GMM News

GMM News > 📰 GMM News – Sahihan Labarai, Wasanni & Shirye-Shiryen Gaskiya daga Arewa.
📞 08105870897 | 🌐 www

Majalisar wakilan Nijeriya ta bukaci kafa 'yan sandan jihohi domin mgance matsalar tsaroMajalisar wakilan Nijeriya ta bu...
02/06/2026

Majalisar wakilan Nijeriya ta bukaci kafa 'yan sandan jihohi domin mgance matsalar tsaro

Majalisar wakilan Nijeriya ta bukaci Gwamnatin Tarayya da hukumomin tsaro su kara kaimi wajen ceto dalibai da malamai da aka sace a jihohin Oyo da Borno, tare da sake jaddada bukatar kafa ’yan sandan jihohi domin magance matsalar tsaro da ke addabar Nijeriya.

Jaridar Premium Times, ta rawaito cewa majalisar ta faɗi haka ne bayan tattauna wasu kudurori biyu da s**a shafi sace-sacen dalibai da hare-haren da ake kai wa al’umma a sassan kasar nan.

Dan majalisar mai wakiltar mazabar Ogbomoso ta Arewa da Ogbomoso ta Kudu a jihar Oyo, Hon. Olamijuwonlo Alao-Akala, ya bayyana damuwarsa kan yadda hare-haren ’yan bindiga ke karuwa a yankunan Ogbomoso da Orire, yana mai cewa hakan ya zama babbar barazana ga rayuka da harkar ilimi.

HOTUNA: An gudanar da bikin ranar yara a garin Kafin Madaki dake ƙaramar hukumar Ganjuwa a jihar Bauchi A yau talata 2 g...
02/06/2026

HOTUNA: An gudanar da bikin ranar yara a garin Kafin Madaki dake ƙaramar hukumar Ganjuwa a jihar Bauchi

A yau talata 2 ga watan Janairun 2026 ɗaliban makarantun daban-daban na cikin garin Kafin Madaki s**a gudanar da bukukuwan ranar yara wato (Children Day), inda s**a gabatar da gasan Fareti, Tsere, Gudun Ƙori da sauransu.

02/06/2026

A jahar Kano Zamu kada Abba Kabir Yusuf kafun karfe 10 safe a zaben 20217

'Yan Majalisar Wakilai 13 Sun Sauya Sheka Bayan Komawa Daga HutuAkalla mambobi 13 na Majalisar Wakilan Najeriya sun sauy...
02/06/2026

'Yan Majalisar Wakilai 13 Sun Sauya Sheka Bayan Komawa Daga Hutu

Akalla mambobi 13 na Majalisar Wakilan Najeriya sun sauya sheka daga jam’iyyunsu zuwa wasu jam’iyyu daban-daban bayan majalisar ta dawo daga hutun da ta yi.

Sauya shekar tasu ya jawo ce-ce-ku-ce a fagen siyasa, yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen tunkarar zaɓen shekarar 2027.

Ana sa ran wannan mataki zai iya yin tasiri ga ƙarfin jam’iyyu da daidaiton siyasa a Majalisar Wakilai a watanni masu zuwa.

MALAMAI A BORNO NA GUDANAR DA ZANGA-ZANGA Kungiyar Malamai NUT a Jihar Borno na gudanar da Zanga-Zangar sace dalibai da ...
02/06/2026

MALAMAI A BORNO NA GUDANAR DA ZANGA-ZANGA

Kungiyar Malamai NUT a Jihar Borno na gudanar da Zanga-Zangar sace dalibai da malamansu.

Malaman sun Bukaci sakin daliban da ake tsare da su da malamansu, kana Gwamnati ta dauki mataki magance hakan.

BANKIN KA ALJIHUNKA: CBN Zai Rage Takardun Naira Dake Hannun Jama'a Zuwa Kasa Da Kashi 40 Cikin 100 Nan Da 2028Daga Asha...
02/06/2026

BANKIN KA ALJIHUNKA: CBN Zai Rage Takardun Naira Dake Hannun Jama'a Zuwa Kasa Da Kashi 40 Cikin 100 Nan Da 2028

Daga Ashafa Murnai Barkiya

Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Olayemi Cardoso, ya bayyana shirin rage yawan takardun kuɗaɗen da ake hadahada a hannun jama'a, daga kusan kashi 90 cikin 100 zuwa ƙasa da kashi 40 cikin 100 nan da shekarar 2028.

Wannan gagarumin shiri dai wani ɓangare ne na ƙoƙarin bunƙasa tattalin arziki ta tsarin hadahadar zamani, wato dijital na ƙasa da kuma ƙarfafa tasirin manufofin kuɗi.

Cardoso ya bayyana hakan ne a ranar Litinin a Abuja yayin ƙaddamar da Tsarin Biyan Kuɗi na Nijeriya 2028 (PSV 2028), wanda wata sabuwar manufa da aka tsara domin sabunta tsarin biyan kuɗi, faɗaɗa ƙasa haɗa jama’a cikin harkokin kuɗi, da kuma ƙarfafa amincewa da mu’amalolin dijital.

