AREWA A YAU

AREWA A YAU Journalism at its finest. We bring you the best situation report.

02/05/2026

MALAM MUHAMMADU NA NEMAN TAI MAKO DAGA BAYIN ALLAH

01/05/2026

ANA SAMU KARUWANCHI A KASAR GANA KAFIN ABAMU ABINCHI.YAN'NIGERIA DA AKA CHETO

APC A YOBE TA AYYANA BABA MALUM WALI AMATSAYIN DANTAKARAR TA 2027daga Ahmad mai Baru
30/04/2026

APC A YOBE TA AYYANA BABA MALUM WALI AMATSAYIN DANTAKARAR TA 2027
daga Ahmad mai Baru

Tarihin Baba Malum Wali (BMW), Gwamnan Yobe Mai jiran gado da yardar Allah. Baba Malum Wali mni shine sakataren Gwamnati...
30/04/2026

Tarihin Baba Malum Wali (BMW), Gwamnan Yobe Mai jiran gado da yardar Allah.

Baba Malum Wali mni shine sakataren Gwamnatin Jihar Yobe kuma jajirceccen ma'aikacin Gwamnati wanda yake aiki da ilimi; yake aiki da tsari; yake aiki da ƙa'ida; aiki domin cigaban al'uma; aiki domin haɓɓakan tattalin arziki da wanzuwar zaman lafiya mai ɗorewa a Jihar mu ta Yobe mai albarka.

Baba Malum Wali a fara aikin Gwamnati a shekarar 1982 (shekaru 42 da s**a wuce), ya samu horaswa a aikin Gwamnati cikin tsari, ilimi da bin ka'ida a wajen masana da turawa na hukumar Chad Basin Development Authority da NEAZDP.

An haife shi a ranar 25 na watan Disamba a shekarar 1958 a garin Nguru (garin Allah). Yayi makarantar firamare na Ngilewa daga shekarar 1965 zuwa shekarar 1972.

Sannan yayi makarantar sakandare na Government Secondary School Nguru, daga shekarar 1972 zuwa shekarar 1977.

Daga nan Baba Malum Wali ya wuce Jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria yayi karatun sharan fage daga shekarar 1977 zuwa shekarar 1978. Sannan ya sake samun gurbin shiga karatun digiri na farko a fannin ilimi yanayi (Geography) daga shekarar 1978 zuwa shekarar 1981.

Domin karatun digiri na biyu, Baba Malum Wali ya sake koma wa Jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria yayi karatun digiri ta biyu daga shekarar 1984 zuwa shekarar 1986.

Yayi aikin Gwamnati k**ar haka:

1. Yayi aiki da hukumar Chad Basin Development Authority
a shekarar 1982,

2. Yayi bautan kasa a makarantar Kwali sakandare a Abuja daga shekarar 1981 zuwa shekarar 1982.

3. Yayi aiki a garin Nguru a matsayin Head of Planning Division na South Chad Irrigation Project. Sannan ya sake rike muƙamin Social Mobilisation officer na karamar hukumar Nguru daga shekarar 1987 zuwa shekarar 1989 karkashin Directorate for Social Mobilisation (MAMSER).

4. A shekarar 1989 ya wuce Jihar Borno domin k**a aiki da Gwamnatin soja a matsayin Principal Personnel officer, domin jajircewar sa har sai da ya kai matsayin Principal Secretary a shekarar 1990.

5. A watan Nuwamba na

BEGO YA YABAWA MUSA GALADIMA KAN GUDUNMAWARSA A FANNIN YADA LABARAI A YOBE.Daga Hassan Ahmed Maibaru.Kwamishinan Ma’aika...
16/04/2026

BEGO YA YABAWA MUSA GALADIMA KAN GUDUNMAWARSA A FANNIN YADA LABARAI A YOBE.

Daga Hassan Ahmed Maibaru.

Kwamishinan Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida, Yaɗa Labarai da Al’adu na Jihar Yobe, Alhaji Abdullahi Bego, ya yabawa tsohon Shugaban gidan rediyon jihar Yobe (YBC), Alhaji Musa Galadima, bisa gudunmawarsa wajen bunƙasa ci gaban kafafen yaɗa labarai na gwamnati, wato YBC da YTV.

Bego ya bayyana hakan ne a yayin bikin bankwana da aka shirya domin karrama Alhaji Musa Galadima, wanda ya kai shekarun ritaya a aikin gwamnati.

