Progress Radio TV Gombe

Progress Radio TV Gombe This platform would serve as a platform for people to progressively express themselves in the drive
(220)

PROGRESS RADIO FOR HIGH QUALITY TRANSMISSION, REPORTAGE, CURRENT AFFAIRS & ENTERTAINMENT

Gwamnatin jihar Gombe za ta kashe Naira miliyan 998.3 domin sayen katifu da matasan kai guda 22,000 ga makarantun sakand...
08/08/2026

Gwamnatin jihar Gombe za ta kashe Naira miliyan 998.3 domin sayen katifu da matasan kai guda 22,000 ga makarantun sakandaren kwana na gwamnati da ke faɗin jihar.

Matakin na daga cikin shirin gwamnatin jihar na gyara harkokin ilimi da inganta walwalar ɗalibai, tare da ƙara ingancin karatu, kamar yadda Jaridar Aminiya ta ruwaito.

Kwamishiniyar Ilimi ta jihar, Aishatu Umar Maigari, ta bayyana cewa kwangilar ta haɗa da saye, jigilar kaya, lodawa da kuma rarraba katifu da matasan kai ga makarantun sakandaren kwana 20 da ke faɗin jihar.

Ta ƙara da cewa majalisar zartarwar jihar ta kuma amince da ƙaddamar da shirin Gombe Basic Education and Skills Transformation (GoBEST), wanda aka tsara domin sauya fasalin ilimin bai ɗaya ta hanyar haɗa koyar da sana’o’i da ƙwarewar fasaha cikin tsarin karatu.

Kwamishiniyar ta bayyana hakan ne bayan kammala zaman majalisar zartarwa karo na 55 da aka gudanar ranar Juma’a.

A cewarta, an yanke shawarar ne bayan gudanar da cikakken bincike kan buƙatun makarantun, inda aka gano ƙarancin kayan kwanciya a matsayin ɗaya daga cikin manyan matsalolin da ɗaliban makarantun kwana ke fuskanta.

Maigari ta ce shirin zai taimaka wajen inganta walwalar ɗalibai, tare da shirya makarantun kwana, ciki har da sabbin manyan makarantun da aka kafa, domin karɓar ƙarin ɗalibai.

Ta ce ana sa ran sabbin manyan makarantun, waɗanda aka fi sani da Mega Schools, za su ɗauki kusan ɗalibai 15,000.

Kwamishiniyar ta kuma bayyana cewa majalisar ta amince da rahoton Kwamitin Gyara da Farfaɗo da Ilimin Bai Ɗaya da na Fasaha na Jihar Gombe, wanda Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya ƙaddamar a ranar 17 ga Nuwamban 2025.

Ta ce an ɗora wa kwamitin alhakin tantance halin da ilimin bai ɗaya da na fasaha ke ciki, tare da bayar da shawarwari masu amfani domin inganta ingancin ilimi da sakamakon karatu.

A cewarta, ɗaya daga cikin muhimman shawarwarin kwamitin shi ne kafa shirin GoBEST, wanda zai zama babban tsarin gwamnatin jihar na sauya fasalin ilimin bai ɗaya.

Ta ce za a aiwatar da shirin tare da yin garambawul ga hukumomin da ke ƙarƙashin Ma’aikatar Ilimi, domin inganta gudanar da ayyuka da samar da ingantattun ayyukan ilimi.

Maigari ta ce shirin GoBEST zai ƙarfafa tsarin ilimin bai ɗaya na shekaru 12 a jihar, ta hanyar haɗa koyar da sana’o’i da ƙwarewar fasaha cikin manhajar karatu.

Ta ƙara da cewa shirin zai kuma ginu ne kan nasarorin da aka samu ta hanyar shirin AGILE, wanda ke da nufin inganta ilimin ‘yan mata da kuma ƙarfafa damar samun ilimi.

Kwamishiniyar ta ce gwamnatin jihar na sa ran fara ganin gagarumin tasirin shirin cikin kwanaki 100 na farko da fara aiwatar da shi.

Gwamnatin Tarayya ta yi Allah-wadai da wani sabon harin da ‘yan Houthi s**a kai kan wuraren fararen hula a yankin Najran...
08/08/2026

Gwamnatin Tarayya ta yi Allah-wadai da wani sabon harin da ‘yan Houthi s**a kai kan wuraren fararen hula a yankin Najran na Saudiyya, tana mai bayyana harin a matsayin keta dokokin ƙasa da ƙasa na jinƙai.

