Progress Radio TV Gombe

Progress Radio TV Gombe This platform would serve as a platform for people to progressively express themselves in the drive
(222)

PROGRESS RADIO FOR HIGH QUALITY TRANSMISSION, REPORTAGE, CURRENT AFFAIRS & ENTERTAINMENT

Gwamnatin jihar Kaduna ta fara horar da dakarun tsaron gandun daji 1,000 domin taimakawa wajen kare dazuka da kuma fatat...
07/06/2026

Gwamnatin jihar Kaduna ta fara horar da dakarun tsaron gandun daji 1,000 domin taimakawa wajen kare dazuka da kuma fatattakar masu aikata laifi da ke fakewa a cikin su domin yaƙi da rashin tsaro a jihar.

An ce dakarun za su rika lura da motsin da ake yi a dazuka, tare da tattara bayanan sirri da taimakawa jami’an tsaro wajen dakile hare-haren ‘yan bindiga musamman a yankunan da ke fama da matsalar tsaro.

Gwamna Uba Sani, wanda sakataren ma’aikatar fadar gwamnati ya wakilta, ya buƙaci wadanda ke karbar horon su kasance masu ladabi da kwarewa, yana mai cewa za a tura su yankunan da s**a fi fama da matsala bayan kammala horaswar makonni shida.

Gwamnatin ta ce shirin na daga cikin matakan da ake dauka domin kare rayuka da dukiyoyi, da kuma bai wa manoma damar komawa gonakinsu cikin kwanciyar hankali.

Rundunar Sojin Najeriya ta ce sojojinta na Operation Hadin Kai sun ceto kimanin mata da yara 360 da '’yan ta’adda' s**a ...
07/06/2026

Rundunar Sojin Najeriya ta ce sojojinta na Operation Hadin Kai sun ceto kimanin mata da yara 360 da '’yan ta’adda' s**a sace daga ƙauyen Ngoshe da ke ƙaramar hukumar Gwoza a Jihar Borno.

A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar a shafinta na X, kakakin rundunar, Manjo Janar Abdulsalam Abubakar, ya ce aikin ceton ya gudana ne a ranar 6 ga Yuni, tare da haɗin gwiwar sauran runduna ta Musamman a yankunan da ke kusa da Dutsen Mandara.

Ya ce sojojin sun gudanar da aikn ne da dabarun da s**a rikita sansanonin ’yan ta’adda, wanda hakan ya ba su damar shiga da kuma kuɓutar da mutanen cikin nasara.

A cewarsa, mutanen da aka ceto an sace su ne a harin da aka kai Ngoshe a ranar 3 ga Maris, 2026.

Sai dai ya ce an samu asarar rayukan jarirai biyu yayin aikin ceto, sakamakon wahalar hanya da yanayin da aka fuskanta yayin fitar da su zuwa wuri mai aminci.

Ya ƙara da cewa dukkan waɗanda aka ceto an yi musu gwaje-gwajen lafiya nan take, inda aka kwantar da wasu a Asibitin Gwamnati da ke Gwoza domin ƙarin kulawa, yayin da aka ba su abinci da ruwa kafin a tura su wurin da ake kula da su na wucin gadi.

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya umarci a sake duba dabarun tsaro da ake amfani da su a jihar sakamakon karuwar hare...
07/06/2026

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya umarci a sake duba dabarun tsaro da ake amfani da su a jihar sakamakon karuwar hare-haren ‘yanbindiga a wasu yankuna.

Umarnin ya biyo bayan taron gaggawa na jami’an tsaro da gwamnati da aka gudanar a Birnin Kebbi, inda aka tattauna hanyoyin magance sabbin matsalolin tsaro, musamman hare-haren kungiyar Lakurawa a masarautar Wasagu da wasu sassan masarautar Argungu.

Gwamnan ya ce kare rayuka da dukiyoyin al’umma shi ne babban abin da gwamnati ta sa a gaba, yana mai jaddada cewa za a dauki duk matakan da s**a dace domin dakile matsalar.

