AMT News

AMT News A media and technology company providing news coverage, documentary production, content creation, digital communication, advertising, and ICT services.

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Najeriya (INEC) ta wallafa jerin sunayen ƙarshe na ƴan takarar shugaban ƙasa da mataimak...
13/09/2026

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Najeriya (INEC) ta wallafa jerin sunayen ƙarshe na ƴan takarar shugaban ƙasa da mataimakansu da za su fafata a babban zaɓen watan Janairun 2027.

Jerin sunayen, wanda Sakatariyar Hukumar, Rose Oriaran-Anthony, ta sanya wa hannu, kuma aka fitar da shi ranar Asabar a Abuja, ya ƙunshi ƴan takarar da jam'iyyun siyasa 18 s**a tsayar domin neman kujerar shugaban ƙasa a 2027.

Hukumar ta INEC ta bayyana sunayen'yantakarar 18 da mataimakansu ga dai wasu daga cikinsu:

APC
Tinubu da Shettima
Shugaban kasa mai ci a Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, shi ne dan takarar shugaban kasa a jam'iyya mai mulkin Najeriya APC, kuma Kashim Shettima, shi ne zai sake yi masa mataimaki a zaben 2027.

ADC
Atiku da Amaechi
Atiku Abubakar, tsohon mataimakin shugaban kasa a Najeriya a lokacin mulkin Obasanjo, shi ne zai yi wa jam'iyyar ADC takarar shugaban kasa, inda Chibuike Rotimi Amaechi kuma zai masa mataimaki.

NDC
Obi da Kwankwaso
Peter Gregory Obi, tsohon gwamnan jihar Anambra kuma tsohon dan takarar shugaban kasa a jam'iyyar Labour a zaben 2023, shi ne zai yi wa jam'iyyar NDC, takarar shugaban kasa a zaben 2027 da ke tafe, yayin da Injiniya Rabi'u Musa Kwankwaso kuma zai masa mataimaki.

Sauran 'yan takarar shugaban kasa da mataimakansu a zaben na 2027, sun hada da;

Jam'iyyar LP, in da Sunday Chibuzo Okereke, zai yi mata takarar shugaban kasa Hajja Bintu Konto, kuma mataimakiya.

Fiye da mutane 7,000 ne aka tabbatar sun kamu da cutar Ebola a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo (DRC), a cikin mummunar ɓ...
13/09/2026

Fiye da mutane 7,000 ne aka tabbatar sun kamu da cutar Ebola a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo (DRC), a cikin mummunar ɓarkewar cutar da aka taɓa samu a ƙasar, a cewar alkaluman da hukumomin Kongo s**a fitar a ranar Asabar.

Sai dai gwamnatin ƙasar ta nuna cewa wataƙila yaɗuwar cutar ta riga ta kai kololuwa, duk da cewa an tabbatar da ɓullar cutar a lardi na bakwai a farkon wannan mako.

Kongo ta tabbatar da sabuwar ɓarkewar cutar a hukumance a tsakiyar watan Mayu, inda kusan mutane 3,400 s**a mutu da wannan annoba ta 17 da cutar mai saurin yaɗuwa ta Ebola ta haddasa a ƙasar.

Barkewar ta fara ne a lardin Ituri da ke arewa maso gabashin ƙasar, kafin ta yaɗu zuwa yankunan gabashi da arewa masu nisa, waɗanda rikice-rikice s**a addaba, inda ƙungiyoyin masu ɗauke da mak**ai s**a shafe shekaru da dama suna kai hare-hare, kasancewar ikon gwamnati ya yi rauni tare da ƙarancin cibiyoyin kiwon lafiya.

A farkon wannan mako ne aka tabbatar da cutar a lardin South-Ubangi, wanda ke iyaka da Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya da kuma Congo-Brazzaville.

A cewar sabbin alkaluman hukumomin Kongo, an samu jumullar mutane 7,022 da s**a kamu da cutar tun bayan fara ɓarkewar. Daga cikinsu, mutane 3,398 sun mutu, yayin da 1,671 s**a warke.

Mafi yawan waɗanda aka tabbatar sun kamu da cutar suna cikin Ituri, inda aka gano Ebola a wasu makarantu kwanaki bayan komawar ɗalibai makarantu bayan hutun bazara, lamarin da ya jefa iyaye da ma’aikatan kiwon lafiya cikin fargaba.

