Gombawa

Gombawa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Gombawa, Media/News Company, JMG Plaza, opposite Immagration Office, Gombe.

Gombawa TV is a digital television platform that broadcasts a wide range of content, including news, entertainment, and cultural programs, with a focus on Northern Nigeria.

05/06/2026

Dan takarar dan majalisa a jihar Gombe Hon Mubarak Musa Dantori, tare da dubunnan magoya bayansa, sun fice daga jam'iyyar ADC zuwa jam'iyyar PDP domin marawa Professor Isa Ali Pantami baya a zaben 2027.

A yau Jumma'a daya daga cikin shahararrun matasa 'yan siyasa masu taimakon al'umma a jihar Gombe Hon Mubarak Musa Dantori kuma dan takarar dan majalisar jiha na Gombe ta kudu karkashin jam’iyyar ADC ya sanar da ficewarshi tare da dubunnan magoya bayansa daga jam'iyyar ADC zuwa jam'iyyar PDP.

Hon Mubarak Musa Dantori yace sun fice daga jam'iyyar ADC ne zuwa jam'iyyar PDP domin marawa tafiyar Pantamiyya baya karkashin jagorancin Professor Isa Ali Pantami domin samar da ingantaccen shugabanci a jihar Gombe.

Hon. Dantori ya bayyana cewa ayyukan Alkhairan da Professor Isa Ali Pantami ya shimfida a jihar Gombe da samawa daruruwan matasa ayyukan yi a jihar Gombe yana daga cikin abubuwan da s**a ja hankalinshi na shiga tafiyar Pantamiyya domin shima ya bada tashi gudummawa na ciyar da al'ummar jihar Gombe gaba.

Hukumar Tsare-tsare da Ci Gaban Birane ta Jihar Gombe (GOSUPDA) ta bai wa daidaikun mutane, ƙungiyoyi da jam’iyyun siyas...
05/06/2026

Hukumar Tsare-tsare da Ci Gaban Birane ta Jihar Gombe (GOSUPDA) ta bai wa daidaikun mutane, ƙungiyoyi da jam’iyyun siyasa da s**a kafa allunan talla, fosta da tutoci a manyan tituna da wuraren jama’a a cikin Babban Birnin Gombe wa’adin cire su kafin ko zuwa ranar 15 ga watan Yunin 2026.

Shugaban Gudanarwa na GOSUPDA, Alhaji Bappayo Samanja Maudo, ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa da manema labarai, inda ya ce hukumar ta lura da yadda ake ci gaba da sanya allunan talla da fosta ba tare da bin ƙa’idojin da s**a dace ba a sassa daban-daban na birnin Gombe.

Ya bayyana cewa irin waɗannan ayyuka sun saɓa wa dokokin tsare-tsaren birane na jihar, tare da kawo cikas ga ƙoƙarin gwamnatin jihar ƙarƙashin jagorancin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na tabbatar da tsafta, tsari da kyawun muhalli a faɗin babban birnin jihar.

Alhaji Bappayo ya jaddada cewa hukumar ba za ta ci gaba da lamuntar duk wani aiki da ya saɓa wa dokokin ci gaban birane ba, yana mai gargadin cewa za a ɗauki matakin doka kan duk wanda ya ƙi bin wannan umarni bayan wa’adin da aka sanya.

Haka kuma, ya gargadi masu motocin haya da na kashin kansu da masu babura da su guji wanke ababen hawansu a kan tituna da sauran wuraren jama’a, yana mai cewa hakan na lalata hanyoyi, toshe magudanan ruwa da kuma ƙara gurbata muhalli.

Shugaban na GOSUPDA ya kuma yi kira ga masu gini, masu yin bulo da ’yan kwangila da su daina haɗa siminti, yashi da sauran kayan gini a kan hanyoyi da wuraren da jama’a ke bi, yana mai cewa hakan na haddasa lalacewar tituna tare da jefa masu amfani da hanya cikin wahala.

Ya ƙara da cewa dole ne dukkan ayyukan gine-gine su kasance cikin tsarin da aka amince da shi tare da bin ƙa’idojin muhalli domin tabbatar da tsaro da kuma ci gaban birane cikin tsari.

