07/06/2026
Babban abin da ya jawo Abhijeet Dipke ya kafa jam'iyyar Kenkesai ta Cockroach Janta Party (CJP), shi ne wasu kalaman "cin mutuncin" matasa da babban alƙalin Indiya ya yi kuma s**a fito fili.
A ranar 15 ga watan Mayu na shekarar 2026, Shugaban Alƙalan Indiya (CJI), Surya Kant, ya yi wani bayani a lokacin shari'a inda ya kwatanta matasa marasa aikin yi da kuma masu rajin kare hakki da "Kenkesai" kuma "annoba a cikin al'umma".
Wannan jawabi ya fusata matasan Indiya matuƙa, inda Abhijeet Dipke, wani matashi mai shekaru 30 masanin dabarun sadarwa na siyasa wanda ke karatu a jami'ar Boston ta Amurka, ya wallafa a shafinsa na X (Twitter) cewa: "Mene ne zai faru idan dukkan Kyankyasai s**a hadu?".
Daga nan ya kafa wannan tafiya a ranar 16 ga Mayu, 2026 a matsayin barkwancin siyasa, inda ya sanyawa jam'iyyar suna, "Cockroach Janta Party," an ari sunan ne don yin ba'a ga jam'iyyar firaminista Narendra Modi mai mulki, wato Bharatiya Janata Party (BJP).
Duk da cewa an fara tafiyar a matsayin wasa da barkwanci a intanet, cikin kwanaki kalilan abubuwa sun sauya saboda fushin da matasa ke ciki.
Cikin mako guda kacal, shafin Instagram na jam'iyyar ya tara mabiya sama da miliyan 22, adadin da ya ninka na jam'iyyar BJP mai mulki.
Matasa sama da dubu dari takwas kuma s**a sanya hannu a takardar koke ta intanet.
Tafiyar ta dauki zafi sosai bayan bullar badakalar satar takardun jarabawar shiga manyan makarantun magani da kwaleji na kasa, kamar jarabawar NEET-UG ta 2026.
Matasa da dama sun shiga damuwa har wasu s**a kashe kansu saboda wannan aika-aika a harkar ilimi.
Baya ga dandalin sadarwa, Abhijeet Dipke ya dawo Indiya daga Amurka, kuma ya jagoranci taron matasa a ranar Asabar 6 ga Yuni, 2026 a dandalin Jantar Mantar da ke birnin Delhi.
Suna fafutuka da zanga-zangar neman lallai sai Ministan Ilimi na Indiya, Dharmendra Pradhan, ya yi murabus saboda gazawa da cin hanci da rashawa a harkar jarabawar kasar.
Sannan suna amfani da damar wajen kalubalantar gwamnatin Modi kan rashin aikin yi ga matasa, hauhawar farashin kayayyaki, da takura wa 'yancin fadin albarkacin baki.
Gwamnatin Indiya ta dauki lamarin da gaske har ta kai ga an toshe shafin X (Twitter) na jam'iyyar a cikin kasar, yayin da wasu ministocin Modi ke zargin tafiyar da samun goyon baya daga kasashen waje don bata wa kasar suna.
Duk da haka, matasan na Gen-Z sun ce ba za su ja da baya ba.