Gombawa

Gombawa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Gombawa, Media/News Company, JMG Plaza, opposite Immagration Office, Gombe.

Gombawa TV is a digital television platform that broadcasts a wide range of content, including news, entertainment, and cultural programs, with a focus on Northern Nigeria.

Wa Zai Fada Mana Nan Wace Jiha Ce Cikin Jahohin Arewa?
23/10/2025

Wa Zai Fada Mana Nan Wace Jiha Ce Cikin Jahohin Arewa?

DA DUMI-DUMI: Professor Isa Ali Pantami Ne Zai Jagoranci Sallar Juma’a  Gobe A Kasar Ingila Tare DA Gabatar Da LakcaDaga...
23/10/2025

DA DUMI-DUMI: Professor Isa Ali Pantami Ne Zai Jagoranci Sallar Juma’a Gobe A Kasar Ingila Tare DA Gabatar Da Lakca

Daga Muhammad Kwairi Waziri

A gobe Juma’a, tsohon ministan sadarwan Nigerian Farfesa Isa Ali Ibrahim (Pantami), CON, zai jagoranci sallar Juma’a a masallacin Seven Sisters Masjid, dake No. 1 Lawrence Road, N15 4EG, London, England, tare da gabatar da lakca mai taken "Mu’amalarmu da Al-Qur’ani".

Ana sa ran hudubar za ta fara ne da misalin ƙarfe 1 na rana, In sha Allah.



’a

YANZU-YANZU: Jarumin Tiktok Na Kasar Nijar Ya Rasu A MakkahRahotanni daga Jaridar Damagaram Post sun tabbatar da rasuwar...
23/10/2025

YANZU-YANZU: Jarumin Tiktok Na Kasar Nijar Ya Rasu A Makkah

Rahotanni daga Jaridar Damagaram Post sun tabbatar da rasuwar wani fitaccen jarumin TikTok daga ƙasar Nijar a Makkah, Saudiyya.

Marigayin ya rasu ne bayan kai ziyara a ƙasa mai tsarki a karon farko a rayuwarsa. Wannan lamari ya girgiza masoyansa da mabiyansa a kafafen sada zumunta, inda mutane ke aike da sakonnin ta’aziyya da addu’a.

Babu karin bayani kan musabbabin rasuwar sa a yanzu, amma al’ummar TikTok da 'yan Nijar na ci gaba da nuna alhini da girmamawa ga rayuwarsa. Allah ya jikansa.

YANZU-YANZU: An Katse Intanet A Kasar Kamaru Yayin Da Ake Dakon Jiran Sakamakon ZabeHukumomin kasar Kamaru sun katse han...
23/10/2025

YANZU-YANZU: An Katse Intanet A Kasar Kamaru Yayin Da Ake Dakon Jiran Sakamakon Zabe

Hukumomin kasar Kamaru sun katse hanyoyin sadarwar Intanet a sassa da dama na kasar, yayin da jama’a ke dakon sanar da sakamakon zaben shugaban kasa da aka gudanar a ranar 12 ga Oktoba, 2025.

Rahotanni daga biranen Garoua, Maroua, Ngaoundéré, da Mokolo sun nuna cewa akwai yunkurin hana yaduwar bayanai, musamman bayan barkewar zanga-zanga kan zargin magudin zabe.

Matakin ya janyo damuwa daga kungiyoyin kare hakkin bil’adama da masu lura da dimokuradiyya, wadanda ke bukatar a saki Intanet domin tabbatar da gaskiya da adalci.

DA DUMI-DUMI: Trailer  Ɗauke Da Kaya Ta Yi Hatsari A Kan Hanyar Darazo Zuwa BauchiWata babbar mota mai ɗauke da kaya ta ...
23/10/2025

DA DUMI-DUMI: Trailer Ɗauke Da Kaya Ta Yi Hatsari A Kan Hanyar Darazo Zuwa Bauchi

Wata babbar mota mai ɗauke da kaya ta yi hatsari da safiyar yau a kusa da ƙauyen Gabarin, a cikin ƙaramar hukumar Darazo ta jihar Bauchi.

Rahotanni sun bayyana cewa motar ta kufce ne yayin tafiya, inda ta fadi a gefen hanya, lamarin da ya haddasa cikas ga zirga-zirgar ababen hawa na wani lokaci.

