Gombe State Apc Social Media Team

Gombe State Apc Social Media Team Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Gombe State Apc Social Media Team, Social Media Agency, G. R. A Tula Road, Gombe.

Gombe ta Arewa: Sanata Dankwambo, Ina Kudin da Aka Ware wa Mazabar Sanatan?A shekarar 2023, an zabi Sanata Ibrahim Hassa...
25/08/2026

Gombe ta Arewa: Sanata Dankwambo, Ina Kudin da Aka Ware wa Mazabar Sanatan?

A shekarar 2023, an zabi Sanata Ibrahim Hassan Dankwambo a matsayin dan Majalisar Dattawa domin wakiltar kananan hukumomi biyar da s**a kunshi Mazabar Sanatan Gombe ta Arewa. Sai dai tun bayan zabensa, ba a ga wasu manyan ayyuka na zahiri da za a iya danganta su da kokarinsa na tallafawa mazabar ba.

Saboda haka, muna neman amsoshi kan wasu tambayoyi da s**a shafi ayyuka da shirye-shiryen da aka ware wa mazabar a cikin kasafin kudin gwamnatin tarayya.

A cikin kasafin kudin shekarar 2024 kadai, bayanan kasafin kudi da ake da su sun nuna cewa an ware biliyoyin naira domin gudanar da ayyuka da shirye-shiryen mazabu daban-daban a Mazabar Sanatan Gombe ta Arewa. Saboda haka, domin tabbatar da gaskiya da rikon amana, muna bukatar cikakken bayani da hujjoji masu gamsarwa kan yadda aka aiwatar da wadannan ayyuka.

Misali, an ware Naira miliyan 150 domin samar da taki ga manoma.

Ina takin yake? Su waye s**a amfana a Gombe, Kwami, Funakaye, Dukku da Nafada? Buhunan taki nawa aka ware wa kowace karamar hukuma? A ina kuma yaushe aka raba takin? Muna son ganin hujjar rabon, ciki har da hotuna, bidiyo da kuma jerin sunayen wadanda s**a amfana wanda za a iya tantance sahihancinsa.

Haka kuma, an ware Naira miliyan 50 domin samar da injinan tura ruwa domin aikin noman rani.

Su waye s**a karbi wadannan injinan? Nawa aka kai Dukku da sauran kananan hukumomi? A ina kuma yaushe aka gudanar da rabon? Muna neman sunayen wadanda s**a amfana da sauran bayanan da za su tabbatar da cewa an aiwatar da wannan shiri.

Bugu da kari, an bayar da rahoton cewa an ware Naira miliyan 400 domin sayen taki, magungunan kashe ciyawa da nau’o’in hatsi daban-daban domin rabawa al’ummar mazabar.

Ina hujjar aiwatar da wannan shiri? Su waye s**a karbi wadannan kayan? Nawa aka ware wa kowace karamar hukuma? Wace hanya aka bi wajen rabon, kuma su waye s**a amfana?

Wadannan tambayoyi ne halastattu kuma sun cancanci samun cikakkun amsoshi masu hujja.

Abin da muke nema ba tsangwama ta siyasa ba ce, illa riko da gaskiya da yin hisabi. Kudaden al’umma da aka ware domin ayyukan mazabu an tanade su ne domin amfanin mutanen da aka ware musu. Don haka, al’ummar Gombe ta Arewa suna da hakkin sanin ko an aiwatar da wadannan ayyuka, yadda aka aiwatar da su, da kuma wadanda s**a amfana.

Akwai karin bayani da ke tafe. Dole ne mu sanya ido sosai kan ayyukan Sanata Dankwambo, domin a halin yanzu ba ma ganin wakilcin nasa a matsayin wanda ke kawo mana moriya.

Hujjojin an samo su ne daga takardar Kasafin Kudi.


DR. JAMILU ISHIYAKU GWAMNA: JAGORAN DA KE TAFIYA DA ZUCIYAR AL’UMMA ZUWA NASARAR 2027A fagen siyasar Jihar Gombe, sunan ...
23/08/2026

DR. JAMILU ISHIYAKU GWAMNA: JAGORAN DA KE TAFIYA DA ZUCIYAR AL’UMMA ZUWA NASARAR 2027

A fagen siyasar Jihar Gombe, sunan Dr. Jamilu Ishiyaku Gwamna ya zama abin da ke ci gaba da ɗaukar hankalin jama'a sak**akon irin karɓuwa, mutunci da kuma kusancinsa da al'umma. A matsayinsa na ɗan takarar Gwamnan Jihar Gombe a ƙarƙashin Jam’iyyar APC, Dr. Jamilu ya samu gagarumar goyon baya daga matasa, mata, dattawa da sauran masu ruwa da tsaki a faɗin jihar.

