Arewa Bridge Media

Arewa Bridge Media Arewa Bridge Media (ABM): Your leading source for daily news & current affairs in Hausa. Owned by ABM Virtual Productions Ltd.
(1)

Connecting Communities, Amplifying Voices. 🌍

📞 For ads/inquiries (WhatsApp/Call): 08149675978
🌐 https://arewabridge.com.ng

MAKIRCIN DA AKA ƘULLA A DARREN JIYA KAN JIHAR GOMBE DA TASIRIN PROFESSOR ISA ALI PANTAMI An gudanar da wani taro a Gidan...
03/06/2026

MAKIRCIN DA AKA ƘULLA A DARREN JIYA KAN JIHAR GOMBE DA TASIRIN PROFESSOR ISA ALI PANTAMI

An gudanar da wani taro a Gidan Gwamnati a daren jiya, Talata 2 ga Yuni, 2026. A cewar bayanan da s**a fito daga taron, babban abin da ya mamaye tattaunawar shi ne Malam Isa Ali Pantami, inda aka mayar da hankali kan muhimman batutuwa uku:

1. Sun sani sarai cewa Malam Isa Ali Pantami bai shiga abin da suke ƙira zaɓen fidda gwani ba. Duk da haka, an yi shawarar cewa a ci gaba da tayar da hayaniya a kan lamarin tare da amfani da wasu da ake ƙira masu ruwa da tsaki daga cikin gida domin jawo ruɗani da tsawaita cece-kuce.

2. Karɓuwar da Professor Isa Ali Pantami da sabuwar jam’iyyarsa ta PDP suke samu a faɗin jihar Gombe na ƙara damun su matuƙa. Shigowarsa ya sake farfaɗo da jam’iyyar gaba ɗaya. A kusan kowane taro da majalisa, Pantami da jam’iyyarsa su ne abin tattaunawa. A cewarsu, bai kamata a bar wannan yanayi ya ci gaba ba.

Abin takaici a gare su, sun manta cewa ikon Allah ne kaɗai ke tabbatar da abin da zai kasance.

3. A yayin da Malam Isa Ali Pantami ke ci gaba da gabatar wa al’ummar Gombe manufofinsa da kuma “Tsarin Sauya Fasalin Jihar Gombe” a fannoni kamar noma, samar da ayyukan yi, tsaro, ilimi, mata, matasa, masana’antu da sauran su, har yanzu ‘yan takarar su ba su gabatar wa jama’a wata cikakkiyar manufa ko tsari ba.

An ce an yi wa dukkan ‘yan takarar da s**a halarci taron tambayoyi kan wannan batu. A yau, Pantami ya zama abin koyi a gare su ta wannan fuska.

Mu ci gaba da lura da abubuwan da suke faruwa yayin da al’amura ke ƙara bayyana.

Allah Ya rushe duk wani mugun nufi da mugun shiri da ake yi wa al’ummar jihar Gombe da kuma duk wani abu da zai hana samuwar shugabanci Nagari a jihar.

Rubutawa:
Barrista Yahaya Ibrahim
03/Yuni/2026

YANZU YANZU: Kodinetan jam'iyyar ADC na jiha kuma tsohon mataimakin sakataren jam'iyyar ya yi murabus, ya bi sahun Farfe...
02/06/2026

YANZU YANZU: Kodinetan jam'iyyar ADC na jiha kuma tsohon mataimakin sakataren jam'iyyar ya yi murabus, ya bi sahun Farfesa Isa Ali

Hon. Salihu Abdulkadir, wanda ya kasance dan takarar majalisar dokokin jihar Gombe na jam'iyyar African Democratic Congress (ADC) a zaben 2023 mai wakiltar Dukku ta Arewa, ya yi murabus a hukumance daga jam'iyyar. Hon. Abdulkadir, wanda ya taba zama Kodinetan jam'iyyar ADC na jiha kuma tsohon mataimakin sakataren jam'iyyar na jiha, ya sanar da matakin da ya dauka na barin jam'iyyar domin shiga tafiyar siyasar da Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami ke jagoranta.

A cikin wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai, Hon. Abdulkadir ya bayyana godiyarsa ga shugabancin jam'iyyar ADC da kuma mambobinta bisa damar da s**a ba shi a lokacin da yake rike da mukamansa. Ya bayyana cewa, matakin da ya dauka na sauya sheka ya samo asali ne daga burinsa na shiga wani dandali da zai dace da hangen nesansa na ganin an samu shugabanci na gari da kuma jagoranci mai amfani ga mutanen Dukku ta Arewa da jihar Gombe baki daya.

