Arewa Bridge Media

  • Home
  • Arewa Bridge Media

Arewa Bridge Media Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Arewa Bridge Media, Broadcasting & media production company, .

"Arewa Bridge Media (ABM) is a news agency that presents programs relating to current affairs in Hausa language, owned by ABM VIRTUAL PRODUCTIONS LTD."

🔗 Follow us on our other social media platforms:
👇 👇👇
https://linktr.ee/arewabrigemedia

YANZU-YANZU: Sanusi Bature Ya Sayi Garin ÆŠanwake Kan Naira Miliyan DayaDaraktan Yada Labarai na Gwamnatin Kano, Hon. San...
21/07/2025

YANZU-YANZU: Sanusi Bature Ya Sayi Garin ÆŠanwake Kan Naira Miliyan Daya

Daraktan Yada Labarai na Gwamnatin Kano, Hon. Sanusi Bature D-Tofa, ya sayi garin Ɗanwake da ke wani yanki a jihar Kano da zunzurutun kuɗi har Naira Miliyan 1. Wannan mataki ya janyo ce-ce-ku-ce da yabo daga mabiyan tafiyar Kwankwasiyya, inda suke ganin hakan a matsayin wani ɓangare na kishin al'umma da ci gaban kasa.

Karya Ce Tsagwaronta: Muhammad Babangida Bai Ƙi Nadin Da Shugaba Tinubu Yayi Masa Ba Wasu mutane masu ƙazamin nufi sun b...
21/07/2025

Karya Ce Tsagwaronta: Muhammad Babangida Bai Ƙi Nadin Da Shugaba Tinubu Yayi Masa Ba

Wasu mutane masu ƙazamin nufi sun bazu da wani labari mara tushe a kafafen sada zumunta da ke cewa Muhammad Babangida, ɗan tsohon shugaban kasa Ibrahim Badamasi Babangida (IBB), ya ƙi amincewa da nadin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya masa na chairman BOA.

Mun tabbatar da cewa wannan labarin ƙarya ne tsagwaronta, domin ba Muhammad Babangida bane ya fitar da sanarwar da ke yawo ba. Lambar da ke jikin takardar da aka yaɗa da kuma sa hannun da ke cikinta duk ba nasa ba ne.

Wannan wata makirci ce ta ɓatanci da ƙoƙarin jefa shakku a tsakanin shugaban ƙasa da manyan 'yan Najeriya, musamman waɗanda ke da sunaye da martaba a cikin al'umma.

Muhammad Babangida bai fito ya musanta nadin ba, kuma babu wata cikakkiyar shaida daga gare shi ko daga hannunsa da ke nuna ya ƙi karɓar kujerar. Wannan yana nuni da cewa an ƙirƙiri wannan labari ne domin yaudarar jama'a da haddasa ruɗani.

Muna kira ga 'yan Najeriya da su yi hattara da labaran ƙarya da ake yawan yaɗawa, su nemi gaskiya daga ingantattun majiyoyi kafin yarda da kowace irin sanarwa.

Allah ya ƙara haɗin kanmu da cigaban ƙasar nan.

RAHOTO: Zanga-Zanga da Tattaunawa Kan Biyan Fansho Ga Tsoffin Ƴan Sanda a AbujaA yau a birnin Abuja, wasu tsoffin jami’a...
21/07/2025

RAHOTO: Zanga-Zanga da Tattaunawa Kan Biyan Fansho Ga Tsoffin Ƴan Sanda a Abuja

A yau a birnin Abuja, wasu tsoffin jami’an ƴan sanda sun fito zanga-zanga cikin lumana domin neman a biya su hakkokinsu na fansho da haƙƙin ritaya. Sai dai rahotanni sun bayyana cewa wasu daga cikin sabbin jami’an ƴan sanda sun shiga tsakani da nufin hana ci gaba da zanga-zangar.

Biyo bayan wannan, Sufeto Janar na Æ´an sanda, IGP Kayode Egbetokun, ya gana da waÉ—anda s**a ritaya a dakin taro na Peacekeeping Hall da ke hedikwatar Æ´an sanda. Taron ya gudana cikin kwanciyar hankali, inda IGP ya bayyana cewa rundunar na sauraron korafe-korafensu da niyyar nemo mafita mai kyau da mutuntaka.

