Babangida Maina

Babangida Maina Babangida Maina II Businessman, Writer, Media Consultant, Multimedia Strategist & Social Commentator.

A nan ne aka yi Yaƙin Khandaq (Ahzab), inda Manzon Allah ﷺ da Sahabbansa s**a fuskanci mushrikai. Wannan wuri shi ne Dut...
18/10/2025

A nan ne aka yi Yaƙin Khandaq (Ahzab), inda Manzon Allah ﷺ da Sahabbansa s**a fuskanci mushrikai. Wannan wuri shi ne Dutse Sila‘, daya daga cikin muhimman wuraren tarihi a birnin Madinatul Rasul.

Allah Ya taimaki Musulmai, ya bamu albarkan ANNABI Muhammadu saww, ya bamu gidan Aljannah. Amiin

Daga: Fityanu Islamic Centre

Garin Da Annabi ﷺ Yayi Addu’a: wannan gari Kabilar Daws ɗaya ce daga cikin kabilun Larabawa, kuma a yau suna zaune a was...
17/10/2025

Garin Da Annabi ﷺ Yayi Addu’a: wannan gari Kabilar Daws ɗaya ce daga cikin kabilun Larabawa, kuma a yau suna zaune a wasu ƙasashen Larabawa, asalin su kuwa shine Tsibirin Larabawa. Annabi ﷺ ya yi musu addu’a da shiriya, kamar yadda aka rawaito a cikin Sahihain Bukhari (4392) da Muslim (2524):

An rawaito daga Abu Huraira رضي الله عنه cewa: “Tufail bin ‘Amr al-Dawsi ya zo wurin Annabi ﷺ ya ce: ‘Garin Daws sun halaka, sun yi tawaye kuma sun ki yin biyayya, ka yi addu’a a kansu.’ Sai Annabi ﷺ yayi masu addu’a ya ce: ‘Ya Allah, ka kiyaye garin Daws, ka dawo dasu kan gaskiya…’” Kuma Allah ya amsa addu’arsa, sai s**a zo s**a Musulunta.

Allah ya daukaka Musulunci da musulmai. Amiin

Daga: Fityanu Islamic Centre

JANA'IZA CIKIN HOTUNA: An Gudanar Da Sallah Jana'izar Babban Malamin Musulunci Kuma Shehi A Darikar Tijjaniya Khalifa Mu...
16/10/2025

JANA'IZA CIKIN HOTUNA: An Gudanar Da Sallah Jana'izar Babban Malamin Musulunci Kuma Shehi A Darikar Tijjaniya Khalifa Muhammad Abare Kamar Yanda Addinin Musulunci Ya Tanadar A Jihar Yobe.

Muna Addu'an Allah Ya Kara Jaddada Masa Rahmah Ya Kara Masa Kusanci Da Manzon Allah SAW. Amiin

Daga; Fityanu Islamic Centre

Wannan shi ne kabarin Sayyidah Ruqayyah, ‘yar  Manzon Allah ﷺ Matar Sayyadina Uthman Ibn AffanAllah Ya ɗaukaka darajar S...
15/10/2025

Wannan shi ne kabarin Sayyidah Ruqayyah, ‘yar Manzon Allah ﷺ Matar Sayyadina Uthman Ibn Affan

Allah Ya ɗaukaka darajar Sayyidah Ruqayyah, Ya kuma bamu albarkacin ta, ya hadamu a gidan Aljannah baki daya. Amiin Yaa ALLAH

Don kaunar Annabi Muhammadu saww kayi comment da sharing don yan'uwa su amfana....

Daga; Fityanu Islamic Centre.

Wannan shine masallacin Tana’im (Masallacin Sayyida A’isha رضي الله عنها) yana daga cikin masallatan Makkah, yana masall...
14/10/2025

Wannan shine masallacin Tana’im (Masallacin Sayyida A’isha رضي الله عنها) yana daga cikin masallatan Makkah, yana masallacin yammacin birnin Makkah, kimanin km 7 daga Masallacin Harami. Daga nan ne mutanen Makkah ke yin niyyar Hajji ko Umrah.

