Daily News Hausa

Daily News Hausa Daily News Hausa, is a licensed Nigerian newspaper company dedicated to delivering verified news and entertainment content in the Hausa language."
(9)

Kotu Za Ta Saurari Ƙarar Da Nafiu Bala Ya Shigar Kan David Mark Da Aregbesola A YauBabbar Kotun Tarayya da ke Abuja za t...
03/06/2026

Kotu Za Ta Saurari Ƙarar Da Nafiu Bala Ya Shigar Kan David Mark Da Aregbesola A Yau

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja za ta saurari ƙarar da Nafiu Bala ya shigar kan shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress, wadda ta shafi David Mark da Rauf Aregbesola.

Mai ƙarar na kalubalantar sahihancin shugabancin jam’iyyar, yana neman kotu ta yi hukunci kan rikicin da ya kunno kai a cikin ADC.

Rahotanni sun nuna cewa Aregbesola ya buƙaci Mai Shari’a Peter Lifu, wanda ke sauraron shari’ar, da ya janye kansa daga ci gaba da sauraron ƙarar tare da barin wani alkalin ya yanke hukunci kan lamarin.

Ana sa ran sauraron shari’ar zai kasance mai muhimmanci ga makomar shugabancin ADC, musamman yayin da jam’iyyar ke ci gaba da shirye-shiryen tunkarar zaɓen shekarar 2027.

An Fara Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya Zuwa GidaNational Hajj Commission of Nigeria ta sanar da fara jigilar alh...
03/06/2026

An Fara Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya Zuwa Gida

National Hajj Commission of Nigeria ta sanar da fara jigilar alhazan Nijeriya da s**a kammala aikin Hajjin shekarar 2026 daga ƙasar Saudi Arabia zuwa gida.

Rahotanni sun nuna cewa alhazan Nasarawa State ne s**a fara dawowa ƙasar, inda jirgin kamfanin MaxAir ya tashi daga birnin Jeddah zuwa Abuja da misalin ƙarfe 9:27 na safe ranar Laraba.

Jirgin ya ɗauko alhazai 560 na Jihar Nasarawa, a wani ɓangare na shirin dawo da mahajjatan Nijeriya bayan kammala ibadun Hajjin bana.

NAHCON ta ce za a ci gaba da jigilar sauran alhazai daga jihohi daban-daban cikin tsari domin tabbatar da dawowarsu gida cikin aminci da kwanciyar hankali.

Allah Ya karɓi Hajjin alhazanmu, Ya dawo da su gida lafiya. Amin.

Tinubu Zai Yi Jawabi A Zauren Majalisar Tarayya Ranar DimokuraɗiyyaShugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, zai gabatar da jawa...
03/06/2026

Tinubu Zai Yi Jawabi A Zauren Majalisar Tarayya Ranar Dimokuraɗiyya

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, zai gabatar da jawabi ga zaman haɗin gwiwar Majalisar Dattawa da ta Wakilai a ranar 12 ga Yuni, a matsayin wani ɓangare na bukukuwan cika shekaru 27 da dawo da mulkin dimokuraɗiyya a Najeriya.

Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume, ya bayyana cewa jawabin shugaban ƙasar zai kasance ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da za su gudana a ranar Dimokuraɗiyya.

Akume ya ce ranar wata dama ce ta tunawa da sadaukarwar waɗanda s**a yi gwagwarmayar tabbatar da dimokuraɗiyya a Najeriya, musamman marigayi Moshood Kashimawo Abiola da sauran jaruman gwagwarmayar 12 ga Yunin 1993.

Ya ƙara da cewa gwamnatin tarayya za ta yi amfani da bikin wajen bayyana nasarorin da ta samu wajen ƙarfafa cibiyoyin dimokuraɗiyya da bunƙasa ci gaban ƙasa.

Daga cikin shirye-shiryen bikin akwai taron manema labarai na duniya, addu’o’in musamman, lacca ta ranar Dimokuraɗiyya, da shirye-shiryen matasa da mata kafin babban taron ranar 12 ga Yuni.

