Sheik abulfathi sani attijjani page

Sheik abulfathi sani attijjani page Domin kawo karatuttukan malaman dariqa da iliman tarwa gamida sanin Labarai na tijjaniyya dake faruwa
(1)

YANZU YANZU: Karku Sake Kiran 'yan Izala da Ahlussunah, domin su ba Ahlu Sunnah bane, Dan Uwansu yayi Batanci ga Manzon ...
10/10/2025

YANZU YANZU: Karku Sake Kiran 'yan Izala da Ahlussunah, domin su ba Ahlu Sunnah bane,

Dan Uwansu yayi Batanci ga Manzon Allah SAW, Amma sun Rufe ido sunce suna tare dashi,

Abun Kunya da Naga video Shugabansu Yana Ikirarin Wai Suna Tare da shi.

Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Usman Bauchi RTA

Daga Sharhin wasu matasa a Jihar Gombe s**ace an sake samun sabbin Sheikh Abulfathi Gombe Imam Junaidu Gombe Sheikh Nasi...
10/10/2025

Daga Sharhin wasu matasa a Jihar Gombe s**ace an sake samun sabbin

Sheikh Abulfathi Gombe
Imam Junaidu Gombe
Sheikh Nasir Gombe

Duk wannan yunquri ne na kauda sharrin wahabiyawa a qasar nan wadan da basa ganin girma ko darajar ma'aiki S.A.W

Allah ya qara kare mana Masoyin mu S.A.W

ABUN BURGEWA: Khadiml Faidha Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Usman Bauchi RTA, Ya Samarwa Mutum 140 Scholarship Zuwa ƙasar ...
09/10/2025

ABUN BURGEWA: Khadiml Faidha Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Usman Bauchi RTA, Ya Samarwa Mutum 140 Scholarship Zuwa ƙasar Algeria.

Faɗa da cikawa sai khadimul faidat general, wato sheikh Alhaji Ibrahim Sheikh Dahiru Usman RTA .

ajiyane su nayen wasu daga cikin Daliban da khadimul faidat Sheikh Alhaji ibrahim Sheikh Dahiru Usman Bauchi RTA ya nema wa Scholarship na karatu zuwa ƙasar algeriya 🇩🇿 su 140 ya fito wan da inshallah cikin wan nan watan 10/2025 zasu wuce kasar algeriya.

kuma wan nan karatu zasuyi shime tundaga matakin DEGREE, MASTERS, PHD , ya danganta da karatune, duk irin kwas ɗin da Dalibi zai yi to shi zai karnata.

ashe karun baya an kai wasu ɗaliban wamda alhamdulillah wasu har sun kammala mastaer digree ɗinsu acan,

san nan wa ɗan nan yaran an ɗebesu daga zawiyoyi da ban da ban ma fadin kasar nan, san nan kuka muna sa ran fitowar na ragiwar yaran insha Allah.

Insha Allah zamu cigaba da kawo muku dukkan wasu lamura na wan nan tafiyar yaran har zuwa ƙasar algeria da kuma makarantun da yaran nan zasuyi karatu.

aƙarshe muna ƙara addu'a zuwaga mai girma khadimul faidat general Sheikh Alhaji ibrahim shek dahir usman bauchi RTA Allah ya ƙara jama na kwanan shi, allah kuma ya tsare mana shi daga dukkan abin halitta na fili da na ɓoye.

📝sing
alhafiz sadiq mi
khadimul faidat media term
niger state chapter.

©️ Abubakar Ayisalaty

09/10/2025

Maulidi Kai tsaye daga Zawiyar Sheikh Gonimi

WATA SABUWA: Muhammadu dan Abdul Wahabu, Baita6a Baiti 2 don Yabon Annabi Muhammadu SAW ba.Misali ace: yayi yabon Annabi...
08/10/2025

WATA SABUWA: Muhammadu dan Abdul Wahabu, Baita6a Baiti 2 don Yabon Annabi Muhammadu SAW ba.

Misali ace: yayi yabon Annabi SAW Saboda Annabi ya burgeshi, bai ta6a yi ba.