Masu sharhi kan harkokin siyasa na ganin cewa babban ƙarfin Dr. Jamilu Ishiyaku Gwamna ba wai kawai kasancewarsa ɗan takara ba ne, illa kasancewarsa mutum mai kyakkyawar mu’amala da jama'a, mai sauraron koke-kokensu tare da neman mafita ga matsalolinsu. Wannan ne ya sanya yake ci gaba da samun karɓuwa a lungu da saƙo na Jihar Gombe.

Tun bayan bayyana shi a matsayin zaɓaɓɓen ɗan takarar APC, ana ci gaba da ganin yadda al'umma daga sassa daban-daban ke bayyana goyon bayansu gare shi. Hakan ya samo asali ne daga irin gudummawar da ya bayar a fannoni da dama da kuma kyakkyawar alaƙarsa da jama'a ba tare da nuna bambanci ba.

Masu nazarin siyasa sun yi imanin cewa zaɓen 2027 zai kasance wata dama ga al'ummar Gombe domin ci gaba da tafiyar da manufofin ci gaba da gwamnatin APC ta shimfiɗa a ƙarƙashin jagorancin Mai Girma Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya CON. A cewarsu, Dr. Jamilu Ishiyaku Gwamna na ɗaya daga cikin fitattun jagororin da za su iya ci gaba da ɗora jihar a kan turbar ci gaba, zaman lafiya da bunƙasa tattalin arziki.

Abin da ya fi jan hankali shi ne yadda matasa ke kallonsa a matsayin jagora mai hangen nesa, yayin da mata da dattawa ke yaba masa kan tawali'u, biyayya da mutunta jama'a. Wannan soyayya da amincewa da yake samu daga al'umma na ƙara tabbatar da cewa yana da kyakkyawar damar samun nasara a zaɓen Gwamnan Jihar Gombe na shekarar 2027.

A yau, yayin da siyasa ke ƙara ɗaukar sabon salo, al'ummar Gombe na ci gaba da bayyana burinsu na ganin an zaɓi shugabanni masu nagarta, hangen nesa da kishin ci gaban jihar. Dr. Jamilu Ishiyaku Gwamna ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda ake kallon za su iya cika wannan buri, tare da haɗa kan al'umma domin gina Gombe mai ɗorewar ci gaba ga kowa da kowa.

Daga dukkan alamu, tafiyar siyasar Dr. Jamilu Ishiyaku Gwamna na ci gaba da samun karɓuwa, yayin da dubban magoya baya ke nuna kwarin gwiwa cewa shekarar 2027 za ta zama wata sabuwar manuniya ta nasara ga Jam'iyyar APC a Jihar Gombe.

Cewar Shugaba Rabiu B Goro
16/08/2026

Cewar Shugaba Rabiu B Goro

Dr. Jamil Isiyaku Gwamna (Sardaunan Gombe) Ya ba da Tallafin Naira Miliyan 1.5 Domin yiwa  Zainab Muhammad Aiki a Asibit...
16/08/2026

Dr. Jamil Isiyaku Gwamna (Sardaunan Gombe) Ya ba da Tallafin Naira Miliyan 1.5 Domin yiwa Zainab Muhammad Aiki a Asibiti

Ɗan takarar kujerar Gwamnan Jihar Gombe na Jam’iyyar APC, Dr. Jamil Isiyaku Gwamna (Sardaunan Gombe), ya bayar da tallafin Naira miliyan 1.5 (N1,500,000) domin taimakawa wajen biyan kuɗin jinya da aikin tiyatar Zainab Muhammad, ’yar Malam Muhammad.

Malam Muhammad ya bayyana cewa tun cikin watan Fabrairu aka ba su takardar tura Zainab domin a yi mata aikin da take buƙata. Sai dai saboda rashin ƙarfin hali da kuma tsadar kuɗin aikin, ya kasa samun damar biyan kuɗin da ake buƙata domin a fara jinyar.

