Madubi - H

Madubi - H The Only Hausa News Blog You Can Trust

Gwamnatin Tarayya ta Fitar da Naira Biliyan 32.9 Don Inganta Kiwon Lafiya — Ministan LafiyaGwamnatin Tarayya ta amince d...
23/10/2025

Gwamnatin Tarayya ta Fitar da Naira Biliyan 32.9 Don Inganta Kiwon Lafiya — Ministan Lafiya

Gwamnatin Tarayya ta amince da sakin Naira Biliyan 32.9 dan gudanar da shirin Basic Health Care Provision Fund (BHCPF), wanda zai tallafawa cibiyoyin kiwon lafiya a matakin ƙasa baki ɗaya. Wannan shi ne zagaye na uku na wannan shirin a bana.

Ministan Lafiya, Farfesa Muhammad Ali Pate, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa mai taken Jar Wasiƙa “The Red Letter”, inda ya jaddada cewa kudaden sun riga sun fara shiga asusun ajiyar kuɗi na cibiyoyin kiwon lafiya na gundumomi a duk faɗin ƙasar.

Pate ya ce wannan mataki na nufin bai wa al’ummomi ikon tsara yadda za su kashe kudaden domin tabbatar da cewa kuɗin ya samar da ingantaccen sakamako ga jama’a.

Ya ce gwamnatin tarayya ta cika nata alkawari wajen samar da kudaden, yanzu al’ummomi ne ke da hakkin tabbatar da cewa an yi amfani da su yadda ya dace.

Ministan ya yi kira ga kowane ɗan Najeriya da ya tashi tsaye wajen kare lafiyar jama’a ta hanyar shiga cikin kwamitocin kula da asibitoci, duba yadda ake kashe kudaden, da kuma tabbatar da gaskiya da bayyananniyar hanya wajen amfani da su.

Ya ƙara da cewa gwamnati tana son ganin wannan saƙo ya isa kowace unguwa, gunduma da gida, don tunatar da ‘yan ƙasa cewa inganta lafiyar Najeriya abu ne da yake hannun yan Najeriya.

Da wane bajinta kake tunawa da Abba Kyari?
23/10/2025

Da wane bajinta kake tunawa da Abba Kyari?

23/10/2025

Sabuwar Sha'ira ta bayyana a Kano

Dame kuka tunawa a duk lokacin da ku ka ga Hoton nan?
23/10/2025

Dame kuka tunawa a duk lokacin da ku ka ga Hoton nan?

23/10/2025

Amarya tace do Allah kyale ni inyi Rawa

Gwamnatin Tarayya Ta Jajanta Wa Jihar Neja Bisa Fashewar Tankar Mai a EssaGwamnatin Tarayya ta bayyana “alhini da jimami...
23/10/2025

Gwamnatin Tarayya Ta Jajanta Wa Jihar Neja Bisa Fashewar Tankar Mai a Essa

Gwamnatin Tarayya ta bayyana “alhini da jimami matuƙa” bisa mummunar fashewar tankar mai da ta auku a Essa da ke Ƙaramar Hukumar Katcha ta Jihar Neja kwanaki kaɗan da s**a wuce, wadda ta yi sanadin mutuwar mutane da dama tare da jikkata wasu.

A cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu a ranar Laraba, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce: “Muna taya Gwamnatin Jihar Neja da al’ummar ta jimamin wannan babban rashi.

“Wannan abin takaici ya sake tunasar da mu illolin da haɗarin fashewar tankar mai ke haifarwa ga rayuka da dukiyoyi a cikin al’ummomin mu.”

Alhaji Idris, wanda shi ma ɗan asalin jihar ne, ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta yi matuƙar baƙin ciki ganin cewa duk da wayar da kai da gargaɗi da aka sha yi kan haɗarin ɗibar mai daga tankokin da s**a faɗi, har yanzu wasu mutane suna ci gaba da irin wannan gangancin da zai iya kai su ga halaka.

Ya ce: “Rayuwar kowane ɗan Nijeriya tana da muhimmanci, kuma irin waɗannan abubuwan da za a iya gujewa suna tuna mana muhimmancin kulawa da bin umarnin tsaro, musamman a lokutan gaggawa.”

Ministan ya ƙara da cewa: “Muna yaba wa yadda Gwamnatin Jihar Neja, jami’an tsaro, da ma’aikatan agajin gaggawa s**a gaggauta ɗaukar mataki wajen kashe wutar, da ceto waɗanda s**a tsira, da kuma tallafa wa iyalan waɗanda abin ya shafa.”

