10/04/2026
Daya daga cikin rijiyar da Annabi SAW, yayi alwala da ruwan ta dake a garin Madinah.
Annabi SAW ya taɓa yin alwala da ruwan rijiya, kuma ya sanya mata suna Al-Yaseerah. A nan ne aka wanke sahabin nan Abu Salama bin Abdul-Asad Al-Makhzumi (Allah Ya yarda da shi) lokacin da ya rasu sakamakon raunukan da ya samu bayan Yaƙin Uhud. Shi ne ɗan’uwan Annabi ﷺ ta fuskar shayarwa, kuma ɗan goggonsa Barrah bint Abdul-Muttalib.
Masanin tarihi Al-Samhoodi ya ambaci cewa sunan Al-Ahn yana nufin ulu mai launi. Haka kuma Al-Mutari ya ce ya ga a rubuce cewa rijiyar da aka ambata a littattafan tarihin Madina ana kiranta Rijiyar Al-Ahn a yankin Al-Aliyah, kuma ana noma a cikin ta, kuma akwai bishiyar Sidr (magarya) a kusa da ita.
Ya kuma ce: wannan rijiyar sananniya ce a yankin Al-Awali, tana da kyau sosai, an hako ta a cikin dutse, kuma tana da bishiyar Sidr a gefenta. Amma daga baya an yanke wannan bishiyar.
Allah SWT ya kara mana soyayyan Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam, ya bamu ikon ziyartan wannan wuri albarkan Annabi SAW. Amiin Yaa ALLAH
Daga: Fityanu Islamic Centre
Rana: April 10, 2026