IGP Egbetokun ya nuna cewa wannan ganawa alama ce ta niyyar shugabancin ƴan sanda wajen kulawa da rayuwar jami’an da s**a ba da gudunmawarsu ga ƙasa bayan kammala aiki.

Ana sa ran ƙarin bayani daga hukumomi nan ba da jimawa ba yayin da tattaunawar ke cigaba.

YANZU-YANZU: Mun Dauki Tsawon Shekaru Talatin Muna Aiki Ba Dare Ba Rana, Amma Yanzu Hakkiñmu Ya Gagara Fita Da Za Mu Ciy...
21/07/2025

YANZU-YANZU: Mun Dauki Tsawon Shekaru Talatin Muna Aiki Ba Dare Ba Rana, Amma Yanzu Hakkiñmu Ya Gagara Fita Da Za Mu Ciyar Da Iyalanmu, Cewar Tsoffin 'Yan Sandan Nijeriya Dake Zañgà-Zañgà A Abuja

TIRKASHI: Yadda sabbin jami'an 'yan sanda suke ta kokarin hana yin zanga-zangar kwato hakkin tsoffin 'yan sanda a Abuja.
21/07/2025

TIRKASHI: Yadda sabbin jami'an 'yan sanda suke ta kokarin hana yin zanga-zangar kwato hakkin tsoffin 'yan sanda a Abuja.

GWANIN BURGEWA: Al’mansoor Gusau Ya Sami Damar Wakiltar Najeriya a Taron Kasa da Kasa a Beijing  Al’mansoor Gusau, ɗan N...
21/07/2025

GWANIN BURGEWA: Al’mansoor Gusau Ya Sami Damar Wakiltar Najeriya a Taron Kasa da Kasa a Beijing

Al’mansoor Gusau, ɗan Najeriya kuma mai fafutukar cigaban al’umma, ya samu damar halartar taron bita na kasa da kasa (International Seminar) a Beijing, babban birnin kasar China. Taron ya gudana ne ƙarƙashin shirin AIBO, wanda ke karkashin Ma’aikatar Kasuwanci ta Jamhuriyar Jama’ar China.

Wannan damar wakiltar Najeriya a matakin duniya, a cewar Al’mansoor, wata babbar girmamawa ce da za ta ba shi damar koyon sabbin dabaru, musayar ra’ayoyi tare da gina alaka da wakilai daga sassa daban-daban na duniya domin amfanin ƙasa.

Ya bayyana godiyarsa ga Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar (Marafan Sokoto) da kuma Hon. (Dr.) Bello Muhammad Matawalle bisa tallafi da goyon bayan da s**a ba shi domin cimma wannan nasara.

A ƙarshe, ya roki addu’o’in ‘yan Najeriya, tare da fatan Allah ya sanya wannan tafiya ta haifar da alheri ga shi, al’ummar Zamfara da Najeriya baki ɗaya.

TA’AZIYYA TA MUSAMMAN: Sadique Abubakar da Sadiya Umar Farouq Sun Nuna Alhini Kan Rasuwar BuhariTsohon hafsan hafsoshin ...
21/07/2025

TA’AZIYYA TA MUSAMMAN: Sadique Abubakar da Sadiya Umar Farouq Sun Nuna Alhini Kan Rasuwar Buhari

Tsohon hafsan hafsoshin sojin sama, Air Marshal Sadique Baba Abubakar, tare da mai dakinsa, Sadiya Umar Farouq—tsohuwar Ministar Jinƙai da Walwala—sun shiga sahun masu alhini kan rasuwar tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Dukkaninsu sun bayyana jimami da tausayin rashin, tare da addu’ar Allah Ya jikan marigayin, Ya sa Aljanna ce makomarsa.

CIKIN HOTUNA 📸: Yau Litinin, bayan sa’o’i biyu da zanga-zangar farko, Dan Bello da Omoyele Sowore sun koma t**i tare da ...
21/07/2025

CIKIN HOTUNA 📸: Yau Litinin, bayan sa’o’i biyu da zanga-zangar farko, Dan Bello da Omoyele Sowore sun koma t**i tare da masu goyon bayansu a Abuja, domin ci gaba da zanga-zangar neman karin albashi da fansho ga ‘yan sanda. Sun ce ba za su ja da baya ba har sai gwamnati ta amsa bukatunsu.

