A-Media TV

A-Media TV Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from A-Media TV, Media/News Company, Gombe.

mun Bude wannan shafinne don kawu muku labarai da photona dama video na duk abunda ke faruwa a duniya mun samarda da wannan dandalin badan chinma wata manufa Wanda bata daceba

31/03/2022

KAYITA MAI MAITA WANNAN ADDU'AR DON NAIMAN KAIWA GA WATAN RAMADAN

Allahumma Ballighna Ramadan - Mishary Al AfasyKAYITA MAI MAITA WANNAN ADDU'AR DON NAIMAN KAIWA GA WATAN RAMADAN

Allahumma Ballighna Ramadan - Mishary Al Afasy

Wani matashi dan jihar Adamawa ya koka akan gasar kyau da Aisha Garko talashi,------------------------------------------...
20/12/2021

Wani matashi dan jihar Adamawa ya koka akan gasar kyau da Aisha Garko talashi,
------------------------------------------------------------
Daga Assalis A Sani

Abubakar Mai Shadda Yayi korafi akan gasar da akayi ta fidda sarauniya kyau a Najeriya, Inda yake cewa anyi babban kuskure da akazabi Aisha Garko, a matsayin Wadda talashe gasar kyau.

Shidai Abubakar dan a salin garin Adamawa ne saboda hake yake ganin Aisha bata dace da tazama sarauniyar kyau a illahirin kasar Najeriya ba.

Mlm Abubakar yabada hotan wata budurwa yar garin Adamawa Wadda anasa ra'ayin itace ta dace da aba wannan sarautar, ma'na mafi kyau a cikin Najeriya baki daya.

Me zaku ce?

Flash News Hausa

Wannan ce budurwar da tafi ko wace mace kyau a faɗin Nijeriya, a cewar masana.Masu karatu shin ko kun yadda da hakan?
20/12/2021

Wannan ce budurwar da tafi ko wace mace kyau a faɗin Nijeriya, a cewar masana.

Masu karatu shin ko kun yadda da hakan?

IKON ALLAH: Yadda Wata Mata Mai Suna Halima Cassi Ta Haifi Ƴaƴa 9Halima Cassi ta haifi ƴaƴa guda 9 a ranar 5 ga watan Ma...
23/10/2021

IKON ALLAH: Yadda Wata Mata Mai Suna Halima Cassi Ta Haifi Ƴaƴa 9

Halima Cassi ta haifi ƴaƴa guda 9 a ranar 5 ga watan Mayu, 2021 a garin Casablanca dake ƙasar Morocco.

Halima ta haifi maza 4 mata 5 kamar yadda aka sa musu suna kamar haka; MAZA: Mohammed, Bah, El-Hadji, da Oumar. MATA: Hawa, Adama, Fatouma, Oumou da Kadidia.

Yanzu haka Halima da yaranta 9 suna nan cikin ƙoshin lafiya.

–Idon Mikiya

Sarkin Obajana Engr. Dr Idowu Isenibi, Oba Of Obajana Ya Bawa Musulman Garin Obajana Makeken Fili Hetka 10 Domin Ya Zama...
11/09/2021

Sarkin Obajana Engr. Dr Idowu Isenibi, Oba Of Obajana Ya Bawa Musulman Garin Obajana Makeken Fili Hetka 10 Domin Ya Zama Maƙabarta Ga Al-ummar Garin, Bayan Ruwan Sama Ya Lalata Tsohuwar Maƙabatarsu

Daga Ƙungiyar "Arewa Media Writers"

Idan baku manta ba, a farkon wannan watan ne Ƙungiyar marubutan Arewa a kafofin sadarwar zamani "Arewa Media Writers" ta fitar da Rahoton neman taimako ga Al-umma kan wani Ruwa mai ƙarfi da aka yi a garin Obajana, wanda yayi sanadiyyar ambaliya a ƙoramu, har ruwa ya gangara cikin maƙabartar garin, Maƙabartar ta zama cikin ruwa tare da tone ƙaburbura sama da 100.

A jiya Lahadi Ƙungiyar "Arewa Media Writers" reshen jihar Kogi ta halarci taron ziyarar godiya zuwa fadar sarkin Obajana Engr. Dr Idowu Isenibi, Oba of Obajana akan gudumuwar da ya bawa musulman garin obajana.

Sarki Engr. Dr. Idowu Isenibi, ya tarbi al-ummar garin hannu biyu-biyu kuma yaji daɗin wannan ziyara kuma yayi Addu'a da fatan zaman lafiya a yankin mu na Arewa dama ƙasar mu Najeriya baki ɗaya.

Sarkin yayi alhini na ibtila'in da ya faru da musulmai na lalacewar maƙabartar su.

Wannan dalilin yasa Sarki Engr Dr. Idowu Isenibi Idowu Isenibi, ya bawa Musulman garin Obajana makeken fili Hetka 10 wato 150×150 guda tamanin 80 a matsayin maƙabarta ga muslim society na Obajana.

