27/07/2026
Ko Saudiyya za ta iya mallakar makamin nukiliya bayan yarjejeniya da Amurka? Amurka da Saudiyya sun rattaba hannu kan wata muhimmiyar yarjejeniya wadda rahotanni ke cewa za ta iya bai wa masarautar Saudiyya damar tace sinadarin uranium a cikin gida.
A cewar Ma'aikatar Mak**ashi ta Amurka, yarjejeniyar wadda aka bayyana a matsayin 'yarjejeniyar haɗin gwiwa kan mak**ashin nukiliya domin zaman lafiya za ta ba kamfanonin Amurka damar shiga da kuma taka muhimmiyar rawa a shirin mak**ashin nukiliya na Saudiyya."
A karkashin yarjejeniyar, Saudiyya za ta bunƙasa shirinta na mak**ashin nukiliya, sai dai har yanzu ba a bayyana abin da yarjejeniyar ta kunsa ga jama'a ba.
Ana iya amfani da uranium da aka tace a matsayin mak**ashi wajen tafiyar da tashoshin samar da wutar lantarki na da kuma wajen ƙera bama-baman nukiliya.
Masana sun ce akwai fargabar cewa yarjejeniyar na iya haifar da yaɗuwar fasahar nukiliya a nan gaba a yankin da tuni ke fama da rashin kwanciyar hankali.
Amurka da Isra'ila sun ce daya daga cikin dalilan da s**a sa s**a kai hari kan Iran shi ne domin hana ta samun damar kera makamin nukiliya a nan gaba.
Sai dai Iran ta musanta cewa tana da wani shiri na samar da irin wannan makami, tana mai cewa shirinta na nukiliya an tsara shi ne domin amfani da mak**ashin zaman lafiya.
Batun mak**ashin nukiliya ya kasance a tsakiyar rikicin da ya dauki watanni Amurka da Isra'ila na yi da Iran.