A yayin taron, mataimakin gwamnan jihar, Umar Abubakar Tafida, ya jagoranci tawagar gwamnati zuwa Wasagu domin jajanta wa wadanda hare-haren s**a shafa tare da tantance halin da ake ciki.

Gwamnatin jihar ta bayyana cewa ta samar da motocin aiki sama da 100, babura 7,000 tare da horas da dubban matasa domin taimakawa ayyukan tsaro a matakin al’umma.

Gwamna Idris ya kuma ce zai gabatar wa Bola Tinubu da hukumomin tsaro na tarayya rahoton halin tsaron jihar da shawarwarin da za su taimaka wajen samar da mafita mai dorewa ga matsalar tsaro a Kebbi.

Atiku ya miƙa ta'aziyya bisa rasuwar Abubakar Sadiq Pharmacy Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya miƙa sa...
07/06/2026

Atiku ya miƙa ta'aziyya bisa rasuwar Abubakar Sadiq Pharmacy

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya miƙa saƙon ta’aziyyarsa bisa rasuwar Malam Sadiq Pharmacy, fitaccen malamin addinin Musulunci a Najeriya.

Atiku ya bayyana Pharmacy a matsayin jajirtaccen malami mai karantar da Alƙur’ani kuma mai ba da magungunan Musulunci wanda iliminsa da ayyukansa s**a yi tasiri ga rayuwar al’umma da dama a Jihar Gombe da ma sauran sassan ƙasar nan.

Ya kuma bayyana marigayin a matsayin mutumin da ya sadaukar da rayuwarsa wajen yaɗa koyarwar Musulunci, tafsirin Alƙur’ani mai girma da kuma hidimtawa al’ummar Musulmi.

Ya ce Malam Sadiq Pharmacy ya samu karɓuwa da girmamawa a tsakanin jama’a sakamakon iliminsa, hikimarsa da kuma ayyukan alheri da ya gudanar tsawon rayuwarsa.

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya jajanta wa iyalan marigayin, ɗalibansa, abokan hulɗarsa da daukacin al’ummar Jihar Gombe bisa wannan babban rashi.

Haka kuma ya yi addu’ar Allah Maɗaukakin Sarki Ya gafarta masa kura-kuransa, Ya yalwata masa kabari, Ya sanya shi cikin Aljannatul Firdaus. Amin.

Babban abin da ya jawo Abhijeet Dipke ya kafa jam'iyyar Kenkesai ta Cockroach Janta Party (CJP), shi ne wasu kalaman "ci...
07/06/2026

Babban abin da ya jawo Abhijeet Dipke ya kafa jam'iyyar Kenkesai ta Cockroach Janta Party (CJP), shi ne wasu kalaman "cin mutuncin" matasa da babban alƙalin Indiya ya yi kuma s**a fito fili.

A ranar 15 ga watan Mayu na shekarar 2026, Shugaban Alƙalan Indiya (CJI), Surya Kant, ya yi wani bayani a lokacin shari'a inda ya kwatanta matasa marasa aikin yi da kuma masu rajin kare hakki da "Kenkesai" kuma "annoba a cikin al'umma".

Wannan jawabi ya fusata matasan Indiya matuƙa, inda Abhijeet Dipke, wani matashi mai shekaru 30 masanin dabarun sadarwa na siyasa wanda ke karatu a jami'ar Boston ta Amurka, ya wallafa a shafinsa na X (Twitter) cewa: "Mene ne zai faru idan dukkan Kyankyasai s**a hadu?".

Daga nan ya kafa wannan tafiya a ranar 16 ga Mayu, 2026 a matsayin barkwancin siyasa, inda ya sanyawa jam'iyyar suna, "Cockroach Janta Party," an ari sunan ne don yin ba'a ga jam'iyyar firaminista Narendra Modi mai mulki, wato Bharatiya Janata Party (BJP).

Duk da cewa an fara tafiyar a matsayin wasa da barkwanci a intanet, cikin kwanaki kalilan abubuwa sun sauya saboda fushin da matasa ke ciki.