LABARI CIKIN HOTUNA: Sojojin Najeriya Sun K**a Mutum 62 da Ake Zargi da Satar Mai a Yankin Neja DeltaDakarun rundunar so...
21/07/2025

LABARI CIKIN HOTUNA: Sojojin Najeriya Sun K**a Mutum 62 da Ake Zargi da Satar Mai a Yankin Neja Delta

Dakarun rundunar sojojin Najeriya ta Division ta 6 sun k**a akalla mutane 62 da ake zargi da aikata satar mai, lalata bututun mai da wasu laifuka a yankin Neja Delta.

An gudanar da wannan samame ne tsakanin ranakun 14 zuwa 20 ga watan Yuli, 2025 a jihohin Rivers, Bayelsa, Delta da Akwa Ibom.

Sojojin sun kuma kwace sama da lita 350,000 na man fetur da aka sace yayin wannan aiki.

YANZU-YANZU: An Fara Zanga-Zangar Neman Karin Albashi da Kula da Fanshon 'Yan SandaA yau ne aka fara gudanar da zanga-za...
21/07/2025

YANZU-YANZU: An Fara Zanga-Zangar Neman Karin Albashi da Kula da Fanshon 'Yan Sanda

A yau ne aka fara gudanar da zanga-zanga a babban birnin tarayya Abuja domin nuna rashin jin daɗi kan matsanancin halin da jami’an ‘yan sanda ke ciki, musamman masu ritaya.

Jagoran zanga-zangar, Omoyele Sowore, ya ce lokaci ya yi da gwamnati za ta mutunta ‘yan sanda da s**a sadaukar da rayukansu wajen kare lafiyar jama’a da dukiyarsu.

Masu zanga-zangar na rike da kwalaye masu taken:
- A biyan ‘yan sanda albashi mai kyau yanzu!
- Rayuwa mai kyau ga masu ritaya!
- ’Yan sanda ma mutane ne!

Zanga-zangar ta kasance cikin lumana, inda jami’an tsaro s**a tabbatar da tsari da zaman lafiya. Ana sa ran gwamnati za ta duba korafe-korafen domin inganta rayuwar waɗanda ke bakin aiki da masu ritaya.

YANZU-YANZU: Shafin Facebook na Abba Sani Pantami, Ya Zama Sahihi (Verified)Shahararren mai harkar sadarwa da siyar da D...
21/07/2025

YANZU-YANZU: Shafin Facebook na Abba Sani Pantami, Ya Zama Sahihi (Verified)

Shahararren mai harkar sadarwa da siyar da Data, Abba Sani Pantami, ya sanar da samun tabbacin sahihanci daga Facebook (blue tick), yana mai jaddada cewa wannan shi ne kadai sahihin shafinsa.

A sanarwar da ya fitar, Pantami ya ce:
"Ina so in fayyace cewa bana siyar da Printing Card, Printer ko wani kayan kasuwa mak**ancin haka. Abin da nake siyarwa kawai shi ne Data, ta cikin Application dina mai suna ABBA PANTAMI DATA."

Ya gargadi mabiyansa da su yi hattara da masu amfani da sunansa a shafukan bogi don yaudarar mutane. Ya bukaci kowa ya tabbatar da cewa yana bin sahihin shafi mai alamar blue tick.

DA ƊUMI-ƊUMI: Rundunar ‘Yan Sanda Ta Gano Babura Masu Yiwuwar Sata a KanoRundunar ‘yan sanda ta jihar Kano ta k**a wasu ...
21/07/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Rundunar ‘Yan Sanda Ta Gano Babura Masu Yiwuwar Sata a Kano

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano ta k**a wasu babura da ake zargin an sace su daga hannun ɓarayin babura.

Kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya bayyana cewa an k**a baburan ne yayin wani samame, kuma yanzu haka suna hannun ‘yan sanda.

An bukaci duk wanda aka sace masa babur da ya je duba ko zai iya gane nasa, domin yiwuwar wasu daga cikin su na daga cikin abin da aka sace.

Ana ci gaba da bincike yayin da rundunar ke ƙara himma wajen rage ayyukan ɓarayi a fadin jihar.

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Bridge Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa Bridge Media:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share