"Ina mai matukar godiya ga jam'iyyar ADC bisa amana da nauyin da aka dora mini a matsayina na kodinetan jiha da kuma mataimakin sakatare.

Matakina na bin Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami a cikin tafiyarsa ta siyasa, shi ne domin in ba da gudunmawa yadda ya kamata wajen ci gaba da kuma tallafawa al'ummarmu," inji Hon. Abdulkadir.

Masu sharhi kan harkokin siyasa sun bayyana cewa, murabus dinsa ya nuna gagarumin sauyi a fagen siyasar jihar Gombe, wanda hakan ke kara nuna tasirin tafiyar Dr. Pantami da kuma yadda take jan hankalin 'yan siyasar da ke neman sabbin hanyoyin yi wa jama'a hidima.

Tsohon kodinetan na ADC, wanda kuma ya kasance daya daga cikin ginshikan kafa jam'iyyar a jihar Gombe, barinsa jam'iyyar ya zama wani muhimmin sauyi a siyasar jihar, wanda ke kara nuna yadda tafiyar Pantami ke samun karbuwa da kuma yadda siyasa ke sauyawa yayin da ake kusantar zaben 2027.

Jam’iyyar APC A Jihar Gombe Ta Yi Dana-sanin Rashin Bai Wa Pantami Tikitin Takarar GwamnaWasu jiga-jigan jam’iyyar APC a...
02/06/2026

Jam’iyyar APC A Jihar Gombe Ta Yi Dana-sanin Rashin Bai Wa Pantami Tikitin Takarar Gwamna

Wasu jiga-jigan jam’iyyar APC a Jihar Gombe sun bayyana cewa jam’iyyar na ci gaba da fuskantar tasirin rashin bai wa Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami tikitin takarar gwamna gabanin zaɓen 2027, lamarin da s**a ce ya haifar da rabuwar kai da kuma rage ƙarfin jam’iyyar a wasu sassan jihar.

A cewarsu, Pantami na daga cikin fitattun jagororin siyasa da s**a yi tasiri sosai a jihar, tare da samun karɓuwa a tsakanin matasa, malamai da sauran al’umma. Sun yi iƙirarin cewa da an ba shi damar fafatawa a sahihin zaɓen fidda gwani, APC za ta samu ƙarin haɗin kai da kuma goyon bayan mambobinta a faɗin jihar.

Majiyoyin jam’iyyar sun bayyana cewa ficewar Pantami daga APC zuwa PDP ta sauya yanayin siyasar Gombe, inda dubban magoya bayansa s**a nuna goyon baya gare shi. Sun ƙara da cewa wannan lamari ya bai wa jam’iyyun adawa damar ƙara faɗaɗa tasirinsu a wasu yankunan jihar.

Wasu daga cikin mambobin APC sun nuna cewa da an gudanar da zaɓen fidda gwani cikin gaskiya da adalci tare da bai wa kowa damar gwada farin jininsa, da jam’iyyar ba za ta fuskanci irin ƙalubalen da take ciki a yanzu ba. Sun yi kira ga shugabannin jam’iyyar da su ɗauki darasi daga abin da ya faru domin tabbatar da adalci, gaskiya da haɗin kai a duk wani tsari na zaɓen cikin gida a nan gaba.

🚨 DA ƊUMI-ƊUMI: Daruruwan matasa maza da mata magoya bayan Khamisu Ahmad Mailantarki daga unguwar Shamaki, ƙarƙashin jag...
01/06/2026

🚨 DA ƊUMI-ƊUMI: Daruruwan matasa maza da mata magoya bayan Khamisu Ahmad Mailantarki daga unguwar Shamaki, ƙarƙashin jagorancin Musa Bajade, sun bayyana goyon bayansu ga ɗan takarar gwamnan Jihar Gombe na jam’iyyar PDP, Professor Isa Ali Pantami.

Matasan sun bayyana hakan ne a wani taro da s**a gudanar a yau Litinin, inda s**a ce sun yanke shawarar mara wa Pantami baya saboda abin da s**a bayyana a matsayin cancantarsa da kuma irin gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban al’umma.

Sun kuma yi alƙawarin ci gaba da wayar da kan jama’a da kuma aiki domin tabbatar da nasarar jam’iyyar PDP a zaɓe mai zuwa a Jihar Gombe.