Sai dai lamarin Zainab ya samu sauyi mai kyau bayan Sardaunan Gombe ya samu labarin halin da take ciki ta hannun wakilansa, Prof. Suleiman Dankade da Shugaban APC na Mazabar Bajoga Ward, Alhaji Nasir Lawal.

Bayan jin halin da iyalan ke ciki, Dr. Jamil Isiyaku Gwamna ya bayar da Naira miliyan 1.5 domin taimakawa wajen biyan kuɗin jinyar Zainab da kuma ba ta damar gudanar da aikin da take buƙata.

Daga bisani, Zainab Muhammad tare da iyayenta sun ziyarci gidan Prof. Suleiman Dankade, inda s**a karɓi wannan tallafi a madadin Dr. Jamil Isiyaku Gwamna.

Ga iyalan Zainab, wannan tallafi ya wuce kuɗi kawai. Fata ne da aka farfaɗo, nauyi ne da aka sauke, da kuma wata dama da aka ba Zainab ta samu kulawar lafiyar da ta daɗe tana jira.

Iyalan sun bayyana matuƙar godiyarsu ga Dr. Jamil Isiyaku Gwamna, Sardaunan Gombe, bisa wannan taimako da ya zo musu a lokacin da suke matuƙar buƙatarsa.

Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya saka wa Sardaunan Gombe da mafificin alheri bisa wannan kyakkyawan aiki na tausayi da jinƙai, Ya ba Zainab Muhammad nasarar aikin da za a yi mata tare da cikakkiyar lafiya, sannan Ya albarkaci dukkan waɗanda s**a taka rawa wajen isar da wannan taimako gare ta.

👉 Sardaunan Gombe: Sabuwar Fata ce ga Rayuwa. 🤲

2027: Pantami Is No Match for Sardauna's Integrity in Gombe Politics. Politics is not built in a day. It is not simply a...
15/08/2026

2027: Pantami Is No Match for Sardauna's Integrity in Gombe Politics.

Politics is not built in a day. It is not simply about academic credentials, social media popularity or the excitement that comes with securing a party ticket. Serious politics is built over time through people, relationships, structures, sacrifice, trust and sustained engagement with the grassroots.

Measured against these realities, Professor Isa Ali Ibrahim Pantami is no match for Dr. Jamil Isyaku Gwamna, the Sardaunan Gombe, in the politics of Gombe State.

For more than two decades, Sardauna has invested in people and relationships across the Gombe State. He supported young people, empowered families, built political networks and maintained relationships that have survived different political seasons.

His network extends beyond professional politicians.It cuts across youths, women, business people, community leaders, religious groups, professionals, retired public servants and ordinary citizens.

Across Gombe State, more than 1,300 volunteer youth and women support groups are working for Sardauna under the coordination of Hon. Ahmed Usman( Fada) Voluntarily.

There is also a strong network of business people under the leadership of Alhaji Saidu Mai Silifas, alongside retired directors and permanent secretaries, Alarammomi forum, community stakeholders and other organised groups.

Add to this the continuing political realignments and defections into the APC and towards the Sardauna movement, and the picture becomes increasingly in favour of Dr. Gwamna

This is not merely a campaign structure. It is the product of years of political investment and grassroots acceptability.

Leadership requires the ability to build relationships, maintain friendships, accommodate differences and inspire loyalty. Sardauna's experience cuts across the private and public sectors, giving him an understanding of both governance and corporate management.

Gombe does not simply need someone who wants to become governor. It needs someone capable of managing government, attracting investment, creating opportunities, building institutions and consolidating the achievements of Governor Muhammadu Inuwa Yahaya.

Ibrahim Sani Shawai
Spokesperson to Dr Jamil Isyaku Gwamna
15th Aug, 2026

GYARA TARIHI: YADDA GWAMNA INUWA YAHAYA KE MAGANCE TSOHON KALUBALEN RUWAN SHA A JIHAR GOMBEBayanin Gaskiya Kan Zuba Jari...
15/08/2026

GYARA TARIHI: YADDA GWAMNA INUWA YAHAYA KE MAGANCE TSOHON KALUBALEN RUWAN SHA A JIHAR GOMBE

Bayanin Gaskiya Kan Zuba Jari, Shirye-shirye da Matakan Dorewa Don Inganta Samar da Ruwan Sha a Fadin Jihar Gombe

Ikirarin Kashe Naira Biliyan 133 zuwa 138 Kan Ruwa Ba Gaskiya Ba Ne!

