Madubi - H

Madubi - H The Only Hausa News Blog You Can Trust

Najeriya Da Maroko Za Su Kulla Yarjejeniya a fannin makamashi, noma, da kuma harkokin cinikayyaAlaƙar diplomasiyya tsaka...
10/05/2026

Najeriya Da Maroko Za Su Kulla Yarjejeniya a fannin makamashi, noma, da kuma harkokin cinikayya

Alaƙar diplomasiyya tsakanin kasashen Najeriya da Maroko ta kara nuna ƙarfafa, inda kasashen biyu s**a kulla yarjejeniyar karfafa dangantaka a fannonin makamashi, noma, da kuma harkokin cinikayya.

Wannan sanarwa ta fito ne bayan wata tattaunawa da aka yi tsakanin Ministar Harkokin Wajen Najeriya, Bianca Ojukwu, da takwaranta na kasar Maroko, Nasser Bourita.

Babban kashin bayan tattaunawar shi ne aikin ginin bututun iskar gas na Najeriya da Maroko (African Atlantic Gas Pipeline). Ministocin biyu sun bayyana wannan gagarumin aiki a matsayin "mai canza alkiblar tattalin arziki" wanda zai samar da tsaro a fannin makamashi da kuma dunkulewar yankin Afirka ta Yamma baki daya.

Ma’aikatar Harkokin Wajen ta tabbatar da cewa tuni kamfanin man fetur na kasa (NNPCL) da takwaransa na kasar Maroko (ONHYM) s**a kammala binciken fasaha na aikin. Ana sa ran Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Sarki Mohammed VI za su sanya hannu kan yarjejeniyar gudanar da aikin a rubuce kafin karshen rubu'i na hudu na wannan shekara.

Baya ga batun iskar gas, kasashen biyu sun tattauna hanyoyin hadin gwiwa wajen sarrafawa da rarraba takin zamani. Wannan mataki na da nufin tabbatar da wadatar abinci ba kawai a kasashen biyu ba, har ma da sauran sassan nahiyar Afirka.

Domin farfado da tsoffin yarjejeniyoyin da aka kulla tun zamanin tsohon Shugaba Muhammadu Buhari a shekarar 2018, Najeriya na shirin karbar bakuncin taron hadin gwiwa na kasashen biyu (Bilateral Joint Commission) karo na biyu.
Haka zalika, ministocin sun jaddada bukatar sake kafa Majalisar Kasuwanci ta Najeriya da Maroko. Sun bayyana cewa yarjejeniyar cinikayya ta bai-daya ta nahiyar Afirka (AfCFTA) da kuma shirin kauce wa biyan haraji ninki biyu, za su bude sabbin kofofin bunkasa tattalin arzikin kasashen biyu.

DOGON DARE: Barcelona Ta Ci Kofin La Liga, Bayan Ta Ragargaji Real Madrid Da Ci 2-0 A Daren Yau Lahadi
10/05/2026

DOGON DARE: Barcelona Ta Ci Kofin La Liga, Bayan Ta Ragargaji Real Madrid Da Ci 2-0 A Daren Yau Lahadi

Ko Kwankwaso ne yake bada mulki a duniya ba zai bawa Peter Obi ba — Inji Garba Kore Dawakin Kudu
10/05/2026

Ko Kwankwaso ne yake bada mulki a duniya ba zai bawa Peter Obi ba — Inji Garba Kore Dawakin Kudu

Kwankwaso yana daya daga cikin matsalar Arewa. Inji Hauwa Farouk Ibrahim
10/05/2026

Kwankwaso yana daya daga cikin matsalar Arewa.

Inji Hauwa Farouk Ibrahim

ZAƁEN GWAJIKwankwaso ko Atiku?
10/05/2026

ZAƁEN GWAJI

Kwankwaso ko Atiku?

RA'AYIN KUShin ƴan Arewa za su aminta da wannan haɗin?
10/05/2026

RA'AYIN KU

Shin ƴan Arewa za su aminta da wannan haɗin?

"Kwankwaso ne ya haddasa rik!cin masarauta a Kano, yanzu kuma ya na so ya kawo ma na rik!cin B!afara a Arewa." — Alhaji ...
10/05/2026

"Kwankwaso ne ya haddasa rik!cin masarauta a Kano, yanzu kuma ya na so ya kawo ma na rik!cin B!afara a Arewa." — Alhaji Tanko Balare

10/05/2026

Goni

FAƊI MU JI: Cikin su waye zai ceci Nigeria?
10/05/2026

FAƊI MU JI: Cikin su waye zai ceci Nigeria?

LABARI DA DUMI-DUMI: Riƙaƙƙen dan fashin daji Kachalla Haire ya mutu, ya mutu yayin karawa da wasu rukunin yan fashin Da...
10/05/2026

LABARI DA DUMI-DUMI: Riƙaƙƙen dan fashin daji Kachalla Haire ya mutu, ya mutu yayin karawa da wasu rukunin yan fashin Daji dake gaba da shi.

BREAKING NEWS: Notorious Bandit leader Kachalla Haire is dead, the ruthless Bandit was killed during an infighting with rival Bandits group.

10/05/2026

Ƙiris ya hana wani fusatacce ya takanɗo Kakakin Majalisar wakilai, Tajuddeen Abbas daga kan mimbari

Address

Gombe

Telephone

+2347080511115

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Madubi - H posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Madubi - H:

Share