GMM News

GMM News > 📰 GMM News – Sahihan Labarai, Wasanni & Shirye-Shiryen Gaskiya daga Arewa.
📞 08105870897 | 🌐 www

Ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar Labour Party (LP) a zaɓen 2023, Yusuf Datti Baba-Ahmed, ya ba...
03/07/2025

Ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar Labour Party (LP) a zaɓen 2023, Yusuf Datti Baba-Ahmed, ya bayyana cewa ƙalubalantar Bola Tinubu a 2027 ba zai kasance da sauƙi ba, ganin yadda duk manyan ‘yan adawa ke son tsayawa takara da kansu.

A cewarsa, “Kowa so yake ya tsaya takara – Peter Obi, Atiku da sauran fitattun ‘yan adawa. Idan ba a daidaita an tsaya da mutum guda ba, da wuya a kayar da Tinubu.”

Datti ya ƙara da cewa ya k**ata ‘yan adawa su yi koyi da Tinubu, wanda ya jure har Buhari ya kammala wa’adinsa kafin ya fito takarar shugabanci:

“Tinubu ya hakura lokacin Buhari, ya jira har ya gama, sannan ya fito. Idan muna so mu samu nasara, sai mun koyi dabarun haɗin kai da irin juriya.”

YANZI-YANZU: Rundunar ‘yan sandan jihar Gombe ta cika hannunta a ranar Talata da safe hadin guiwa da jami’an sintiri na ...
03/07/2025

YANZI-YANZU: Rundunar ‘yan sandan jihar Gombe ta cika hannunta a ranar Talata da safe hadin guiwa da jami’an sintiri na Operation Hattara da ke sintiri na yau da kullum sun dakile wani yunkurin kutsawa cikin shaguna a unguwar Buba Shongo da ke karamar hukumar Gombe a jihar Gombe.

K**ar yadda jami'in hulda da jama'a na 'yan sanda a jihar Gombe DSP Buhari Abdullahi ya tabbatar yace, a yayin sintiri, jami’an su sun hango wasu gungun ‘yan fashi da makami da ba a san ko su waye ba suna yunkurin shiga wani shago da karfi da yaji na wani mai suna Muhammadu Adamu Musa mai shekaru 42 a anguwar.

Gungun da s**a hango motar ‘yan sandan da ke sintiri ta nufo su, wadanda ake zargin sun tsere daga yunkirin da suke shirin yi, s**a gudu ta hanyoyi daban-daban.

Abubuwan da aka kwato a wurin sun hada da:
1. Babur Yamaha Baƙar fata guda ɗaya mai lamba GME 480 VN
2. Karfe guda daya
3. Silifan roba guda biyu

Dukkan abubuwan da aka kwato suna hannun 'yan sanda yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin hadin baki da yunkurin aikata laifi.

Indai za'a tuna cewa, Rundunar tace saboda karuwar laifukan da s**a shafi amfani da babura a cikin dare, yasa ta sanya dokar hana zirga-zirgar babur a cikin dare a fadin jihar.

Wannan lamarin da sauran mak**antan su sun kara tabbatar da wajabcin wannan hukunci, yayin da babura ke ci gaba da yin fice a wajen aikata tsarin ayyukan masu laifi.

Rundunar ‘yan sandan na son tabbatar wa da jama’a cewa, ana kokarin damke wadanda ake zargi da wannan yunkiri domin gurfanar da su a gaban kuliya.

Rundunar 'yan sandan jihar Gombe na cigaba da kira ga jama’a da su sanya ido tare da ci gaba da baiwa ‘yan sanda bayanan sirri don tabbatar da ci gaba da kare rayuka da dukiyoyi a jihar.

DA DUMI-DUMI: Rotimi Amaechi ya fice daga APC, Yace Najeriya ta lalace gaba dayaAmaechi wanda ya taba zama gwamnan jihar...
02/07/2025

DA DUMI-DUMI: Rotimi Amaechi ya fice daga APC, Yace Najeriya ta lalace gaba daya

Amaechi wanda ya taba zama gwamnan jihar Ribas, ya kuma zargi jam’iyyar APC mai mulki da kuma hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC da hada baki wajen sace zabukan kasar da ke tafe A 2027.

DA DUMI-DUMI: Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe Ta K**a Wani  Matashi Da Zargin Mallakar Jabun Daloli A Yamaltu-DebaRundu...
02/07/2025

DA DUMI-DUMI: Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe Ta K**a Wani Matashi Da Zargin Mallakar Jabun Daloli A Yamaltu-Deba

Rundunar ‘yan sandan jihar Gombe karkashin jagorancin Kwamishinan ‘Yan Sanda CP Bello Yahaya, psc(+), ta samu nasarar k**a wani mutum bisa zargin hada baki da kuma mallakar kuɗin jabun Dalar Amurka.

