02/07/2025
Dan gwagwarmayar kare haƙƙin ɗan Adam kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a ƙarkashin jam'iyyar AAC a zaɓen 2023, Omoyele Sowore, ya bayyana cewa ba zai taɓa shiga cikin haɗakar ƴan adawan da ke neman kifar da jam’iyyar APC mai mulki a zaɓen 2027 ba.
A wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata, Sowore, ya ce, ba zai iya haɗa kai da wasu fitattun ƴan siyasa da ya zarga da rusa Najeriya ta hanyar cin hanci da rashawa, cin amanar ƙasa da zalunci.
"Ban taba haɗa kai da Bola Ahmed Tinubu wajen rarraba hodar iblis a birnin Chicago ba," in ji Sowore.
"Ban haɗa kai da Atiku Abubakar wajen wawure dukiyar Hukumar Kwastam ba, kuma ban taɓa shiga cikin barnar David Mark wanda ya saci kuɗaɗen da aka ware don gyara wayoyinmu sannan ya taimaka wajen murƙushe burin dimokuradiyyarmu a ranar 12 ga Yuni ba."
A cikin wannan s**a mai zafi ga tsarin siyasar Najeriya, Sowore ya jero wasu daga cikin manyan ƴan siyasa da ya ce, sun taka rawa wajen lalata ƙasar, ciki har da tsofaffin gwamnoni, ministoci da ƴan takarar shugaban ƙasa.
Sowore ya ƙi amincewa da ƙira da ake yi masa da ya sassauta tsayuwarsa kan aƙida saboda buƙatar siyasa, yana mai cewa,
bai taɓa shiga cikin ƙungiyoyin ƴan fashi da makami ba.