Daraktan Yaɗa Labarai na ma’aikatar, Alhaji Ali Musa Yawale, shirya wakilci kwamishinan, inda ya nuna gamsuwarsa kan yadda Alh. Musa Galadima ya yi amfani da ƙwarewarsa a aikin jarida wajen inganta ayyukan kafafen yaɗa labarai guda biyu mallakin gwamnatin jiha.

Alhaji Abdullahi Bego ya taya Alhaji Musa Galadima murnar kammala aikinsa cikin nasara, tare da yi masa fatan samun jagorancin Allah Madaukakin Sarki da nasara a rayuwarsa ta gaba.

A nasa jawabin, Mataimakin Shugaban Ƙungiyar shugabannin kafafen Watsa Labarai ta Najeriya (BON), wanda kuma shi ne shugaban gidan Telebijin ta jihar Yobe wato YTV, Alhaji Yusuf Isa, ya bayyana Musa Galadima a matsayin gogaggen ɗan jarida mai ƙwazo, wanda ya sadaukar da kansa wajen ci gaban harkokin yaɗa labarai a jihar da ma ƙasa baki ɗaya.
[16/04, 11:05 am] farming: A cikin ja abinda Shugaban Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta kasa reshen jihar Yobe (NUJ), Kwamared Rajab Mohammed, ya bayyana Musa Galadima a matsayin mutum abin koyi kuma jagora mai ba da shawara ga matasa a fannin aikin jarida.

Haka kuma, shugabannin NUJ da RATTWU na tashar YBC, Yusuf Bukar Biriri da Adamu Dauda Tokare, sun bayyana shi a matsayin jagora wanda ya taimaka wa ‘yan jarida wajen gudanar da aikinsu cikin nasara.

A nasu bangaren, Mataimakiyar Daraktan Sashen Labarai da Al’amuran Yau da kullum , Fati Mohammed Bukar, tare da ma’aikaciyar kwamfuta Arugbemi Amosun Mercy, sun yabawa kyakkyawan salon shugabancin da ya nuna, tare da yi masa fatan alheri a rayuwarsa ta gaba.

Da yake jawabi, Alhaji Musa Galadima ya nuna godiyarsa ga Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, bisa ba shi damar jagorantar YBC da YTV.

Ya kuma gode wa ma’aikatan YBC da YTV bisa goyon baya da haɗin kai da s**a ba shi a lokacin aikinsa, tare da kira gare su da su bai wa duk wanda za a naɗa a matsayin sabon shugaba irin wannan goyon baya.

14/04/2026

Enjoy the videos and music you love, upload original content, and share it all with friends, family, and the world on YouTube.

YOBE TAYI SABON KWAMISHINA.Daga Hassan Ahmed Maibaru.Rundunar ‘Yan Sanda Jihar Yobe ta sanar da sabon Kwamishinan ‘Yan S...
10/04/2026

YOBE TAYI SABON KWAMISHINA.

Daga Hassan Ahmed Maibaru.

Rundunar ‘Yan Sanda Jihar Yobe ta sanar da sabon Kwamishinan ‘Yan Sanda, CP Usman Kamfani Jibrin, ya karɓi ragamar aiki a hukumance a ranar Alhamis 9 ga Afrilu, 2026.

Ya maye gurbin tsohon Kwamishina, CP Emmanuel Ado, wanda aka tura zuwa wani babban matsayi a rundunar ‘yan sanda.

Sabon Kwamishinan, wanda ɗan asalin jihar Sokoto ne, ya shafe sama da shekaru 30 yana hidima a rundunar ‘yan sanda, inda ya rike muk**ai daban-daban a jihohi da dama na ƙasar Nan.

Mai magana da yawun rundunar ƴan sanda na jihar Yobe SP Dungus Abdulkarim, ya tabbatar da cewa sabon kwamishinan zai mayar da hankali wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a tare da ƙarfafa haɗin kai da al’umma domin tabbatar da zaman lafiya a faɗin jihar.

Kiwon Kajin Gida a Matsayin Hanyar Dogaro da Kai a Arewa Maso GabasDaga Umar Baba KumoWani babban jami’in noma a Kwaleji...
10/04/2026

Kiwon Kajin Gida a Matsayin Hanyar Dogaro da Kai a Arewa Maso Gabas

Daga Umar Baba Kumo

Wani babban jami’in noma a Kwalejin Noma ta Horticulture da ke Dadin Kowa, Abdul Hamid Abubakar Mohammed, ya yi kira ga matasa a Jihar Gombe da sauran yankin Arewa maso Gabas da su rungumi harkokin noma, musamman kiwon kaji, domin magance matsalolin talauci da rashin aikin yi.