Jam’iyyar Nigeria Democratic Congress wato NDC ta yi watsi da rahotannin da ke cewa ba ta da ’yan takarar gwamna a jihoh...
06/09/2026

Jam’iyyar Nigeria Democratic Congress wato NDC ta yi watsi da rahotannin da ke cewa ba ta da ’yan takarar gwamna a jihohi 12, tana mai bayyana ikirarin a matsayin farfagandar ƙarya da aka shirya domin rage tasirin jam’iyyar da ke ƙara samun karɓuwa a fagen siyasa.

Jam’iyyar ta ce ta gabatar da ’yan takararta yadda ya k**ata a zaɓen gwamna a dukkan jihohi 28 da za a gudanar da zaɓen a shekarar 2027.

Sakataren Yaɗa Labarai na Ƙasa na NDC, Osa Director, ne ya bayyana matsayar jam’iyyar a cikin wata sanarwa, inda ya zargi waɗanda ke yaɗa rahoton da yin hakan da gangan domin yaudarar ’yan Najeriya game da shirin da jam’iyyar ta yi na tunkarar zaɓen.

Osa ya ce NDC ba jam’iyyar siyasa ce ta wani yanki kawai ba, illa dai wata ƙungiyar siyasa ce ta ƙasa baki ɗaya wadda ke da tsare-tsare, ’yan takara da magoya baya a dukkan jihohi 36 da kuma Babban Birnin Tarayya.

Domin karyata rahoton, jam’iyyar ta wallafa sunayen ’yan takararta a jihohi 12 da rahoton ya ambata a matsayin wuraren da ake zargin ba ta da ’yan takara.

Sun haɗa da Sanata Kabiru Marafa a Zamfara; Rear Admiral Ibrahim Sanusi Kasim (Mai Ritaya) a Borno; Hon. John Odey a Cross River; Babanta Michael Okon a Akwa Ibom; Nwofe Boniface a Ebonyi; da Yakubu Solomon Ndam a Filato.

Aƙalla mutane 23 sun mutu, yayin da aka samu fiye da mutane 310 da s**a kamu da cutar kwalara ko kuma ake zargin sun kam...
06/09/2026

Aƙalla mutane 23 sun mutu, yayin da aka samu fiye da mutane 310 da s**a kamu da cutar kwalara ko kuma ake zargin sun kamu da ita a yankuna biyu na Kordofan ta Yamma da ke kudancin Sudan, k**ar yadda wata ƙungiyar agaji ta yankin ta bayyana a ranar Lahadi.

Ƙungiyar Dar Hamar Emergency Room, wadda ƙungiyar agaji ce da al'umma ke tafiyar da ita, ta yi gargaɗi a cikin wasu jerin sanarwa biyu da ta fitar kan taɓarɓarewar yanayin lafiya da na jinƙai a ƙauyen Humeir da Hilla Hussein da ke Ƙaramar Hukumar Al-Udayyah.

Ƙungiyar ta ce Humeir na fuskantar “mummunan yanayin lafiya,” inda aka kwantar da mutane 120 da ake zargin sun kamu da cutar kwalara a wata cibiyar killace masu cutar, yayin da aka samu mutuwar mutane 11.

Ta ce cibiyar killace masu cutar ba ta da isasshen ruwan allura da magungunan ceton rai, a daidai lokacin da adadin mutanen da ake zargin sun kamu da cutar ke ci gaba da ƙaruwa.

Ƙungiyar ta yi kira ga hukumomin lafiya da ƙungiyoyin agaji da su gaggauta samar da kayan aikin jinya da magunguna, tana mai gargadin cewa yanayin na iya ƙara taɓarɓarewa.

A wata sanarwa ta daban, ƙungiyar ta ce rikicin lafiya da na jinƙai ya ƙara ta'azzara a Hilla Hussein, inda aka samu fiye da mutane 190 da s**a kamu da cutar kwalara, yayin da mutane 12 s**a mutu sak**akon cutar.

Ta ƙara da cewa matsalolin sufuri sun ware yankin, lamarin da ya sa aka samu matsala wajen fitar da marasa lafiya da ke cikin mawuyacin hali domin kai su asibiti don samun magani.

Yayin da cutar diphtheria ke ci gaba da hallaka mutane a sassan Najeriya, wata kaka mazauniyar birnin Jos, babban birnin...
30/08/2026

Yayin da cutar diphtheria ke ci gaba da hallaka mutane a sassan Najeriya, wata kaka mazauniyar birnin Jos, babban birnin Jihar Plateau, Fatimatu Abdullahi, ta bayyana yadda ta rasa jikokinta biyu cikin mako guda sak**akon cutar.