An gina shi a wurin da Sayyida A’isha bint Abubakar رضي الله عنها ta yi niyyar Umrah a Hajjatu Wada’a shekara ta 9 bayan Hijira. An fara gina masallacin a zamanin Khalifa Al-Mutawakkil (240H), daga baya aka faɗaɗa shi har zuwa murabba’in 84,000m².

Masallacin na cikin iyakokin harami guda shida, kuma ya samo sunansa daga kasancewarsa tsakanin duwatsu biyu — Ná‘m da Na‘īm.

Allah ubangiji madaukakin sarki ya bamu albarkacin wannan wuri, ya bada ikon ziyara albarkan Annabi Muhammadu saww. Amiin Yaa ALLAH.

Daga: Fityanu Islamic Centre

Wannan ragowar gine-ginen tarihi ne da tsofaffin abubuwa a yankin Qurban, kusa da gidajen Banu Umayya bin Zayd al-Awsi. ...
12/10/2025

Wannan ragowar gine-ginen tarihi ne da tsofaffin abubuwa a yankin Qurban, kusa da gidajen Banu Umayya bin Zayd al-Awsi. Abin lura shi ne, wannan wuri mai tarihi Annabi Muhammadu (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya taba ziyartan wurin.

A kusa da gine-ginen kuma, akwai wata rijiyar al-‘Ihn, wadda aka yi amfani da ruwanta wajen wanke jikin sahabin Annabi mai girma Abu Salama, mijin Ummu Salama (Allah ya yarda da su).

Muna rokon Allah Subhanahu Wata'ala ya bamu ikon ziyartan wannan wurin, albarkacin Annabin rahma SAW, Amiin Yaa ALLAH

Daga: Fityanu Islamic Centre

Wannan wurin ake kira da suna Shiq al-Mahras dake a Dutsen Uhud da Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gar...
10/10/2025

Wannan wurin ake kira da suna Shiq al-Mahras dake a Dutsen Uhud da Manzon Allah (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya nemi mafaka bayan mayakan Romawa sun bar Dutsen Rumāt (dutsen masu harbi da baka). Wannan “shiq” wani rami ne a cikin dutsen Uhud inda Annabi (S.A.W) ya zauna tare da sahabbai guda bakwai daga cikin Ansar da kuma Talha bn Ubaydillah da Sa’ad bn Abi Waqqas (Allah ya yarda da su).

Sa’ad bn Abi Waqqas ya ci gaba da harba makiya, yayin da Talha bn Ubaydillah (R.A) ya yi bajinta sosai har sai da aka yanke yatsunsa. Sai Annabi (S.A.W) ya ce: “Wajabat Talha!” wato “Aljanna ta tabbata ga Talha!”

Allah ya bamu albarkacin wannan dutse na Uhud, ya bamu albarkan ANNABI SAW. Amiin Yaa ALLAH

Daga: Fityanu Islamic Centre

Allah ya yiwa daya daga cikin manyan malamin addinin musulunci kuma shehin darika Malam Kabiru Babban Malami na Madabo j...
09/10/2025

Allah ya yiwa daya daga cikin manyan malamin addinin musulunci kuma shehin darika Malam Kabiru Babban Malami na Madabo jihar Kano rasuwa.

Za'a gudanar da sallah jana'izar sa ranar juma'a karfe 10:00am a kofar Kudu fadar Mai martaba Sarkin Kano.

Allah ubangiji madaukakin sarki ya jikan sa da rahma ya gafarta masa albarkan Annabi SAW. Amiin

Daga: Fityanu Islamic Centre

Wannan shine gonar da Annabi Muhammadu saww ya zauna a cikin ta, kuma nan ne wuri na farko da Manzon Allah ﷺ ya isa daga...
08/10/2025

Wannan shine gonar da Annabi Muhammadu saww ya zauna a cikin ta, kuma nan ne wuri na farko da Manzon Allah ﷺ ya isa daga Makka zuwa Madina. An tarbe shi da farin ciki, kuma nan ce rakumarsa ta zauna, sai mutanen Madina s**a yi ta gayyatar sa gida don su sauke shi.

