Progress Radio TV Gombe

Progress Radio TV Gombe This platform would serve as a platform for people to progressively express themselves in the drive
(212)

PROGRESS RADIO FOR HIGH QUALITY TRANSMISSION, REPORTAGE, CURRENT AFFAIRS & ENTERTAINMENT

Tsohon mai magana da yawun tsohon shugaban ƙasar Najeriya Muhammadu Buhari, Malam Garba Shehu, ya faɗi hakan ne a taron ...
02/07/2025

Tsohon mai magana da yawun tsohon shugaban ƙasar Najeriya Muhammadu Buhari, Malam Garba Shehu, ya faɗi hakan ne a taron manema labarai gabanin bikin ƙaddamar da littafin da ya rubuta a babban birnin tarayya Abuja.

Shehu ya ce, Buhari ya cire tallafin man fetur ne da kyakkyawar niyya, don bunƙasa arziƙin ƙasa, ba wata manufar siyasa ba.

Shahararen ɗan wasan ƙwallon ƙafa a duniya, Cristiano Ronaldo, ya ce, Saudiyya ta zama tamkar gida a gare shi da ya ke f...
02/07/2025

Shahararen ɗan wasan ƙwallon ƙafa a duniya, Cristiano Ronaldo, ya ce, Saudiyya ta zama tamkar gida a gare shi da ya ke fatan zama har abada a tsawon rayuwarsa.

Ronaldo, ya bayyana haka ne a yayin da yake tsawaita kwantiraginsa da ƙungiyarsa ta Al Nassr da yake taka wa leda, kamar yadda Aminiya ta ruwaito.

Ya kuma sha alwashin zura ƙwallaye 100 a kakar wasa ta bana, yana mai cewa, "Kakar wasa ta gaba za ta zamo mana kaka mafi kyau da za muyi alfahari da ita."

Dan gwagwarmayar kare haƙƙin ɗan Adam kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a ƙarkashin jam'iyyar AAC a zaɓen 2023, Omoyele Sow...
02/07/2025

Dan gwagwarmayar kare haƙƙin ɗan Adam kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a ƙarkashin jam'iyyar AAC a zaɓen 2023, Omoyele Sowore, ya bayyana cewa ba zai taɓa shiga cikin haɗakar ƴan adawan da ke neman kifar da jam’iyyar APC mai mulki a zaɓen 2027 ba.

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata, Sowore, ya ce, ba zai iya haɗa kai da wasu fitattun ƴan siyasa da ya zarga da rusa Najeriya ta hanyar cin hanci da rashawa, cin amanar ƙasa da zalunci.

"Ban taba haɗa kai da Bola Ahmed Tinubu wajen rarraba hodar iblis a birnin Chicago ba," in ji Sowore.

"Ban haɗa kai da Atiku Abubakar wajen wawure dukiyar Hukumar Kwastam ba, kuma ban taɓa shiga cikin barnar David Mark wanda ya saci kuɗaɗen da aka ware don gyara wayoyinmu sannan ya taimaka wajen murƙushe burin dimokuradiyyarmu a ranar 12 ga Yuni ba."

A cikin wannan s**a mai zafi ga tsarin siyasar Najeriya, Sowore ya jero wasu daga cikin manyan ƴan siyasa da ya ce, sun taka rawa wajen lalata ƙasar, ciki har da tsofaffin gwamnoni, ministoci da ƴan takarar shugaban ƙasa.

Sowore ya ƙi amincewa da ƙira da ake yi masa da ya sassauta tsayuwarsa kan aƙida saboda buƙatar siyasa, yana mai cewa,
bai taɓa shiga cikin ƙungiyoyin ƴan fashi da makami ba.

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, tsohon shugaban ƙasar Najeriya, Muhammadu Buhari na fama da rashin lafiya, inda majiyoy...
02/07/2025

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, tsohon shugaban ƙasar Najeriya, Muhammadu Buhari na fama da rashin lafiya, inda majiyoyi da dama s**a ce, kwanan nan aka sallame shi daga ɗakin kula da masu matsananciyar rashin lafiya (ICU) a wani asibiti da ke Landan a ƙasar Birtaniya.

Jaridar The Cable ta rawaito daga Empowered Newswire, wani makusancin tsohon shugaban na cewa, Buhari ya kamu da rashin lafiya ne a Landan yayin da ya je don duba lafiyarsa.

Rahoton ya ce an kwantar da Buhari a dakin ICU, amma daga bisani aka sallame shi a makon da ya gabata.

Ko da ya ke ba a bayyana irin cutar da ke damunsa ba, rahotanni sun nuna cewa yana samun sauƙi a Landan, kuma ana sa ran zai dawo Najeriya da zarar ya warke gaba ɗaya.