Fatimatu, wadda ke zaune a unguwar Bauchi Road da ke Jos, ta ce mutuwar yaran ta kasance abin bakin ciki da ba za ta manta da shi ba, domin cutar ta k**a su cikin gaggawa ba tare da sanin ainihin abin da ke damunsu ba.

Wadanda s**a rasu sun hada da Umar Muktar mai shekaru 14 da Hauwa Shapi'u mai shekaru 17, wadanda dukkansu ke zaune tare da kakarsu kafin rasuwarsu.

Da take bayyana yadda lamarin ya faru, Fatimatu ta ce Umar ne ya fara nuna alamun rashin lafiya.

Ta ce, “Umar ya fara rashin lafiyar ne kuma cikin kwanaki uku zuwa hudu ya rasu. A lokacin ba mu san ainihin cutar da ke damunsa ba saboda ba a kai shi asibitin kwararru ba.”

Ta kara da cewa kwanaki biyu bayan rasuwar Umar, Hauwa ma ta fara nuna irin wadannan alamomi kuma daga bisani ita ma ta rasu.

A cewarta, an kai Hauwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jos (JUTH), inda aka killace ta a cibiyar kula da masu kamuwa da cututtuka, kuma daga baya aka tabbatar tana dauke da cutar diphtheria.

“Amma lokacin ya kure domin ceton rayuwarta. Daga nan ne muka fahimci cewa Umar ma cutar diphtheria ce ta kashe shi saboda dukkaninsu sun nuna alamomi iri daya,” in ji kakar.

Ta bayyana cewa rashin lafiyar ta fara ne da ciwon makogwaro, sannan daga baya makogwaron ya kumbura har s**a kasa cin abinci ko shan ruwa.

A nasa bangaren, mahaifin Hauwa, Shapi’u Abdullahi, ya bayyana rasuwar diyarsa a matsayin babban rashi ga iyalinsu.

Ya ce Hauwa ita ce diyarsa ta fari kuma daliba ce mai hazaka da biyayya.

“Hauwa ta samu shiga aji na SS3 kuma ana sa ran za ta rubuta jarabawar kammala sakandare nan gaba. Na rasa diya mai hankali da biyayya, kuma wannan babban rashi ne ga iyalinmu,” in ji shi.

Rahotanni sun nuna cewa an yi wa sauran 'yan uwa da s**a yi mu'amala da wadanda s**a rasu allurar rigakafin cutar domin hana yaduwarta.

Hukumomin lafiya a Jihar Plateau na ci gaba da wayar da kan jama'a kan muhimmancin garzayawa asibiti da kuma kai rahoton duk wata rashin lafiya da ke dauke da alamomin diphtheria domin dakile yaduwar cutar.

Wani farfesa a Jami’ar Kimiyyar Aikace-aikace da Fasaha da ke Tehran, Mostafa Khoshcheshm, ya ce kiran da Jagoran Kolin ...
30/08/2026

Wani farfesa a Jami’ar Kimiyyar Aikace-aikace da Fasaha da ke Tehran, Mostafa Khoshcheshm, ya ce kiran da Jagoran Kolin Iran, Ayatullah Mojtaba Khamenei, ya yi ga ƙasashen Musulmi su haɗa kai domin fuskantar Amurka da Isra’ila ya yi daidai da matsayar da Iran ta daɗe tana ɗauka.

Da yake zantawa da tashar Al Jazeera, Khoshcheshm ya bayyana cewa Iran na son ƙasashen yankin Tekun Fasha su katse alaƙar soji da Amurka, wadda a cewarsa ke amfani da yankunansu da kuma mashigar ruwan Hormuz wajen gudanar da ayyukan soji kan Iran.

Ya ce idan aka sake buɗe mashigar Hormuz a halin yanzu, Amurka za ta samu damar gyara cibiyoyinta na tsaro da na kariyar sama tare da shirya wani sabon hari kan Iran.

“Abin da Iran ke so shi ne a fitar da Amurkawa daga yankin domin a samar da yanayi na zaman lafiya ga kowa,” in ji Khoshcheshm.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da rikicin da ke tsakanin Iran da Amurka ke ci gaba da haifar da tashin hankali a Gabas ta Tsakiya, yayin da ake ci gaba da tattaunawa da ƙoƙarin sasanta ɓangarorin biyu ta hannun wasu ƙasashe na yankin.