Wannan rubutu ba an yi shi domin mayar da martani ga wani mutum ko wata magana ba, kuma ba domin shiga wata muhawara ba ne. Manufarta ita ce gabatar da hakikanin bayanai ga al'umma domin su fahimci girman kalubalen ruwa da jihar Gombe ke fuskanta, irin jarin da aka zuba a wannan fanni, da kuma matakan da gwamnatin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, CON, ke dauka domin samar da mafita mai dorewa.

Kalubalen samar da ruwan sha ba sabon abu ba ne a jihar Gombe. Yawan jama'a da ke karuwa, fadada birane, tsufan kayayyakin aiki, karancin wuraren ajiya, tsadar mak**ashi da kuma tsohuwar hanyar rabon ruwa da aka tsara tun lokacin da Gombe ba ta da yawan jama'ar yau, duk sun taimaka wajen tsananta matsalar.

Tun bayan hawansa mulki a shekarar 2019, Gwamna Inuwa Yahaya ya dauki matakan da s**a shafi dukkan bangarorin samar da ruwa, daga hakowa da samarwa, tacewa, ajiyewa, tura ruwa, rabawa, samar da mak**ashi, sanya mitoci, gyare-gyare da kuma karfafa cibiyoyin gudanarwa.

Daya daga cikin wuraren farko da gwamnan ya ziyarta bayan k**a aiki shi ne Hukumar Ruwa ta Jihar Gombe da kuma Matatar Ruwa ta Dadin Kowa. Ya gana kai tsaye da injiniyoyi da ma'aikatan wuraren domin gano dalilan da s**a sa duk da dimbin kayayyakin aiki da aka gada, al'umma ba sa samun isasshen ruwa.

Binciken ya gano matsaloli da dama da s**a hada da karancin karfin samar da ruwa, rashin isassun tankunan ajiya, tsufan kayayyakin aiki, matsalolin wutar lantarki, gazawar hanyoyin tura ruwa da kuma kalubalen gudanarwa da gyare-gyare.

Bisa haka ne gwamnan ya kafa Kwamitin Musamman Kan Samar da Ruwa karkashin jagorancin Injiniya Abubakar Bappa domin gudanar da cikakken nazari tare da gabatar da shawarwari masu dorewa.

Sak**akon wannan bincike ne ya zama tubalin dabarun da gwamnati ke amfani da su har zuwa yau: gyara abin da za a iya gyarawa, fadada abin da bai isa ba, sabunta tsarin da kuma magance tushen matsalolin da s**a dade suna haddasa cikas ga samar da ruwa.



A SAKA LAMBOBIN CIKIN MAHANGAR DA TA DACE

Domin amfanin jama'a, yana da muhimmanci a bambance tsakanin kudaden gudanarwa na yau da kullum, bashin da aka gada, kudaden ayyukan raya kasa, shirye-shiryen hadin gwiwa da abokan ci gaba, tanadin kasafin kudi da kuma ainihin kudaden kwangila.

Wadannan fannoni daban-daban ne, kuma ba daidai ba ne a hada su gaba daya a ce duk kudin aikin ruwa ne guda daya.

Saboda haka, ikirarin cewa gwamnatin jihar ta kashe Naira biliyan 133 ko biliyan 138 a bangaren ruwa ba gaskiya ba ne kuma ba ya nuna hakikanin abin da aka kashe.

Lokacin da gwamnatin Inuwa Yahaya ta karbi mulki, ta tarar da bashin kusan Naira biliyan 5 da ake bin kamfanin CGC wanda ke kula da gudanarwa da gyaran Matatar Ruwa ta Dadin Kowa.

Gwamnatin ta biya wannan bashi tare da ci gaba da samar da kudaden gudanar da matatar. Daga shekarar 2019 zuwa 2025, jimillar kudaden gudanarwa da tallafin aiki sun kai sama da Naira biliyan 9.5.

Wadannan kudade na gudanarwa ne, ba kudaden sabbin ayyukan gine-ginen ruwa ba.

ZUBA JARI DA HADIN GWIWAR ABOKAN CIGABA

Tsakanin shekarun 2020 zuwa 2025, gwamnatin jihar ta ware manyan kudade domin fadada hanyoyin samar da ruwa, hakar rijiyoyi da kuma ayyukan da aka gudanar ta hannun RUWASSA da shirye-shiryen hadin gwiwa da abokan ci gaba.