Dr. Haris Salihu Jos

Gayyatar Taron Zikirin Juma’a da aka Saba Gudanarrwa duk Shekara a Jihar Zamfara
08/10/2025

Gayyatar Taron Zikirin Juma’a da aka Saba Gudanarrwa duk Shekara a Jihar Zamfara

07/10/2025

MUHADARA mai taken:
" KARE MARTABA DA DARAJAN MA'AIKI صلى الله عليه وآله وسلم

SHIRYAWA: Lajnatus Sab'ah, Gombe.

MALAMAI:

Sayyadi Shafi'u Sheikh Saleh Danaje
Hafiz Modibbo Sheikh Adamu Chilo
Hafiz Auwal Modibbo Sule

07/10/2025

SAKON YAN FAIRAR SHEHU RTA ZUWA GA MUTANEN DUNIYA

Dr. Atiku Sheikh Balarabe Zawiyya Gusau

CIKIN HOTUNA: Yadda Aka Gudanar da Sallar Jana'izar Babban Malamin Addinin Musulunci Sheikh Dokta Ahmad Umar Hashim, yau...
07/10/2025

CIKIN HOTUNA: Yadda Aka Gudanar da Sallar Jana'izar Babban Malamin Addinin Musulunci Sheikh Dokta Ahmad Umar Hashim, yau Talata 07/10/2025

HANYAR SHEIKH YAHYA MASASSUKA. A hakikanin gaskiya, ya wajaba  a gare mu musamman mabiya darikun Sufaye musamman darikar...
07/10/2025

HANYAR SHEIKH YAHYA MASASSUKA.

A hakikanin gaskiya, ya wajaba a gare mu musamman mabiya darikun Sufaye musamman darikar Tijjaniyya, Mu farka a kan wannan lamarin mu dawo cikin hayyacinmu kada mu manta da manhajin da Shehu Tijjani ya doramu da shi da babban Halifansa Shehul Islam Alhaji Ibrahim Niass Allah ya kara musu yarda..

Akwai wani lamari mai tayar da hankali a zamanin nan: Shugaban wata da’awa mai taken Alƙur'ani zalla da ake kira Sheikh Yahya Masuss**a ya zama abin kwaikwayo da kafa hujja da shi ga wasu ba'ari na biyan buƙatar wasu daga cikinmu. Da yawa daga cikinmu mabiya ɗariƙa muna murna da shi saboda yana tsananta wa ‘yan Izala/Wahabiyya, muna ganin tamkar yana kare mutuncinmu. Wannan ra’ayin kuskure ne.

"Mai hankali ba ya rungumar kuskure saboda ya ga yana cutar da abokin adawarsa; domin kuskuren nan zai dawo ya cutar da shi da kansa."

~Hikimar Malaman Sufaye)

1. Matsalar Da’awar Masuss**a

Da’awar da Masus**a yake yadawa tana da hatsari sosai, ba iya ga ‘yan Izala kadai ba, har ma ga mabiya Sufaye. Tabbas Ya kauce daga tafarkin Annabi yana yaki da kalaman da suke sabawa ilimin Ahlus-Sunnah wal-Jama’ah.

Babban hatsarin da ke tattare da da’awarsa shi ne:Yana wulakanta ko ƙaryata wasu daga cikin hadisai da a ka tabbatar da ingancinsu. Ko kuma karyata hadisai dukka. Amman na ga wani gajaren bidiyo da yake cewa karyata hadisain sunfi ga nauin guda uku Hadisin da ya taɓa darajar Annabi da kuma hadisin da ya karyata ayar Alƙur'ani, da kuma hadisin da yake koya ta'addanci.

Idan karyata hadisin iya haka ya tsaya muma a kan wannan Layin muke domin ba ma bukatar duk hadisin da yake munana ladabi ga Annabi ko kuma yake cin karo da ayoyin Alƙur'ani da hadisin da karara yake koya ta'addanci duk da bana tunanin tun asalin ma akwai irin wadanna Hadisan..

Ina ganin tafiyar Masass**a tana k**a da irin fikirar irin wadanda suke kafa sabuwar da'awa suke da ita duk da tsohuwar da'awa ce amman tasa tafi daukar hankali fiye da sauran wadanda s**a gabace shi sai ya nake ganinta k**ar ta fito a matsayin sabuwar fikira ko sabuwar da'awa.