A ƙarshe, Alhaji Bappayo Samanja Maudo ya yi kira ga mazauna jihar Gombe da su mara wa hukumar baya wajen tabbatar da tsafta da kyawun birnin, yana mai cewa ci gaban birane nauyi ne da ya rataya a wuyan kowa da kowa.

Majiyar Rahoto: Hukumar Tsare-tsare da Ci Gaban Birane ta Jihar Gombe (GOSUPDA).

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa duk wani zaɓen fidda gwani da jam’iyyun siyasa s**a gudanar ...
05/06/2026

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa duk wani zaɓen fidda gwani da jam’iyyun siyasa s**a gudanar bayan wa’adin ranar 30 ga watan Mayu, 2026, ba zai kasance cikin tsarin jadawalin da hukumar ta amince da shi ba.

Hakan na zuwa ne bayan wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta soke wasu sassa na jadawalin zaɓukan fidda gwani da INEC ta fitar domin shirye-shiryen babban zaɓen shekarar 2027, inda kotun ta ce hukumar ba ta da ikon takaita wa’adin da Dokar Zaɓe ta tanada ga jam’iyyun siyasa.

INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UNCikin alhini da jimami muka samu labarin rasuwar Malam Abubakar Sadiq (Pharmacy), Gomb...
05/06/2026

INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN

Cikin alhini da jimami muka samu labarin rasuwar Malam Abubakar Sadiq (Pharmacy), Gombe.

Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya gafarta masa, Ya yi masa rahama, Ya yalwata kabarinsa, Ya sa Aljannatul Firdausi ta zama makomarsa.

Allahumma ighfir lahu warhamhu wa 'afihi wa'fu anhu.

Allah Ya ba iyalansa, 'yan'uwansa da abokan arziki haƙurin jure wannan babban rashi.

Inna Lillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un.Allah Ya yi wa Malam Abubakar Sadiq Pharmacy rasuwa a yau a garin Kano.Muna roƙon Al...
05/06/2026

Inna Lillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un.

Allah Ya yi wa Malam Abubakar Sadiq Pharmacy rasuwa a yau a garin Kano.

Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya gafarta masa, Ya jiƙansa da rahama, Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarsa. Allah Ya sa wannan ya zama ƙarshen wahalarsa, Ya ba iyalansa, abokansa, da al'ummar Musulmi haƙurin jure wannan babban rashi.

Allahumma-ghfir lahu warhamhu wa 'afihi wa'fu anhu.

Ameen.

DA DUMI-DUMI: Daruruwan matasan garin Lawanti sun fice daga jam'iyyar APC zuwa jam'iyyar PDP domin marawa Professor Isa ...
04/06/2026

DA DUMI-DUMI: Daruruwan matasan garin Lawanti sun fice daga jam'iyyar APC zuwa jam'iyyar PDP domin marawa Professor Isa Ali Pantami baya a zaben 2027.

A yau Alhamis matasan garin Lawanti dake karamar hukumar Akko jihar Gombe s**a gudanar da taro na musamman na jaddada goyon bayansu ga dan takarar Gwamnan jihar Gombe a jam’iyyar PDP Professor Isa Ali Pantami (Majidadin Daular Usmaniyya) tare da Hon Gidado Lawanti a matsayin dan takarar Majalisar Tarayya mai wakiltar karamar hukumar Akko.

A yayin taron daruruwan matasa ne s**a bayyana ficewarsu daga jam'iyyar APC zuwa jam'iyyar PDP domin tabbatar da samun ingantattun shugabanni a zabe mai zuwa.

CNG Ta Nuna Damuwa Kan Bambancin Kulawa Tsakanin Wadanda Aka Sace A Oyo Da BornoGamayyar Ƙungiyoyin Arewacin Najeriya (C...
04/06/2026

CNG Ta Nuna Damuwa Kan Bambancin Kulawa Tsakanin Wadanda Aka Sace A Oyo Da Borno

Gamayyar Ƙungiyoyin Arewacin Najeriya (CNG) ta bukaci Gwamnatin Tarayya da hukumomin tsaro da su tabbatar da cewa duk waɗanda matsalar tsaro ta shafa a Najeriya na samun kulawa iri ɗaya ba tare da la’akari da yankin da s**a fito ba.