Manzon Allah SAW Ya sha daga ruwan rijiyar ‘Azuq (عذق), ya ci ɗan itacen gonar, ya yi musu addu’ar albarka. Daga nan ya wuce gidan Kulthum bn al-Hidam (RA). Wannan gonar har yanzu tana nan, ana kiranta Bustan al-Mustazil — tana kusa da Masallacin Quba. Wuri ne mai tarihi, cike da kyawu, albarka da tarihin Hijirar Manzon Allah ﷺ.

Allah ubangiji madaukakin sarki ya bamu albarkacin sunan sa Sallallahu Alaihi Wasallam, Amiin Yaa ALLAH

Daga: Fityanu Islamic Centre

Sheikh Farfesa Ibrahim Maqari RA, Ya bayyana cewa bai dace a yi haɗin kai da waɗanda ke nuna rashin girmamawa ga Manzon ...
07/10/2025

Sheikh Farfesa Ibrahim Maqari RA, Ya bayyana cewa bai dace a yi haɗin kai da waɗanda ke nuna rashin girmamawa ga Manzon Allah (SAW) ba, sai dai idan sun gyara matsayinsu kuma s**a dawo kan hanya madaidaiciya.

A cewarsa, “Idan wani yana tunanin za a iya haɗa kai da waɗanda ke yin kalamai da ba su dace ba kan Manzon Allah (SAW), toh ya kamata ya sake duba hankalinsa.”

Allah ubangiji madaukakin sarki ya bamu albarkan Annabi Muhammadu saww, ya kiyaye mu daga sharrin makiya. Amiiiin Yaa ALLAH

Wannan masallaci yana a bustan Banī Rabīʿah (yana ƙetaren hanyar Ṭā’if zuwa Makka, kimanin mil uku daga garin Ṭā’if.) wu...
05/10/2025

Wannan masallaci yana a bustan Banī Rabīʿah (yana ƙetaren hanyar Ṭā’if zuwa Makka, kimanin mil uku daga garin Ṭā’if.) wurin da Manzon Allah ﷺ ya huta bayan wahalar da ya sha daga mutanen Ṭā’if. A nan ne bawan ƴan Rabīʿah mai suna ʿAddās, mabiyin addinin Kirista daga Nīnawā, ya kawo masa inabi.

Da Annabi ﷺ ya ce “Bismillāh” kafin ya ci, sai ʿAddās ya tambaye shi, ya ce: “Ba mu saba jin wannan kalma ba.” Sai Annabi ﷺ ya ce masa: “Kai daga garin Yūnus ɗan Matta ne?” Ya ce: “Yaya ka san shi?” Sai Annabi ﷺ ya ce: “Shi ɗan uwana ne, Annabi ne, ni ma Annabi ne.”

Sai ʿAddās ya gaskata Annabi Muhammadu saww, ya addinin musulunta a wurin.

📍 Wannan wurin ne aka gina Masallacin ʿAddās (R.A) domin nuna alamar bayan wahalar ManzonSa saw yasha a Ta’if. Allah ya bamu albarkacin sa. Amiin

Daga: Fityanu Islamic Centre

Masha'Allahu: muna godiya Allah ubangiji madaukakin sarki yasa sanya mu cikin ni'imar sa mun gode masa, zamu dawo rubuce...
05/10/2025

Masha'Allahu: muna godiya Allah ubangiji madaukakin sarki yasa sanya mu cikin ni'imar sa mun gode masa, zamu dawo rubuce-rubucen da mukeyi na kayayyakin tarihi tare da fadakarwa wanda muka saba gabatar wa a lokaci bayan lokaci insha Allahu. Mun godewa yan'uwa da muka nuna sha'awar mu dawo aiki.

Address

Manawachi Pantami
Gombe
760101

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Babangida Maina posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Babangida Maina:

Share