Rahoton ya bayyana cewa a ranar Asabar, 28 ga Yuni, 2025, da misalin karfe 10:04 na safe, jami’an ‘yan sanda da ke aiki a sashin tsaro na Filin Jirgin Sama na Lawanti yayin gudanar da ayyukansu na sa-ido, sun k**a wani mutum mai suna Usman Kawu, ɗan shekaru 35, a kauyen Kuji Kwadon, da ke cikin karamar hukumar Yamaltu-Deba, jihar Gombe.

Abubuwan Da Aka Gano

A cewar bayanan ‘yan sanda, an k**a wanda ake zargin da jabun takardun kuɗi na Dalar Amurka guda goma (10), kowanne mai darajar $100, wanda jimillar su ya kai $1,000. Ana zargin ya yi niyyar amfani da kuɗin wajen yaudarar jama’ar gari.

Binciken farko ya bayyana cewa idan an canza jabun kuɗin zuwa kuɗin Najeriya, zai kai kusan ₦1,500,000 (Naira miliyan daya da dubu dari biyar). Haka kuma, an gano wani adadin ₦10,000 a matsayin kuɗin Najeriya a boye cikin gajeren wandonsa na ciki.

Bayanin Wanda Ake Zargi

A lokacin tambayarsa, Usman Kawu ya amsa cewa ya san da kudin jabun, amma ya bayyana cewa wani ne ya bashi domin gudanar da kasuwanci. Sai dai har yanzu rundunar ‘yan sanda na ci gaba da bincike domin gano asalin wanda ya ba shi kudin, tare da bankado duk wata alaka da wasu rukuni ko gungu da ke safarar jabun kuɗi a cikin ƙasa.

Sanarwa Daga Rundunar

Rundunar ‘yan sandan jihar Gombe ta bayyana cewa bincike na ci gaba, kuma za a sanar da al’umma sak**akon binciken a nan gaba.

Shekarar 2025 ta raba tsakiya inda tuni aka shafe watanni 6 daga cikin 12 na cikintaCikin burinkanku, wane kuka cimma ka...
01/07/2025

Shekarar 2025 ta raba tsakiya inda tuni aka shafe watanni 6 daga cikin 12 na cikinta

Cikin burinkanku, wane kuka cimma kawo yanzu, wadanne kuma s**a rage?

Zan tsaya takarar shugaban kasa a 2027 – Peter ObiDan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party a zaben 2023, Pete...
01/07/2025

Zan tsaya takarar shugaban kasa a 2027 – Peter Obi

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party a zaben 2023, Peter Obi, ya tabbatar wa magoya bayansa cewa zai tsaya takarar shugaban kasa a zaben shekarar 2027, kuma ba zai yi fiye da wa’adi guda ba idan ya ci zabe.

Mista Obi ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Peter Obi Media Reports, Ibrahim Umar, ya fitar a ranar Litinin a Abuja.

Tsohon dan takarar shugaban kasar ya tabbatar da cewa yana cikin tattaunawar kafa kawancen jam’iyyu, yana mai cewa burinsa shi ne ceton Najeriya daga halin da ta tsinci kanta.

“Ban taba shiga wata tattaunawa kan hadin gwiwar tikitin takara da kowa ba, har da Atiku,” inji shi.

“Idan za a samu wata yarjejeniya da za ta takaita wa’adin mulkina zuwa shekaru hudu, zan yarda da ita, kuma zan bar ofis ranar 28 ga Mayu, 2031.

“Idan kawancen ba ya magana ne kan dakatar da kashe-kashen da ake yi a Benue da Zamfara, dawo da tattalin arzikinmu, farfado da masana’antunmu, da ciyar da ‘yan Najeriya, to ku cire ni a ciki,” inji shi.

Obi ya yi alkawarin kawo kwanciyar hankali a kasar nan cikin shekaru biyu da fara mulkinsa.

Dangane da halin da jam’iyyar Labour Party ke ciki, Obi ya ce suna aiki tukuru domin samun sahalewar INEC ga shugabancin Nenadi Usman bisa hukuncin Kotun Koli.

A Senegal ana can ana cigaba da gudanar da gasar sarauniyar kyau ta Tumaki, kawo yanzu dai ba'akai ga fidda wacce tafi k...
01/07/2025

A Senegal ana can ana cigaba da gudanar da gasar sarauniyar kyau ta Tumaki, kawo yanzu dai ba'akai ga fidda wacce tafi kowacce kyau ba.

Tsohon Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, tare da Attajiri Alhaji Aliko Dangote a Madina, yayin da ake dakon gudanar ...
01/07/2025

Tsohon Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, tare da Attajiri Alhaji Aliko Dangote a Madina, yayin da ake dakon gudanar da jana'izar Marigayi Alhaji Aminu Dantata.

Kamfanin NNPC ya ce ribarsa ta karu da kashi 40% zuwa N1.05 tiriliyan a watan MayuKamfanin Man Fetur na Kasa, wato NNPC,...
01/07/2025

Kamfanin NNPC ya ce ribarsa ta karu da kashi 40% zuwa N1.05 tiriliyan a watan Mayu

Kamfanin Man Fetur na Kasa, wato NNPC, ya bayyana cewa ya samu riba bayan biyan haraji har Naira tiriliyan 1.05 a watan Mayu 2025.

