Gombawa

Gombawa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Gombawa, Media/News Company, Pantami Hurmindau, Gombe.

Gombawa TV is a digital television platform that broadcasts a wide range of content, including news, entertainment, and cultural programs, with a focus on Northern Nigeria.

Amnesty International Ta Bukaci A Janye Sammacin K**a Hamdiyya, Matashiyar Da Ta Soki Gwamnan Jihar SokotoKungiyar kare ...
11/07/2025

Amnesty International Ta Bukaci A Janye Sammacin K**a Hamdiyya, Matashiyar Da Ta Soki Gwamnan Jihar Sokoto

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta duniya, Amnesty International, tare da wasu ƙungiyoyi 45, sun yi kira ga gwamnatin Jihar Sokoto da ta janye sammacin k**a da aka fitar kan wata matashiya mai suna Hamdiyya Sidi Sharif, wadda ta yi rubuce-rubuce na s**ar gwamna Ahmed Aliyu Sokoto a kafafen sada zumunta.

A cewar Amnesty, Hamdiyya, mai shekaru 17, ta fuskanci tsangwama da barazana bayan ta soki salon mulkin gwamnan Sokoto a shafinta na TikTok, inda ta bayyana matsalolin da talakawa ke fuskanta, musamman kan batun tsaro da rayuwar al’umma a jihar.

Rahotanni sun nuna cewa an sace Hamdiyya a cikin watan Nuwamba 2024, inda wasu da ba a san ko su wane ba s**a dauke ta daga Sokoto zuwa wani daji, s**a buge ta, sannan s**a jefar da ita a kusa da wani asibiti a garin Bakura, Jihar Zamfara.

Amnesty International ta bayyana cewa, “Yayin da take bukatar kulawar lafiya da kariya, gwamnati maimakon ta bi doka da kare hakkin ta, sai ta fitar da sammaci domin cafketa.”

Kungiyoyin sun bayyana lamarin a matsayin wani yunkuri na cusa tsoro cikin matasa, musamman ‘yan kasa da shekara 18, don hana su bayyana ra’ayoyinsu a fili.

Sun bukaci gwamnatin jihar da ta janye duk wata shari’a ko bincike da aka bude a kanta, tare da tabbatar da cewa ba za a kuma tsorata masu adawa da gwamnati ba.

Sheikh Sani Yahaya Jingir Ya Nuna Fushin Sa Kan Tarbar Da Mataimakinsa Ya Yi Wa Peter ObiFitaccen malamin addinin Musulu...
11/07/2025

Sheikh Sani Yahaya Jingir Ya Nuna Fushin Sa Kan Tarbar Da Mataimakinsa Ya Yi Wa Peter Obi

Fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Sani Yahaya Jingir, ya bayyana baƙin cikinsa kan yadda mataimakinsa, Sheikh Yusuf Sambo, ya karɓi tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party, Mr. Peter Obi, tare da saka masa babbar riga a yayin ziyarar da ya kai masa a gidansa da ke Kaduna.

A wani bidiyo da ke yawo a shafukan sada zumunta, Sheikh Jingir ya ce wannan mataki bai dace da tafiyarsu ta addini da siyasa ba, yana mai cewa bai da masaniya kan wannan ziyara, kuma bai amince da hakan ba.

“Ba a tuntube ni ba kafin wannan abu ya faru. Irin wannan tarba na iya haifar da ruɗani da rikita al’umma. Wannan ba tsarin tafiyarmu ba ne,” inji Sheikh Jingir.

Malamin ya ci gaba da bayyana cewa wannan lamari ya girgiza shi, yana mai nuna takaicinsa kan yadda wasu daga cikin mabiyansa ke ɗaukar matakai ba tare da tuntuba ba.

Haka kuma, Sheikh Jingir ya jaddada matsayin tafiyarsu na goyon bayan tsarin Muslim-Muslim ticket a babban zaɓen da ke tafe na 2027, yana mai cewa wannan ra’ayi nasu bai canza ba, kuma za su ci gaba da tsayawa kan matsayinsu na farko.

Jam’iyyun Adawa 19 Sun Haɗa Kai Domin Kawar Da Gomnatin APC A Jihar GombeGamayyar jam’iyyun adawa guda 19 da ke aiki ƙar...
11/07/2025

Jam’iyyun Adawa 19 Sun Haɗa Kai Domin Kawar Da Gomnatin APC A Jihar Gombe

Gamayyar jam’iyyun adawa guda 19 da ke aiki ƙarƙashin sunan Gombe State Coalition Working Group sun ƙaddamar da wani babban shiri domin kifar da jam’iyyar All Progressives Congress (APC) daga mulki a jihar Gombe a zaɓen shekarar 2027.