Jihar Gombe tana cikin jihohi bakwai da ke amfana da shirye-shiryen Bankin Duniya, musamman SURWASH da Programme for Results (P4R).

Kasancewar jihar ta cika sharuddan da ake bukata ya taimaka wajen jawo irin wadannan shirye-shirye, wanda ya haifar da hakowa da gyaran daruruwan rijiyoyi a sassa daban-daban na jihar tare da sauran ayyukan samar da ruwa.

TANADIN NAIRA BILIYAN 88.4 A KASAFIN 2026

Hakazalika, tanadin Naira biliyan 88.4 da ke cikin kasafin kudin shekarar 2026 ba yana nufin an kashe wannan kudi gaba daya kan samar da ruwa a birnin Gombe ba.

Wannan tanadi ya shafi Ma'aikatar Albarkatun Ruwa, Muhalli da Dazuzzuka tare da hukumomin da ke karkashinta k**ar Hukumar Ruwa ta Jihar Gombe, RUWASSA, SURWASH da GOSEPA.

Ya kunshi ayyuka da dama da s**a hada da:

- Sauya cibiyoyin ruwa zuwa tsarin mak**ashin hasken rana da hadakar mak**ashi.
- Gyaran da fadada Tsarin Ruwa na Malam Inna.
- Gyaran manyan rijiyoyin ruwa na yankin arewa.
- Samar da ababen more rayuwa na ruwa a Yankin Bunƙasa Noma da Kiwo.
- Sauran shirye-shiryen ma'aikatar da hukumominta.

Saboda haka, tanadin kasafin kudi ba daidai yake da kudin da aka kashe ba, kuma ba za a iya daukar kasafin bangarori da dama a matsayin kudin aikin ruwa guda daya ba.

AIKIN FADADA TSARIN RUWA NA YANKIN GOMBE NA NAIRA BILIYAN 11.4

Daya daga cikin manyan ayyukan gwamnatin Inuwa Yahaya shi ne aikin fadada tsarin ruwa na yankin Gombe mai darajar Naira biliyan 11.4 wanda aka aiwatar tare da gwamnatin tarayya bisa tsarin kaso 70 zuwa 30.

Kamfanin Jidadu Ventures Nigeria Limited ne ya aiwatar da aikin, wanda yanzu ya kammala kuma ana gwajin tsarin kafin fara aiki gaba daya.

Aikin Wuro Juli

Aikin ya samar da:

- Sabbin rijiyoyi 14.
- Sauya famfo 14 zuwa tsarin mak**ashi na hadaka.
- Matatar ruwa mai karfin tace mita kubik 200 a awa guda.
- Sabbin tsarin famfo.
- Tsarin hasken rana, janareta da lantarkin gwamnati.

Yankin Musamman na Ci Gaba

An samar da:

- Tankin ajiya mai karfin mita kubik 1,000.
- Tankin sama mai karfin mita kubik 500.
- Sabbin na'urorin tura ruwa.
- Tsarin mak**ashi na hadaka.

Tunfure

An samar da:

- Karin tankunan ajiya.
- Tsarin famfo na hadaka.
- Bututun ruwa mai tsawon kilomita 5 zuwa tashar NTA Booster.
- Sauran kayayyakin aiki masu muhimmanci.

Tashar NTA Booster

An gudanar da:

- Gyaran tsofaffin kayayyakin aiki.
- Karin tankunan ajiya.
- Sabbin famfo da tsarin samar da mak**ashi.
- Karin bututun ruwa mai tsawon kilomita 6 zuwa kusa da Cibiyar Taro ta Kasa (ICC).

Har ila yau aikin ya kunshi fadada hanyoyin rarraba ruwa, sanya na'urorin auna ruwa na zamani, tsarin tattara bayanai, horar da ma'aikata, taswirar hanyoyin ruwa da kuma tsarin zamani na sarrafa bayanai.

Wannan ya nuna cewa aikin bai takaita ga guri guda ba, an tsara shi ne domin karfafa dukkan tsarin samar da ruwa baki daya.

SHIRIN FADADA AIKI A SHEKARAR 2026

Bayan nasarorin da aka samu, gwamnati ta amince da sabbin ayyuka da kudinsu ya kai kusan Naira biliyan 54.66 domin bunkasa ruwa da mak**ashi.