A cikin sabon rahotonsa, kamfanin ya ce wannan adadi ya karu da kashi 40.37 cikin dari daga Naira biliyan 748 da aka samu a watan Afrilu.

Kamfanin ya kuma bayyana cewa ya samu kudaden shiga har Naira tiriliyan 6 a cikin lokacin, wanda hakan ke nuna karuwar kashi 1.87 cikin dari daga Naira tiriliyan 5.89.

PRESS RELEASEGOMBE STATE POLICE COMMAND01/07/2025PUBLIC SAFETY ADVISORY ON DROWNING INCIDENTS: CAUTION AND PREVENTIVE TI...
01/07/2025

PRESS RELEASE
GOMBE STATE POLICE COMMAND
01/07/2025

PUBLIC SAFETY ADVISORY ON DROWNING INCIDENTS: CAUTION AND PREVENTIVE TIPS

The Gombe State Police Command wishes to alert and sensitize members of the public on the need for heightened caution and vigilance around water bodies, particularly during the rainy season, as cases of accidental drowning continue to pose a serious public safety concern.

Recently, the command recorded four (4) incidents at various parts of the state namely; Hayin kwarin-Misau Akko LGA, Bojude Kwami LGA, Bajoga Funakaye LGA and Difa Yamaltu Deba LGA, involving individuals, especially children and young persons, who have drowned in rivers, erosion sites, and unprotected water channels.

In view of this, the Command urges the public to adhere to the following safety guidelines to prevent avoidable loss of lives:
1. Avoid Swimming in Open or Unregulated Water Bodies; Rivers and erosion channels are not safe for swimming, especially during heavy rainfall when water currents may be unpredictable.

2. Monitor Children at All Times; Parents, guardians and School administrators are strongly advised to keep close watch over their children and students and prevent them from going outdoor while raining or wandering near water bodies.

3. Ensure Installation of Warning Signs and Fencing; Communities are encouraged to erect clear warning signs and barricades around dangerous water sites to deter public access.

4. Avoid Flooded Areas; Do not attempt to walk, drive, or swim through flooded zones as the depth and strength of the water may be misleading.

5. Report Suspicious or Dangerous Water Hazards; Members of the public are advised to report any uncovered or dangerous erosion sites or drainage channels to local authority or those responsible for prompt action.

The Gombe State Police Command remains committed to safeguarding the lives and property of residents and calls on all stakeholders, community leaders, and caregivers to play an active role in

Garkuwa da mutane: Matasa sun ƙone fadar sarki da ofishin hukumar NDLEA a KwaraWasu fusatattun matasa a garin Lafiagi, h...
01/07/2025

Garkuwa da mutane: Matasa sun ƙone fadar sarki da ofishin hukumar NDLEA a Kwara

Wasu fusatattun matasa a garin Lafiagi, hedikwatar karamar hukumar Edu da ke Jihar Kwara, sun kai farmaki ranar Litinin zuwa Fadar Sarkinsu, wato Sarkin Lafiagi, da kuma Ofishin Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi (NDLEA), inda s**a cinna musu wuta sak**akon yawaitar sace-sacen mutane da ke faruwa a yankin ba tare da dakilewa ba.

Tashin hankali ya mamaye al’ummar Lafiagi a ranar Litinin, lamarin da ya haifar da zanga-zangar matasa domin bayyana fushinsu kan sace wani sanannen ɗan kasuwa a yankin.

Fusatattun matasan sun fara zanga-zangar ne da safiyar jiya Litinin kan sabon lamarin sace mutum, inda s**a toshe hanyoyi, s**a kunna tayoyi da s**a ƙone, tare da neman gaggawar ɗaukar matakin gwamnatin jihar kafin daga bisani su bankawa Fadar Sarkin da ofishin NDLEA wuta.

A wani faifan bidiyo da ya yadu, masu zanga-zangar sun ambaci sace wani matashi da ke aikin kasuwancin POS a matsayin karin hujja da ke nuna tabarbarewar tsaro a yankin.

Wasu mazauna Lafiagi sun shaida wa Vanguard cewa an sace Alhaji Chemical ne daga gidansa da ke unguwar Taiwo da misalin karfe 1:00 na dare, inda wasu da ake zargin 'yan bindiga ne s**a mamaye yankin.

Da aka tuntube shi, Kwamishinan ‘Yansanda na Jihar Kwara, Mista Adekimi Ojo, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa yana cikin garin Lafiagi ranar Litinin tare da Kwamandan Rundunar Sojoji ta 22 da ke Sobi, Ilorin. Ya bayyana cewa wasu bata-gari ne s**a shirya zanga-zangar inda s**a lalata wasu gilashin Fadar Sarkin sannan s**a ƙone ofishin NDLEA.

Address

Gombe

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when GMM News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share