Jagoran Kolin Iran, Ayatullah Mojtaba Khamenei, ya yi kira ga shugabannin ƙasashen Musulmi da su gane hakikanin maƙiyins...
30/08/2026

Jagoran Kolin Iran, Ayatullah Mojtaba Khamenei, ya yi kira ga shugabannin ƙasashen Musulmi da su gane hakikanin maƙiyinsu tare da fahimtar manufofinsa domin fuskantar su yadda ya k**ata.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a rubuce, Khamenei ya buƙaci ƙasashen Musulmi su haɗa kai wajen tinkarar barazanar da ke fuskantar duniyar Musulmi.

A wani cigaban kuma, wasu mutane sun jikkata sak**akon wani hari ta sama da Isra’ila ta kai a tsakiyar Zirin Gaza.

Haka kuma, rahotanni sun ce an ji wata babbar fashewa a kudancin Lebanon bayan wani hari da Isra’ila ta kai a yankin.

Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Iran, Kazem Gharibabadi, ya bayyana cewa har yanzu mashigar ruwa ta Hormuz na ci gaba da kasancewa a rufe, yana mai cewa Iran ba ta da gaggawar sake buɗe ta.

Shi ma rundunar kare juyin juya halin Musulunci ta Iran (IRGC) ta ce tana da cikakken iko a kan mashigar ruwan, tare da zargin shugabannin Amurka da yaɗa bayanan da ba su dace ba domin tasiri kan farashin mak**ashi a kasuwannin duniya.

A nata ɓangaren, gwamnatin Iraki ta bayyana aniyarta ta zama gada tsakanin Tehran da Washington domin rage zaman ɗarɗar da ke tsakanin ɓangarorin biyu.

Mai ba Firaministan Iraki shawara kan harkokin tsaro, Qasim al-Araji, ya shaida wa Al Jazeera cewa ƙasarsa na ƙoƙarin taka rawar sasanci tsakanin Iran da Amurka.

A yankin Gabar Yamma da Isra’ila ke mamaye da ƙarfi, rahotanni sun nuna cewa wasu yahudawan matsugunai tare da goyon bayan sojojin Isra’ila sun kewaye wani gidan Bafalasdine a ƙauyen Qusra da ke kudancin Nablus.

Lamarin na ƙara nuna yadda rikicin Gabas ta Tsakiya ke ci gaba da tsananta a yankuna da dama.

Ƙungiyar Tarayyar Ƙasashen yankin Sahel (AES) ta sake jaddada cikakken goyon bayanta ga hukumomin Jamhuriyar Nijar ranar...
30/08/2026

Ƙungiyar Tarayyar Ƙasashen yankin Sahel (AES) ta sake jaddada cikakken goyon bayanta ga hukumomin Jamhuriyar Nijar ranar Asabar, biyo bayan boren da wasu sojoji s**a yi a Yamai, inda ta yaba wa biyayya da jaruntaka na Dakarun Tsaron Nijar da ta ce su s**a daƙile ƙoƙarin tayar da zaune tsayen.

Kamfanin dilancin labaran Jamhuriyar Nijar (ANP) ya ambato wata sanarwar da AES ta fitar ranar Asabar tana cewa tana tare da ƙasar wajen ci-gaba da “gwagwarmayar ‘yancin kai da zaman lafiya.”

“Saboda jaruntaka da ƙwarewa na dakarun jamhuriyar masu biyayya, an daƙile wannan sabon yunƙurin,” in ji sanarwar ta AES.

Kazalika ta yaba wa "biyayya da jaruntaka da tunani na aiki na dakarun tsaron Nijar, " waɗanda "suke biyayya ga rantsuwar da s**a sha, s**a fuskanci boren da kuma taka rawa wajen dawo da doka da oda ".

Ƙungiyar tarayyar ƙasashen ta kuma sake jaddada dagewarta wajen kiyaye "haɗin kai da zaman lafiyar yankin ƙungiyar tarayyar ƙasashen” inda ta yi kira ga mutane Burkina Faso da Mali da kuma Nijar su kasance masu sa ido sosai kan yaɗa labaran ƙarya da ƙoƙarin yamutsa tunanin mutane da kuma ƙoƙarin rarraba kawuna.