MALAM INNA, BIRNIN GOMBE DA YANKIN NOMA DA KIWO

An bayar da kwangilar Naira biliyan 24.26 domin:

- Gyaran rijiyoyi 9 da ake da su.
- Hako sabbin rijiyoyi 11.
- Tsarin famfo mai amfani da hasken rana.
- Sabbin wuraren tace ruwa.
- Tankin ajiya mai karfin mita kubik 4,000.
- Karin tankunan rarraba ruwa.
- Bututun ruwa na kilomita 3.
- Sama da kilomita 50 na sabbin hanyoyin rarraba ruwa.
- Karin wuraren samar da ruwa ga al'umma.

DADIN KOWA DA TABRA

An bayar da kwangilar Naira biliyan 7.07 ga kamfanin Ceylon Construction Services Limited domin inganta samar da mak**ashi ga cibiyoyin ruwa na Dadin Kowa da Tabra.

TSARIN MAKAMASHIN HASKEN RANA

Gwamnatin ta kuma ware Naira biliyan 23.33 domin samar da mak**ashin hasken rana ta hannun kamfanin Off-grid Electric Nigeria Limited.

Manufar ita ce rage dogaro da mak**ashin gargajiya, rage kudaden aiki da kuma tabbatar da dorewar samar da ruwa.

ME YA SA WANNAN TSARI YA BANBANTA?

Kalubalen ruwa ba zai kare ta hanyar samar da karin ruwa kadai ba.

Dole ne ruwa ya bi matakai na samarwa, tacewa, tura shi, adanawa, jigilar sa da kuma rabawa.

Saboda haka, shirye-shiryen gwamnati sun shafi:

- Samar da ruwa.
- Tace ruwa.
- Samar da mak**ashi.
- Famfo da tura ruwa.
- Ajiya.
- Jigilar ruwa.
- Rarrabawa.
- Sanya mitoci.
- Gyare-gyare da kula da kayayyakin aiki.

Wannan shi ne ainihin tsarin gwamnatin Inuwa Yahaya na samar da mafita mai dorewa.

GWAMNATI MAI GASKIYA DA BAYYANA AIKI

Daya daga cikin abubuwan da s**a bambanta wadannan ayyuka shi ne yadda gwamnatin jihar ke bayyana su ga jama'a.

Ta hanyar bayanan majalisar zartarwa, gabatar da kasafin kudi, ziyarce-ziyarcen ayyuka da sauran hanyoyin sadarwa, gwamnati ta rika bayyana wuraren ayyuka, kudaden kwangila, kamfanonin da ke gudanar da su da kuma irin ayyukan da ake yi.

Wannan tsari na gaskiya da bayyana aiki ne ya sa Gombe ke ci gaba da samun amincewa daga manyan cibiyoyin ci gaba na duniya.

MAFITA GA MATSALAR RUWA TA KUSA

Babban sakon da ya k**ata al'ummar Gombe su fahimta shi ne cewa akwai dalilai masu yawa na fatan alheri.

Gwamnatin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ta fahimci cewa jama'a sun dade suna fama da matsalar ruwa.

Sai dai irin girman ayyukan da ake gudanarwa a yanzu ya nuna cewa gwamnati ba ta kallon matsalar a matsayin wani abu na wucin gadi ba.

Manufarta ita ce gina tsarin ruwa mai karfi, mai dorewa, mai amfani da mak**ashi cikin hikima kuma mai iya biyan bukatun Gombe mai saurin bunkasa.

Haɗuwar aikin fadada tsarin ruwa na Naira biliyan 11.4 da kuma sabbin ayyukan ruwa da mak**ashi na Malam Inna da gyaran manyan rijiyoyi 44 na daga cikin mafi girman ayyukan ruwa da aka taba yi a tarihin jihar Gombe.

Da zarar an kammala wadannan ayyuka kuma s**a fara aiki yadda ya k**ata, ana sa ran za a samu gagarumin ci gaba wajen samar da ruwa, ajiya, karfin matsin ruwa, fadada rarrabawa da kuma tabbatar da samuwar ruwa a kai a kai.

Saboda haka, ranar da al'ummar Gombe za su waiwayi wannan matsala a matsayin tarihi mai wucewa ba ta da nisa.

Hakika, babu wata gwamnatin baya a tarihin jihar Gombe da ta dauki irin wannan tsari mai zurfi, mai hade dukkan bangarori da kuma dorewar zuba jari domin magance tushen matsalar ruwa k**ar gwamnatin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya.

Zuba jarin yana da girma.
Dabarun suna da inganci.
Ayyukan suna ci gaba da kank**a.