Duk da cewa ba a tabbatar da asarar rai ba, wasu ganau sun ce akwai barazanar hatsari ga wasu fasinjoji da ke kusa da wurin.

Jami’an tsaro da na agajin gaggawa sun garzaya wurin domin tabbatar da tsaro da kuma dakile yuwuwar aukuwar karin hadurra.

DA DUMI-DUMI: Majalisar Wakilai Ta Fara Duba Kudirin Gyaran Dokar EFCC Don Ba Ta Cikakken ‘YanciMajalisar Wakilan Tarayy...
23/10/2025

DA DUMI-DUMI: Majalisar Wakilai Ta Fara Duba Kudirin Gyaran Dokar EFCC Don Ba Ta Cikakken ‘Yanci

Majalisar Wakilan Tarayyar Najeriya ta fara nazarin wani kudirin gyaran dokar Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) da nufin ba ta cikakken ‘yanci daga tsoma bakin bangaren zartarwa.

Kudirin wanda wani dan majalisar ya gabatar, yana neman tabbatar da cewa hukumar EFCC za ta kasance cikakkiyar hukuma mai ‘yancin gudanar da ayyukanta ba tare da dogaro da umarni daga Ma’aikatar Shari’a ko Ofishin Shugaban Kasa ba.

A cewar ‘yan majalisar, sauye-sauyen da kudirin ke dauke da su za su taimaka wajen inganta aikin yaki da cin hanci da rashawa a kasar, tare da tabbatar da cewa hukumar na iya aiwatar da aikinta ba tare da tsoro ko nuna son rai ba.

Ana sa ran majalisar za ta ci gaba da karanta kudirin a mataki na biyu a makonni masu zuwa, tare da gayyatar jama’a da masana don bayar da shawarwari kafin amincewa da shi gaba ɗaya.

Gwamnatin Najeriya Ta Nemi Tallafin Dala Biliyan 10 Daga Majalisar Dinkin Duniya Don ‘Yan Gudun HijiraA wani mataki na k...
23/10/2025

Gwamnatin Najeriya Ta Nemi Tallafin Dala Biliyan 10 Daga Majalisar Dinkin Duniya Don ‘Yan Gudun Hijira

A wani mataki na kokarin magance matsalar ‘yan gudun hijira a cikin gida, gwamnatin Najeriya ta nemi taimakon Majalisar Dinkin Duniya (UN) domin samun tallafin dogon lokaci na dala biliyan 10.

Gwamnatin ta bayyana cewa an nemi wannan tallafi ne don tallafa wa dubban ‘yan Najeriya da s**a rasa matsugunansu sakamakon rikice-rikicen da s**a hada da rashin tsaro da bala’o’in dan adam a sassa daban-daban na kasar.

An bayyana bukatar tallafin ne a wani taro da wakilan Najeriya s**a halarta, inda s**a jaddada cewa samar da mafita mai dorewa ga ‘yan gudun hijira ya zama dole domin dorewar zaman lafiya da ci gaban kasa.

YANZU-YANZU: Zanga-Zanga Ta Barke A Jihohin Kasar Kamaru Kan Zargin Magudin ZabeRahotanni daga kasar Kamaru na nuna cewa...
23/10/2025

YANZU-YANZU: Zanga-Zanga Ta Barke A Jihohin Kasar Kamaru Kan Zargin Magudin Zabe

Rahotanni daga kasar Kamaru na nuna cewa zanga-zanga ta barke a jihohin Garoua, Maroua, Ngaoundéré, Guider da Mokolo, sakamakon zargin da ake yi na magudin zaben shugaban ƙasa da aka gudanar a ranar 12 ga Oktoba, 2025.

Masu zanga-zangar na bayyana rashin amincewa da yadda aka tafiyar da zaben, suna masu kira da a kare muradun jama’a tare da tabbatar da gaskiya da adalci.

A halin yanzu, gwamnatin Kamaru ta fara daukar matakan dakile yaduwar bayanai ta hanyar rufe hanyoyin sadarwa a wasu daga cikin jihohin da ke fama da zanga-zangar.

Lamarin na ci gaba da daukar hankalin kafafen yada labarai da kungiyoyin kare hakkin bil’adama, yayin da ake jiran hukuncin karshe daga hukumar zabe ta kasar.

