Arewa Bridge Media

Arewa Bridge Media Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Arewa Bridge Media, Broadcasting & media production company, No. 10, Pantami Quarters Near, , Water Board, Gombe.
(1)

Arewa Bridge Media (ABM) kafa ce ta yaɗa labarai da ke watsa shirye-shirye kan al’amuran yau da kullum cikin harshen Hausa, Mallakin Kamfanin ABM Virtual Productions Ltd.

📞 Domin talla, a tuntube mu ta WhatsApp ko kira wannan lamba: 08149675978.

TIRKASHI: Sojojin Amurka Sun Gudanar da Atisaye Na Musamman Don Kara Shiri a Fannin TsaroSojojin Ma’aikatar Tsaro ta Amu...
04/11/2025

TIRKASHI: Sojojin Amurka Sun Gudanar da Atisaye Na Musamman Don Kara Shiri a Fannin Tsaro

Sojojin Ma’aikatar Tsaro ta Amurka sun gudanar da wani atisaye na musamman a sansanin soja, inda aka ga dakarun suna motsa jiki da tsari, domin ƙara ƙarfin jiki da ƙwarewa a ayyukan tsaro.

Hotunan da aka wallafa sun nuna yadda matasa dakarun ke aiwatar da atisayen cikin natsuwa da jajircewa, wanda ke nuna yadda rundunar ke kasancewa cikin shiri a kowane lokaci don tabbatar da tsaro da kariya ga kasa.

Rahotanni sun bayyana cewa irin wannan atisaye yana daga cikin shirye-shiryen da ake gudanarwa akai-akai domin tabbatar da cewa sojoji suna cikin koshin lafiya da cikakken shiri wajen aiwatar da ayyukansu.

DA DUMI DUMI: Ana Zargin Shugaban kasar Korea ta Arewa Kim Jong-Un ya Fashe da Kuka Saboda yarasa Wanda Zai kai Masa Har...
04/11/2025

DA DUMI DUMI: Ana Zargin Shugaban kasar Korea ta Arewa Kim Jong-Un ya Fashe da Kuka Saboda yarasa Wanda Zai kai Masa Hari domin Suyi y@ƙi

- Ya shafe tsawon lokaci yana jiran a tsokane shi fada amma anki.
- Ya tsokana ya tsokana anyi banza dashi.
- Yayi habaice-habaice anyi banza dashi.
- Shi kadai ya yita kugi, amma an gagara tanka mishi.

Akwai lokacin da Donald Trump yaje ziyara Korea ta kudu, saboda tsabar neman rigima Kim Jong-Un, ya yita gwajin sabbin manya-manyan mak**ai a bakin iyakar kasarsa da Korea ta kudu amma Donald Trump ya kasa tankawa.

Yauwa, a fadawa Donald J. Trump a can kasar Korea ta Arewa ta Kim Jong-Un, can ne ake mulkin k**a karya da take hakkin Dan Adam don haka ya gaggauta zuwa ya dauki matakin da ya dace.

Mu a nan Najeriya muna zaune lafiya da kowane addini kowa yana da 'yancin yin addininsa sai-dai masu kwana da yunwa suna da yawa, sai-dai idan zai raba mana tallafin Daloli kyauta, muna matukar bukata.

ABIN A YABA: Gwamnan Bauchi Ya Warware Matsalar Wutar Lantarki a Unguwar Dr. Sulaiman Adamu QuartersBauchi – Dogon lokac...
03/11/2025

ABIN A YABA: Gwamnan Bauchi Ya Warware Matsalar Wutar Lantarki a Unguwar Dr. Sulaiman Adamu Quarters

Bauchi – Dogon lokaci da mazauna unguwar Dr. Sulaiman Adamu Quarters, dake Behind Vanilla, Col. Hamidu Ali Street, ke fama da matsalar wutar lantarki ya zo karshe.