1. ASALIN SABON MANHAJI DA DALILANSA

Masu kirkirar da’awa galibi ba sa fitowa don neman gaskiya, sai dai saboda wasu kwakwara dalilai k**ar:

1. Sha’awar iko da mulki:
Suna neman rinjayar jama’a domin mallake zukata dan neman kuɗi da shugabanci.

2. Rashin ilimi da zurfin fahimtar addini:
Jahilci kan kai mutum ya ɗauka cewa yana gyara addini.

3. Hassada da kyashi:
Wasu s**an tashi domin rusa mutuncin malamai da jagororin da jama’a ke bi.

4. Zuga ta siyasa ko bukatar duniya:
Sau da yawa ana yin amfani da addini domin cika wasu manufofin siyasa.

Wannan yanayi ya kasance tun zamanin farko bayan Annabi, k**ar yadda aka gani wajen Musailamah al-Kadhdhab da wasu ƙungiyoyin irin nasa.

2. HANYOYIN DA SUKE BI WAJEN WAWANTAR DA JAMA’A

Akwai dabaru da s**a kusan zama gama-gari a duk lokacin da aka tashi kirkirar sabuwar da’awa:

Ruguza amincin malamai da tsarin da ake bi

i) Suna fara bayyana cewa malamai da shugabannin addini sun ɓace ko suna amfani da addini ne domin neman kudi.
Da wannan, jama’a suke fara ƙyamatar malamai su rabu da su.

ii) Kirkirar matsala ta ƙarya

Suna fakewa da cewa akwai wata babbar illa a cikin tafarkin da aka gada, wadda su za su gyara. Suna amfani da kalmomi irin su: “Ku dawo zuwa ga asali” ko “Addinin da kuke bi an gurbata shi”.

iii) Sake fasalta tarihi da nassosi

Suna rage darajar malamai da sahabbai ta hanyar zaben nassosi da suke taya kafa akidar domin su taya su zama hujja, ko ƙaryata sahihan hadisai da tafsirin malaman baya.

iv) Ƙarfafa kai da kiran juyin juya hali

Suna ɗaga kansu zuwa matsayin tsarkaka.
Suna cewa su ne masu ceton al’umma, s**an kira sauran musulmi da ƴan bidi’a ko jahilai.

v) Amfani da dabarun motsa zuciya (psychological manipulation)

Yin wa’azi mai motsa, matasa da kuma kawo zargi. Tsoratar da jama’a da cewa idan ba a bi su ba za a hallaka. Yin amfani da harshen da yake ƙone zuciya.

3. MATSAYIN SHEHU TIJJANI ABUL ABBAS A KAN DA'AWAR IRIN SU MASASSUKA.

Shehu Tijjani ya yi tsayayyen gargadi game da kowane irin harshe da ya ke rage darajar Annabi Sallalahu alaihi wa Salam
Ya ce:

“Duk wanda ya rage girmar Annabi da magana ko da’awa, Allah zai toshe masa hanyoyin alheri kuma ya ruguza abin da yake nema.”
(Jawāhir al-Ma’ānī, Babi na farko)

Shehu Tijjani ya karanta dukkan wadannan littattafan na Hadisi a kansu ya ginu kuma a kansu ya kafa darikarmu ta Tijjaniyya.

4. Tasirin Irin Wannan da'awar ta su Musass**a a kan al'ummarmu

1. Ruguza amincewa da malamai da gadon tafarkinsu – jama’a su bar tushen shari’a.

2. Rarrabuwar kai da tashin hankali – mabiyan sabon manhaji su yi adawa da sauran musulmi.

3. Sauke darajar Annabi a zukatan mutane – su daina girmama sunnah da ibadu.

4. Rashin zaman lafiya da fitina a al’umma – tashin hankali da rikice-rikice.

Al’ummar Musulmi, musamman mabiya ɗariƙa, su tsare kansu daga bin kowane harshe da ya kauce daga wannan tafarki, su tsaya a kan girmama Annabi da jagorancin malamai na gaskiya.

Ku jira yi Massus**a idan ya yiwa Wahabiyya ritaya dole lallai kanmu zai fado.