Ya bayyana cewa an umarci Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) da ta haɗa gwiwa da gwamnatin Jihar Neja wajen ci gaba da bayar da taimakon gaggawa da jinya ga waɗanda abin ya ritsa da su da iyalan su.

Haka kuma ya ce Gwamnatin Tarayya ta umarci Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa (NOA) da ta ƙara ƙaimi wajen wayar da kan jama’a a duk faɗin ƙasar nan, musamman a yankunan karkara da wuraren da ake fuskantar irin waɗannan haɗurra, domin hana maimaituwar irin wannan bala’i.

Ministan ya ƙare da cewa: “Tunanin mu da addu’o’in mu suna tare da waɗanda abin ya shafa, da iyalan su, da al’ummar Jihar Neja baki ɗaya a wannan lokaci na jimami. Allah Ya jiƙan waɗanda s**a rasu, ya kuma ba iyalan su haƙuri da ƙarfin zuciya wajen jure wannan babban rashi.”

23/10/2025

🤔🤔🤔

23/10/2025

Wannan Dattijan sunfi Wasu samarin Iya soyayya

Jiya da Yau!
22/10/2025

Jiya da Yau!

Me Wushirya Da Yar Guda Daya Sunje Gwajin Jini Gabanin Auren Su.
22/10/2025

Me Wushirya Da Yar Guda Daya Sunje Gwajin Jini Gabanin Auren Su.

Gwamnatin Tarayya za ta zuba jarin Dalar Amurka Miliyan 220 don samar da ayyukan yi — ShettimaGwamnatin Tarayya ta sanar...
22/10/2025

Gwamnatin Tarayya za ta zuba jarin Dalar Amurka Miliyan 220 don samar da ayyukan yi — Shettima

Gwamnatin Tarayya ta sanar da shirin zuba jarin Dalar Amurka miliyan 220 domin samar da sabbin damammakin ayyukan yi ga matasan ƙasar.

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ne ya bayyana haka a ranar Laraba yayin ƙaddamar da shirin Nigeria Jubilee Fellows Programme (NJFP) 2.0 a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.

Shirin, wanda aka haɗa gwiwa da Tarayyar Turai (EU) da Asusun Raya Ƙasashe na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNDP), na nufin haɗa matasa masu ƙwarewa da dama ta fannin horo, gogewa da kuma jagoranci (mentorship), domin taimaka musu su shiga sahun masu dogaro da kai.

Shettima ya ce burin gwamnati shi ne rage tazara tsakanin karatu da samun aiki, ta hanyar bai wa matasa damar amfani da ilimin da s**a samu wajen gina tattalin arziƙin ƙasa.

Ya ƙara da cewa gwamnatin Shugaba Bola Tinubu za ta tabbatar da cewa shirin ya samu tallafi kai tsaye daga kasafin kuɗi na ƙasa, tare da buɗe “NJFP Basket Fund” domin samar da hanyoyin samun kuɗaɗen da za su dore.

Mataimakin shugaban ƙasar ya yi kira ga masu zuna jari masu zaman kansu, ƙungiyoyin ci gaba da masu ba da gudummawa su haɗa kai wajen tabbatar da nasarar shirin.

Ya bayyana cewa gwamnati za ta tabbatar da adalci da haɗin kai wajen aiwatar da mataki na biyu na shirin, domin ya shafi matasa daga kowane yanki da bangare na ƙasa, musamman a fannoni kamar noma, makamashi, fasahar zamani, masana’antu da kuma harkokin kirkire-kirkire.

Ministan Ci gaban Matasa, Ayodele Olawande, ya bayyana NJFP 2.0 a matsayin ci gaba daga nasarorin da aka samu tun 2021, inda sama da matasa 13,000 s**a amfana da horo da ayyuka.

Ya ce gwamnati na da burin samar wa matasa 100,000 aiki cikin shekaru biyar masu zuwa.

Jakadiyar UNDP a Najeriya, Ms Elsie Attafuah, ta ce haɗin gwiwar da ake da EU da UNDP ta samar da damammaki da ta kai sama da matasa 40,000 cikin fannoni daban-daban na tattalin arziƙi.

Ita ma jakadiyar Tarayyar Turai a Najeriya, Gauthier Mignot, ta ce EU na fatan ganin NJFP 2.0 ya zama ɓangare na tsarin gwamnati, domin tabbatar da dorewarsa.

22/10/2025

Kanuri

Address

Gombe

Telephone

+2347080511115

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Madubi - H posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Madubi - H:

Share