Cikin mako guda kacal, shafin Instagram na jam'iyyar ya tara mabiya sama da miliyan 22, adadin da ya ninka na jam'iyyar BJP mai mulki.

Matasa sama da dubu dari takwas kuma s**a sanya hannu a takardar koke ta intanet.

Tafiyar ta dauki zafi sosai bayan bullar badakalar satar takardun jarabawar shiga manyan makarantun magani da kwaleji na kasa, kamar jarabawar NEET-UG ta 2026.

Matasa da dama sun shiga damuwa har wasu s**a kashe kansu saboda wannan aika-aika a harkar ilimi.

Baya ga dandalin sadarwa, Abhijeet Dipke ya dawo Indiya daga Amurka, kuma ya jagoranci taron matasa a ranar Asabar 6 ga Yuni, 2026 a dandalin Jantar Mantar da ke birnin Delhi.

Suna fafutuka da zanga-zangar neman lallai sai Ministan Ilimi na Indiya, Dharmendra Pradhan, ya yi murabus saboda gazawa da cin hanci da rashawa a harkar jarabawar kasar.

Sannan suna amfani da damar wajen kalubalantar gwamnatin Modi kan rashin aikin yi ga matasa, hauhawar farashin kayayyaki, da takura wa 'yancin fadin albarkacin baki.

Gwamnatin Indiya ta dauki lamarin da gaske har ta kai ga an toshe shafin X (Twitter) na jam'iyyar a cikin kasar, yayin da wasu ministocin Modi ke zargin tafiyar da samun goyon baya daga kasashen waje don bata wa kasar suna.

Duk da haka, matasan na Gen-Z sun ce ba za su ja da baya ba.

06/06/2026

Jam'iyyar Kyankyasai ta Cockroach Janta Party, kaddamar da gangamin zanga-zangar adawa da yadda gwamnatin Firaministan Indiya Narendra Modi, ke tafiyar da harkokin ilimi a kasar.

Shugaban kungiyar ta Cockroach Janta Party, Abhijeet Dipke, mai shekaru 30, wanda ke zaune a kasar Amurka a tsawon shekaru biyu, ya ce iyayensa na cikin fargaba saboda yunkurin gwamnati na cafke shi.

Ga rahoton Maryam Atiku.

DAGA WAKILAN PROGRESS. Ana ci gaba da kwashe ‘yan ci-rani daga Afirka ta Kudu bayan ƙarin hare-hare da tashin hankali da...
06/06/2026

DAGA WAKILAN PROGRESS.

Ana ci gaba da kwashe ‘yan ci-rani daga Afirka ta Kudu bayan ƙarin hare-hare da tashin hankali da ta shafe su a wasu yankuna na ƙasar.

Jam'iyyar Kyankyasai ta Cockroach Janta Party, kaddamar da gangamin zanga-zangar adawa da yadda gwamnatin Firaministan Indiya Narendra Modi, ke tafiyar da harkokin ilimi a kasar.

A Najeriya, Al'ummomin Garin Bela da ke jihar Zamfara sun bukaci gwamnatin jihar ta tallafawa mazauna yankin da ruwan sama ya rushe musu gidaje.

An sanya dokar hana fita a ƙaramar hukumar Karim-Lamido biyo bayan ƙaruwar tashe-tashen hankula da kashe mutane da lalat...
06/06/2026

An sanya dokar hana fita a ƙaramar hukumar Karim-Lamido biyo bayan ƙaruwar tashe-tashen hankula da kashe mutane da lalata dukiya da wasu da ake zargi ’yan sa-kai ne masu ɗauke da makamai suke yi.

Rahoranni sun bayyana cewa, ana zargin wasu rukunin ’yan sa-kan da kai hare-hare da dama a kan al’ummomin Wurkum da ke kewayen Didango da Mutum Daya, Kodai, Gurum, da sauran unguwanni, waɗanda s**a yi sanadin asarar rayukan mutane da dama.
An gano cewa lamura sun lafawa a unguwannin da abin ya shafa kwanaki biyu da s**a gabata bayan tura jami’an tsaro, sai dai kuma ’yan sa-kan sun sake ƙaddamar da wasu hare-haren a ranakun Alhamis da Juma’a.