Me kuke sa ran Shugaba Tinubu zai fi mayar da hankali a kai a jawabinsa na ranar Dimokuraɗiyya?

MAKIRCIN DA AKA ƘULLA A DARREN JIYA KAN JIHAR GOMBE DA TASIRIN PROFESSOR ISA ALI PANTAMI An gudanar da wani taro a Gidan...
03/06/2026

MAKIRCIN DA AKA ƘULLA A DARREN JIYA KAN JIHAR GOMBE DA TASIRIN PROFESSOR ISA ALI PANTAMI

An gudanar da wani taro a Gidan Gwamnati a daren jiya, Talata 2 ga Yuni, 2026. A cewar bayanan da s**a fito daga taron, babban abin da ya mamaye tattaunawar shi ne Malam Isa Ali Pantami, inda aka mayar da hankali kan muhimman batutuwa uku:

1. Sun sani sarai cewa Malam Isa Ali Pantami bai shiga abin da suke ƙira zaɓen fidda gwani ba. Duk da haka, an yi shawarar cewa a ci gaba da tayar da hayaniya a kan lamarin tare da amfani da wasu da ake ƙira masu ruwa da tsaki daga cikin gida domin jawo ruɗani da tsawaita cece-kuce.

2. Karɓuwar da Professor Isa Ali Pantami da sabuwar jam’iyyarsa ta PDP suke samu a faɗin jihar Gombe na ƙara damun su matuƙa. Shigowarsa ya sake farfaɗo da jam’iyyar gaba ɗaya. A kusan kowane taro da majalisa, Pantami da jam’iyyarsa su ne abin tattaunawa. A cewarsu, bai kamata a bar wannan yanayi ya ci gaba ba.

Abin takaici a gare su, sun manta cewa ikon Allah ne kaɗai ke tabbatar da abin da zai kasance.

3. A yayin da Malam Isa Ali Pantami ke ci gaba da gabatar wa al’ummar Gombe manufofinsa da kuma “Tsarin Sauya Fasalin Jihar Gombe” a fannoni kamar noma, samar da ayyukan yi, tsaro, ilimi, mata, matasa, masana’antu da sauran su, har yanzu ‘yan takarar su ba su gabatar wa jama’a wata cikakkiyar manufa ko tsari ba.

An ce an yi wa dukkan ‘yan takarar da s**a halarci taron tambayoyi kan wannan batu. A yau, Pantami ya zama abin koyi a gare su ta wannan fuska.

Mu ci gaba da lura da abubuwan da suke faruwa yayin da al’amura ke ƙara bayyana.

Allah Ya rushe duk wani mugun nufi da mugun shiri da ake yi wa al’ummar jihar Gombe da kuma duk wani abu da zai hana samuwar shugabanci Nagari a jihar.

Rubutawa:
Barrista Yahaya Ibrahim
03/Yuni/2026

YANZU YANZU: Kodinetan jam'iyyar ADC na jiha kuma tsohon mataimakin sakataren jam'iyyar ya yi murabus, ya bi sahun Farfe...
02/06/2026

YANZU YANZU: Kodinetan jam'iyyar ADC na jiha kuma tsohon mataimakin sakataren jam'iyyar ya yi murabus, ya bi sahun Farfesa Isa Ali

Hon. Salihu Abdulkadir, wanda ya kasance dan takarar majalisar dokokin jihar Gombe na jam'iyyar African Democratic Congress (ADC) a zaben 2023 mai wakiltar Dukku ta Arewa, ya yi murabus a hukumance daga jam'iyyar. Hon. Abdulkadir, wanda ya taba zama Kodinetan jam'iyyar ADC na jiha kuma tsohon mataimakin sakataren jam'iyyar na jiha, ya sanar da matakin da ya dauka na barin jam'iyyar domin shiga tafiyar siyasar da Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami ke jagoranta.