A cikin wata sanarwa da kakakin ma’aikatar harkokin wajen Najeriya, Kimiebi Imomotimi Ebienfa, ya fitar, Najeriya ta ce harin ya jikkata fararen hula da dama, ciki har da mata da yara.

Gwamnatin ta bayyana damuwa kan ƙara tsananta rikicin tsakanin ‘yan Houthi a Yemen da Saudiyya, tare da yin kira ga dukkan ɓangarorin da su yi taka-tsantsan tare da mutunta dokokin ƙasa da ƙasa.

Najeriya ta ce hare-haren da ake kai wa fararen hula da abubuwan more rayuwa na fararen hula ba abin karɓa ba ne, ko da wanene ya aikata su.

Gwamnatin Tarayya ta yi kira da a ƙara ƙoƙarin diflomasiyya domin samar da mafita cikin lumana kuma mai ɗorewa ga rikicin, tare da buƙatar dukkan ɓangarorin su mutunta ikon ƙasashe, iyakokinsu da kuma tsaron ƙasashen yankin.

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, kuma Shugaban Majalisar Ƙoli ta Harkokin Addinin Musulunci ta Najeriya (NSCIA), Alhaji Muham...
08/08/2026

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, kuma Shugaban Majalisar Ƙoli ta Harkokin Addinin Musulunci ta Najeriya (NSCIA), Alhaji Muhammadu Sa’ad Abubakar III, ya ƙaddamar da manhajar EasyZakat, wadda aka ƙirƙira domin inganta gaskiya da riƙon amana wajen karɓa da rarraba Zakka a Najeriya.

Gidauniyar Ummah Zakat Foundation (UZF) ce ta samar da manhajar, inda Sarkin Keffi, Dakta Shehu Usman Chindo Yamusa III, ya ƙaddamar da ita a madadin Sarkin Musulmi a wani biki da aka gudanar a Abuja.

Taron ya samu halartar malaman addinin Musulunci, jami’an gwamnati, abokan hulɗar ci-gaba da kuma mambobin ƙungiyar diflomasiyya.

Haka kuma, an ƙaddamar da Kwamitin Amintattu na Gidauniyar, yayin da mahalarta taron s**a bayyana cewa amfani da fasahar zamani wajen tafiyar da harkokin Zakka na da muhimmiyar rawa wajen rage talauci, kare marasa ƙarfi da kuma bunƙasa ƙwarewar jama’a.

Da yake gabatar da jawabin Sarkin Musulmi, Sarkin Keffi ya ce Zakka ba kawai sadaka ce da mutum ke bayarwa ba, illa dai wajibi ne na addini, sannan kuma wata hanya ce ta tabbatar da adalci a cikin al’umma, rabon dukiya da kuma kare masu rauni.

Ya ce kafa Gidauniyar Ummah Zakat ya zo a daidai lokacin da ake matuƙar buƙatar haɗa ƙa’idojin Musulunci da fasahar zamani domin inganta yadda ake gudanar da harkokin Zakka da kuma faɗaɗa tasirinta a cikin al’umma.

Ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS) ta Najeriya, tare da haɗin gwiwar Ƙungiyar Ƙasashen Musulm...
08/08/2026

Ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS) ta Najeriya, tare da haɗin gwiwar Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya, za ta gudanar da wani taron ƙasa da ƙasa a Abuja domin tattauna tsaron ƙasa, yaƙi da tsattsauran ra’ayi da kuma hanyoyin samun ci-gaba mai ɗorewa ta fuskar tattalin arziki da zamantakewa.

Za a gudanar da taron mai taken “Taron Ƙasa da Ƙasa kan Tsaron Ƙasa domin Ci Gaban Tattalin Arziki da Zamantakewa Mai Ɗorewa” a ranar 12 ga Agustan 2026, a Cibiyar Taro ta Ƙasa da Ƙasa da ke Abuja.

Taron zai haɗa malamai, masu tsara manufofi, ƙwararru a harkokin tsaro da wakilan ƙasashen duniya domin tattauna hanyoyin inganta zaman lafiya, daidaito da kuma ci-gaban da zai amfani kowa.

Ana sa ran Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai buɗe taron, yayin da manyan jami’an shari’a, ƙwararru a fannin tsaro da wakilan ƙasashen duniya za su halarta a matsayin manyan baƙi da masu gabatar da muhimman jawabai.

Masu shirya taron sun ce an tsara shi ne domin samar da tattaunawa, ƙarfafa haɗin gwiwa da kuma samar da hanyoyi masu ɗorewa wajen magance matsalolin tsaro tare da inganta ci-gaba.

