Gombawa

Gombawa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Gombawa, Media/News Company, JMG Plaza, opposite Immagration Office, Gombe.

Gombawa TV is a digital television platform that broadcasts a wide range of content, including news, entertainment, and cultural programs, with a focus on Northern Nigeria.

YANZU-YANZU: An Ruwaito Cewa Goodluck Ebele Jonathan Zai Fice Daga Jam'iyyar PDP Daga Yanzu Zuwa Kowane LokaciShin a gan...
04/08/2025

YANZU-YANZU: An Ruwaito Cewa Goodluck Ebele Jonathan Zai Fice Daga Jam'iyyar PDP Daga Yanzu Zuwa Kowane Lokaci

Shin a ganin ku wace jam'iyya zai koma ?

Dattijo Mai Shekaru Sittin Ya Shiga Makarantar Firamare A Jihar Adamawa Domin Cika Burinsa Na Zama LikitaA karamar hukum...
03/08/2025

Dattijo Mai Shekaru Sittin Ya Shiga Makarantar Firamare A Jihar Adamawa Domin Cika Burinsa Na Zama Likita

A karamar hukumar Girei , dake Jihar Adamawa, wani dattijo mai shekaru da s**a haura 60 ya jawo hankalin al’umma bayan ya koma makarantar firamare da burin zama likita. Wannan matakin ya biyo bayan damuwarsa da yadda ake gudanar da harkar lafiya a asibitocin kasar nan.

Dattijon, wanda ya bukaci a sakaya sunansa a halin yanzu, ya bayyana cewa ya dade yana sha’awar ilimi da aikin jinya, kuma ganin yadda ake fama da gazawar kula da lafiya ya kara masa kwarin gwiwar fara karatu daga tushe. Ya ce: “Ba zan zura ido na dinga kallon yadda ake wulakanta marasa lafiya ba, sai na tsaya na zama cikin masu kawo sauyi."

Malamai da dalibai a makarantar sun bayyana girmamawa da goyon baya ga wannan dattijo, suna mai cewa yana zama abin koyi da karfafa gwiwa ga matasa.

Jama’a a kafafen sada zumunta sun cika da yabo da fatan alheri, inda wasu ke ganin cewa wannan al’amari ya kara haskaka muhimmancin ilimi da himma, komai shekaru.

Yanzu Cikin Daren Nan Mutanen Garin Kuruwa Dake Tureta A Jihar Sokoto, Sun Gudu Sun Bar Garin Su Kan Matsalar Rashin Tsa...
03/08/2025

Yanzu Cikin Daren Nan Mutanen Garin Kuruwa Dake Tureta A Jihar Sokoto, Sun Gudu Sun Bar Garin Su Kan Matsalar Rashin Tsaro

DA DUMI-DUMI: Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan Jihar Katsina, Sanata Saddiq Yar’adua, Ya Fice Daga Jam’iyyar Apc Zuwa Jam’iyya...
03/08/2025

DA DUMI-DUMI: Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan Jihar Katsina, Sanata Saddiq Yar’adua, Ya Fice Daga Jam’iyyar Apc Zuwa Jam’iyyar Hadaka Ta Adc (African Democratic Congress).

Wannan mataki na zuwa ne a daidai lokacin da jiga-jigan siyasa ke fara sauya sheƙa gabanin zaɓen 2027, tare da nuna rashin gamsuwa da halin da Najeriya ke ciki karkashin gwamnatin yanzu.

Da Wahala Najeriya Ta Ɗore Idan APC Ta Sake Kafa Gwamnati A 2027, Inji El-RufaiTsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Ruf...
03/08/2025

Da Wahala Najeriya Ta Ɗore Idan APC Ta Sake Kafa Gwamnati A 2027, Inji El-Rufai

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya yi gargadin cewa makomar Najeriya na cikin babban hadari idan jam’iyyar APC ta sake lashe zaben shugaban kasa a shekarar 2027.

A cewarsa, gazawar APC wajen gudanar da mulki ta jefa kasa cikin mawuyacin hali, kuma ci gaban mulkin jam’iyyar ka iya *rushe tubalin zamantakewar kasa* baki daya.

Ya bayyana hakan ne a jihar Sakkwato, yayin wani taron wayar da kan jama’a da jam’iyyar hamayya ta ADC ta shirya. El-Rufai ya ce *bai shiga siyasa don riba ba, sai don ceto Najeriya daga rugujewa.

A yanzu, El-Rufai na daga cikin jiga-jigan jam’iyyar ADC, kuma ya ce zai hada kai da sauran ’yan Najeriya domin kifar da mulkin APC a matakin *jihohi da tarayya a 2027.

Wace Jaha Kuke fatan Dan Bello ya ziyarta?
03/08/2025

Wace Jaha Kuke fatan Dan Bello ya ziyarta?

Mazauna Unguwar Zango Dake Kano Na Zangà-Zàñgaŕ Nuna Damuwar Su Kan Fadan Daba© Rariya
03/08/2025

Mazauna Unguwar Zango Dake Kano Na Zangà-Zàñgaŕ Nuna Damuwar Su Kan Fadan Daba

© Rariya

Ina Roƙon Ƴan Nigeria Da Su Sake Bawa Shugaba Tinubu Dama Wajen Zaɓen Sa A 2027, Inji Femi GbajabiamilaShugaban ma’aikat...
03/08/2025

Ina Roƙon Ƴan Nigeria Da Su Sake Bawa Shugaba Tinubu Dama Wajen Zaɓen Sa A 2027, Inji Femi Gbajabiamila

Shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila, ya roki al’ummar Arewa da su sake mara wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu baya a zaben shekarar 2027.