A cikin wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai, Hon. Abdulkadir ya bayyana godiyarsa ga shugabancin jam'iyyar ADC da kuma mambobinta bisa damar da s**a ba shi a lokacin da yake rike da mukamansa. Ya bayyana cewa, matakin da ya dauka na sauya sheka ya samo asali ne daga burinsa na shiga wani dandali da zai dace da hangen nesansa na ganin an samu shugabanci na gari da kuma jagoranci mai amfani ga mutanen Dukku ta Arewa da jihar Gombe baki daya.

"Ina mai matukar godiya ga jam'iyyar ADC bisa amana da nauyin da aka dora mini a matsayina na kodinetan jiha da kuma mataimakin sakatare.

Matakina na bin Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami a cikin tafiyarsa ta siyasa, shi ne domin in ba da gudunmawa yadda ya kamata wajen ci gaba da kuma tallafawa al'ummarmu," inji Hon. Abdulkadir.

Masu sharhi kan harkokin siyasa sun bayyana cewa, murabus dinsa ya nuna gagarumin sauyi a fagen siyasar jihar Gombe, wanda hakan ke kara nuna tasirin tafiyar Dr. Pantami da kuma yadda take jan hankalin 'yan siyasar da ke neman sabbin hanyoyin yi wa jama'a hidima.

Tsohon kodinetan na ADC, wanda kuma ya kasance daya daga cikin ginshikan kafa jam'iyyar a jihar Gombe, barinsa jam'iyyar ya zama wani muhimmin sauyi a siyasar jihar, wanda ke kara nuna yadda tafiyar Pantami ke samun karbuwa da kuma yadda siyasa ke sauyawa yayin da ake kusantar zaben 2027.

Ban Taba Ganin Mutumin Da Yana Cikin Musifa Kuma Yake Kara Jefa Kansa Cikinta Kamar Dan Arewa Ba, Inji Barista Hamza Nuh...
02/06/2026

Ban Taba Ganin Mutumin Da Yana Cikin Musifa Kuma Yake Kara Jefa Kansa Cikinta Kamar Dan Arewa Ba, Inji Barista Hamza Nuhu Dantani

Ban taba ganin mutumin da yana cikin masifa (wahalar rayuwa), ya san kuma yana cikin masifar, kuma yana kuka akan masifar, kuma yana neman maganin masifar, amma yana kara saka kansa cikin masifar kamar dan Arewa ba.

Idan kuma ka taimaka masa da hanyar magance masifar zai zage ka ko ya ci mutuncinka. Wannan sai dan Arewa.

Siyasa ko zabe ra’ayi ne, kuma 'yancin ka ne, amma kuma masifa da wahalar rayuwa zabinka ne.

Tinubu Ya Koma Abuja Bayan Hutun Babbar Sallah A LegasShugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya koma Abuja bayan kammala hutu...
02/06/2026

Tinubu Ya Koma Abuja Bayan Hutun Babbar Sallah A Legas

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya koma Abuja bayan kammala hutun Babbar Sallah da ya yi a jihar Legas.

Yayin da ya dawo bakin aiki, al’ummar Najeriya na ci gaba da bayyana fatan ganin gwamnati ta ƙara mayar da hankali kan muhimman batutuwan da s**a shafi rayuwar yau da kullum, musamman tsaro, tattalin arziki, samar da ayyukan yi, rage tsadar rayuwa da kuma inganta walwalar jama'a.

Jam’iyyar APC A Jihar Gombe Ta Yi Dana-sanin Rashin Bai Wa Pantami Tikitin Takarar GwamnaWasu jiga-jigan jam’iyyar APC a...
02/06/2026

Jam’iyyar APC A Jihar Gombe Ta Yi Dana-sanin Rashin Bai Wa Pantami Tikitin Takarar Gwamna

Wasu jiga-jigan jam’iyyar APC a Jihar Gombe sun bayyana cewa jam’iyyar na ci gaba da fuskantar tasirin rashin bai wa Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami tikitin takarar gwamna gabanin zaɓen 2027, lamarin da s**a ce ya haifar da rabuwar kai da kuma rage ƙarfin jam’iyyar a wasu sassan jihar.