Sun ce haɗin gwiwar JIBWIS da Muslim World League ya nuna irin ƙudurin ƙungiyoyin biyu na inganta bambancin al’adu da addinai, zaman lafiya a tsakanin al’umma, haɗin gwiwa da kuma zaman tare cikin lumana.

“Haɗin gwiwar JIBWIS da Ƙungiyar Musulmi ta Duniya ya nuna irin ƙudurinmu na inganta bambancin al’adu da addinai, zaman lafiyar al’umma, haɗin gwiwa tsakanin al’ummomi da kuma zaman tare cikin lumana,” in ji masu shirya taron.

A cewarsu, wannan shiri ya ginu ne kan tattaunawa da haɗin gwiwar da aka gudanar a baya tsakanin shugabannin addinin Musulunci da Kirista, tare da ƙarfafa ra’ayin cewa bambancin addini da al’adu na iya taimakawa wajen samar da haɗin kai, zaman lafiya da ci-gaban al’umma.

Masu shirya taron sun ce za a gudanar da zaman tattaunawa na musamman na manyan baƙi, inda za a duba batutuwan tsaro ƙasa da ci-gaba a mahangar duniya.

Haka kuma, wasu zaman za su mayar da hankali kan bambancin al’adu da addinai da kuma samar da damar zaman tare cikin haɗin kai, yayin da ƙwararru za su tattauna hanyoyin yaƙi da tsattsauran ra’ayi da ƙarfafa juriyar al’umma wajen tunkarar matsalolin tsaro.

Shirin taron zai kuma ƙunshi zaman tattaunawa tsakanin ƙasashe da ƙungiyoyi daban-daban domin samar da haɗin gwiwar da za ta taimaka wajen bunƙasa tattalin arziki da zamantakewa mai ɗorewa.

Masu shirya taron sun ce taron zai zama wata dama ga mahalarta wajen musayar ra’ayoyi da ƙarfafa haɗin gwiwa domin samun zaman lafiya, daidaito da ci gaba mai ɗorewa.

A cikin wata sanarwa da rundunar dakarun juyin-juya-halin Iran (IRGC) ta fitar a yayin bikin ranar ƴan jarida, rundunar ...
08/08/2026

A cikin wata sanarwa da rundunar dakarun juyin-juya-halin Iran (IRGC) ta fitar a yayin bikin ranar ƴan jarida, rundunar ta ce Amurka da Isra’ila ba su cimma manufofinsu ba a yaƙe-yaƙen baya-bayan nan da s**a yi da Iran.

Ta ce abin da ta kira “yarjejeniyoyin da aka cimma” ba komai ba ne illa “takardar miƙa wuya da Amurka ta yi ga halin da ake ciki a fagen daga da kuma ƙarfin Iran wajen tattaunawa.”

Sanarwar ta kuma ce Washington ta fuskanci “tsaka mai wuya ta fuskar dabarun yaƙi” a yaƙin da take yi da Iran, sannan kuma an samu ɓaraka tsakanin ƙawayenta na ƙasashen Yamma.

Sai dai IRGC ba ta bayyana takamaiman yarjejeniyoyin da take magana a kansu ba.

Haruna Bashir, mutumin da ya rasa matarsa da ‘ya’yansa shida a wani mummunan hari da ya faru a unguwar Chiranchi (Dorayi...
08/08/2026

Haruna Bashir, mutumin da ya rasa matarsa da ‘ya’yansa shida a wani mummunan hari da ya faru a unguwar Chiranchi (Dorayi) da ke Kano, ya shiga cikin shirin Auren Gata da Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya shirya.

Haruna na daga cikin angwaye 1,500 da aka daura wa aure a karkashin shirin da gwamnatin jihar ta gudanar domin taimaka wa matasa wajen kafa iyalai da rage matsalolin rashin aure.

A baya, bayan faruwar kisan iyalansa, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi alkawarin tallafa wa Haruna tare da sake masa aure, bayan an kuma ba shi gida da kuma tallafin zuwa aikin Hajji.

Ana iya tunawa cewa a ranar 17 ga Janairun 2026, wasu mutane s**a kutsa cikin gidan Haruna Bashir da ke Chiranchi, inda s**a kashe matarsa, Fatima Abubakar mai shekaru 35, tare da ‘ya’yansu shida.

Lamarin ya janyo matukar alhini a Kano da ma fadin Najeriya, inda jama’a s**a bukaci hukumomin tsaro su kamo wadanda s**a aikata wannan ta’asa.

Daga bisani, Rundunar ‘yansandan Kano ta cafke wasu da ake zargi da hannu a kisan, ciki har da Umar Auwalu, wanda ‘yan sanda s**a ce ana zargin yana da alaka da marigayiya Fatima Abubakar.

