Daily News Hausa

Daily News Hausa Daily News Hausa, is a licensed Nigerian newspaper company dedicated to delivering verified news and entertainment content in the Hausa language."
(1)

DA DUMI-DUMI: Shugaban Hukumar EFCC yace yanzu haka suna gudanar da bincike kan gwamnoni 18 da ke kan mulki, bisa zargin...
19/07/2025

DA DUMI-DUMI: Shugaban Hukumar EFCC yace yanzu haka suna gudanar da bincike kan gwamnoni 18 da ke kan mulki, bisa zargin almundahana da kudade.

Taron Addu’a a Jimeta Don Marigayi Baba BuhariDaga Nafiu Director YolaAlhamdulillah, an gudanar da taron addu’a na musam...
19/07/2025

Taron Addu’a a Jimeta Don Marigayi Baba Buhari

Daga Nafiu Director Yola

Alhamdulillah, an gudanar da taron addu’a na musamman domin marigayi tsohon shugaban ƙasa a birnin Jimeta, jihar Adamawa.

Taron, wanda ya samu halartar 'yan uwa, masoya da abokan arziki, ya gudana cikin kwanciyar hankali da nutsuwa. An yi addu’o’i na neman gafara da rahamar Allah ga marigayin, tare da fatan samun Aljannatul Firdaus a matsayin makomarsa.

Masu shirya taron sun nuna godiya ga duk wanda ya halarta, da kuma waɗanda s**a yi niyya amma ba su samu zuwa ba. Haka kuma, an yi fatan Allah Ya saka da alheri ga kowa.

"Muna roƙon Allah Madaukakin Sarki Ya gafarta wa Baba Buhari, Ya sanya kabarinsa ya kasance lambun Aljanna. Amin."

SHUGABA TINUBU YA NADA MUHAMMAD BABANGIDA A MATSAYIN SHUGABAN BANKIN NOMA NA KASAShugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amin...
19/07/2025

SHUGABA TINUBU YA NADA MUHAMMAD BABANGIDA A MATSAYIN SHUGABAN BANKIN NOMA NA KASA

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da nadin Muhammad Babangida, ɗan tsohon Shugaban Mulkin Soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, a matsayin Shugaban Hukumar Bankin Noma na Ƙasa (Bank of Agriculture), bayan sake fasalin bankin da aka yi.

Sanarwar da mai bai wa Shugaban Ƙasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai da dabarun sadarwa, Bayo Onanuga, ya fitar a yau Juma’a, ta bayyana cewa shugaban ya kuma amince da nadin wasu shugabanni da daraktoci na hukumomin gwamnati guda bakwai.

Sauran waɗanda aka naɗa su sun haɗa da:
• Lydia Kalat Musa (Daga Jihar Kaduna): Shugabar Hukumar Yankunan ’Yancin Kasuwanci na Man Fetur da Gas (Oil and Gas Free Zone Authority - OGFZA).
• Jamilu Wada Aliyu (Daga Jihar Kano): Shugaban Hukumar Nazarin Harshe da Ci gaban Ilimi (National Educational Research and Development Council - NERDC).
• Hon. Yahuza Ado Inuwa (Daga Jihar Kano): Shugaban Hukumar Tsarance da Daidaita Kayayyaki ta Ƙasa (Standard Organisation of Nigeria - SON).
• Sanusi Musa SAN (Daga Jihar Kano): Shugaban Cibiyar Zaman Lafiya da Warware Rikice-rikice (Institute of Peace and Conflict Resolution - IPCR).
• Prof. Al-Mustapha Alhaji Aliyu (Daga Jihar Sokoto): Darakta Janar na Hukumar Haɗin Gwiwar Fasaha a Afirka (Directorate of Technical Cooperation in Africa - DTCA).
• Sanusi Garba Rikiji (Daga Jihar Zamfara): Darakta Janar na Ofishin Najeriya kan Tattaunawar Kasuwanci (Nigerian Office for Trade Negotiations - NOTN).
• Mrs Tomi Somefun (Daga Jihar Oyo): Manajan Darakta na Hukumar Ci gaban Wutar Lantarki (National Hydro-Electric Power Areas Development Commission - HYPPADEC).
• Dr Abdulmumini Mohammed Aminu-Zaria (Daga Jihar Kaduna): Darakta Mai Gudanarwa na Hukumar Gudanar da Albarkatun Ruwa ta Ƙasa (Nigerian Integrated Water Resources Management Commission - NIWRMC).