A cewarsu, Pantami na daga cikin fitattun jagororin siyasa da s**a yi tasiri sosai a jihar, tare da samun karɓuwa a tsakanin matasa, malamai da sauran al’umma. Sun yi iƙirarin cewa da an ba shi damar fafatawa a sahihin zaɓen fidda gwani, APC za ta samu ƙarin haɗin kai da kuma goyon bayan mambobinta a faɗin jihar.

Majiyoyin jam’iyyar sun bayyana cewa ficewar Pantami daga APC zuwa PDP ta sauya yanayin siyasar Gombe, inda dubban magoya bayansa s**a nuna goyon baya gare shi. Sun ƙara da cewa wannan lamari ya bai wa jam’iyyun adawa damar ƙara faɗaɗa tasirinsu a wasu yankunan jihar.

Wasu daga cikin mambobin APC sun nuna cewa da an gudanar da zaɓen fidda gwani cikin gaskiya da adalci tare da bai wa kowa damar gwada farin jininsa, da jam’iyyar ba za ta fuskanci irin ƙalubalen da take ciki a yanzu ba. Sun yi kira ga shugabannin jam’iyyar da su ɗauki darasi daga abin da ya faru domin tabbatar da adalci, gaskiya da haɗin kai a duk wani tsari na zaɓen cikin gida a nan gaba.

Sardauna, Kwankwaso da Obi. Zuwa ga Aliyu Aliyu Dahiru AliyuDaga Fatuhu Mustapha Ban san me yasa ka dau zafi akan wannan...
02/06/2026

Sardauna, Kwankwaso da Obi. Zuwa ga Aliyu Aliyu Dahiru Aliyu

Daga Fatuhu Mustapha

Ban san me yasa ka dau zafi akan wannan maganar ba. Na yi tunanin in kira ka ta waya mu tattauna akan maganar, amma sai naga gara in jawo hankalin ka anan, domin mu hadu mu gudu tare mu tsira tare. Musamman saboda na san ni da kai duk muna da tarbiya irin ta sufanci, sannan akwai kyakkyawar fahintar da mutunta juna a tsakanin mu. Hakan ne ya sanya nayi mamakin maganar ka, da ka soki al'adar nan ta bahaushe, ta in mutum ya mutu ba a son fadin munanan ayyukan sa. Wanda nasan ka sani sarai, wannan tarbiya ce ta sufaye, saboda hadisin nan da ya ce "ku kyatatawa mumini zato"

Malan Aliyu, ba wanda ya ce Sardauna ma'asumi ne. Tabbas kamar kowanne danAdam mutum ne kamar kowa. Yana da nasa inda ya gaza, amma ina ganin da zaka masa adalci, da sai ka kuma kalli kyawawan ayyukan sa, sannan sai kayiwa tarihin sa adalci.

A matsayinka na manazarci, kuma gogaggen mai sharhi akan al'amurra ina ganin bai kamata ka kira ayyukan da manyan Daktoci da Farfesoshi s**a yi akan Sardauna da Hagiography ba. Domin dai nasan kasan su waye s**a yi aikin, da kuma irin kwarewarsu a nazarin tarihi. Yanzu a kalli rubutun masani kamar John Paden a matsayin haka?

Wani abun lura anan, in ana cin baure ba a tona cikin sa. Ka kuwa san, koda Malam Aminu Kano, in za a tona wasu abubuwan kare ba zai ci ba? Kila in na samu lokaci muka yi magana, in gaya maka wasu abubuwan da baka da labarin su.

Shin meye laifin Sardauna? Shin Sardauna baya kaunar talaka? Shin malam Aminu Kano baya kaunar sarakuna? Kana ganin da Malam Aminu na da rai, zai yadda ya goyi bayan a taka mutuncin Sardauna?