Matsalar ruwa gaskiya ce.
Martanin gwamnati ma gaskiya ne.
Kuma ga al'ummar Gombe, mafita mai dorewa tana kara bayyana a sarari.

Gombe State APC Social Media Team

Gombe Ta Samu Gagarumar Nasara a LafiyaJihar Gombe ta samu babban ci gaba a fannin kiwon lafiya, bayan dakin gwaje-gwaje...
13/08/2026

Gombe Ta Samu Gagarumar Nasara a Lafiya

Jihar Gombe ta samu babban ci gaba a fannin kiwon lafiya, bayan dakin gwaje-gwajen Molecular Diagnostic Laboratory na Gombe State Specialist Hospital ya samu sahalewar WHO wajen gwajin cututtukan kyanda (measles) da rubella.

Wannan nasara ta sanya Gombe cikin cibiyoyin da WHO ta amince da su a Najeriya, tare da bai wa jihar damar gudanar da gwaje-gwajen wadannan cututtuka cikin gida, maimakon tura samfurori zuwa wurare masu nisa.

A cewar CMD na Gombe State Specialist Hospital, Dr. Dawa Sambo, wannan ci gaba zai taimaka wajen samun sak**akon gwaji cikin gaggawa, da saurin gano barkewar cututtuka, tare da daukar matakan kariya da allurar rigakafi cikin lokaci.

Wannan nasara ta kara tabbatar da irin zuba jari da gwamnatin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ke yi wajen inganta kiwon lafiya, kayan aiki, kwararru da ingancin ayyukan asibiti.

Gombe yanzu na daga cikin cibiyoyi takwas kacal a Najeriya da WHO ta amince da su wajen gwajin measles da rubella—babbar nasara ga jihar da ma yankin Arewa maso Gabas.

Gombe 2027: Ana Cin Zabe a Rumfunan Zaɓe, Ba a Shafukan Sada Zumunta ba A shekarar 2027, ba Facebook, X, Instagram ko Ti...
13/08/2026

Gombe 2027: Ana Cin Zabe a Rumfunan Zaɓe, Ba a Shafukan Sada Zumunta ba



A shekarar 2027, ba Facebook, X, Instagram ko TikTok ne za su zabi sabon Gwamnan Jihar Gombe ba. Mutanen da ke zaune a cikin al’ummomin jihar Gombe, wadanda kuma za su rayu da sak**akon zabin da s**a yi, su ne za su yanke wannan hukunci a rumfunan zaɓe daban-daban na jihar.

Wannan bambanci yana da matukar muhimmanci.

Kafafen sada zumunta sun sauya yadda ake sadar da sakonnin siyasa. Dan siyasa na iya yin fice a cikin kasa baki daya cikin ‘yan sa’o’i, har ya zama batun tattaunawa a wurare masu nisa da mazabarsa. Amma shahararsa a kafafen sada zumunta ba lallai ne ta zama tabbacin samun kuri’u ba.

Wannan na daga cikin muhimman abubuwan da ya k**ata a fahimta game da siyasar Dr. Jamil Isyaku Gwamna, Sardaunan Gombe, yayin da tattaunawar Gombe 2027 ke kara daukar hankali.

Ga Sardaunan Gombe, wannan alaka ba ta fara ne da gabatowar zaben 2027 ba. Ya fara tafiyar neman amincewar al’umma sama da shekaru ashirin da s**a gabata, tun kafin wannan fafatawar siyasa ta yanzu.

Duk wata alaka da aka gina a tsawon wannan lokaci tana da muhimmanci. Duk wata dama da aka samar tana da muhimmanci. Duk mutumin da rayuwarsa ta samu tasiri saboda ayyukansa yana da muhimmanci.

Shekarun da ya shafe a harkar kasuwanci, gogewarsa a aikin gwamnati, ayyukan siyasa, taimakon al’umma da kuma alakar da ya kulla da al’ummomin Gombe, duk sun taimaka wajen gina matsayinsa na siyasa wanda ya samo asali daga Jihar Gombe.

Saboda haka, abin da ake gani a wannan matakin na tafiyar siyasar Sardauna bai k**ata a fahimce shi kawai a matsayin tafiya ne domin gabatar da kansa ga jama’a ba. Ga da dama daga cikin jama’ar Gombe, sun riga sun san shi tun shekaru da dama.