Mai girma Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulkadir Muhammad (Kauran Bauchi), ya samar da sabon transformer ga unguwar domin magance matsalar, wanda ya kawo ƙarshen duhu da tsadar wuta da ya addabi al’umma na tsawon lokaci.

Mazauna unguwar sun bayyana farin cikinsu, inda s**a nuna godiya ga gwamna Bala Abdulkadir Muhammad bisa wannan matakin, wanda ya sauƙaƙa rayuwarsu da walwalar sana’o’i.

Wasu daga cikin mazauna sun ce wannan aiki ya tabbatar da cewa gwamnatin Kauran Bauchi na sauraron bukatun al’umma tare da daukar matakai masu amfani a lokuta daban-daban.

Atiku Abubakar Ya Kai Ziyarar Ta’aziya Ga Ƙungiyar Gidan H.E. Ahmadu Adamu Mu’azu A safiyar yau, Atiku Abubakar, tare da...
03/11/2025

Atiku Abubakar Ya Kai Ziyarar Ta’aziya Ga Ƙungiyar Gidan H.E. Ahmadu Adamu Mu’azu

A safiyar yau, Atiku Abubakar, tare da wata tawagar abokai da abokan hulɗa, sun kai ziyarar ta’aziya ga iyalan H.E. Ahmadu Adamu Mu’azu, tsohon Gwamnan Jihar Bauchi kuma tsohon Shugaban Kasa na PDP, bisa rasuwar mahaifiyarsa, Hajiya Halima Suleman.

A yayin ziyarar, sun yi addu’o’i domin samun rahama ga marigayiya, tare da roƙon Allah Madaukakin Sarki ya jikanta, ya ba ta Aljannah Firdausi.

Atiku ya bayyana cewa rasuwar Hajiya Halima Suleman ta bar gibi mai yawa a cikin iyalan, kuma za a yi kewarta sosai.

Ya kara da cewa za su ci gaba da roƙon Allah ya ba iyalan marigayiya ƙarfin zuciya da haƙuri wajen jure wannan babban rashi. Amin.

DA ƊUMI ƊUMI: Gwamnatin Najeriya na Shirin Dakatar da Amfani da Dollar wajen Siyan Tikitin Jiragen SamaGwamnatin tarayya...
03/11/2025

DA ƊUMI ƊUMI: Gwamnatin Najeriya na Shirin Dakatar da Amfani da Dollar wajen Siyan Tikitin Jiragen Sama

Gwamnatin tarayya na duba yiwuwar hana siyan tikitin jiragen sama na kasashen waje da ake biyan su da Dollar, domin karfafa darajar Naira a cikin kasar.

A yanzu, kamfanonin jiragen sama da dama da ke jigilar fasinjoji daga Najeriya, ciki har da British Airways, Lufthansa, da Emirates, suna siyar da tikitinsu da Dollar, duk da cewa ana amfani da su a Najeriya. Wannan abu yana karawa Dollar daraja yayin da yake rage martabar Naira.

Gwamnatin ta ce za ta gabatar da tsare-tsaren da zasu tabbatar da cewa amfani da Dollar a cikin Najeriya ba zai cigaba da faruwa ba, tare da karfafa amfani da Naira a cikin kasuwannin cikin gida.

An bayyana cewa matakin na daga cikin kokarin bunkasa darajar Naira, rage dogaro da kudin waje, da kuma karfafa tattalin arzikin Najeriya. Wannan na nuni da cewa, k**ar yadda Dollar ke aiki a kasashen waje, Naira ma ya k**ata ta zama kudi na farko a Najeriya

LABARI MAI DAƊI: Shahararren mawakin Najeriya, Damini Ogulu, wanda aka fi sani da Burna Boy, ya bayyana cewa ya sauya ad...
03/11/2025

LABARI MAI DAƊI: Shahararren mawakin Najeriya, Damini Ogulu, wanda aka fi sani da Burna Boy, ya bayyana cewa ya sauya addini daga Kiristanci zuwa Musulunci bayan dogon tunani da bincike kan gaskiyar rayuwa da addini.