Kar ka manta, Sardauna bai ware makarantar yayan sarakuna daban da na talakawa ba. Amma a yau yayan talakawa su Kwankwaso da su Ganduje da su Malam Ibragim Shekarau, ba za su taba yadda su kai yayan su makarantar da yayan talakawa suke zuwa ba. A lokacin sa, damar da aka baiwa Mamman Bashar dan Sarkin Daura, ita aka baiwa Maitama Sule dan bawan Madakin Kano. Shekarar Kwankwaso 8 yana gwamna, amma bai gina makarantar gwamnati da zai iya yadda ya kai dan sa Mustapha ba. A lokacin sa, da Buhari da Babangida yayan talakawa, dama daya aka basu da Yar'adua dan Ministan Babban Birnin Tarayya.

Sardauna har ya mutu bai bar mansion kamar wanda dan talaka Kwankwaso ya ke ciki a Miller Road ba. A lokacin da ya zama Firimiya na Arewa, kwakwata makarantun Sakandire 5 ne a Arewa. A shekara 6 da yayi yana mulki, ya samar da sakandire 64 a fadin arewa. Shekara kusan 60 da turawan mulki s**a yi suna mulki, gaba daya masu digiri a Arewa su 4 ne. A shekara 6 na mulkin sa, ya bayar da tallafin karatu ga dan talaka da yaya masu da shi, da yayan sarakuna ba tare da nuna banbanci ba.

Kila a ce ai sun takurawa talakawa akan haraji. Amma ya kamata a kalli yadda a dan kankanin lokaci ya yi amfani da harajin ya samar da Bank of the North, a Kano, wanda yayan talakawan da ya samarwa guraben karatu a manyan Jami'o'ina duniya, irin su Cambridge, Oxford da Havard, s**a zo s**a lalata. Ya lura bamu da jami'a ta kan mu, ya samar da University of Northern Nigeria, ya kwato Abdullahi Bayero College ya hade ta da University din. A dan karamin lokacin ya kafa NNDC, domin habaka tattalin arzikin Arewa, NNDC ita ta kafa Ashaka Cement, ta kafa Savanna Sugar, ta kafa Benue Cement
, duk dan kar a bar arewa a baya. A yau yayan talakawan da ya dage sai sun yi karatu, su s**a dage sai da s**a kashe wadannan kamfanoni da ya kafa. Duk wadannan da kudin haraji ya kafa su, ba da kudin rarar man fetur ba.

Ina ganjn, a dan karamin hankalina, wanda yayi wannan babban aiki, ai kuwa guga ko bai tsiran komai ba, yayi na igiya. Ina ganin kamar kai, ya kamata kasan akuya ko bata haihuwa tafi kare. Domin ba don Arewa agenda da ya kafa, tabbas da bana jin a yau mun isa mu ce zamu yi kafada da yan kudu.

Daga karshe ina wa Gamji Uban Yanboko adduar, Allah ya jikansa ya yafe kurakuransa, yasa aljanna makoma. Ina maka fatan alheri da fatan wannan rubuta zai sa ka sake wa wannan abu da ka dauko kallon nutsuwa da adalci.

'Yan Majalisar Wakilai 13 Sun Sauya Sheka Bayan Komawa Daga HutuAkalla mambobi 13 na Majalisar Wakilan Najeriya sun sauy...
02/06/2026

'Yan Majalisar Wakilai 13 Sun Sauya Sheka Bayan Komawa Daga Hutu

Akalla mambobi 13 na Majalisar Wakilan Najeriya sun sauya sheka daga jam’iyyunsu zuwa wasu jam’iyyu daban-daban bayan majalisar ta dawo daga hutun da ta yi.

Sauya shekar tasu ya jawo ce-ce-ku-ce a fagen siyasa, yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen tunkarar zaɓen shekarar 2027.

Ana sa ran wannan mataki zai iya yin tasiri ga ƙarfin jam’iyyu da daidaiton siyasa a Majalisar Wakilai a watanni masu zuwa.

Address

Gombe
7979101

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Daily News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Daily News Hausa:

Share