FARFESA ISA ALI PANTAMI YA KAMMALA RABON BARKA DA SALLAH GA 'YAN SIYASA A UNGUWAR PANTAMI A yau 31/May/2026 mun kammala ...
31/05/2026

FARFESA ISA ALI PANTAMI YA KAMMALA RABON BARKA DA SALLAH GA 'YAN SIYASA A UNGUWAR PANTAMI

A yau 31/May/2026 mun kammala rabon barka da sallah na unguwar Pantami ga dukkan 'yan siyasa, talakawa da sauran 'yan uwa.

Daga cikin tsarin Malam Professor Isa Ali Pantami (Wazirin Pantami) baya banbance mutane a Pantami dalilin banbancin jam'iyaa.

Shekaru da dama a Unguwar Pantami idan ya tashi taimakon Azumi ko kuma wani lokaci na tsanani ko bukukuwa yana bayarwa ga dukkan Jam'iyun siyasa kamar PDP da APC, NNPP, da makamantansu.

Malam yana cewa bai dace muki taimakon mutane don banbancin jam'iya ba. Wadanda s**a samu taimakon sun yi godiya daga dukkan bangarorin jam'iyyu da sauran mabukata da aka bawa kudi ko laguna ko kuma naman shanu da aka yanka. Wadanda bai isa kan su ba, su yi hakuri. Gaba tafi baya yawa in Allah Ya yarda.

Wannan darasi ne da ya dace mu koya. Mu taimaki duk wanda Allah ya bamu daman taimakawa.

Muna godiya ga dukkan wadanda s**a yi wannnan hidima na rabon, Alhaji Jamilu Jamoo, Comrade Abba Sani Pantami da Malam Zubairu da Muhammad Yusuf Ali (Danbaba) da makamantansu.

Daga
Muhammad Umar Danmasani
(Daga Matasan Pantamiyya Movement).

ALLAHU AKBAR: Maigirma dan takarar Gwamnan jihar Gombe a jam’iyyar PDP Professor Isa Ali Pantami tare da jagora Distingu...
29/05/2026

ALLAHU AKBAR: Maigirma dan takarar Gwamnan jihar Gombe a jam’iyyar PDP Professor Isa Ali Pantami tare da jagora Distinguished Senator Ibrahim Hassan Dankwambo, sun gabatar da Sallar Jumma'a, a Masallacin ADP dake GRA Gombe.

A ranar 19 ga Mayu, 2026, Professor Isa Ali Pantami ya mika takardar ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance. An sanya ...
28/05/2026

A ranar 19 ga Mayu, 2026, Professor Isa Ali Pantami ya mika takardar ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance. An sanya hannu a takardar tare da tabbatar da karɓarta daga Shugaban APC na mazabar Pantami.

An bayyana cewa matakin ya biyo bayan dogon nazari da tuntuba da masu ruwa da tsaki daga sassa daban-daban na Jihar Gombe da ma wajenta. A cewar sanarwar, an ɗauki wannan mataki ne bayan tantance inda zai fi iya yi wa al’ummar Jihar Gombe hidima yadda ya kamata.

Prof. Pantami ya sake jaddada cewa ƙudurinsa na ci gaban Jihar Gombe da walwalar al’ummarta yana nan daram. An wallafa takardar ne domin tunatar da jama’a cewa siyasa ya kamata ta kasance bisa hidima, gaskiya da kuma hangen nesa na bai ɗaya domin makomar al’umma.

✍️ Rubuta:
Comrade Abba Sani Pantami

A jiya Laraba Maigirma dan takarar Gwamnan jihar Gombe a jam'iyyar PDP Professor Isa Ali Pantami CON (Wazirin Pantami) y...
28/05/2026

A jiya Laraba Maigirma dan takarar Gwamnan jihar Gombe a jam'iyyar PDP Professor Isa Ali Pantami CON (Wazirin Pantami) ya ziyarci masallacin da yake ginawa a kofar Sarkin Pantami.

YANZU-YANZU: Jam’iyyar PDP Ta Tsayar Da Sheikh Isa Ali Pantami A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Jihar Gombe
26/05/2026

YANZU-YANZU: Jam’iyyar PDP Ta Tsayar Da Sheikh Isa Ali Pantami A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Jihar Gombe

Address

No. 10, Pantami Quarters Near, , Water Board
Gombe
760253

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Bridge Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa Bridge Media:

Share