Gbajabiamila ya ce wannan bukata tana da muhimmanci ne domin a samu damar kammala manyan ayyukan ci gaban da shugaban kasa ya fara a yankin Arewa tun bayan hawansa mulki.

Ya kara da cewa Tinubu ya nuna cikakken kishin Arewa ta hanyar saka jari a bangarori da dama kamar hanyoyi, noma, lafiya, da makamashi, don haka yana da kyau a ba shi dama ya gama.

Ya ce ci gaban Arewa ba zai tabbata ba sai an ba Tinubu cikakken goyon baya, musamman a zaben 2027.

JIBWIS GOMBE TA GABATAR DA TARO DA WA’AZI A KARAMAR HUKUMAR KALTUNGOKungiyar Jama’atu Izalatil Bid’a Wa Iqamatis Sunnah ...
03/08/2025

JIBWIS GOMBE TA GABATAR DA TARO DA WA’AZI A KARAMAR HUKUMAR KALTUNGO

Kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’a Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS) reshen Jihar Gombe, ƙarƙashin jagorancin Shugaban Jiha, Alhaji Injiniya Salisu Muhammad Gombe, ta gudanar da babban taron wa’azi na jiha a Karamar Hukumar Kaltungo.

Taron, wanda ya gudana da yammacin ranar Asabar a Masallacin Juma’a na Kofar Fadar Mai Kaltungo, ya samu halartar dukkan shuwagabannin Kungiyar daga matakin jiha har zuwa ƙananan hukumomi. Tattaunawar ta mayar da hankali ne kan inganta da kuma ci gaban da’awa a faɗin Jihar Gombe.

Kafin fara taron, Shugaban Kungiyar ya jagoranci wata tawaga zuwa fadar Mai Martaba Engr. Sale Muhammad, Mai Kaltungo, domin kai gaisuwar ziyara. A jawabinsa, Mai Martaba ya bayyana Engr. Salisu Muhammad Gombe a matsayin shugaba nagari, abin koyi, wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen hidimar al’umma da ci gaban da’awa a jihar.

Daga bisani, an gudanar da babban wa’azi a harabar Kofar Fada, inda manyan malamai s**a gabatar da muhimman wa’azozin ilimi da tunatarwa. Daga cikin wadanda s**a gabatar da wa’azi akwai:

Sheikh Muhammad Hajjun Kumo

Professor Sheikh Rashid Abdulganiyu

Allah ya saka da alheri, ya ƙara ɗaukaka da ƙarfafa mu a harkar da’awa.

✍️ Muhammad chigari kumo

Wace Lamba State Dinku Take ?
03/08/2025

Wace Lamba State Dinku Take ?

DA DUMI-DUMI: Sojojin Najeriya Sun Yi Nasarar  Ceto Malamin Jami’ar Jihar Taraba da Aka Yi Garkuwa Da ShiA ranar 31 ga Y...
03/08/2025

DA DUMI-DUMI: Sojojin Najeriya Sun Yi Nasarar Ceto Malamin Jami’ar Jihar Taraba da Aka Yi Garkuwa Da Shi

A ranar 31 ga Yuli, 2025, wasu ’yan bindiga sun sace Injiniya Joshua Saleh, malami a Jami’ar Taraba, a kan hanyar Chinkai–Kente–Wukari da ke cikin Karamar Hukumar Wukari.

Sai dai a jiya, dakarun Runduna ta 6 na Sojojin Najeriya, Sashen Operation Whirl Stroke (OPWS) tare da hadin gwiwar Ma’aikatar Tsaro ta Ƙasa (DSS) sun yi nasarar ceto shi ba tare da wata illa ba.

An bayyana cewa an gudanar da aikin ceton ne da gaggawa kuma cikin tsari, wanda ya kai ga kubutar da malamin cikin koshin lafiya.

Kampanin MTN Da Airtel Sun Bayyana Cewa Masu Amfani Da Layukansu Sun Kashe Naira Tiriliyan 2.53 A ShekaraKamfanonin sada...
03/08/2025

Kampanin MTN Da Airtel Sun Bayyana Cewa Masu Amfani Da Layukansu Sun Kashe Naira Tiriliyan 2.53 A Shekara

Kamfanonin sadarwa na MTN da Airtel sun fitar da rahoton cewa a cikin farkon shekarar 2025 kadai, masu amfani da layukansu sun kashe kusan Naira Tiriliyan 2.53 wajen kiran waya da siyan data. Wannan na cikin kididdigar da aka tattara daga miliyoyin masu amfani da su a faɗin ƙasar.

Wannan adadi ya jawo ce-ce-ku-ce a dandalin sada zumunta, inda wasu ke bayyana damuwa game da yawan kudin da suke kashewa ba tare da daidaitaccen saukin sabis ba.

Masana sun bayyana cewa, karuwar amfani da intanet da shigowar sabbin fasahohi na da matukar tasiri wajen ƙara kashe kuɗi a wannan fanni.

Haka kuma, ana sa ran za a samu karin farashin sabis nan gaba sakamakon hauhawar farashin kayayyaki a ƙasa.

Address

JMG Plaza, Opposite Immagration Office
Gombe
741212

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Gombawa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Gombawa:

Share