AREWA A YAU

AREWA A YAU Journalism at its finest. We bring you the best situation report.

Ko Saudiyya za ta iya mallakar makamin nukiliya bayan yarjejeniya da Amurka? Amurka da Saudiyya sun rattaba hannu kan wa...
27/07/2026

Ko Saudiyya za ta iya mallakar makamin nukiliya bayan yarjejeniya da Amurka? Amurka da Saudiyya sun rattaba hannu kan wata muhimmiyar yarjejeniya wadda rahotanni ke cewa za ta iya bai wa masarautar Saudiyya damar tace sinadarin uranium a cikin gida.

A cewar Ma'aikatar Mak**ashi ta Amurka, yarjejeniyar wadda aka bayyana a matsayin 'yarjejeniyar haɗin gwiwa kan mak**ashin nukiliya domin zaman lafiya za ta ba kamfanonin Amurka damar shiga da kuma taka muhimmiyar rawa a shirin mak**ashin nukiliya na Saudiyya."

A karkashin yarjejeniyar, Saudiyya za ta bunƙasa shirinta na mak**ashin nukiliya, sai dai har yanzu ba a bayyana abin da yarjejeniyar ta kunsa ga jama'a ba.

Ana iya amfani da uranium da aka tace a matsayin mak**ashi wajen tafiyar da tashoshin samar da wutar lantarki na da kuma wajen ƙera bama-baman nukiliya.

Masana sun ce akwai fargabar cewa yarjejeniyar na iya haifar da yaɗuwar fasahar nukiliya a nan gaba a yankin da tuni ke fama da rashin kwanciyar hankali.

Amurka da Isra'ila sun ce daya daga cikin dalilan da s**a sa s**a kai hari kan Iran shi ne domin hana ta samun damar kera makamin nukiliya a nan gaba.

Sai dai Iran ta musanta cewa tana da wani shiri na samar da irin wannan makami, tana mai cewa shirinta na nukiliya an tsara shi ne domin amfani da mak**ashin zaman lafiya.

Batun mak**ashin nukiliya ya kasance a tsakiyar rikicin da ya dauki watanni Amurka da Isra'ila na yi da Iran.

Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta na Operation FANSAN YAMMA sun ceto mutum 48 da aka yi garkuwa da su bayan da s**...
26/07/2026

Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta na Operation FANSAN YAMMA sun ceto mutum 48 da aka yi garkuwa da su bayan da s**a kai ɗauki cikin gaggawa sak**akon harin da wasu da ake zargin ’yan ta’adda s**a kai.

Ƴan ta'addan sun kai harin ne a ƙauyen Magami da ke ƙaramar hukumar Kaura Namoda a Jihar Zamfara da sanyin safiyar ranar 26 ga Yulin 2026.

Sai dai mutum ɗaya ya rasa mutu a harin, yayin da wasu mutum biyu s**a samu raunukan harbin bindiga, inda aka kai su asibitin ƙwararru na Kaura Namoda domin samun kulawar likitoci.

A cikin sanarwa da rundunar ta fitar, ta ce sojojin sun samu kiran neman taimako ne bayan wasu mahara masu yawa da ke kan babura 40 s**a mamaye ƙauyen, inda s**a tattara mazauna yankin da nufin tafiya da su cikin daji.

A yayin da sojojin s**a isa wurin, s**a fafata da maharan, lamarin da ya tilasta wa ’yan bindigar yin watsi da mutanen da s**a sace tare da tserewa zuwa cikin daji domin tsira da rayukansu.

Rundunar ta ce wannan mataki ya ba da damar kuɓutar da dukkan mutum 48 da aka yi garkuwa da su.

Ta kuma ƙara da cewa sojojin sun ci gaba da sintiri a yankin domin hana sake aukuwar mak**ancin wannan hari da kuma tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma.

NAFDAC Ta Tsaya Kan Hana Sayar da Giya a Cikin Saches, Ta Ce Manufofi Har Yanzu Na AikiHukumar Kula da Abinci da Magungu...
26/07/2026

NAFDAC Ta Tsaya Kan Hana Sayar da Giya a Cikin Saches, Ta Ce Manufofi Har Yanzu Na Aiki
Hukumar Kula da Abinci da Magunguna ta Kasa (NAFDAC) ta sake tabbatar da cewa har yanzu tahana sayar da giya a cikin saches da kuma kwantena ƙanana fiye da 200ml yana nan daram.
Daraktan-na Kasa, Farfesa Mojisola Adeyeye, ta ce hukumar ba ta taɓa ɗaga wannan haramcin ba, inda ta jaddada cewa duk wannan don kare lafiyar jama'a da kuma rage yawaitar shan giya, musamman a tsakanin matasa. Haka zalika ta ce NAFDAC za ta sake tunani kan wannan doka ne kawai idan an umurce ta ta hanyar da ta dace na shari'a ko dokoki.
Haka kuma, NAFDAC kwanan nan ta yi wasu gargadi ga 'yan Najeriya kan yiwuwar magunguna na karya da kayayyakin da ba a yi rijista da su ba a kasuwa, tana ba da shawarar mutane su saya daga wuraren da s**a yarda da su kawai kuma su bayar da rahoto idan sun ga wani abu da ya yi k**a da shakka.

26/07/2026

Anyi kiraga makiyaya da manoma dasu hadakai domin kaucema rigingimu dake haddasa asaran Rayuka da Dukiya. dasu sani zaman lafiya shine ginshigin cigaba, acewar Hon.Ibrahim Buba Mak**a shugaban karamar hukumar kwami ajihar Gombe. yace duk wanda aka k**a da yunkurin tada Hankali zai fuskanchi fushin hukuma.

26/07/2026

AREWA MUFARKA

18/07/2026

MUNA

Address

Madaki Street
Gombe

Telephone

+2347053480165

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AREWA A YAU posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to AREWA A YAU:

Shortcuts

Share