An kuma gano cewa, tsanantar hare-haren ta tilasta wa Shugabar ƙaramar hukumar, Madam ɓirginia Bambur sanya dokar hana fita ta tsawon sa’o’i 24 a yankin, ciki har da garin Karim wanda shi ne babban birnin ƙaramar hukumar Karim-Lamido.

Shugabar Majalisar ƙaramar hukumar ta Karim-Lamido, Virginia Baba Bambur, ta bayyana a cikin wata sanarwa cewa, shawarar sanya dokar hana fita “A Karim da Didango da ɗaukacin yankunan da abin ya shafa ta zama dole saboda tsanantar rikicin, ci gaba da kai hare-hare da kuma asarar rayuka da dukiya sakamakon tashin hankalin da ya dabaibaye waɗannan yankuna.

Ta kuma umarci ɗaukacin jami’an tsaro, wato Sojoji da ’Yan sanda da jami’an tsaron farin kaya DSS, da na Civil Defense NSCDC da sauransu da ke ƙaramar hukumar da su lura da wannan umarni kuma su tabbatar an kiyaye dokar.

Virginia Baba Bambur ta ci gaba da cewa, gwamnati za ta gudanar da bincike na tsaf domin gano ainihin tushen lamarin, sannan ta tabbatar da cewa an hukunta waɗanda ke da hannu a ciki.

A Najeriya yayinda matsalar tsaro ke ƙara ta'azzara, ɗaya daga cikin jiga-jigan siyasa a shiyar arewa maso gabashin ƙasa...
06/06/2026

A Najeriya yayinda matsalar tsaro ke ƙara ta'azzara, ɗaya daga cikin jiga-jigan siyasa a shiyar arewa maso gabashin ƙasar, wato tsohon gwamnan Gombe, kuma sanata mai wakiltar Gombe ta tsakiya Muhamadu Danjuma Goje, ya ce ɗaya daga cikin dalilan da ke ƙara rura wutar matsala shi ne rashin hanyoyin sufuri.

A cewar sanatan, ya jima yana jan hankali da neman ganin an inganta hanyoyin jihohin yankin don shawo kan matsalar, kuma da alama a yanzu shugaban kasa ya ji kokensu, la'akari da yadda ya bada kwangilar soma aikin wasu muhimman hanyoyi a yanzu.

A cewarsa, ya ji daɗi a shugaban ƙasa ya amince da fara aikin tagwayen hanya daga Akwanga zuwa Jos zuwa Bauchi zuwa Gombe. "Da ya yi wannan ne sai na sake tashi na yi godiya, sannan na nemi a isar da hanyar ta kai Biu zuwa Maiduguri. Sannan na nemi a yi daga Gombe a yi tagwayen hanyar zuwa Yola ta ratse zuwa Jalingo. Idan an yi haka arewa maso gabas an mana komai."

Goje ya ƙara da cewa ya ji daɗi da ya ga har an je an duba aikin, saboda a cewarsa, "maganar gyara hanya na da muhimmanci, saboda masu ɓarna sun fi yi a wuraren da hanya babu kyau. Idan an gyara hanya, hakan zai taimaka wajen rage matsalolin tsaro a arewa musamman arewa maso gabas."

Hotunan yadda matasa mambobin jam'iyyar Kenkesai wato (Cockroach Janta Party), ke gudanar da zanga-zanga a birnin New De...
06/06/2026

Hotunan yadda matasa mambobin jam'iyyar Kenkesai wato (Cockroach Janta Party), ke gudanar da zanga-zanga a birnin New Delhi na Indiya.

Address

Plot No. 5988, Tumfure, Bauch Road, North-Eastern
Gombe

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Progress Radio TV Gombe posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Progress Radio TV Gombe:

Share