wanzar da bayanai na gaskiya.

3. Shirya takardun hujjoji da bayanai na ƙasa da ƙasa don kare martabar kasar a Majalisar Ɗinkin Duniya da sauran cibiyoyin kasa da kasa.

4. Gina hadin kai a cikin gida domin kada ra’ayoyin addini ko siyasa su zama makamin da wasu ke amfani da shi don kawo rarrabuwar kawuna.

A halin yanzu, Trump yana amfani da tsohuwar dabarar “Diversionary Theory of War”, wato kirkirar barazana daga waje domin kau da hankali daga matsalolinsa na cikin gida. Zargin da yake yi wa Najeriya game da “kisan kiyashi ga mabiya addinin kiristanci” wani ƙoƙari ne na siyasa da yaudara domin ya tabbatar da tasirin Amurka da kuma ceto kansa daga matsin lamba a cikin gida.

Najeriya dole ta fahimci cewa wannan dabarar ba wai kawai magana ce ta siyasa ba, amma ƙoƙari ne na lalata martabarta da tasirinta a duniya. Don haka, tsare muradun ƙasa da ƙimar Najeriya ne babbar mafita.

~Aliyu Samba
4th Nov, 2025

DA DUMI DUMI: Ana Zargin Shugaban kasar Korea ta Arewa Kim Jong-Un ya Fashe da Kuka Saboda yarasa Wanda Zai kai Masa Har...
04/11/2025

DA DUMI DUMI: Ana Zargin Shugaban kasar Korea ta Arewa Kim Jong-Un ya Fashe da Kuka Saboda yarasa Wanda Zai kai Masa Hari domin Suyi y@ƙi

- Ya shafe tsawon lokaci yana jiran a tsokane shi fada amma anki.
- Ya tsokana ya tsokana anyi banza dashi.
- Yayi habaice-habaice anyi banza dashi.
- Shi kadai ya yita kugi, amma an gagara tanka mishi.

Akwai lokacin da Donald Trump yaje ziyara Korea ta kudu, saboda tsabar neman rigima Kim Jong-Un, ya yita gwajin sabbin manya-manyan mak**ai a bakin iyakar kasarsa da Korea ta kudu amma Donald Trump ya kasa tankawa.

Yauwa, a fadawa Donald J. Trump a can kasar Korea ta Arewa ta Kim Jong-Un, can ne ake mulkin k**a karya da take hakkin Dan Adam don haka ya gaggauta zuwa ya dauki matakin da ya dace.

Mu a nan Najeriya muna zaune lafiya da kowane addini kowa yana da 'yancin yin addininsa sai-dai masu kwana da yunwa suna da yawa, sai-dai idan zai raba mana tallafin Daloli kyauta, muna matukar bukata.

LABARI MAI DAƊI: Gwamnan Bauchi Ya Warware Matsalar Wuta a Unguwar Dr. Sulaiman Adamu QuartersBauchi – Dogon lokaci da m...
03/11/2025

LABARI MAI DAƊI: Gwamnan Bauchi Ya Warware Matsalar Wuta a Unguwar Dr. Sulaiman Adamu Quarters

Bauchi – Dogon lokaci da mazauna unguwar Dr. Sulaiman Adamu Quarters, dake Behind Vanilla, Col. Hamidu Ali Street, ke fama da matsalar wutar lantarki ya zo karshe a yau.

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulkadir Muhammad (Kauran Bauchi), ya samar da sabon transformer ga unguwar domin tabbatar da wutar lantarki mai dorewa, lamarin da ya kawo sauƙi ga rayuwar al’umma da sana’o’in su.

Mazauna sun bayyana jin daɗinsu tare da godiya ga gwamna saboda wannan gagarumin tallafi, inda s**a ce matakin ya nuna kulawar gwamnati ga bukatun jama’a.

Wannan aiki ya zama misali na yadda gwamnatin Kauran Bauchi ke tabbatar da jin daɗin al’umma da inganta walwalar rayuwa a matakai daban-daban.

Address

Gombe
7979101

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Daily News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Daily News Hausa:

Share