
11/07/2025
Amnesty International Ta Bukaci A Janye Sammacin K**a Hamdiyya, Matashiyar Da Ta Soki Gwamnan Jihar Sokoto
Kungiyar kare hakkin dan Adam ta duniya, Amnesty International, tare da wasu ƙungiyoyi 45, sun yi kira ga gwamnatin Jihar Sokoto da ta janye sammacin k**a da aka fitar kan wata matashiya mai suna Hamdiyya Sidi Sharif, wadda ta yi rubuce-rubuce na s**ar gwamna Ahmed Aliyu Sokoto a kafafen sada zumunta.
A cewar Amnesty, Hamdiyya, mai shekaru 17, ta fuskanci tsangwama da barazana bayan ta soki salon mulkin gwamnan Sokoto a shafinta na TikTok, inda ta bayyana matsalolin da talakawa ke fuskanta, musamman kan batun tsaro da rayuwar al’umma a jihar.
Rahotanni sun nuna cewa an sace Hamdiyya a cikin watan Nuwamba 2024, inda wasu da ba a san ko su wane ba s**a dauke ta daga Sokoto zuwa wani daji, s**a buge ta, sannan s**a jefar da ita a kusa da wani asibiti a garin Bakura, Jihar Zamfara.
Amnesty International ta bayyana cewa, “Yayin da take bukatar kulawar lafiya da kariya, gwamnati maimakon ta bi doka da kare hakkin ta, sai ta fitar da sammaci domin cafketa.”
Kungiyoyin sun bayyana lamarin a matsayin wani yunkuri na cusa tsoro cikin matasa, musamman ‘yan kasa da shekara 18, don hana su bayyana ra’ayoyinsu a fili.
Sun bukaci gwamnatin jihar da ta janye duk wata shari’a ko bincike da aka bude a kanta, tare da tabbatar da cewa ba za a kuma tsorata masu adawa da gwamnati ba.