Shugaban ƙungiyar, Kwamared Jamilu Aliyu Charanchi, ya bayyana haka yayin wata hira da Daily Trust ranar 3 ga Yunin 2026, inda ya nuna damuwa kan abin da ya bayyana a matsayin bambancin yadda ake mayar da hankali kan sace ɗalibai a jihohin Oyo da Borno.

A cewarsa, rahotanni sun nuna cewa a ranar 15 ga Mayu, 2026, an sace ɗalibai da malamai kusan 46 daga wasu makarantu da ke ƙaramar hukumar Oriire ta jihar Oyo. Hakazalika kuma, an yi garkuwa da ɗalibai 42 daga makarantar M***a Primary da Junior Secondary School da ke Askira Uba a jihar Borno a wannan rana.

Charanchi ya ce CNG na Allah wadai da duk wani nau’in ta’addanci, garkuwa da mutane da kashe-kashe a ko’ina cikin Najeriya, yana mai cewa rayuwar kowane ɗan ƙasa tana da muhimmanci kuma ta cancanci kariya daga gwamnati.

Ya bayyana cewa ƙungiyar ba ta ce a rage kulawar da ake bai wa jihar Oyo ba ne, sai dai tana kira da a nuna tausayi, goyon baya da kulawa iri ɗaya ga waɗanda abin ya shafa a Borno da sauran sassan ƙasar nan.

“Duk inda aka sami matsalar tsaro a Najeriya, gwamnati dole ta nuna damuwa iri ɗaya saboda babu rayuwar da ta fi wata muhimmanci,” in ji Charanchi.

Shugaban na CNG ya kuma bukaci gwamnatin tarayya da ta ƙara ƙaimi wajen ceto waɗanda aka sace, tare da samar da ingantacciyar dabarar tsaro domin magance matsalar ta’addanci, garkuwa da mutane da sauran laifukan tashin hankali da ke addabar ƙasar.

Haka kuma ya nemi a ƙarfafa tsaron makarantu da yankunan karkara, tare da inganta tattara bayanan sirri domin dakile ayyukan masu aikata laifuka a faɗin Najeriya.

A ƙarshe, Charanchi ya ce idan gwamnati ta ci gaba da bai wa dukkan yankunan ƙasar kulawa iri ɗaya wajen matsalolin tsaro, hakan zai taimaka wajen ƙarfafa haɗin kan ƙasa da dawo da amincewar jama’a ga hukumomi.

Kungiyar “Arewa Media Writers” Ta Nuna Matuƙar Damuwa Kan Sace Ɗaliban Federal Polytechnic Kaura Namoda A Jihar Zamfara…...
03/06/2026

Kungiyar “Arewa Media Writers” Ta Nuna Matuƙar Damuwa Kan Sace Ɗaliban Federal Polytechnic Kaura Namoda A Jihar Zamfara

…Ƙungiyar ta ce cigaba da hare-haren ‘yan bindiga kan ɗalibai na barazana ga ilimi da zaman lafiyar al’umma a Arewacin Najeriya.

Daga Ƙungiyar “Arewa Media Writers”

Ƙungiyar "Arewa Media Writers" karkashin jagorancin shugaban kungiyar na ƙasa Comr Haidar H Hashim, ta bayyana matuƙar damuwa da alhini kan rahotannin da ke nuna cewa ‘yan bindiga sun yi garkuwa da ɗalibai guda bakwai na Federal Polytechnic Kaura Namoda da ke Jihar Zamfara.

Rahotanni sun nuna cewa maharan sun sace ɗaliban ne daga matsuguninsu da ke yankin Low-Cost a garin Kaura Namoda, lamarin da ya sake jefa iyayen ɗalibai da al’ummar yankin cikin fargaba da rashin tabbas.