A wata sanarwa da s**a fitar a taron manema labarai da aka gudanar a Gombe, gamayyar jam’iyyun ta bayyana gwamnatin da ke ci gaba da mulki karkashin APC a matsayin gwamnati mai gazawa a fannoni da dama, ciki har da tattalin arziki, samar da ababen more rayuwa da kare martabar rayuwar al’umma.

Jam’iyyun da s**a shiga wannan haɗin gwiwa sun haɗa da:

Peoples Democratic Party (PDP)

Social Democratic Party (SDP)

African Democratic Congress (ADC)

Labour Party (LP)

Da sauran jam’iyyu 15.

Shugaban gamayyar, Idris Umar, wanda kuma tsohon Ministan Sufuri ne, ya bayyana cewa sun yanke shawarar haɗa ƙarfi da ƙarfi ne domin fuskantar APC da kuma ceto al’ummar jihar daga halin da suke ciki.

“Wannan haɗin gwiwa ba wai don kifar da APC kadai ba ne, amma domin samar da sabuwar gwamnati mai gaskiya da kishin talaka,” inji Idris Umar.

A cewar rahoton, gamayyar ta zaɓi jam’iyyar ADC a matsayin dandalin da za ta yi amfani da shi domin tsayawa takara a zaɓen mai zuwa. Tuni aka fara rajistar mambobi a dukkan kananan hukumomi na jihar Gombe, domin ƙarfafa shirin su.

Suleiman Barde Ya Shiga Hannun Hukuma Bisa Zargin Matar Kakakin Majalisa Da Karɓar Cin HanciDaga Muhammad Kwairi WaziriA...
11/07/2025

Suleiman Barde Ya Shiga Hannun Hukuma Bisa Zargin Matar Kakakin Majalisa Da Karɓar Cin Hanci

Daga Muhammad Kwairi Waziri

A ranar Alhamis, 10 ga Yuli, 2025, jami’an tsaro sun k**a wani matashi mai suna Suleiman Barde tare da ɗan uwansa a garin Zaria, jihar Kaduna, bisa zargin wallafa rubutun da ya danganta Matar Shugaban Majalisar Wakilai, Hon. Tajudeen Abbas, da karɓan cin hanci, a shafinsa na Facebook.

Rahoton da Sahara Reporters ta fitar ya bayyana cewa, rubutun na Suleiman ya ƙunshi wasu kalmomi da hukumomi ke kallon su a matsayin zargi da batanci ga matar shugaban majalisar, lamarin da ya janyo hankalin jami’an tsaro.

Yayin da aka tura su zuwa gidan yari, ba a bayyana ko za a gurfanar da su a gaban kotu ba, kuma babu cikakken bayani daga bangaren 'yan sanda ko ofishin Attorney General na jihar Kaduna kan matakin da za a dauka a gaba.

Haka zalika, babu wata hujja ko cikakken tabbaci da ke nuna cewa an gurfanar da Suleiman gaban kotu ko an ba shi beli zuwa yanzu.

DA DUMI-DUMI: Sanata Natasha Ta Turawa Majalisa Wasikar Komawa Bakin Aiki A Ranar TalataDaga Muhammad Kwairi WaziriSanat...
11/07/2025

DA DUMI-DUMI: Sanata Natasha Ta Turawa Majalisa Wasikar Komawa Bakin Aiki A Ranar Talata

Daga Muhammad Kwairi Waziri

Sanata mai wakiltar mazabar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta rubuta wasika zuwa ga shugabancin majalisar dattawa domin sanar da niyyarta ta komawa bakin aiki ranar Litinin, 15 ga watan Yuli, 2025.

Wasikar ta biyo bayan hukuncin da wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yanke, inda ta rushe dakatarwar da majalisar ta yi mata, tana mai cewa hakan ya saba wa kundin tsarin mulki kuma babu hurumin majalisar ta dauki irin wannan mataki.

A cikin wasikar da Natasha ta tura, ta bayyana cewa, "Ina sanar da majalisa cewa bisa hukuncin kotu da ya dawo min da dukan hakkina, zan koma bakin aikina a zauren majalisar daga ranar Litinin mai zuwa."