Waɗannan nade-nade na nuna jajircewar Shugaban Ƙasa Tinubu na cike guraben shugabanci da mutane nagari domin tabbatar da ingantaccen aiki a hukumomin gwamnati.

Kimamin matasa su 611 'yan jihar Gombe Sheikh Professor Isa Ali Pantami, ya samawa aiki, a lokacin da ya rike mukamin Mi...
19/07/2025

Kimamin matasa su 611 'yan jihar Gombe Sheikh Professor Isa Ali Pantami, ya samawa aiki, a lokacin da ya rike mukamin Ministan Sadarwa na tsawon shekaru 4 kacal.

Me kuke tsammanin zai faru idan ya zama Gwamnan jihar Gombe?

Ga jadawalin wuraren da ya samawa matasa ayyukan;

1️⃣ Chief Executive Officers – 12
2️⃣ Board Chairmen & Members – 19
3️⃣ Executive Directors – 6
4️⃣ NITDA – 78
5️⃣ NCC – 69
6️⃣ Galaxy Backbone – 73
7️⃣ NIMC – 170
8️⃣ Data Protection Bureau – 3
9️⃣ Emergency Call Centres – 62
🔟 NFIU – 6
1️⃣1️⃣ CBN – 9
1️⃣2️⃣ Fed. Polytechnic, Kaltungo – 4
1️⃣3️⃣ Immigration – 6
1️⃣4️⃣ Police Academy, Wudil – 2
1️⃣5️⃣ NIMASA – 2
1️⃣6️⃣ Fed. College of Horticulture – 3
1️⃣7️⃣ Borno State University – 1
1️⃣8️⃣ Fed. Teaching Hospital – 18
1️⃣9️⃣ NSITF – 2
2️⃣0️⃣ Police Force – 9
2️⃣1️⃣ Civil Defence – 5
2️⃣2️⃣ Health Registration Council – 5
2️⃣3️⃣ Transmission Company – 1
2️⃣4️⃣ Airspace Management – 2
2️⃣5️⃣ National Population Commission – 5
2️⃣6️⃣ Civil Aviation Authority – 2
2️⃣7️⃣ Federal Airports Authority – 2
2️⃣8️⃣ Jos Electricity Distribution – 10
2️⃣9️⃣ FUT Minna – 2
3️⃣0️⃣ FCE Gombe – 3
3️⃣1️⃣ FCE Zaria – 3
3️⃣2️⃣ Kaduna Polytechnic – 2
3️⃣3️⃣ PPPRA – 2
3️⃣4️⃣ Petroleum Equalization Fund – 2
3️⃣5️⃣ Federal Fire Service – 2
3️⃣6️⃣ BUK – 2
3️⃣7️⃣ Ministry of Communications & Digital Economy – 2
3️⃣8️⃣ FIRS – 1
3️⃣9️⃣ Miscellaneous / Others – 3

Total: 611

Da iznin Ubangiji Sheikh Prof Isa Ali Pantami, Alkhairi ne ga al-ummar jihar Gombe, kuma sharri da kazafi da mutanen banza suke mishi a banza, bazai rage shi da komai ba saima dai ya kara mishi farin jini ga al'umma.