Goyon baya a Abuja, Kano ko Kaduna ba zai iya kada kuri’a a Gombe ba.

Tafawa a Abuja ba za ta maye gurbin amincewar al’umma a Akko ba.

Tattaunawar da ta yi fice a wajen jihar ba za ta maye gurbin alakar da aka gina a Balanga, Billiri, Dukku, Funakaye, Kaltungo, Kwami, Nafada, Shongom, Yamaltu/Deba ko Gombe ba.

Lokacin da ranar zabe ta zo, a nan Gombe ne za a yanke hukuncin wanda zai zama Gwamna.

Wannan ba yana nufin kafafen sada zumunta ba su da muhimmanci ba. Suna da muhimmiyar rawa wajen bayyana manufofi, mu’amala da matasa, mayar da martani ga labaran karya da kuma fadada shigar jama’a cikin harkokin siyasa. Amma ba za su iya maye gurbin siyasar kasa-kasa ba.

Saboda haka, ga Sardaunan Gombe, aikin da ke gabansa a fili yake: ya ci gaba da kasancewa tare da jama’a, ya saurare su, ya yi hulda da su, ya kara gina kyakkyawar alaka da su, sannan ya gabatar da ingantaccen shiri na makomar jihar.

🟢 KWADNETOTIN MARIGAYI HON. YAYA BAUCHI TONGO SUN SAUYA SHEƘA ZUWA APCKwadnetotin Marigayi Hon. Yaya Bauchi Tongo sun ba...
10/08/2026

🟢 KWADNETOTIN MARIGAYI HON. YAYA BAUCHI TONGO SUN SAUYA SHEƘA ZUWA APC

Kwadnetotin Marigayi Hon. Yaya Bauchi Tongo sun bayyana cikakken goyon bayansu ga jam’iyyar APC mai mulki, inda s**a sauya sheƙa daga ADC zuwa APC, tare da jaddada mubaya’a da amincewarsu da tafiyar jam’iyyar a Jihar Gombe.

A yayin wannan sauya sheƙa, Kwami Coordinator na Yaya Bauchi Tongo, Malam Ali Garba M. Yashi, tare da Hon. Yaya Bauchi Tongo da sauran Kwadnetoti daga gundumomi 10 na Ƙaramar Hukumar Kwami, sun jaddada mubaya’arsu ga Mai Girma Gwamnan Jihar Gombe, Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya, CON, da kuma ɗan takarar kujerar Gwamnan Jihar Gombe na jam’iyyar APC, Dr. Jamilu Isyaku Gwamna, tare da dukkan ‘yan takarar jam’iyyar a matakai daban-daban.

Sun bayyana aniyarsu ta yin aiki tukuru, tare da haɗa ƙarfi da sauran masu ruwa da tsaki, domin ganin APC ta samu gagarumar nasara a babban zaɓe mai zuwa na 2026. 🟢✊

A yayin wannan sauya sheƙa, tawagar ta ziyarci gidan Marigayi Hon. Yaya Bauchi Tongo, inda aka gudanar da taron haɗin kai da nuna goyon baya ga jam’iyyar APC, tare da halartar iyalan Marigayin da wasu daga cikin Hadimansa, musamman Alhaji Adamu Chanji, da sauran masu ruwa da tsaki.

An gabatar da jawabai masu cike da godiya, biyayya da ƙudurin ci gaba da aiki tare, domin ƙarfafa jam’iyyar APC da tabbatar da nasara a zaɓe mai zuwa.

Wannan sauya sheƙa na ƙara tabbatar da cewa haɗin kai, amana da kyakkyawan jagoranci su ne ginshiƙan samun nasarar siyasa mai ɗorewa.

Sunayen Kwadneto na Gundumomin Kwami

Sure 🙏. I copied the names as clearly as I can read them from the paper:

1. Mohd Adam — Dukul

2. Suleiman Haruna — Doho

3. Ibrahim Hassan — Konfulata

4. Salisu Abubakar— Daban Fulani

5. Alh Umar Adam — Gadam

6. Abubakar Muhammad — Bojude

7. Alh. Ali Garba — Malam Sidi

8. Hon. Inusa Barga — Kwami

9. Lunbi — Jurara

10. Mal. Babangida --- Jamari

Address

G. R. A Tula Road
Gombe

Telephone

+2347065485477

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Gombe State Apc Social Media Team posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Gombe State Apc Social Media Team:

Shortcuts

Share