Arewa Bridge Media

Arewa Bridge Media Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Arewa Bridge Media, Broadcasting & media production company, No. 10, Pantami Quarters Near, , Water Board, Gombe.
(1)

Arewa Bridge Media (ABM) kafa ce ta yaɗa labarai da ke watsa shirye-shirye kan al’amuran yau da kullum cikin harshen Hausa, Mallakin Kamfanin ABM Virtual Productions Ltd.

📞 Domin talla, a tuntube mu ta WhatsApp ko kiran wannan lamba: 08149675978.

DAY 9: A yau Jumma'a aka gudanar da Quiz  tsakanin ajin 'yan safe da ajin 'yan rana don gwada kokarin abubuwan da aka ko...
19/12/2025

DAY 9: A yau Jumma'a aka gudanar da Quiz tsakanin ajin 'yan safe da ajin 'yan rana don gwada kokarin abubuwan da aka koya musu.

Wanda gidauniyar Professor Isa Ali Pantami hadin guiwa da Mujaddadi Care Foundation take horar da matasa 200 'yan jihar Bauchi sana'ar gyaran wayoyi, AI da tsaron yanar gizo, a yau Jumma'a rana ta tara.

Hakika munsha mamaki sosai na jin yadda matasan s**a taka muhimmiyar rawa na abubuwan da aka koya musu, idan 'yan ajin safe s**a lashe Quiz din 'yan ajin rana s**a zo na biyu.

An bawa matasan da s**a yi Quiz din kyautar Naira dubu 250k domin kara karfafawa matasan guiwa.

Matasa Daga Arewacin Najeriya Sun Bukaci Tinubu Ya Sallami Ministan Tsaro Bello MatawalleƘungiyar Northern Christian You...
19/12/2025

Matasa Daga Arewacin Najeriya Sun Bukaci Tinubu Ya Sallami Ministan Tsaro Bello Matawalle

Ƙungiyar Northern Christian Youth Coalition (NCYC) ta bukaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya sallami Ministan Ƙasa na Tsaro, Dr. Bello Muhammed Matawalle, sakamakon zarge-zargen da suke nuna cewa yana da alaƙa da ta'addanci wanda tsohon hadiminsa Musa Kamarawa yayi ikirari.

A cikin wata sanarwa da Babban Kwamishinan ƙungiyar, Jeremaid Hudso Bako, ya fitar, ƙungiyar ta ce kira da take yi na nufin ƙarfafa gaskiya, riƙon amana, da dawo da amincewar jama’a ga gwamnati, musamman a bangaren tsaro.

Ƙungiyar ta yaba wa Shugaba Tinubu kan tsige tsohon Shugaban Hukumar NMDPRA, Farouk Ahmed, tana mai cewa hakan alama ce ta ƙoƙarin gwamnati wajen yaƙi da cin hanci da rashawa. Sai dai ta ce ya dace a yi adalci iri ɗaya ga kowa, ciki har da Matawalle.

NCYC ta jaddada cewa zarge-zargen da ake yi wa Matawalle suna da nauyi sosai, musamman ganin cewa suna da alaƙa da tsaron ƙasa da rayukan al’umma, don haka bai dace a yi shiru a kansu ba.

Ƙungiyar ta ce idan har gwamnatin Tinubu na son a san ta da gaskiya, adalci da shugabanci nagari, to ya zama dole ta ɗauki mataki cikin gaggawa kan duk wani jami’i da ake zargi da aikata abubuwan da za su iya lalata amincin ƙasa tare da sauke ƙaramin ministan da kuma gudanar da binciken gaggawa a kansa.

DA DUMI-DUMI: Hadakar kungiyoyin Mata dake Kaltungo jihar Gombe, sunyi kira ga Sheikh Professor Isa Ali Pantami, da ya f...
18/12/2025

DA DUMI-DUMI: Hadakar kungiyoyin Mata dake Kaltungo jihar Gombe, sunyi kira ga Sheikh Professor Isa Ali Pantami, da ya fito takarar Gwamnan jihar Gombe a zaben 2027.

Ƙungiyar hadakar kungiyoyin Mata magoya bayan Sheikh Pantami, Kaltungo (Pantami Women Supporters, Kaltungo) sun gayyaci wakilan gidan Prof Pantami, domin nuna cikakken goyon bayansu tare da kiranye ga Farfesan da ya fito takarar Gwamnan jihar Gombe a zaben 2027.