DA DUMI-DUMI: An K**a Matashiya Ƴar "TikTok" Fatima Zahra Kan Zargin S**a Ga Marigayi Buhari Rahotanni daga Zaria sun ta...
19/07/2025

DA DUMI-DUMI: An K**a Matashiya Ƴar "TikTok" Fatima Zahra Kan Zargin S**a Ga Marigayi Buhari

Rahotanni daga Zaria sun tabbatar da cewa jami’an rundunar ‘yan sandan Najeriya sun k**a wata matashiya mai suna Fatima Zahra Saidu, wadda aka fi sani a dandalin TikTok, bisa zargin yin s**a ga tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Lamarin ya faru ne ranar Juma’a da ta gabata, inda aka ce an k**a ta ne a cikin garin Zaria, kuma yanzu haka tana tsare a ofishin ‘yan sanda na Sabon Gari, Zaria.

Majiyoyi sun bayyana cewa abin da ya janyo wannan k**a shi ne bidiyon da Fatima Zahra ta wallafa, inda ta bayyana ra’ayinta cewa bai k**ata a yafe wa Buhari bisa abubuwan da s**a faru a lokacin mulkinsa ba.

Wannan lamari ya tayar da kura a kafafen sada zumunta, inda jama’a ke bayyana damuwa da takaici, suna ganin hakan a matsayin take hakkin fadin albarkacin baki da tsarin mulkin Najeriya ya tanada.

Kungiyoyin kare hakkin bil’adama da masu rajin dimokuradiyya na ci gaba da kiran a sako Fatima Zahra ba tare da wani sharadi ba. Suna kuma rokon jami’an tsaro da su daina zama kayan aikin siyasa, su koma kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Hukumomin ‘yan sanda na Jihar Kaduna dai har yanzu ba su fitar da wata sanarwa ba kan lamarin, sai dai ana ci gaba da bin diddigin batun.

DA DUMI-DUMI: An fara hadawa fadar shugaban kasa Solar a Villa.Me Hakan yake nufi ga makomar Wutar lantarki a Najeriya?
19/07/2025

DA DUMI-DUMI: An fara hadawa fadar shugaban kasa Solar a Villa.

Me Hakan yake nufi ga makomar Wutar lantarki a Najeriya?

GA DALILIN DA KE SANYA SHUGABANNI TAFIYA ƘASASHEN WAJE NEMAN LAFIYA — Inji Dr. Abdurrahman DambazauDr. Abdurrahman Damba...
19/07/2025

GA DALILIN DA KE SANYA SHUGABANNI TAFIYA ƘASASHEN WAJE NEMAN LAFIYA — Inji Dr. Abdurrahman Dambazau

Dr. Abdurrahman Dambazau ya bayyana wata ƙwaƙƙwarar hujja kan dalilin da ya sa shugabanni ke fita ƙasashen waje don neman lafiya, yana mai bayani da misalin wani mara lafiya da ya rasu sak**akon ɗaukar wutar lantarki a babban asibiti.

Ya ce matsalolin rashin kayan aiki, ƙarancin wuta, ƙwararrun ma’aikata da magunguna suna haddasa mutuwa da za a iya kaucewa. Duk da cewa rayuwa na hannun Allah ce, ya nemi shugabanni su gyara asibitocin cikin gida domin amfanar kowa.

Ya kuma ce rasuwar tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari da ta faru a ƙasashen waje ya k**ata ta zama darasi ga masu mulki.

DA ƊUMI-ƊUMI: Ana Hasashen Ɗan Bello Zai Tsaya Takarar Shugaban Ƙasa A Sabuwar Jam'iyyar Matasa A Zaben 2027 Shin Kana Ɗ...
19/07/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Ana Hasashen Ɗan Bello Zai Tsaya Takarar Shugaban Ƙasa A Sabuwar Jam'iyyar Matasa A Zaben 2027

Shin Kana Ɗaya Daga Cikin Waɗanda Zasu Zabe Shi Idan Maganar Ta Tabbata?