‘Yansanda sun bayyana cewa binciken farko ya nuna cewa ana zargin an shirya harin ne tare da taimakon wasu mutane. An gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu kan tuhume-tuhume da s**a hada da hada baki, kisan kai da sauran laifuka.

Har yanzu shari’ar na ci gaba a kotu, inda ba a yanke hukuncin karshe kan lamarin ba.

Shigar Haruna Bashir cikin shirin Auren Gata na gwamnatin Kano ya jawo hankalin jama’a, inda da dama s**a bayyana hakan a matsayin damar fara sabuwar rayuwa bayan babban rashi da ya fuskanta.

Masu fatan alheri sun yi masa addu’ar samun zaman lafiya da kwanciyar hankali, tare da rokon Allah Ya jikansa da matarsa da ‘ya’yansa shida da rahama.

Manyan ƙungiyoyin ƙwadago na Biritaniya 10 waɗanda ke wakiltar ma'aikata sama da miliyan biyu sun roƙi gwamnatin Labour ...
08/08/2026

Manyan ƙungiyoyin ƙwadago na Biritaniya 10 waɗanda ke wakiltar ma'aikata sama da miliyan biyu sun roƙi gwamnatin Labour ta yi adawa da yaƙin Amurka da Isra'ila a kan Iran, suna cewa yaƙin yana ƙara tsananta rikicin tsadar rayuwa a Biritaniya.

A cikin wasiƙar da s**a aika wa Firaminista, ƙungiyoyin sun buƙaci gwamnati ta soke izinin ba da damar hare-haren jiragen yaƙi na Amurka daga yankunan Biritaniya.

Sun ce kuɗin makamashi na shekara-shekara na iyali guda ya ƙaru da fam 221 tun lokacin da aka fara yaƙin, yayin da ake hasashen kuɗin abinci na wata-wata zai ƙaru da fam 32.80.

"Kawo ƙarshen wannan yaƙi maimakon ƙara tsananta shi, yana da mahimmanci don manufar gwamnati ta rage tsada ta yi nasara," in ji su.

Masu sanya hannu sun haɗa da UNISON, ƙungiyar ƙwadago mafi girma a Biritaniya mai mambobi sama da miliyan 1.3, tare da Ƙungiyar Ilimi ta Ƙasa, PCS da RMT. Waɗannan huɗun kaɗai ke wakiltar mambobi sama da miliyan biyu.

"Yin adawa da wannan yaƙi wajibi ne idan shirin tsadar rayuwa zai yi nasara," in ji wasiƙar.

A cewar jaridar The Wall Street Journal, Donald Trump ya bayar da umarnin a fara sabon bincike domin gano mutanen da s**...
07/08/2026

A cewar jaridar The Wall Street Journal, Donald Trump ya bayar da umarnin a fara sabon bincike domin gano mutanen da s**a fitar da bayanan sirri daga Ma'aikatar Tsaron Amurka (Pentagon) game da raguwar ajiyar makamai da harsasai na Amurka a lokacin rikicin da Iran.

Jaridar ta ce wannan matakin ya zo ne yayin da Fadar White House ke ci gaba da jaddada cewa rundunar sojin Amurka tana da isassun makamai da kayan yaƙi da za su iya gudanar da duk wani aikin soja.

Rahoton ya kuma ƙara da cewa Trump ya nuna matuƙar rashin jin daɗi a makonnin baya-bayan nan game da wallafa rahotannin da ke nuna cewa ajiyar makaman linzami da harsasan Amurka na raguwa.

A cewarsa, irin waɗannan rahotanni na iya ƙarfafa gwiwar Iran tare da raunana matsayin Washington a ƙoƙarinta na tilasta wa Tehran dakatar da shirinta na nukiliya.

07/08/2026
Iran ta sanar da cimma yarjejeniya da Oman kan mashigin Hormuz, amma sai dai har yanzu ba a bayyana cikakkun bayanai gam...
07/08/2026

Iran ta sanar da cimma yarjejeniya da Oman kan mashigin Hormuz, amma sai dai har yanzu ba a bayyana cikakkun bayanai game da yarjejeniyar ba.

Kafafen yada labaran Iran sun ruwaito cewa sake bude zirga-zirga a muhimmiyar hanyar za ta dogara ne kan matakin da Amurka za ta dauka na kakaba takunkumin toshe tashoshin jiragen ruwan kasar.

Address

Plot No. 5988, Tumfure, Bauch Road, North-Eastern
Gombe

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Progress Radio TV Gombe posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Progress Radio TV Gombe:

Shortcuts

Share