A cewar Burna Boy, wannan mataki bai samo asali daga matsin lamba ba, sai dai daga zurfin tunani da nazari da ya yi kan ma’anar rayuwa da manufar addini.

“Na dade ina tambayar kaina meye gaskiya game da rayuwa da addini. A ƙarshe, na ji zuciyata ta natsu da Musulunci. Wannan ne dalilin da ya sa na rungumi wannan hanya,” in ji shi.

Mawakin ya kara da cewa, duk da wannan sauyi, yana girmama sauran addinai kuma yana kira ga mutane su zauna lafiya da juna ba tare da bambancin addini ko ƙabila ba.

Burna Boy, wanda ya shahara da wakokinsa na duniya, ya ce burinsa shi ne ya zama mutum mai gaskiya da mutunci, komai bambancin fahimta.

CIKIN HOTUNA: Sanata Natasha Akpoti Ta Tallafa Wa Sama da Ƴan Mazaɓanta 2,000  Sanata Natasha Akpoti, mai wakiltar Kogi ...
03/11/2025

CIKIN HOTUNA: Sanata Natasha Akpoti Ta Tallafa Wa Sama da Ƴan Mazaɓanta 2,000

Sanata Natasha Akpoti, mai wakiltar Kogi ta Tsakiya a Majalisar Dattijai, ta raba kayan tallafi ga sama da ƴan mazaɓanta sama da mutum dubu 2 a cikin ƴan kwanakin nan.

Kayan tallafin sun haɗa da abinci da sauran abubuwan bukatu na yau da kullum, inda hakan ya faranta ran al’umma sosai.

Tallafin ya zo ne a matsayin wani ɓangare na ayyukan jin ƙai da Sanata Natasha ke yi domin inganta rayuwar al’ummar da ta ke wakilta.

YANZU-YANZU: An Gudanar da Jana'izar Malam Nata'ala a Fadar Sarkin Fika, Jihar Yobe, Tare da Halartar Daruruwan Mutane  ...
03/11/2025

YANZU-YANZU: An Gudanar da Jana'izar Malam Nata'ala a Fadar Sarkin Fika, Jihar Yobe, Tare da Halartar Daruruwan Mutane

An gudanar da jana’izar Malam Nata’ala, jarumin Kannywood, a Fadar Mai Martaba Sarkin Fika, Jihar Yobe, inda daruruwan jama’a s**a hallara domin yin ta’aziya da girmamawa ga marigayin.

Allah Ya gafarta masa, ya jikan shi, ya sanya makoma alkhairi a lahira.

HOTUNA: Hassan Peppe

ALLAHU AKBAR: An ɗauko gawar Jarumin Kannywood Malam Nata’ala daga Babbar Asibitin Maiduguri zuwa garin Potiskum, Jihar ...
03/11/2025

ALLAHU AKBAR: An ɗauko gawar Jarumin Kannywood Malam Nata’ala daga Babbar Asibitin Maiduguri zuwa garin Potiskum, Jihar Yobe, domin gudanar da jana’iza.

Tawagar hukumar bada agajin gaggawa ta Jihar Yobe (SEMA) ta isa babban asibitin domin ɗaukar gawar marigayin zuwa Potiskum.

Ismail Danmallam Buniyadi, mai taimaka wa Gwamnan Yobe kan yaɗa labarai, ya tabbatar da hakan a shafinsa na Facebook, inda ya ce ana sa ran gudanar da jana’izar a fadar Mai Martaba Sarkin Fika da misalin ƙarfe 2:30 na rana.

Jarumin fina-finan Hausa ya rasu ne ranar Lahadi bayan fama da jinya a asibitin Maiduguri.