Kungiyar, wadda ta ƙunshi kungiyoyin mata daban-daban da s**a haɗu a ƙarƙashin inuwa guda, ta bayyana cewa sun ɗauki wannan matsaya ne bisa ayyukan alheri da tasiri da Farfesa Pantami ya yi wa al'umma, musamman wajen taɓa rayuwar matasa kai tsaye ta hanyar koyar da sana'o'i, samar da damar aikin yi, tallafawa ɗalibai da ƙarfafa ilimi.

A cewar kwa'odinetar haɗakar kungiyoyin, Hajiya Fatima Abdulmalik, Kaltungo, Sheikh Pantami na da tarihin ayyukan alheri, hangen nesa da kishin al'umma, inda ta ce fitowarsa takarar Gwamna a 2027 zai zama babbar dama ta samar da shugabanci nagari da cigaban jihar Gombe da al'ummar cikinta.

Gayyatar ta samu jagorancin Malam Hamza Abdullahi tare da haɗin kan Abba Sani Pantami, Hon Hon Aliyu Y Zannah, Naziru Aliyu, Mudassir Ibrahim da kuma Oga Salees.

HOTUNA: Yadda aikin sabuwar tagwaye hanyar da ta taso daga mahaɗar Asibitin koyarwa na gwamnatin tarayya zuwa kolejin il...
18/12/2025

HOTUNA: Yadda aikin sabuwar tagwaye hanyar da ta taso daga mahaɗar Asibitin koyarwa na gwamnatin tarayya zuwa kolejin ilimi na gwamnatin tarayya zuwa hanyar Bojago, yake gudana.

Wannan aiki yana ɗaya daga cikin aiyukan sabunta birane da gwamnatin Muhammadu Inuwa Yahaya CON take ci gaba da gudanarwa a jihar Gombe.

Daga Haji Shehu
S. A. Media

YANZU-YANZU: Injiniya Farouk Ahmad ya yi murabus daga mukaminsa na Shugaban Hukumar Kula da Albarkatun Man Fetur (NMDPRA...
17/12/2025

YANZU-YANZU: Injiniya Farouk Ahmad ya yi murabus daga mukaminsa na Shugaban Hukumar Kula da Albarkatun Man Fetur (NMDPRA), bayan zargin da attajirin ɗan kasuwa Aliko Dangote ya yi masa na karɓar cin hanci.

Rahotanni sun nuna cewa Dangote ya zargi Farouk da karɓar dala miliyan 5 don biyan kuɗin makarantar ‘ya’yansa huɗu a ƙasar Switzerland, lamarin da ya janyo ce-ce-ku-ce a kafafen yaɗa labarai da kuma cikin masu ruwa da tsaki a bangaren man fetur.

Wasu na ganin ya kamata a gudanar da bincike mai zaman kansa cikin gaggawa domin tabbatar da gaskiyar lamarin, yayin da wasu ke ganin ya kamata a bari shiru ya lafa.

Me ra’ayinku? A binciki lamarin ko a rufe shafin?

INNALILLAHI WA’INNA ILAIHI RAJI’UN Zargin 3-in-1: Ɗan Achaba Ya Rasa Ransa a Hannun ‘Yan Sanda a GombeRahotanni daga Jih...
17/12/2025

INNALILLAHI WA’INNA ILAIHI RAJI’UN

Zargin 3-in-1: Ɗan Achaba Ya Rasa Ransa a Hannun ‘Yan Sanda a Gombe

Rahotanni daga Jihar Gombe sun tabbatar da cewa wani matashi ɗan achaba ya rasa ransa bayan dukan da wasu jami’an ‘yan sanda s**a yi masa da kulki, bisa zargin ɗaukar fasinja fiye da ƙima — wato 3-in-1.

Lamarin ya tayar da hankula a garin, inda ɗaruruwan abokan aikinsa s**a fito zanga-zanga, suna toshe titin Union Bank zuwa Sabon Layi, tare da bukatar adalci kan abin da s**a kira kisa ba tare da hakki ba.

Al’umma da dama sun bayyana damuwa da alhini kan faruwar lamarin, suna kira ga hukumomi da su gudanar da bincike mai zaman kansa, tare da hukunta duk wanda aka samu da laifi.