Rasuwar Prof. G. D. Kalayi: Babban Rashi a Fannin Ilimin LafiyaInna lillahi wa inna ilaihi raji’un. An tabbatar da rasuw...
19/07/2025

Rasuwar Prof. G. D. Kalayi: Babban Rashi a Fannin Ilimin Lafiya

Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un. An tabbatar da rasuwar Professor G. D. Kalayi, wanda shi ne provost na farko a Kwalejin Kimiyyar Lafiya ta Jami’ar Gombe (GSU).

Muna mika ta’aziyya ga iyalansa, abokan aikinsa, da duk masu kaunarsa. Allah Ya jikansa, Ya saka masa da Aljannatul Firdaus, Ya kuma bai wa danginsa hakurin jure wannan babban rashi.

Kwalejin Fasahar Sufuri ta NITT, Zaria ta Gwada Jiragen Sama Marasa MatukiKwalejin Fasahar Sufuri ta Ƙasa (NITT) da ke Z...
19/07/2025

Kwalejin Fasahar Sufuri ta NITT, Zaria ta Gwada Jiragen Sama Marasa Matuki

Kwalejin Fasahar Sufuri ta Ƙasa (NITT) da ke Zaria ta gudanar da gwajin jirage marasa matuƙa da injiniyoyinta s**a ƙera, a wani babban mataki da ke nuna ci gaban fasaha da ƙirƙira a Najeriya.

Wannan gwaji na nuna alfahari da ƙwarewar da kwararrun kwalejin s**a cimma, tare da tabbatar da sahihancin fasahar da ake ƙera a cikin gida.

📸: NITT

Shugaban Ƙasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, GCFR, ya sauka a Kano yau da yamma domin kai ziyarar ta’aziyya bisa rasuwar fit...
18/07/2025

Shugaban Ƙasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, GCFR, ya sauka a Kano yau da yamma domin kai ziyarar ta’aziyya bisa rasuwar fitaccen ɗan kasuwa, Alhaji Aminu Alhassan Dantata (rahimahullah).

Gwamna Abba Kabir Yusuf da manyan jami'an gwamnati sun tarbe shi a filin jirgin Mallam Aminu Kano. Ana sa ran shugaban zai ziyarci iyalan marigayin a gidansu da ke cikin birnin Kano.

KBC Hausa

Professor Isa Ali Pantami  Ya Ziyarci Hajiya Mama Zainab, Dattijuwar Da Ta Raini Buhari A DauraDaga Muhammad Kwairi Wazi...
18/07/2025

Professor Isa Ali Pantami Ya Ziyarci Hajiya Mama Zainab, Dattijuwar Da Ta Raini Buhari A Daura

Daga Muhammad Kwairi Waziri

A wani mataki na nuna girmamawa da daraja ga dattijai, fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Professor Isa Ali Ibrahim Pantami, ya kai ziyara ta musamman ga Hajiya Mama Zainab a garin Daura, jihar Katsina.

Hajiya Mama Zainab, wadda yanzu haka take da shekaru 104, ita ce ta raini marigayi tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, tun yana jariri. A lokacin da Buhari ke shugabantar ƙasa, Hajiya Zainab ta kasance tare da shi a fadar shugaban ƙasa, tana ci gaba da taka muhimmiyar rawa a rayuwarsa.

Sheikh Pantami ya bayyana ziyarar a matsayin alamar girmamawa ga dattijai da kuma karrama tarihin mutanen da s**a taka rawa a rayuwar manyan shugabannin ƙasar nan.

"Ziyarar ba siyasa ba ce, sai dai nuna daraja da girmamawa ga dattijuwar da ta rayu da shugabanni kuma ta shafe shekaru tana bayar da gudunmawa," in ji Pantami.

Ziyarar ta ja hankalin jama'a a kafafen sada zumunta, inda mutane da dama ke yabawa Sheikh Pantami bisa irin wannan dabi'a ta kula da dattijai da rungumar tarihi da al’adu.

Address

Kaduna

Telephone

+2348149675978

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Daily News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Daily News Hausa:

Share