14/01/2026
Daga Abū Huraira (R.A) ya ce:
Manzon Allah ﷺ ya ce:
“Haƙƙin Musulmi a kan Musulmi guda shida ne.” Sai aka ce: Menene su, ya Manzon Allah?
Ya ce: “Idan ka haɗu da shi, ka yi masa sallama, idan ya gayyace ka, ka amsa masa, idan ya nemi kayi masa Nasiha; kayi masa, idan ya yi atishawa ya gode wa Allah, ka ce masa: Allah ya ji ƙanka; ( ُيَرْحَمُكَ اللَّه) idan ya yi rashin lafiya, ka ziyarce shi, idan ya rasu, ka bi jana’izarsa.”
📚 Muslim (2162)