05/12/2022
KUNGIYAR MASU SAYAR DA SHAYI DA INDOMIE NA JIHAR GOMBE SUN NUNA GAMSUWA DA AYYUKAN OFISHIN GINA AL'UMMA DA BUNKASA SU
A ranar Litinin din nan 5 ga watan Disamba, 2022 kungiyar masu saida shayi da Indomie na jihar Gombe s**a ziyarci ofishin gina al'umma da bunkasa su, domin jaddada goyon baya ga ayyukan Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya.
Shugaban Kungiyar masu sayar da Shayi na jiha Shu'aibu Musa Ibrahim yace la'akari da yadda ofishin ke tafiyar da ayyukan sa da gamsuwa dasu tare da maraba baya a nan gaba don dorewar ayyukan, shine makasudin ziyarar.
Malam Shu'aibu Musa yace sun shaida wasu alkawura da Gwamna Inuwa Yahaya yayi wa kungiyar masu sayar da Shayi da Indomie na jihar Gombe, don haka suna bayan sa dari bisa dari.
Da yake mayar da martani, Babban mai taimakawa Gwamna ta fannin gina Al'umma da bunkasa su Barista Sani Ahmadu Haruna, ya ce sun daura dukkanin kungiyar bisa gaskiya ta yadda zasu ci moriyar shirye-shiryen ofishin.
Barista Sani Haruna yace yanzu haka sun karbi sunayen mambobin kungiyar guda dari 5 domin sanya su cikin shirin fadada ayyukan gina al'umma a fadin jihar Gombe nan bada jimawa ba, ganin yadda sana'ar sayar da Shayi da Indomie ke samar da ayyukan yi ga dimbin jama'a.
Kungiyar ta kuma karrama Barista Sani Haruna da lambar yabo bisa jajircewar aiki, inda tayi masa fatan tarin nasarori cikin ayyukan sa.
Mohammed Babawuro
Media Assistant to the SA on Human Capital Development.