Progress Radio TV Gombe

Progress Radio TV Gombe This platform would serve as a platform for people to progressively express themselves in the drive
(218)

PROGRESS RADIO FOR HIGH QUALITY TRANSMISSION, REPORTAGE, CURRENT AFFAIRS & ENTERTAINMENT

Mai Alfarma Sarkin Musulmi kuma shugaban majalisar ƙoli ta harkokin addinin Musulunci, Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar ya...
24/08/2025

Mai Alfarma Sarkin Musulmi kuma shugaban majalisar ƙoli ta harkokin addinin Musulunci, Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar ya sanar da gobe Litinin a matsayin 1 ga watan Rabi'ul Awwal.

Hakan na masu ƙunshe ne cikin wata sanarwa daga Wazirin Sakkwato kuma shugaban majalisar shawarwari ta fadar Sarkin Musulmi, Farfesa Sambo Junaidu a ranar Asabar.

Ya ce sanarwar, wacce aka yi ta da haɗin gwiwar kwamitin duban wata, ta zo ne biyo bayan kasa ganin jaririn watan na Rabi'ul Awwal a jiya Asabar.

"Damina," a ƙarasa mana wannan karin maganar, Progress Radio ke muku barka da safiyar Lahadi.
24/08/2025

"Damina," a ƙarasa mana wannan karin maganar, Progress Radio ke muku barka da safiyar Lahadi.

Gwamnonin jam'iyyar adawa ta PDP a Najeriya sun hallara a birnin Gusau na jihar Zamfara domin yin wani taron tattaunawa....
23/08/2025

Gwamnonin jam'iyyar adawa ta PDP a Najeriya sun hallara a birnin Gusau na jihar Zamfara domin yin wani taron tattaunawa.

Suna gudanar da taron ne a matsayin sharar fage kafin taron kwamatin gudanarwa mai muhimmanci da za su yi ranar Litinin mai zuwa.

Ministan Abuja Nyesom Wike - wanda har yanzu yake iƙirarin zama ɗan jam'iyyar duk da kasancewarsa a gwamnatin APC mai mulki - ya soki taron da za a yi a jihar Oyo, inda ya ci alwashin hana gudanar da shi.

Gwamna Dauda Lawal ne ke karɓar baƙuncin gwamnonin tara daga sassan Najeriya a yau Asabar.

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya buƙaci ƴan ƙasar da ke ƙetare su dawo gida, ya na mai cewa ƙasa ta gyaru. Tinubu...
23/08/2025

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya buƙaci ƴan ƙasar da ke ƙetare su dawo gida, ya na mai cewa ƙasa ta gyaru.

Tinubu ya ce, tattalin arziƙin Najeriya ya inganta tun bayan zuwansa kan madafun iko, don haka duk ƴan ƙasar da ke zaune a ƙasashen waje su koma gida.

Ku kasance da Maryam Atiku a Zango Na Biyu na kafar yaɗa labarai ta Progress Radio Gombe Najeriya.
23/08/2025

Ku kasance da Maryam Atiku a Zango Na Biyu na kafar yaɗa labarai ta Progress Radio Gombe Najeriya.

Hedikwatar tsaron Najeriya ta yi ƙarin haske game da ƙiran da babban hafsan hafsoshin ƙasar, Janar Christopher Musa, ya ...
23/08/2025

Hedikwatar tsaron Najeriya ta yi ƙarin haske game da ƙiran da babban hafsan hafsoshin ƙasar, Janar Christopher Musa, ya yi, cewa jama'a su fara tunanin koyon dabarun kare kansu da aka amince da su a duk faɗin duniya.

Ta ce jama'a sun yi wa wannan ƙira wata fahimta ta daban, to amma abin da babban jami'in tsaron ke nufin shi ne ba wai mutane su ɗauki makami su kare kansu ba, a'a yana nufin su koyi abubuwa k**ar kokowa da judo da dambe da ninkaya da gudu dama tukin mota da dai sauransu.

Birgediya Janar Tukur Gusau, shi ne daraktan yada labarai na rundunar tsaron Najeriya, ya shaida wa kafar yaɗa labarai ta BBC cewa shi babban hafsan tsaron na nufin cewa a matsayinka na ɗan adam bai k**ata ka zauna haka kawai ba tare da ka koyi wata dabara da za ka kare kanka ba.

Ya ce," A misali irin mutanen nan da ke ƙetare mutane suna kwace musu waya da yawansu wasunsu basa ɗauke da makami ƙarfi kawai suke nuna wa jama'a, to irin wannan yanayi ne shi babban hafsan tsaron ke ganin ya k**ata mutane su koyi dabarun kansu k**ar kokawa da gudu, inda duk wanda ya nuna maka ƙarfi kai ma sai ka ware gwanjinka."

"Maganar a ɗauki makami ma dokoki na Najeriya ma basu yadda wanda ba shi da hurumin ɗaukar makami su ɗauka ba, idan kuwa har s**a ɗauki makami to akwai dokar da zata yi aiki a kansu."In ji Janar Tukur Gusau.

"Inuwar giginya," a ƙarasa mana wannan karin maganar, Progress Radio ke muku barka da safiyar Asabar.
23/08/2025

"Inuwar giginya," a ƙarasa mana wannan karin maganar, Progress Radio ke muku barka da safiyar Asabar.

Gwamnatin Najeriya ta sanar da cewa ba za ta gajiya ba har sai ta farauto maharan da s**a kashe masallata a garin Malumf...
22/08/2025

Gwamnatin Najeriya ta sanar da cewa ba za ta gajiya ba har sai ta farauto maharan da s**a kashe masallata a garin Malumfashi da ke jihar Katsina, saboda a cewarta, maharan sun nuna rashin imani a harin.

Cikin wata sanarwa da ministarn yaɗa labaran ƙasar ya fitar, gwamnatin tarayya za ta tabbatar an maharan tare da gurfanar da su a gaban shari'a, k**ar yadda kafar yaɗa labarai ta BBC ta ruwaito.

Ministan ya ce tuni jami'an tsaro s**a fara bibiyar maharan, inda ya ƙara da cewa ba za su gajiya ba sai an k**a waɗannan s**a kai harin.

Ya ce Shugaba Tinubu na miƙa ta'aziyarsa ga iyalan waɗanda aka kashe, da mutanen Malumfashi da jihar Katsina da ma ƙasar baki ɗaya da ma iyalan waɗanda aka kashe.

Ya ce daga cikin ƙoƙarin da gwamnati ke yi na kawo ƙarshen lamarin akwai k**a fitattun ƴan ƙungiyar Ansaru da ake zargi da fasa gidan yarin Kuje da sauran nasarori.

Fadar shugaban ƙasa ta ce shugaba Bola Tinubu ya zarce Brazil bayan halartar taruka a Japan.A wata sanarwa da kakakin sh...
22/08/2025

Fadar shugaban ƙasa ta ce shugaba Bola Tinubu ya zarce Brazil bayan halartar taruka a Japan.

A wata sanarwa da kakakin shugaban ƙasar, Bayo Onanuga ya fitar, Tinubu zai yada zango a birnin Los Angeles na ƙasar Amurka kafin ya wuce birnin Brasilia na ƙasar Brazil domin ziyarar aiki da zai fara daga ranar 24 ga watan Agusta.

Address

Plot No. 5988, Tumfure, Bauch Road, North-Eastern
Gombe

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Progress Radio TV Gombe posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Progress Radio TV Gombe:

Share