“Idan aka ci gaba da watsi da irin wannan zalunci, to jama’a za su rasa amincewa da hukumomin tsaro,” inji wani mai magana da yawun matasan unguwar.

Har yanzu rundunar ‘yan sandan jihar ba ta fitar da cikakken bayani kan lamarin ba. Ana ci gaba da dakon martani daga hukumomi.

CIGIYA: Ana cigiyan wannan yarinya mai suna Suhaima ‘yar kimanin shekaru 6, wadda ta bace a garin Gombe.Suhaima sun zone...
17/12/2025

CIGIYA: Ana cigiyan wannan yarinya mai suna Suhaima ‘yar kimanin shekaru 6, wadda ta bace a garin Gombe.

Suhaima sun zone daga Filiya domin halartar biki a unguwar Hammadu Kafi, dake cikin birnin Gombe. Ta batane a ranan 16/12/2025, da misalin karfe 11:00 na safe, tana sanye da doguwar riga da dankwali

Ga duk Wanda Allah yasa ya ganta, don Allah a tuntubi waɗannan lambobin nan take:

📞 08089877095
📞 07066029106

Allah ya sa a sameta lafiya. Amin.

YANZU-YANZU: Amb. Zainab Musa Ya’u ta bayyana farin cikinta bisa samun damar halartar bikin ƙaddamar da Connect Network ...
16/12/2025

YANZU-YANZU: Amb. Zainab Musa Ya’u ta bayyana farin cikinta bisa samun damar halartar bikin ƙaddamar da Connect Network Foundation, wanda aka shirya tare da haɗin guiwar Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci ta Ƙasa (NCTC) ƙarƙashin Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro (ONSA).

A taron, an tattauna yadda haɗin kai tsakanin gwamnati, ƙungiyoyi, da al’umma ke da muhimmanci wajen kawo zaman lafiya da tabbatar da tsaro a ƙasa. Amb. Zainab ta samu damar yin jawabi a madadin mata na Arewacin Najeriya, inda ta bayyana matsalolin da mata ke fuskanta – irin su rashin tsaro, talauci, da ƙarancin ilimi.

Ta yi kira da a ba mata dama a cikin harkokin yanke shawara, a tallafa musu da ilimi da hanyoyin samun jari, da kuma a mayar da hankali wajen kawo tsare-tsare da s**a shafi rayuwar mata. Taron ya ƙarfafa buƙatar haɗin kai domin samar da zaman lafiya mai ɗorewa a Najeriya.

Odua People’s Assembly Ta Nemi Gwamnati Ta Gudanar Da Bincike Gaggawa Kan Matawalle....Zargin alaƙa da ‘yan bindiga bara...
16/12/2025

Odua People’s Assembly Ta Nemi Gwamnati Ta Gudanar Da Bincike Gaggawa Kan Matawalle
....Zargin alaƙa da ‘yan bindiga barazana ce ga tsaron Najeriya.

Ƙungiyar Odua People’s Assembly (OPA) ta nuna damuwa matuƙa kan zargin da ake yi wa Ministan Tsaron Ƙasa (State), Bello Matawalle, dangane da alaƙa da ‘yan bindiga. Ƙungiyar ta ce zargin yana da hatsari ga tsaron ƙasa da amincewar jama’a.

OPA ta buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta gudanar da bincike mai zaman kansa, tare da sanya gaskiya kuma ba tare da son kai ba, domin fayyace gaskiyar lamarin. Ta ce rashin daukar mataki zai ƙara raunana amincewar jama’a da hukumomin gwamnati, musamman a lokacin da Najeriya ke fama da matsanancin matsalar tsaro.

Ƙungiyar ta ce bayyanar wani bidiyo da ke nuna Bello Turji, shugaban ‘yan bindiga, yana kare Matawalle abin tayar da hankali ne, domin yana nuna yiyuwar haɗin kai tsakanin jami’an gwamnati da masu laifi.

OPA ta bayyana cewa duk wata alaƙa, kai tsaye ko a kaikaice, tsakanin jami’an gwamnati da ‘yan bindiga cin amanar ‘yan Najeriya ne, musamman waɗanda s**a sha wahala sakamakon rashin tsaro.

