AMT News

AMT News A media and technology company providing news coverage, documentary production, content creation, digital communication, advertising, and ICT services.

25/03/2026
Ƙungiyar Yan Jarida a Bauchi Ta Yi Allah-wadai da Zargin Cin Zarafin Ma’aikacin Gidan RediyoƘungiyar ‘yan jarida ta Naje...
25/03/2026

Ƙungiyar Yan Jarida a Bauchi Ta Yi Allah-wadai da Zargin Cin Zarafin Ma’aikacin Gidan Rediyo

Ƙungiyar ‘yan jarida ta Najeriya reshen Bauchi, ta yi kakkausar s**a kan zargin cin zarafin da wasu ‘yan sanda s**a yi wa ma’aikacin Albarka Radio a garin Bununu, ƙaramar hukumar Tafawa Balewa, a lokacin bukukuwan Sallah.

A cikin wata sanarwa da sakataren ƙungiyar a jihar, Isah Garba Gadau, ya fitar, ya bayyana lamarin a matsayin take haƙƙin ɗan adam da kuma barazana ga ‘yancin aikin jarida.

Sanarwar ta ce, irin wannan hali na cin zarafi abin takaici ne daga jami’an da ake sa ran su kare rayuka da dukiyoyin jama’a, ba wai su cutar da su ba, tare da ƙara da cewa hakan na zuwa ne a lokacin da ƙungiyar ke ƙoƙarin ƙarfafa ƙwarewa da bin doka a tsakanin jami’an tsaro.

Ƙungiyar ta buƙaci kwamishinan ‘yan sandan jihar, Sani-Omolori Aliyu, da ya gaggauta bincike kan lamarin tare da hukunta dukkan jami’an da ke da hannu.

Haka kuma NUJ ta ce dole ne rundunar ‘yan sandan jihar ta ɗauki alhakin biyan dukkan kuɗaɗen jinyar wanda abin ya shafa.

Ƙungiyar ta yi gargaɗin cewa idan ba a ɗauki mataki cikin gaggawa ba, za ta kira taron gaggawa domin yanke hukuncin mataki na gaba.

A ƙarshe, ta buƙaci kafafen yaɗa labarai su kasance cikin shiri, tana mai jaddada cewa ba za ta lamunci duk wani tsoratarwa ko cin zarafi ga ‘yan jarida ba.

Facebook Kano, Nigeria BBC Hausa RFI Hausa DW Hausa

Yau shekara biyu kenan da rasuwar Saratu Gidado, wacce aka fi sani da Daso, shararriyar yar wasan kwaikwayo a masana'ant...
19/02/2026

Yau shekara biyu kenan da rasuwar Saratu Gidado, wacce aka fi sani da Daso, shararriyar yar wasan kwaikwayo a masana'antar shirya fina-finai ta Kanywood, wadda fina-finanta sun zama kusan mafi karbuwa a lokacin da take fagen wasan kwaikwayo.

Da wane Abu kuke tunawa da ita

Facebook Kano, Nigeria

18/02/2026

Kasuwar Duniya inda hausawa ke cinikayya a saudiya

18/02/2026

Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai

Saudiyya ta sanar da ganin watan Ramadan na shekarar 1447. A wata sanarwa da shafin da ke kula da Masallatai Biyu Masu D...
17/02/2026

Saudiyya ta sanar da ganin watan Ramadan na shekarar 1447. A wata sanarwa da shafin da ke kula da Masallatai Biyu Masu Daraja na Inside Haramain ya wallafa a X, ya ce an ga watan ne a yau Talata, kuma hakan na nufin za a tashi da azumin Ramadan a gobe Laraba 18 ga watan Fabrairun 2026 a ƙasar.

Da'awa: Adam Ashaka Da Baban Chinedu; yaya kuke ganin yunkuri da salon dawarsu ga musulunci?
11/02/2026

Da'awa: Adam Ashaka Da Baban Chinedu; yaya kuke ganin yunkuri da salon dawarsu ga musulunci?

HOTO: 'Ya 'yan Marigayi Sheikh Usman Kusfa Zaria (Rigi-rigi) a lokacin da suke karɓar Gaisuwar ta'aziyyar mahaifin su.
06/02/2026

HOTO: 'Ya 'yan Marigayi Sheikh Usman Kusfa Zaria (Rigi-rigi) a lokacin da suke karɓar Gaisuwar ta'aziyyar mahaifin su.

DAGA AIKIN JARIDA ZUWA SIYASA Sanannen Dan Jarida Nan a Jihar Gombe da Arewacin Najeriya Usman Abubakar Usmaniyya ya ams...
30/01/2026

DAGA AIKIN JARIDA ZUWA SIYASA

Sanannen Dan Jarida Nan a Jihar Gombe da Arewacin Najeriya Usman Abubakar Usmaniyya ya amsa kiraye-kirayen tsayawa takarar Majalisar Dokoki na Jihar Gombe da al-umar Akko ta Arewa Ke yi Masa.

Jama'ar yankin na ta kira wa Usmaniyya ya fito ya jagorance su, don Kawo shugabanci na gari a yankin, saboda hazaka da basirar da Allah ya h**e Masa.

Tuni dai Dan Jaridar dake aiki da Gidan radiyon Progress Gombe ya shahara wajen rajin tabbatar da samar da shugabanci nagari.

Wani fata za Ku yiwa Usmaniyya.

An tara wa Haruna Bashir da aka kashe wa mata da 'ya'ya 6 sama da Naira 25,000,000, karkashin jagorancin Barr. Abba Hiki...
24/01/2026

An tara wa Haruna Bashir da aka kashe wa mata da 'ya'ya 6 sama da Naira 25,000,000, karkashin jagorancin Barr. Abba Hikima Fagge.

Address

Gombe

Telephone

07066010257

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AMT News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to AMT News:

Share