Empowered Newswire, ta ƙara da cewa, bisa bayanan da s**a samu daga wasu majiyoyi masu tushe, Mamman Daura da ke zama kawun Buhari kuma amintaccensa, shima yana samun sauki daga rashin lafiya a kasar Birtaniya.

Buhari bai halarci bikin cika shekaru 50 da kafuwar Kungiyar raya Tattalin Arziƙin Ƙasashen Yammacin Afrika (ECOWAS) da aka gudanar a Legas ranar 28 ga Mayu ba.

A wata wasika da ya aika wa Shugaba Bola Tinubu, Buhari ya bayyana cewa rashin halartar sa taron ya samo asali ne bisa tafiyarsa ta duba lafiya a Birtaniya.

"Ɓatar Basira" a ƙasa mana wannan karin maganar, Progress Radio ke muku barka da safiyar Laraba.
02/07/2025

"Ɓatar Basira" a ƙasa mana wannan karin maganar, Progress Radio ke muku barka da safiyar Laraba.

Shin ka na layin masu baza Capacity ne ko kuma Pacacity?
01/07/2025

Shin ka na layin masu baza Capacity ne ko kuma Pacacity?

Wani rahoto ya nuna cewa kashi 85% na matsa a Arewacin Najeriya, ba sa iya mai da hankali wajen sarrafa kafafen sada zum...
01/07/2025

Wani rahoto ya nuna cewa kashi 85% na matsa a Arewacin Najeriya, ba sa iya mai da hankali wajen sarrafa kafafen sada zumunta domin janyo hankalin gwamnati kan matsalolin da ke addabar yankunan su a cikin ƙarewa.

An haɗa wannan rahoto ne ta hanyar tattara bayanan jama’a, da kuma abin da suke wallafa a shafukan sada zumunta, inda aka yi amfani da shafukan Facebook, Tiktok, X (Twitter) da kuma Instagram.

Binciken ya gano matasa da dama a Arewacin ƙasar ke ba da fifiko ga bangarorin nishaɗi da kuma tsegumi a kafafen, saɓanin bayyana wa shugabanni girman matsalolin da s**a dabaibaye yankin.

Matsalolin da ke damun yankin sun haɗa da, matsalar tsaro, rashin aiki ga matasa, talauci da yunwa da kuma rashin ingantaccen ilimi ga al'umma musamman karkara.

Rahoton mai suna (Youth Future Leaders 2025) a turance da aka shafe kimanin wata 6 ana tattara alƙaluma kafin kammala shi, daga ranar 1 ga watan Janairu zuwa 30 ga watan Yuni 2025, ya shawarci matasa su ba da fifiko wajen bayyana matsalolin da ke addabar sassa daban-daban na Arewacin ƙasar.

Tsohon ɗan takarar shugabancin Najeriya a zaɓen 2023, Peter Obi, ya ce, zai sake tsayawa takara shekara ta 2027. Wannan ...
01/07/2025

Tsohon ɗan takarar shugabancin Najeriya a zaɓen 2023, Peter Obi, ya ce, zai sake tsayawa takara shekara ta 2027.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da gamayyar ƴan adawa ke ƙoƙarin kafa jam'iyyar mai ƙarfi a Najeriya, domin tunkarar jam'iyyar APC mai mulkin ƙasar.

Kamfanin Man Fetur na ƙasa NNPC, ya bayyana cewa ya samu riba bayan biyan haraji har Naira Tiriliyan 1.05 a watan Mayu 2...
01/07/2025

Kamfanin Man Fetur na ƙasa NNPC, ya bayyana cewa ya samu riba bayan biyan haraji har Naira Tiriliyan 1.05 a watan Mayu 2025.

A cikin sabon rahotonsa, kamfanin ya ce wannan adadi ya masu ƙaru da kashi 40.37 cikin ɗari daga Naira biliyan 748 da aka samu a watan Afrilu.

Kamfanin ya kuma bayyana cewa ya samu kuɗaɗen shiga har Naira Tiriliyan 6 a cikin lokacin, wanda hakan ke nuna ƙaruwar kashi 1.87 cikin ɗari daga Naira tiriliyan 5.89.

ZANGON FARKO : ake saurare daga nan Progress Radio Gombe Najeriya.
01/07/2025

ZANGON FARKO : ake saurare daga nan Progress Radio Gombe Najeriya.

Address

Plot No. 5988, Tumfure, Bauch Road, North-Eastern
Gombe

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Progress Radio TV Gombe posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Progress Radio TV Gombe:

Share