DA DUMI-DUMI: Jami'an tsaro sun k**a Indabawa Imam Aliyu, kan laifin kirkirar karya, kazafi, sharri da cin mutunci da ya...
03/11/2025

DA DUMI-DUMI: Jami'an tsaro sun k**a Indabawa Imam Aliyu, kan laifin kirkirar karya, kazafi, sharri da cin mutunci da ya shafe tsawon shekaru yana yadawa akan Sheikh Professor Isa Ali Pantami CON (Majidadin Daular Usmaniyya).

Ku duba hotunan dake kasa, na wasu shafukan da yake kula dasu, tun a 2022 yake kirkirar karya da kazafi da sharri, cin mutunci, yana sakawa a shafukan nashi na yada labarai, amma aka yi shiru aka barshi domin wata kila zai gaji ya daina, amma duk da haka kwanan nan ya kara kirkiro wani labarin karyar tare da kafa source na wata jaridar karya da aka neme ta aka rasa a Facebook.

Tuni jami'an tsaro sun kamo shi a jihar Kano, inda a yau Litinin za'a gabatar dashi a gaban kotu, bayan an kammala zaman kotun zamu sanar muku.

Wa 'yan nan kadan ne daga cikin irin cin mutunci da kirkirar karya haka kawai don yasa al'umma su zagi Sheikh Professor Professor Isa Ali Pantami, mun kawo muku wannan rahoton ne ba don cin mutuncin shi ba sai-dai masu irin wannan halin su gyara.

GARGADI: Duk wanda yasan yana cin mutuncin Sheikh Professor Isa Ali Pantami, na kirkirar karya, sharri da kazafi a social media ko a gidajen Radio to tabbas ya sani wallahi doka za tayi aiki akanshi.

Siyasa da adawa ba'a hana kowa ba, kuma ba'a taba tankawa wani don yayi adawa da Malam ba, amma ba zamu taba lamunta da cin mutunci, sharri da kazafi ba, domin mutane da yawa suna ganin saukin taba Malam saboda ya kasance Malamin Addinin musulunci kuma mutumin kirki.

Yau, a jihar Gombe akwai manyan 'yan siyasar da wallahi ko zaginsu ba'a isa a yi ba, saboda kowa yana tsoron daure shi za suyi, b***e ka dinga kirkira musu karya, kazafi, sharri da cin mutuncinsu, amma kasancewar shi Pantami malamin Addinine yasa kowane kare ya tashi haushi da cin mutunci sai ya dirka kan Pantami. Ya k**ata duk wani matashin a jihar Gombe dama Najeriya ya sani, yanzu ba baya bane, doka za tayi aiki akan duk wanda yaci mutuncin Sheikh Pantami.

Shafukanshi na CNN HAUSA da VANGUARD HAUSA kullum cikin yada labaran karya da yiwa al'umma sharri suke yi, a guji yadda da abubuwan da suke ruwaitowa kasancewar shafukane na bogi.

YANZU-YANZU: Allah ya yi wa jarumin Kannywood Malam Nata'ala rasuwa  Shahararren ɗan wasan Kannywood na shirin Daɗin Kow...
02/11/2025

YANZU-YANZU: Allah ya yi wa jarumin Kannywood Malam Nata'ala rasuwa

Shahararren ɗan wasan Kannywood na shirin Daɗin Kowa, Malam Nata'ala, ya rasu yau Lahadi a Asibitin koyarwa na Jami’ar Maiduguri.

Za a kai gawarsa Potiskum domin gudanar da Sallar jana'iza.

Har zuwa yanzu, ba a bayyana lokacin jana'iza ba.

02/11/2025

DA DUMI DUMI: Al'ummar Dukku sun fito zanga-zanga cikin lumana domin nuna damuwa kan lalacewar hanyar Gombe–Dukku–Darazo. Matasa da dattawa sun ɗauki banner da rubuce-rubuce suna kira ga gwamnati da hukumomin da abin ya shafa su gyara hanya kafin ta zama barazana ga rayuka da dukiyoyi.

Address

No. 10, Pantami Quarters Near, , Water Board
Gombe
760253

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Bridge Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa Bridge Media:

Share