A taƙaice shiri domin ganin kusan kowane ɗan Nijeriya ya komawa tsarin hadahada ta asusun bankin sa kai-tsaye.

Sabon rahoton ƙididdigar kuɗi da lamuni na CBN dai ya tabbatar da cewa a yanzu haka kuɗin da ke yawo a hannun jama’a ya kai naira tiriliyan 5.65 a watan Afrilun 2026, yayin da naira tiriliyan 5.08 daga cikin wannan adadi ke wajen tsarin banki.

Wannan na nufin cewa kusan naira 90 daga cikin kowace naira 100 na takardun kuɗin da ke yawo a halin yanzu ba su shiga cikin bankuna.

Da yake nuna damuwa kan wannan yanayi, Cardoso ya ce CBN na da niyyar rage yawan kuɗaɗen da ke yawo a wajen hanyoyin kuɗi na hukuma cikin shekaru uku masu zuwa.

Ya ce, “Ina son ganin an rage kuɗaɗen da ke wajen tsarin banki zuwa ƙasa da kashi 40 cikin 100 na kuɗin da ke yawo a hannun jama’a.”

Gwamnan CBN ya bayyana cewa rage dogaro da kuɗin takarda zai taimaka wajen inganta tasirin manufofin kuɗi, ƙara gaskiya a harkokin kuɗi, da kuma saurin sauya Nijeriya zuwa tsarin biyan kuɗi na zamani mai inganci.

Haka kuma Cardoso ya nuna damuwar sa kan yadda har yanzu ake ci gaba da dogaro da kuɗin takarda duk da saurin bunƙasar hanyoyin biyan kuɗi na zamani a faɗin ƙasar nan.

Yayin da yake tun

02/06/2026

Saurara kaji🧏‍♂️

BREAKING NEWS: Retired Permanent Secretary of Gombe and Thousands of Followers Join PDP to Support Professor Isa Ali Pan...
01/06/2026

BREAKING NEWS: Retired Permanent Secretary of Gombe and Thousands of Followers Join PDP to Support Professor Isa Ali Pantami

The retired Permanent Secretary of Gombe State and traditional title holder of Katukan Kaltungo, Alhaji Daudu Yusuf, along with thousands of his supporters, have joined the People’s Democratic Party (PDP) to support Professor Isa Ali Ibrahim Pantami’s victory in the 2027 gubernatorial election.

During his PDP membership registration, he stated that he was part of the 2023 APC Governorship Campaign Council in Gombe State. He expressed optimism that Professor Pantami has demonstrated his capacity during his time as Director General of NITDA and Minister of Communications and Digital Economy of Nigeria. “Gombe needs him now more than ever,” he said.

Katukan Kaltungo is highly respected in Gombe State for his proven integrity and work experience as a former Permanent Secretary who trained many civil servants in the state.

The Pantamiyya Movement is bringing many people into the PDP through its activities and massive grassroots support.

Ɗan Majalissar Dokokin Kano Mai Wakiltar Mazaɓar Makoɗa, Muhammad Ahmad Tomas Ya Watsar Da Jam'iyyar NDC Ya Koma APCToma...
01/06/2026

Ɗan Majalissar Dokokin Kano Mai Wakiltar Mazaɓar Makoɗa, Muhammad Ahmad Tomas Ya Watsar Da Jam'iyyar NDC Ya Koma APC

Tomas ya sanar da komawarsa APC ne a ranar Litinin yayin wata ziyara da ya kai wa mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau Jibrin, a gidansa da ke Abuja, kamar yadda Dokin Ƙarfe TV ta ruwaito.

A wata sanarwa da ya fitar, Barau ya bayyana matakin a matsayin mai muhimmanci ga APC, yana mai cewa komawar ɗan majalisar za ta ƙara wa jam’iyyar ƙarfi a Kano ta Arewa da jihar Kano gaba ɗaya.

Amaechi bai da katabus a jam'iyyar ADC, sai abin da Atiku ya ce - Nyesom WikeMinistan Abuja, Nyesom Wike, ya ce tun fark...
01/06/2026

Amaechi bai da katabus a jam'iyyar ADC, sai abin da Atiku ya ce - Nyesom Wike

Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya ce tun farko ya san cewa tsohon gwamnan Rivers, Rotimi Amaechi, ba zai samu adalci ba a neman tikitin shugaban kasa na jam’iyyar a zaben 2027.

Da yake magana da manema labarai a Abuja, Wike ya bayyana tsarin shugabancin ADC a matsayin “tsarin Atiku kashi 100 bisa 100,” yana mai cewa hakan ya nuna tun daga farko cewa Amaechi ba shi da wata dama ta lashe tikitin jam’iyyar.

Address

Tumfure
Gombe

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when GMM News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share