Idan za a iya tunawa, majalisar dattawa ta dakatar da Natasha a ranar 6 ga watan Maris, bisa zargin ta tada zaune tsaye da kuma yin rubuce-rubuce da s**a saba ka'idojin majalisa, ciki har da zargin cin zarafi da ta yi wa shugaban majalisar, Godswill Akpabio.

Kotun da ta saurari karar ta bayyana cewa dakatarwar ba ta da tushe, kuma ta umurci majalisar da ta dawo da ita nan take, sai dai majalisar ta sanya sharudda k**ar biyan tara ta Naira miliyan 5 da bayar da hakuri a fili kafin a karɓe ta.

A halin yanzu, ba a tabbatar da ko majalisa za ta karɓe ta a ranar da ta ambata ba, duk da cewa ta rigaya ta bayyana shirinta na komawa aiki

ZABEN 2027: A Wace Akwati Za Ka Jefa Kuri'arka?
11/07/2025

ZABEN 2027: A Wace Akwati Za Ka Jefa Kuri'arka?

BARKA DA JUMA’A MAI MARTABAMai Martaba Sarkin Gombe, Alhaji Abubakar Shehu Abubakar III CFR muna taya Mai Martaba murna ...
11/07/2025

BARKA DA JUMA’A MAI MARTABA

Mai Martaba Sarkin Gombe, Alhaji Abubakar Shehu Abubakar III CFR muna taya Mai Martaba murna da farin cikin wannan rana mai albarka ta Juma’a.

Muna rokon Allah Madaukakin Sarki Ya kara wa Mai Martaba lafiya, hikima, nisan kwana da jagoranci na adalci da lumana.

Allah Ya sanya wannan Juma’ar ta kasance cike da alheri da tsarkaka, Ya bar zaman lafiya da arziki a masarautar Gombe da daukacin Najeriya.

Juma’atu Mubarak Mai Martaba.

DA DUMI DUMINSA: Bazan daina yiwa Tinubu fatan Sake Zama  shugaban kasa a 2027 Ba,  inji  ganduje.Dr Abdullahi Umar gand...
11/07/2025

DA DUMI DUMINSA: Bazan daina yiwa Tinubu fatan Sake Zama shugaban kasa a 2027 Ba, inji ganduje.

Dr Abdullahi Umar ganduje yace zai cigaba marawa Tinubu sai inda karfinsa ya kare wajan ganin yayi Nasarar lashe Zaben shugaban kasa.

ganduje ya Kara da cewa baya tunanin akwai wata jam iyya da zatayi tasiri a jihar Kano bayan jam iyyar APC sabida har yanzu al'ummar jihar Kano na cigaba da goyon bayan jam iyyar sannan munada tabbacin APC ce zata lashe kowanne zabe a jihar Kano.

Me za ku ce?

"Ba na goyon bayan dan Arewa ya sake zama shugaban kasa a 2027", Inji Ministar Al’adu Hannatu Musa MusawaMinistar Al’adu...
11/07/2025

"Ba na goyon bayan dan Arewa ya sake zama shugaban kasa a 2027", Inji Ministar Al’adu Hannatu Musa Musawa

Ministar Al’adu da Zamantakewa, Hannatu Musa Musawa, ta bayyana cewa ba ta goyon bayan shugabancin kasa ya koma yankin Arewa a shekarar 2027.

A cewar ta, bayan shugabancin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari wanda ya fito daga Arewa ya shafe shekaru takwas a mulki, ya dace a bar yankin Kudu su ma su samu cikakken damar yin shekaru takwas a kan madafun iko kafin a sake tunanin mayar da mulki Arewa.

Musawa ta ce wannan ra’ayi nata yana da tushe ne bisa adalci da daidaito tsakanin sassan kasar, domin tabbatar da zaman lafiya da hadin kai a Najeriya.

“Tunda Buhari ya yi 8, k**ata yayi a bar Kudu su ma sai sun yi 8.” — inji Ministar.

Wannan kalamai nata na zuwa ne a daidai lokacin da ake ta fargabar rikice-rikicen siyasa da shiri tun daga yanzu game da zaben shugaban kasa na 2027, inda wasu daga Arewa ke harin komawa mulki.

