Jewel Online Media TV

Jewel Online Media TV JOM-TV tashar telebijin ce ta yanar gizo dake yada sahihan labarun duniya da shirye-shirye masu ilmantarwa da wayar da kan al'umma.

Wannan ita ce fitar Buhari ta ƙarshe daga Villa
13/07/2025

Wannan ita ce fitar Buhari ta ƙarshe daga Villa

An sassauto da tutocin Nijeriya ƙasa, domin girmamawa ga marigayi tsohon shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari.
13/07/2025

An sassauto da tutocin Nijeriya ƙasa, domin girmamawa ga marigayi tsohon shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari.

Buhari dattijon arziki ne - Shugaba Tinubu
13/07/2025

Buhari dattijon arziki ne - Shugaba Tinubu

Innalillahi wa inna ilaihi rajiun Allah yayi wa Buhari Rasuwa😭
13/07/2025

Innalillahi wa inna ilaihi rajiun

Allah yayi wa Buhari Rasuwa😭

Ba Na Cikin Haɗakar ADC Domin Suma Buƙatar Kai Ce A Gabansu Ba Al'ummar Nijeriya Ba, Inji Manjo Al-MustaphaBabban dogari...
13/07/2025

Ba Na Cikin Haɗakar ADC Domin Suma Buƙatar Kai Ce A Gabansu Ba Al'ummar Nijeriya Ba, Inji Manjo Al-Mustapha

Babban dogarin tsohon shugaban ƙasa Abacha, Hamza Al-mustapha, ya nesanta kansa da haɗakar jam'iyyu ta ADC, inda ya bayyana ta a matsayin taron 'yan siyasa da buƙatar kansu ta zarta ta 'yan Nijeriya.

Me zaku ce?

Tarbar da Daliban Jihar Gombe karkashin Gombe State Students Association (GOSSA) dake karatu a Federal University Gashua...
13/07/2025

Tarbar da Daliban Jihar Gombe karkashin Gombe State Students Association (GOSSA) dake karatu a Federal University Gashua, su ka yi wa Majidadin Daular Usmaniyya, Professor Isa Ali Ibrahim Pantami, CON a ya yin zuwan sa Jaami'ar domin gabatar da Convocation Lecture na ya ye dalibai da dadin su ya kai, 3449.
Allah Ya saka wa GOSSA Federal University Gashua da alheri da dukkan sauran dalibai, Ya karawa Ilminsu albarka duniya da lahira.

Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya karɓi baƙuncin Shugaban Jam’iyyar Labour Party na Ƙasa, Mista Julius Abure, yau a Abuja.
13/07/2025

Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya karɓi baƙuncin Shugaban Jam’iyyar Labour Party na Ƙasa, Mista Julius Abure, yau a Abuja.

Hotunan Yaƙin Neman Zaɓen Shugaban Ƙasa Tinubu Da Kashim Shettima A Jihar Borno A Zaɓen 2023Shin Kuna Ganin Cewa Taba Ka...
13/07/2025

Hotunan Yaƙin Neman Zaɓen Shugaban Ƙasa Tinubu Da Kashim Shettima A Jihar Borno A Zaɓen 2023

Shin Kuna Ganin Cewa Taba Kashim Shettima Na Iya Sawa Ƴan Jihar Su Juyawa Jam’iyyar APC Baya ?

SANARWA: Jama’a Ku Yi Watsi Da Duk Wani Saƙo Da Za Ku Gani A Shafin X Na Gwamnan Jihar Adamawa Ba Daga Shi Ba Ne, Cewar ...
13/07/2025

SANARWA: Jama’a Ku Yi Watsi Da Duk Wani Saƙo Da Za Ku Gani A Shafin X Na Gwamnan Jihar Adamawa Ba Daga Shi Ba Ne, Cewar Fadar Gwamnatin Jihar

Gwamnatin Jihar Adamawa ta yi kira da jan hankalin jama’a da su yi watsi da duk wani saƙo da za su gani a shafin X (Twitter) na gwamnan Jihar, Ahmadu Umaru Fintiri, a cewar fadar gwamnatin Jihar, masu kutse (Hackers) ne s**a kutsa cikin shafin, dan haka duk wani bayani ko saƙo da za a ci karo da shi daga shafin ba shi da alaƙa da gwamnan ko gwamnatinsa, kamar yadda Dokin Ƙarfe TV ta ruwaito.

Sanarwar mai ɗauke da sa hannun babban sakataren yaɗa labarai na gwamnan, Humwashi Wonosikou, ta ƙara da cewa, "Mai girma gwamna ya bayyana takaicinsa matuƙa kan faruwar wannan al’amari marar daɗi ko zubda kima da masu kutse s**a yi. Muna aiki tuƙuru domin dawo da shafin cikin aminci". Cewar sanarwar.

Sanarwar ta kuma ƙara da sanar da al’umma cewa a yanzu za a riƙa ɗora duk wata sanarwa, bayani ko jawabi daga ofishin gwamnan kai tsaye a sahihan shafuka da aka aminta da su a hukumance. "Muna ƙara jan hankalin al’umma da su kula, su yi watsi da duk wani bayani ko saƙo da za su gani daga wancan shafi da aka yi wa kutse, mun gode da fahimtarku da haɗin-kanku kan wannan al’amari". In ji sanarwar.

Zan Jagoranci Kayar Da Jam’iyyar APC A Zaɓen 2027 Insha Allah -inji Malam Nasiru El-Rufa'iKana ɗaya daga cikin ƴan Nijer...
13/07/2025

Zan Jagoranci Kayar Da Jam’iyyar APC A Zaɓen 2027 Insha Allah -inji Malam Nasiru El-Rufa'i

Kana ɗaya daga cikin ƴan Nijeriya masu goyon bayan wannan ƙuduri na El-Rufa’i?

ZAƁEN GWAJI: Tsakanin Jam'iyyar APC Da ADC Wace Jam'iyya Zaka Jafawa Ƙuri'a A Zaɓen 2027 ?A Kafta....
13/07/2025

ZAƁEN GWAJI: Tsakanin Jam'iyyar APC Da ADC Wace Jam'iyya Zaka Jafawa Ƙuri'a A Zaɓen 2027 ?

A Kafta....

MU TATTAUNA: Idan Jam'iyyar ADC Ta Tsayar Da Malam Nasiru El-rufa'i Takarar Shugaban Ƙasa A Zaɓen 2027; Za Ka Iya Zaɓars...
13/07/2025

MU TATTAUNA: Idan Jam'iyyar ADC Ta Tsayar Da Malam Nasiru El-rufa'i Takarar Shugaban Ƙasa A Zaɓen 2027; Za Ka Iya Zaɓarsa Ka Ajiye Tinubu A Gefe?

Address

Gombe

Telephone

+2348162588596

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jewel Online Media TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jewel Online Media TV:

Share

Category