A matsayin mataki na dawo da amincewar jama’a, OPA ta buƙaci a sauke Matawalle daga muƙaminsa nan take, tare da kafa cikakken tsari na bincike mai zaman kansa. Ta kuma gargadi cewa rashin daukar mataki mai tsauri zai ƙarfafa ‘yan bindiga tare da ƙara ta’azzara rashin tsaro.

Ƙungiyar ta bukaci ‘yan Najeriya su kasance masu faɗakarwa, su kuma riƙa kira ga alhakin shugabanni, tana jaddada cewa yaƙi da ‘yan bindiga ya zama na bai ɗaya, ba tare da la’akari da siyasa ko yanki ba.

Sa Hannun
Sunday Daniel
Mai magana da yawun Odua People’s Assembly

ALBISHIRIN KU GOMBAWA: Gwamnatin Jihar Gombe ta rattaba hannu kan wata yarjejeniyar fahimtar juna (MoU) da Hukumar Samar...
16/12/2025

ALBISHIRIN KU GOMBAWA: Gwamnatin Jihar Gombe ta rattaba hannu kan wata yarjejeniyar fahimtar juna (MoU) da Hukumar Samar da Wutar Lantarki a Karkara (REA) don samar da wutar lantarki mai amfani da hasken rana da rarraba ta Jihar.

Wannan tsari zai maida hankali ne kan al'ummomin da basu da wutar lantarki, wuraren da suke da ƙarancin ingantaccen wuta, da kuma yankunan karkara.

Wannan tsari zai bawa yankunan da s**a kasance cikin tsarin damar zaɓar layin wutarlantarki Ko Wutar Solar a gidajen su.

Daga Haji Shehu
S. A. Media

Sako mai matukar muhimmanci ga yankunan da suke fama da matsalar tsaro kuma ake yin sulhu da 'yan bindiga Comr Umar Gaga...
16/12/2025

Sako mai matukar muhimmanci ga yankunan da suke fama da matsalar tsaro kuma ake yin sulhu da 'yan bindiga

Comr Umar Gagarau Faskari Katsina ne ya rubuta👇

Wannan rikicin da ake ta samu tsakanin Matawalle, da wani Yaron sa Kamarawa da Malam Murtala Asada da har ya kai ga Bello Turji ya fito da bidiyo ya ƙara bayyana min wani babban kuskure da mutanenmu na Faskari Katsina s**a tafka ko suke tafkawa har yanzu haka.

Na sakar wa tubabbun ’yan ta’adda jiki bayan sasanci da su.

Wasu daga cikinsu yanzu sun koma kamar 'yan uwa ana waya da su, ana ziyarta gida, har ma da huldar yau da kullum.

Duk da muna fatan sasancin ya tabbata, ainihin gaskiyar lamarin ita ce yawancin rikice-rikicen da ake zargin su Matawalle da hannu a ciki, sun faru ne bayan an riga an kulla wannan sulhu ba kafin ba a tunani na kenan.

Amma yanzu, abin da ya rage shi ne babu mai iya wanke sunan Matawalle sai Allah kadai.

Ya Allah muna rokon ka tona asirin duk mai hannu a cikin ta'addacin da ake yi a Arewa dama Najeriya baki daya.

Daga Comr Umar Gagarau
15-Dec.-2025.

Duk wanda ya sayi Datar 500MB da 1GB ta MTN mai 30DAYS a Application din ABBA PANTAMI DATA LTD to sai tayi kwanaki 30 sa...
16/12/2025

Duk wanda ya sayi Datar 500MB da 1GB ta MTN mai 30DAYS a Application din ABBA PANTAMI DATA LTD to sai tayi kwanaki 30 sannan za tayi Expired. Akwai bambanci tsakanin Expired da kuma karewa.

Kamfanin ABBA PANTAMI DATA LTD, ya rage muku farashin Data, kowa ya duba Application dinshi domin more garabasa.

Matukar kuna amfani da Application din ABBA PANTAMI DATA LTD da zaran ka hadu da matsalar network ko matsalewar kudi kana yiwa customer care dinsu magana anan take zasu gyara maka.

Idan baka taba amfani da Application din ba ka gwada, idan ka dade baka yi amfani dashi ba ka sake gwadawa a yanzu domin tabbatar da ingancin shi.

Address

No. 10, Pantami Quarters Near, , Water Board
Gombe
760253

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Bridge Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa Bridge Media:

Share