Ya bayyana hakan ne yayin wata hira a shirin talabijin na Arewa Ayau, inda aka tattauna dashi kan bunƙasa harkokin kasuwancin noma na zamani, yana mai jaddada muhimmancin kiwon kaji a matsayin wata hanya mai sauƙi ta rage talauci.

Abdul Hamid ya bayyana cewa kajin gida sun fi dacewa ga masu farawa, domin suna da juriya kuma basu da tsadar kulawa, kasancewar ana iya ciyar da su da ragowar abinci da hatsi, sabanin kajin zamani masu tsadar kiwo.

Ya ƙara da cewa manomi na iya farawa da kaji shida kacal, waɗanda za su iya yin ƙwai sama da goma tare da fitar da aƙalla ƙwai takwas zuwa ƙanana cikin watanni uku zuwa huɗu.

A cewarsa, hakan na iya sa manomi ya samu kusan ƙananan kaji 50 cikin watanni huɗu, kuma su kai kusan kaji 100 cikin ƙasa da shekara guda.

Dangane da wannan hasashe, ya ce manomi na iya samun kusan naira 500,000 cikin shekara guda idan ya sayar da kowace kaza a kan naira 5,000.

Don haka, ya ƙarfafa gwiwar matasa da su yi amfani da damar da ke cikin harkar kiwon kaji domin su dogara da kansu.

Haka kuma ya bayyana cewa Kwalejin Noma ta Horticulture da ke Dadin Kowa na da kayan aiki da ƙwararrun ma’aikata da za su horas da matasa kan kiwon kaji da sauran harkokin kasuwancin noma.

A ƙarshe, ya yi kira ga gwamnatocin jihohi a yankin da su tallafa wa matasa ta hanyar samar da tallafi da kayan aiki, yana mai cewa hakan zai taimaka matuka wajen rage rashin aikin yi da kuma matsalolin tsaro da talauci ya haddasa a yankin.

Poultry Farming As Tool For Empowerment In The North East..... College Lecturer Charges Youth To Embark In Poultry Farmi...
10/04/2026

Poultry Farming As Tool For Empowerment In The North East..
... College Lecturer Charges Youth To Embark In Poultry Farming.

*By Umar Baba Kumo*

The Chief Agricultural Officer Federal College of Horticulture Dadin Kowa Abdul Hamid Abubakar Mohammed has called on youth in Gombe State and North East to embrace agricultural activities to confront the challenges of poverty in the region.

He made the call during an interview programme on Arewa Ayau Television on modern agribusiness development emphasising the potentials of poultry farming as a gateway towards poverty reduction.

He highlighted the viability of local poultry breeds which he said are more resilient and cheaper to maintain a using food leftovers and grains compared to highbreed poultry which are expensive to feed.

Mr Abdul Hamid noted that a farmer can start with 6 local chicken breeds that can lay about 10 or more eggs and produce at least 8 chicks in the span of 3 to 4 months.

With these he said poultry farmers may end up with about 50 chicks within a period of four months and about 100 chickens in less than one year.

According to this estimate he said a poultry farmer will generate about 500,000 in less than a year if he sells a hen at a cost of 5,000 per head.

Malam Abdul Hamid therefore charged youth in the region to strive and unlock the potentials available in the poultry sector to become self reliant.

He hinted that the Federal College of Horticulture Dadin Kowa has training facilities and Manpower to train youth poultry farming and other agri businesses.

He further called on state governments in the region to support youth empowerment through provision of incentives and support facilities which he said would go along way in reducing unemployment and other security challenges caused by poverty that has devastated the region.

08/04/2026
Masu ruwa da tsaki na jam’iyyun PDP da ADC sun shiga wani taron gaggawa domin tattauna matsalolin da jam’iyyun adawa ke ...
08/04/2026

Masu ruwa da tsaki na jam’iyyun PDP da ADC sun shiga wani taron gaggawa domin tattauna matsalolin da jam’iyyun adawa ke fuskanta.

Taron wanda ke gudana a Abuja ya samun halartar manyan jagororin jam’iyyun, wanda s**a hada Atiku Abubakar, Rabiu Kwankwaso, Devid Mark, Tanimu Turaki da dai sauransu.

Wannan na zuwa ne daidai lokacin da jam’iyyun adawa ke ci gaba da zargin gwamnatin tarayya da jam’iyyar APC wajen haddasa musu rikici.

Address

Madaki Street
Gombe

Telephone

+2347053480165

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AREWA A YAU posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to AREWA A YAU:

Share