Mujaheed M Muh'd
07/10/2025

YANZU YANZU: Babban Malamin Addinin Musulunci Sheikh Dokta Ahmad Umar Hashim, Allah Yayi Masa RasuwaCikakken Tarihin Dr....
07/10/2025

YANZU YANZU: Babban Malamin Addinin Musulunci Sheikh Dokta Ahmad Umar Hashim, Allah Yayi Masa Rasuwa

Cikakken Tarihin Dr. Ahmad Omar Hashim (1941 – 2025)

--- Asalin Rayuwa

An haifi Dr. Ahmad Omar Hashim a shekara ta 1941 a ƙauyen Bani Amer, garin Zagazig, a yankin Sharqiyyah, ƙasar Masar (Egypt).

Ya tashi cikin gida mai tsananin kishin addini, inda ya haddace Al-Qur’ān tun yana ƙarami.

--- Ilimi da Karatu

Ya karanci Shari’a da Hadisi a Jami’ar Al-Azhar, cibiyar da ta fi tsufa kuma mafi daraja a ilimin addinin Musulunci.

Ya sami digiri na farko (B.A.) a fannin Hadisi a 1967, digirin Masters a 1969, sannan digirin PhD a 1973.

Ya zama malami (Professor) a fannin Hadisi da Ulum al-Hadith a shekarar 1983.

--- Ayyuka da Muk**ai

Shugaban Jami’ar Al-Azhar daga 1995 zuwa 2003 — inda ya taimaka wajen buɗe sababbin cibiyoyi na nazarin Hadisi da Tafsiri.

Memba na Majalisar Manyan Malamai (Majma’ al-Kibar al-Ulama) ta Al-Azhar.

Memba a Majalisar Wakilai (Egyptian Parliament), inda ya kare darajar malamai da tsarin addini a cikin dokokin ƙasa.

Shugaban Majalisar Malamai ta Duniya don Ginin Zaman Lafiya da Taimakon Addinai.

Ya wakilci Al-Azhar a tarurruka da dama a duniya — Saudiyya, Pakistan, Indonesia, Morocco, Sudan, da sauran ƙasashe.

--- Littattafai Masu Tasiri da Rubuce-Rubuce

Dr. Ahmad Omar Hashim ya rubuta fiye da littattafai 40 da s**a shafi Hadisi, Akida, Da’awah, da Harshe. Ga wasu daga cikin shahararrun ayyukansa:

1. “Nūr min Sunnat al-Nabī ﷺ” – Hasken daga Sunnan Annabi.

2. “Al-Tarbiyyah al-Rūhiyyah fī al-Islām” – Tarbiyyar Ruhaniya a Musulunci.

3. “Al-Islām wa al-Da’wah al-Hadīthah” – Addinin Musulunci da Da’awah a zamani.

4. “Al-Sabr wa Fadhluh” – Juriya da falalarsa.

5. “Al-Hadīth Nabawiyy wa ‘Ulūmuh” – Nazarin Hadisi da ka’idojinsa.

6. “Al-Tasamuh fī al-Islām” – Haƙuri da fahimtar juna a Musulunci.

--- Gudummawarsa ga Al-Ummah

Ya yi wa’azi a gidajen talabijin da radiyo na Masar fiye da shekaru 40.

An san shi da murya mai nutsuwa da hikima wajen bayyana Hadisi da fassarar Sunnah.

Ya taka rawa wajen ƙarfafa haɗin kai tsakanin mazhabobi da yaki da tsatsauran ra’ayi.

A 2023, an ba shi lambar yabo ta “Islamic Personality of the Year” a Dubai International Holy Qur’an Award, saboda irin gudummawarsa ga addini da ilimi.

--- Rasuwa

Ya rasu a ranar 6 ga Oktoba, 2025 (2 Rabīʿ al-Thānī, 1447 AH).

An yi masa Sallar Jana’iza a Al-Azhar Mosque, inda dubban mutane s**a halarta daga sassa daban-daban na duniya.

Ana fatan Allah Ya ba shi Al-Jannah al-Firdaws, tare da Annabi Muhammad ﷺ da Salihin.

--- Maganarsa ta Ƙarshe da aka fi tunawa da ita:

> “Manzon Allah ﷺ ya bar mana hanyar gaskiya. Duk wanda ya bi ta da sadaukarwa, Allah zai haskaka rayuwarsa da ilimi da imani.”

©️ Abubakar Ayisalaty

Address

Gombe State Ng West Africa Hausa
Gombe
+234810 825 6575

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sheik abulfathi sani attijjani page posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Sheik abulfathi sani attijjani page:

Share