Ƙungiyar ta bayyana wannan hari a matsayin wani babban abin takaici da ke nuna yadda matsalar tsaro ke ci gaba da ta’azzara a wasu sassan Arewacin Najeriya, musamman a wuraren da ya kamata ɗalibai su kasance cikin kwanciyar hankali suna gudanar da karatunsu.

A cewar ƙungiyar, yawaitar hare-haren da ake kaiwa makarantu da matsugunan ɗalibai na iya haifar da koma baya ga harkar ilimi, tare da kara tsoratar da iyaye daga tura ‘ya’yansu neman ilimi.

Ƙungiyar ta jaddada cewa akwai buƙatar jami’an tsaro su ɗauki matakan gaggawa domin ceto ɗaliban da aka sace tare da tabbatar da kamo waɗanda s**a aikata wannan ɗanyen aiki, domin su fuskanci hukuncin da ya dace.

Haka kuma, "Arewa Media Writers" ta yi kira ga gwamnatin tarayya da gwamnatin Jihar Zamfara da su ƙara ƙaimi wajen samar da tsaro a cibiyoyin ilimi da matsugunan ɗalibai, domin hana sake aukuwar irin wannan lamari a nan gaba.

A ƙarshe, ƙungiyar ta yi addu’ar Allah Ya kare rayukan waɗanda aka sace, Ya ba jami’an tsaro nasarar ceto su cikin koshin lafiya, tare da dawo da zaman lafiya a yankunan da ke fama da matsalar rashin tsaro.

Comr. Muhammad Kwairi Waziri
National Director, Media and Publicity I
"Arewa Media Writers"

'Yan Bindiga Sun Sace Dalibai Bakwai a ZamfaraWasu da ake zargin 'yan bindiga ne sun sace dalibai bakwai na makarantar F...
03/06/2026

'Yan Bindiga Sun Sace Dalibai Bakwai a Zamfara

Wasu da ake zargin 'yan bindiga ne sun sace dalibai bakwai na makarantar Federal Polytechnic Kaura Namoda da ke Jihar Zamfara, bayan sun kai hari gidan da daliban ke zaune a wajen harabar makarantar, a yankin Low-Cost da ke garin Kaura Namoda.

Lamarin ya haifar da fargaba da tashin hankali tsakanin ɗalibai da mazauna yankin, yayin da jami'an tsaro s**a fara bincike da ƙoƙarin ceto waɗanda aka sace.

Ana ci gaba da jiran ƙarin bayani daga hukumomin da abin ya shafa game da wannan al'amari.

Yadda Ruwa da Iska S**a Lalata Gidaje a Wuro Dole, Karamar Hukumar Akko ta Jihar GombeMazauna garin Wuro Dole da ke Ƙara...
03/06/2026

Yadda Ruwa da Iska S**a Lalata Gidaje a Wuro Dole, Karamar Hukumar Akko ta Jihar Gombe

Mazauna garin Wuro Dole da ke Ƙaramar Hukumar Akko a Jihar Gombe sun shiga cikin damuwa bayan wata guguwa mai ƙarfi tare da ruwan sama ta yi barna mai yawa a yankin.

Lamarin ya faru ne lokacin da iska mai ƙarfi da ruwan sama s**a mamaye garin, lamarin da ya janyo rushewar wasu gidaje tare da lalata rufufin wasu da dama. Haka kuma, an samu asarar dukiyoyi da kayayyakin amfanin gida sakamakon wannan ibtila'i.

Wasu daga cikin mazauna yankin sun bayyana cewa barnar ta shafi iyalai da dama, inda wasu s**a rasa matsugunansu tare da shiga halin ƙunci. Sun yi kira ga gwamnati da ƙungiyoyin agaji da masu hannu da shuni da su kawo musu ɗauki domin rage radadin halin da suke ciki.

Al'ummar yankin na ci gaba da ƙididdige asarar da aka yi, tare da fatan samun taimakon gaggawa daga hukumomin da abin ya shafa.

Allah Ya kiyaye gaba, Ya kuma bai wa waɗanda abin ya shafa ikon jure wannan jarabawa. Ameen.

Address

JMG Plaza, Opposite Immagration Office
Gombe
741212

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Gombawa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Gombawa:

Share