Ba Na Tsoma Baki A Gudanarwar Gwamnatin Jihar Kano Ko Raba Kwangiloli, Inji Rabi’u Musa KwankwasoTsohon Gwamnan Kano kum...
23/10/2025

Ba Na Tsoma Baki A Gudanarwar Gwamnatin Jihar Kano Ko Raba Kwangiloli, Inji Rabi’u Musa Kwankwaso

Tsohon Gwamnan Kano kuma jagoran jam’iyyar NNPP a matakin ƙasa, Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana cewa ba ya tsoma baki a cikin tafiyar da gwamnatin Kano, b***e ma batun raba kwangiloli ko yanke shawara a gwamnati.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da manema labarai, inda ya ce, gwamnatinsu tana da tsarin bin doka da oda, kuma kowa na da aikinsa.

A cewarsa, “Ni da Gwamna Abba Kabir Yusuf muna da cikakken fahimta, amma ba na cikin gwamnati. Ba ni da hannu a tsarin raba kwangila ko yanke hukunci a cikin gwamnati.”

Ya ce duk da kasancewarsa jagora a jam’iyyar, yana bai wa gwamna damar gudanar da aikinsa cikin ’yanci da mutuntaka.

Kwankwaso ya kuma bukaci ’yan adawa su guji yada jita-jita da kawo rudani, yana mai cewa zaman lafiya da ci gaban Kano shi ne buri.

YANZU-YANZU: Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban Hukumar Zabe INECShugaban ƙasa Bola Ahmed T...
23/10/2025

YANZU-YANZU: Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban Hukumar Zabe INEC

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Farfesa Adebayo Amupitan a matsayin sabon shugaban hukumar zaɓe ta ƙasa (INEC) bayan kammala wa’adin Farfesa Mahmood Yakubu.

An gudanar da rantsuwar ne da safiyar yau a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja, inda Tinubu ya jaddada muhimmancin yin gaskiya da adalci wajen gudanar da harkokin zaɓe a ƙasar.

Sabon shugaban INEC, Farfesa Amupitan, ya sha alwashin inganta tsarin zaɓe, ya kuma tabbatar da cewa hukumar za ta zama abar amincewa da dukkan ‘yan Najeriya.

An sa ran sabon shugaban zai fuskanci kalubale da dama, ciki har da gyara tsarin BVAS da kuma dawo da amincewar jama’a da sahihancin zaɓe a ƙasar.

TIRKASHI: Yadda Nnamdi Kanu Ya Fashe Da Kuka A Farfajiyar Kotu Tarayya Dake Abuja
23/10/2025

TIRKASHI: Yadda Nnamdi Kanu Ya Fashe Da Kuka A Farfajiyar Kotu Tarayya Dake Abuja

DA ƊUMI-ƊUMI: Jami’an Tsaro Sun Kashe Ƴan Ta’adda Sama da 300 A Jihar Borno, Sun Ƙwato Fursunoni Da MakamaiRahotanni dag...
23/10/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Jami’an Tsaro Sun Kashe Ƴan Ta’adda Sama da 300 A Jihar Borno, Sun Ƙwato Fursunoni Da Makamai

Rahotanni daga jihar Borno sun bayyana cewa dakarun tsaron Najeriya sun kai gagarumar samame a jiya, inda s**a kashe ƴan ta’adda sama da 300 a dazukan Dikwa, Mafa, Gajiko da Katarko.

Bayan kashe gungun ƴan ta’addan, jami’an tsaron sun kuma ceto mutane da dama da aka yi garkuwa da su, tare da ƙwato muggan makamai da mashinan hawa sama da guda 200 da ke hannun miyagun.

Wannan samame na cikin jerin matakan da rundunar tsaro ke ɗauka domin murkushe ta’addanci da kawo zaman lafiya mai ɗorewa a yankin Arewa maso Gabas.

Jami’an tsaro sun bayyana cewa za su ci gaba da sintiri da kai farmaki a wuraren da ake zargin mafakar ƴan ta’adda ne har sai an tabbatar da murkushe su gaba ɗaya.

Address

JMG Plaza, Opposite Immagration Office
Gombe
741212

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Gombawa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Gombawa:

Share