An shafe sa'o'i ana jin harbe-harbe masu ƙarfi cikin daren Asabar zuwa safiyar Lahadi a Yamai babban birnin ƙasar yayin da wasu sojoji s**a yi boren da ma'aikatar tsaron ƙasar ta ce dakarun gwamnati sun samu sun daƙile shi.

Jagoran addinin Iran, Mojtaba Khamenei ya ce Amurka da Isra'ila maƙiya ne ga al'ummar Musulmi baki ɗaya ba wai ga Iran d...
30/08/2026

Jagoran addinin Iran, Mojtaba Khamenei ya ce Amurka da Isra'ila maƙiya ne ga al'ummar Musulmi baki ɗaya ba wai ga Iran da ƙungiyoyin gwagwarmayar Musulunci kaɗai ba,

A cikin saƙon, Mojtaba Khamenei ya ce shugabannin Amurka da Isra'ila suna adawa da Iran amma ya jaddada cewa adawarsu ta shafi al'ummomin Musulmi na Gabas ta Tsakiya da Arewacin Afirka gaba ɗaya.

Ya kuma ce hatta wasu shugabannin ƙasashen yankin da ake zargin suna hada kai da waɗannan ƙasashe ba su tsira daga wannan adawar ba.

Ya kuma yi kira ga Musulmai su rungumi haɗin kai, yana mai cewa duk wanda ya aikata abin da zai haddasa rarrabuwar kawuna ko saɓani tsakanin Musulmai, ko da da gangan ko ba da gangan ba, yana taimakawa wajen cimma manufar maƙiya Musulunci.

Tun daga shekarar 1981 ne ake gudanar da Makon Haɗin Kan Musulmi tsakanin ranar 12 zuwa 17 ga watan Rabi'ul Awwal, lokacin da ake gudanar da tarurrukan ƙasa da ƙasa kan haɗin kan Musulmi.

Taron Ƙasa da Ƙasa na 40 kan Haɗin Kan Musulmi ya kammala a yau a Tehran.

BBC Hausa

Masu garkuwa da mutanen da s**a sace wasu ’yan bautar ƙasa (NYSC) kwanaki uku da s**a gabata sun buƙaci a biya su Naira ...
30/08/2026

Masu garkuwa da mutanen da s**a sace wasu ’yan bautar ƙasa (NYSC) kwanaki uku da s**a gabata sun buƙaci a biya su Naira miliyan 20 kan kowanne daga cikin waɗanda suke tsare da su domin a sake su.

A baya Daily Trust ta ruwaito cewa an yi garkuwa da wasu ’yan bautar ƙasa da ke kan hanyarsu ta komawa Abuja daga Jihar Bayelsa bayan kammala atisayen sansanin horaswa na makonni uku.

Lamarin ya faru ne a kan hanyar Aloma-Egane da ke Ƙaramar Hukumar Ofu a Jihar Kogi.

Wani ɗan uwa na ɗaya daga cikin waɗanda aka sace ya shaida wa Daily Trust cewa masu garkuwar sun tuntubi iyalan yarinyar tare da bayyana adadin kuɗin fansar da suke nema.

A cewarsa, “Daya daga cikin ’ya’yanmu da aka sace tana kan hanyarta daga Bayelsa zuwa Abuja bayan kammala sansanin horaswa. Masu garkuwar sun nemi Naira miliyan 20 domin su sake ta.”

Wannan na zuwa ne bayan rundunar ’yan sandan Jihar Kogi ta tabbatar da sace wasu fasinjoji, ciki har da ’yan bautar ƙasa, a kan wannan hanya.

Rundunar ta ce an ceto mutum 11 daga cikin waɗanda aka sace, ciki har da direbobin motocin da abin ya shafa, bayan wani samame da jami’an tsaro s**a gudanar tare.

Ta kuma bayyana cewa ana ci gaba da ƙoƙarin gano inda sauran waɗanda ke hannun masu garkuwa suke domin ceto su.

A halin yanzu, iyalan wasu daga cikin waɗanda har yanzu suke tsare sun yi kira ga Gwamnatin Tarayya, Hukumar NYSC da jami’an tsaro da su ƙara kaimi wajen tabbatar da sakin ’yan bautar ƙasar da sauran mutanen da ke hannun masu garkuwar.

Freedom Radio BBC Hausa

Address

Gombe

Telephone

07066010257

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AMT News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to AMT News:

Share