DA DUMI-DUMI: An K**a Ƴan Sanda 7 Saboda Goyon Bayan Zanga-zangar Ƴan FanshoDaga Muhammad Kwairi WaziriAn samu tabbaci d...
11/07/2025

DA DUMI-DUMI: An K**a Ƴan Sanda 7 Saboda Goyon Bayan Zanga-zangar Ƴan Fansho

Daga Muhammad Kwairi Waziri

An samu tabbaci daga babban jami’in ‘yan sanda na ƙasa (DIG), Benjamin Okolo, cewa an k**a jami’an rundunar ‘yan sanda guda bakwai da ake zargi da shiga muhawara ko goyon bayan wani shiri na zanga-zanga da ke neman inganta walwalar jami’an tsaro a Najeriya.

Rahotanni daga Sahara Reporters sun nuna cewa ana zargin su da laifin yunkurin tawaye, sabanin cewa kawai sun yi magana kan halin kuncin da suke ciki da kuma bukatar a kyautata musu albashi da jin daɗi.

Zanga-zangar da ake shirin yi a ranar 21 ga Yuli 2025 na neman baiwa jami’an tsaro daman bayyana damuwarsu da ƙalubalen rayuwa, musamman ‘yan sanda da s**a ritaya da kuma waɗanda ke ci gaba da aiki.

Omoyele Sowore, dan gwagwarmayar kare ‘yancin ɗan adam, ya bayyana cewa tuhumar da aka yi wa jami’an na nuni da yadda ake ci gaba da tauye ‘yancin jama’a a Najeriya, musamman ma wadanda ke kokarin kare al’umma.

A wata sanarwa daga hedikwatar ‘yan sanda, an bayyana umarnin hana duk wani tsohon jami’in tsaro daga shiga wannan zanga-zangar, tare da gargaɗin cewa duk wanda aka k**a zai fuskanci hukunci mai tsanani.

Shin tambaya anan ita ce: Idan har jami’in tsaro ba zai iya koka ba, wane ne zai kare shi?

Rarara Da Amaryarsa Aisha Humaira Sun Ziyarci Gwamna Jihar Gombe Alh  Inuwa Yahaya Mai Girma Shugaban Kasar Mawaka, Alha...
10/07/2025

Rarara Da Amaryarsa Aisha Humaira Sun Ziyarci Gwamna Jihar Gombe Alh Inuwa Yahaya

Mai Girma Shugaban Kasar Mawaka, Alhaji Dauda Kahutu Rarara, tare da amininsa, Dr Abdullahi Al-Hikima, da amaryarsa, Hajiya Ayshatulhumaira, sun kai ziyarar girmamawa ga Gwamnan Jahar Gombe, His Excellency Muhammadu Inuwa Yahaya, CON.

Ziyarar ta gudana ne a ofishin Gwamna da ke gidan gwamnatin jihar Gombe, inda s**a tattauna kan batutuwan da s**a shafi al'umma, ci gaban matasa, da kuma cigaban fasaha da ilimi a arewacin Najeriya.

Wannan ziyara na daga cikin irin mu’amala da girmamawa da Rarara ke nunawa shugabannin da ke aikin alheri da kishin kasa.

Baka Da Ikon Cire Gwamna Fubara, Doka Bata Baka Dama Ba, Kashim Shettima Ga Shugaba TinubuDaga Muhammad Kwairi WaziriMat...
10/07/2025

Baka Da Ikon Cire Gwamna Fubara, Doka Bata Baka Dama Ba, Kashim Shettima Ga Shugaba Tinubu

Daga Muhammad Kwairi Waziri

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bashi da ikon cire Gwamnan Jihar Rivers, Siminalayi Fubara, bisa tsarin mulki da kundin dokar kasa.

Shettima ya fadi haka ne a cikin wani taron rufe shirin ci gaban matasa da ake gudanarwa a Abuja, inda ya jaddada cewa kowane mataki da zai keta doka ko murƙushe tsarin mulki zai iya lalata dimokuraɗiyyar Najeriya.

Ya ce, "Ko shugaban ƙasa bashi da ikon da zai tsige Gwamna. Wannan ikon yana hannun Majalisar Dokoki ta Jiha ne, bisa tanadin kundin tsarin mulki."

Wannan jawabi na Shettima na zuwa ne bayan samun takaddama da sabani a siyasar Jihar Rivers, inda aka zargi wasu bangarori da yunkurin tsige Gwamna Fubara, tare da raba gardama kan rinjayen iko tsakanin bangaren zartarwa da majalisar jihar.

A ƙarshe, Shettima ya shawarci shugabanni da su mutunta dokar kasa tare da kauce wa duk wata tafiya da zata iya tayar da tarzoma ko janyo rikici a kasa.

Address

Pantami Hurmindau
Gombe

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Gombawa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Gombawa:

Share