25/03/2026
Ƙungiyar Yan Jarida a Bauchi Ta Yi Allah-wadai da Zargin Cin Zarafin Ma’aikacin Gidan Rediyo
Ƙungiyar ‘yan jarida ta Najeriya reshen Bauchi, ta yi kakkausar s**a kan zargin cin zarafin da wasu ‘yan sanda s**a yi wa ma’aikacin Albarka Radio a garin Bununu, ƙaramar hukumar Tafawa Balewa, a lokacin bukukuwan Sallah.
A cikin wata sanarwa da sakataren ƙungiyar a jihar, Isah Garba Gadau, ya fitar, ya bayyana lamarin a matsayin take haƙƙin ɗan adam da kuma barazana ga ‘yancin aikin jarida.
Sanarwar ta ce, irin wannan hali na cin zarafi abin takaici ne daga jami’an da ake sa ran su kare rayuka da dukiyoyin jama’a, ba wai su cutar da su ba, tare da ƙara da cewa hakan na zuwa ne a lokacin da ƙungiyar ke ƙoƙarin ƙarfafa ƙwarewa da bin doka a tsakanin jami’an tsaro.
Ƙungiyar ta buƙaci kwamishinan ‘yan sandan jihar, Sani-Omolori Aliyu, da ya gaggauta bincike kan lamarin tare da hukunta dukkan jami’an da ke da hannu.
Haka kuma NUJ ta ce dole ne rundunar ‘yan sandan jihar ta ɗauki alhakin biyan dukkan kuɗaɗen jinyar wanda abin ya shafa.
Ƙungiyar ta yi gargaɗin cewa idan ba a ɗauki mataki cikin gaggawa ba, za ta kira taron gaggawa domin yanke hukuncin mataki na gaba.
A ƙarshe, ta buƙaci kafafen yaɗa labarai su kasance cikin shiri, tana mai jaddada cewa ba za ta lamunci duk wani tsoratarwa ko cin zarafi ga ‘yan jarida ba.
Facebook Kano, Nigeria BBC Hausa RFI Hausa DW Hausa