Mutane da dama sun taimaka sanadiyar kai koken su ga al-umma da manyan ƙasar da Ƙungiyar "Arewa Media Writers" tayi wanda zuwa yanzu an samu kuɗi da s**a kai kimanin Naira Miliyan Ɗaya da Rabi 1,500,000.

Oba na Objana Engr Dr. Idowu Isenibi, ya bada takardar fili ga sarkin Hausawan Obajana da limaman masallatan Obajana.

Shuwagabanni da Limaman Obajana sun yiwa Sarki Addu'a ta ɗaukaka da zaman Lafiya a ƙasar dama yankin mu na Arewa dama ƙasar mu baki ɗaya.

Rubutawa✍️✍️✍️
Abu Bilal Dan Majema,
Chairman "Arewa Media Writers" Kogi State Chapter.

KACICI-KACICI: Masu karatu ko zaku iya faɗa mana sunan waɗanda suke cikin wannan hoton gaba ɗayan su ?
06/09/2021

KACICI-KACICI: Masu karatu ko zaku iya faɗa mana sunan waɗanda suke cikin wannan hoton gaba ɗayan su ?

ALLAHU AKBAR...DAGA Comrade Musa Garba Augie.Marigayi Abubakar Sadiq kenan, kafin da bayan an tasa ƙeyar wadda su ka kas...
29/07/2021

ALLAHU AKBAR...

DAGA Comrade Musa Garba Augie.

Marigayi Abubakar Sadiq kenan, kafin da bayan an tasa ƙeyar wadda su ka kashe shi zuwa inda s**a binneshi a gidan da yake haya a Damaturu. Ciki har da yaronsa da yake masa aikace-aikace, Amana tayi ƙaranci, da na jikinka za'a haɗa kai a kashe ka, Innalillahy Wa'inna ilaihi Raji'un.

Jaridar A-Media TV da gaba ɗaya ma'aikatan wannan jarida, muna yin Allah-wadai da rubutun ɓatanci ga Fiyayyen Halitta An...
26/07/2021

Jaridar A-Media TV da gaba ɗaya ma'aikatan wannan jarida, muna yin Allah-wadai da rubutun ɓatanci ga Fiyayyen Halitta Annabi Muhammadu S.A.W da jaridar Sahara Reporters ta Wallafa. Allah ka la'ance su, ka wulaƙantasu duniya da lahira.

Buhari Ya Cika Kowane Alkawali da Ya Daukarwa 'Yan Najeriya Lokacin Kamfen~Inji Jigon APC a BenuwaiWani Babban jigon jam...
26/07/2021

Buhari Ya Cika Kowane Alkawali da Ya Daukarwa 'Yan Najeriya Lokacin Kamfen~Inji Jigon APC a Benuwai

Wani Babban jigon jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya Hon. Terhemba Ishegh dake jihar Benuwai ya bayyana cewar, gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari ta yi bakin kokari na ganin ta cika dukkan alkawalin da ta yiwa yan Najeriya lokutan kamfen.

Terhemba a cikin wata zantawa da kamfanin dillancin labarai Najeriya ya yi dashi a ranar yau litinin a Makudi.

Jigon APC ya bayyana cewar, duk wanda ke kallon gwamnatin Buhari a matsayin ba daidai ba to munafuki ne kuma bai da adalci a zuciyar shi.

Terhemba Ishegh ya bayyana cewar, alamu ma sun nuna cewar duk shuwagabannin kasar da aka taba yi a Najeriya ba wanda ya yi aikin Buhari.

Ya bayyana cewar, gwamnatin Buhari ta samu nasarorin masu yawa a fannoni samar da ababen more rayuwa kamar ilimi, tattalin arziki, gami da yaki da cin hanci da rashawa.

Kan maganar samar da tsaron kuma, Terhemba ya bayyana cewar shugaba Buhari bai da laifi kuma yana bakin kokarin sa ba dare ba rana domin ganin al'umma sun zauna cikin kwanciyar hankali.

Mi Zaku Ce?

Har Abada Na Fita Daga Addinin Musulunci Na Koma Na Kiristoci~Inji Dr. Ahmed AmadiWani mutun malami a karamar hukumar Be...
25/07/2021

Har Abada Na Fita Daga Addinin Musulunci Na Koma Na Kiristoci~Inji Dr. Ahmed Amadi

Wani mutun malami a karamar hukumar Bende jihar Abia mai suna Dakta Ahmed Amadi ya sanar da ficewar sa daga addinin musulunci zuwa addinin kirista a yau lahadi.

Kamin komawar sa addinin kirista Dakta Ahmed Amadi shi ne shugaban kungiyar dake yaki da ta'addanci karkashin addinin musulunci wato (MATO) ya ce kamun ficewar sa daga addinin musulunci sai da ya sanar da mambobin kungiyar.

Mi Zaku Ce?

Address

Gombe

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when A-Media TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to A-Media TV:

Share