02/06/2026
Sardauna, Kwankwaso da Obi. Zuwa ga Aliyu Aliyu Dahiru Aliyu
Daga Fatuhu Mustapha
Ban san me yasa ka dau zafi akan wannan maganar ba. Na yi tunanin in kira ka ta waya mu tattauna akan maganar, amma sai naga gara in jawo hankalin ka anan, domin mu hadu mu gudu tare mu tsira tare. Musamman saboda na san ni da kai duk muna da tarbiya irin ta sufanci, sannan akwai kyakkyawar fahintar da mutunta juna a tsakanin mu. Hakan ne ya sanya nayi mamakin maganar ka, da ka soki al'adar nan ta bahaushe, ta in mutum ya mutu ba a son fadin munanan ayyukan sa. Wanda nasan ka sani sarai, wannan tarbiya ce ta sufaye, saboda hadisin nan da ya ce "ku kyatatawa mumini zato"
Malan Aliyu, ba wanda ya ce Sardauna ma'asumi ne. Tabbas kamar kowanne danAdam mutum ne kamar kowa. Yana da nasa inda ya gaza, amma ina ganin da zaka masa adalci, da sai ka kuma kalli kyawawan ayyukan sa, sannan sai kayiwa tarihin sa adalci.
A matsayinka na manazarci, kuma gogaggen mai sharhi akan al'amurra ina ganin bai kamata ka kira ayyukan da manyan Daktoci da Farfesoshi s**a yi akan Sardauna da Hagiography ba. Domin dai nasan kasan su waye s**a yi aikin, da kuma irin kwarewarsu a nazarin tarihi. Yanzu a kalli rubutun masani kamar John Paden a matsayin haka?
Wani abun lura anan, in ana cin baure ba a tona cikin sa. Ka kuwa san, koda Malam Aminu Kano, in za a tona wasu abubuwan kare ba zai ci ba? Kila in na samu lokaci muka yi magana, in gaya maka wasu abubuwan da baka da labarin su.
Shin meye laifin Sardauna? Shin Sardauna baya kaunar talaka? Shin malam Aminu Kano baya kaunar sarakuna? Kana ganin da Malam Aminu na da rai, zai yadda ya goyi bayan a taka mutuncin Sardauna?
Kar ka manta, Sardauna bai ware makarantar yayan sarakuna daban da na talakawa ba. Amma a yau yayan talakawa su Kwankwaso da su Ganduje da su Malam Ibragim Shekarau, ba za su taba yadda su kai yayan su makarantar da yayan talakawa suke zuwa ba. A lokacin sa, damar da aka baiwa Mamman Bashar dan Sarkin Daura, ita aka baiwa Maitama Sule dan bawan Madakin Kano. Shekarar Kwankwaso 8 yana gwamna, amma bai gina makarantar gwamnati da zai iya yadda ya kai dan sa Mustapha ba. A lokacin sa, da Buhari da Babangida yayan talakawa, dama daya aka basu da Yar'adua dan Ministan Babban Birnin Tarayya.
Sardauna har ya mutu bai bar mansion kamar wanda dan talaka Kwankwaso ya ke ciki a Miller Road ba. A lokacin da ya zama Firimiya na Arewa, kwakwata makarantun Sakandire 5 ne a Arewa. A shekara 6 da yayi yana mulki, ya samar da sakandire 64 a fadin arewa. Shekara kusan 60 da turawan mulki s**a yi suna mulki, gaba daya masu digiri a Arewa su 4 ne. A shekara 6 na mulkin sa, ya bayar da tallafin karatu ga dan talaka da yaya masu da shi, da yayan sarakuna ba tare da nuna banbanci ba.
Kila a ce ai sun takurawa talakawa akan haraji. Amma ya kamata a kalli yadda a dan kankanin lokaci ya yi amfani da harajin ya samar da Bank of the North, a Kano, wanda yayan talakawan da ya samarwa guraben karatu a manyan Jami'o'ina duniya, irin su Cambridge, Oxford da Havard, s**a zo s**a lalata. Ya lura bamu da jami'a ta kan mu, ya samar da University of Northern Nigeria, ya kwato Abdullahi Bayero College ya hade ta da University din. A dan karamin lokacin ya kafa NNDC, domin habaka tattalin arzikin Arewa, NNDC ita ta kafa Ashaka Cement, ta kafa Savanna Sugar, ta kafa Benue Cement
, duk dan kar a bar arewa a baya. A yau yayan talakawan da ya dage sai sun yi karatu, su s**a dage sai da s**a kashe wadannan kamfanoni da ya kafa. Duk wadannan da kudin haraji ya kafa su, ba da kudin rarar man fetur ba.
Ina ganjn, a dan karamin hankalina, wanda yayi wannan babban aiki, ai kuwa guga ko bai tsiran komai ba, yayi na igiya. Ina ganin kamar kai, ya kamata kasan akuya ko bata haihuwa tafi kare. Domin ba don Arewa agenda da ya kafa, tabbas da bana jin a yau mun isa mu ce zamu yi kafada da yan kudu.
Daga karshe ina wa Gamji Uban Yanboko adduar, Allah ya jikansa ya yafe kurakuransa, yasa aljanna makoma. Ina maka fatan alheri da fatan wannan rubuta zai sa ka sake wa wannan abu da ka dauko kallon nutsuwa da adalci.