Ramfak RTV

Ramfak RTV Ramfak Radio is a Nigerian online radio station with global reach. It streams quality news, education, and entertainment programs.

The station focuses on community stories and real information. Enjoy clear online radio streaming anytime, anywhere.

Tsohon Ministan Matasa da Wasanni a Najeriya, kuma ɗan gwagwarmaya, Barrister Solomon Dalung, ya zargi jam’iyyar APC da ...
26/01/2026

Tsohon Ministan Matasa da Wasanni a Najeriya, kuma ɗan gwagwarmaya, Barrister Solomon Dalung, ya zargi jam’iyyar APC da amfani da hukumomin tsaro, musamman EFCC, domin matsa wa Gwamnatin Jihar Bauchi lamba da nufin tilasta mata sauya sheƙa zuwa jam’iyyar.

Dalung ya bayyana hakan ne a Bauchi yayin da yake jawabi a wani taron bayar da lambar yabo, inda ya ce k**a ma’aikatan gwamnatin jihar Bauchi da EFCC ke yi a halin yanzu na da alaƙa kai tsaye da siyasa, ba yaki da cin hanci ba.

A cewarsa,

“Ni lauya ne, aikina kenan. Kowace rana ina roƙon Allah ya bani aiki, kuma ga shi Allah ya bani aiki. EFCC sun je sun k**a ma’aikatan Bauchi suna tuhumar su da almundahana da ta’addanci, toh mu dai muna bada gudunmawa ne domin ganin an yi yaki da cin hanci da gaskiya.”

Dalung ya zargi APC da nuna wariya wajen yaƙi da cin hanci, inda ya ce ana kallon fuskar mutum kafin a k**a shi.

Ya ce,

“Shugabannin APC sun ce ko mutum ya saci banki ne idan ya gudu ya shiga APC, ya shiga Tudun Natsira. Shi ya sa manyan barayi da ake yi wa shari’a suna komawa APC, aka daina tuhumar su.”

Tsohon ministan ya yi ikirarin cewa ana matsa wa Gwamnatin Bauchi lamba ne saboda ana son tilasta mata shiga APC.

“Yanzu ana matsa wa Gwamnatin Bauchi ne, ana son Gwamnan Bauchi ya koma APC. Rashin yarda da hakan ne yasa ake kwashe ma’aikatan jihar domin a karyashi.”

Dalung ya ce gwagwarmaya da suke yi ita ce kare dimokuradiyya da zaman lafiyar Bauchi, ba kare mutum ɗaya kawai ba.

“Ba wanda ya isa ya tilasta wa Gwamnan Bauchi shiga APC. Idan Allah ne ya so zai je, amma ba da karfi ba. Idan ya ce ba zai je ba, ba hujja ba ce da za a rika k**a ma’aikata.”

Ya kara da cewa manufar k**a manyan jami’an kuɗi ita ce tayar da hankalin jama’a ta hanyar jawo tsaikon biyan albashi, wanda hakan ka iya haddasa rikici.

“Ana son a k**a Kwamishinan Kuɗi, a k**a Accountant General, a hana biyan albashi domin a tayar da rigima. Bauchi tana zaman lafiya, amma ana neman a kawo rikicin kabilanci, addini da siyasa.”

A ƙarshe, Dalung ya ce gwagwarmayarsu na nufin dakile duk wani yunƙuri da zai jefa jihar cikin rikici.

“Mun tashi tsaye ne domin mu kare Gwamnatin Bauchi da Jihar Bauchi gaba ɗaya, mu dakile wannan iskancin.”

Wani mutum ya hau bene mai hawa 101 ba tare da igiya ko kayan kariya ba!Daga Ayau News Shahararren mai hawa dutse ɗan Am...
26/01/2026

Wani mutum ya hau bene mai hawa 101 ba tare da igiya ko kayan kariya ba!

Daga Ayau News

Shahararren mai hawa dutse ɗan Amurka, Alex Honnold, ya zama mutum na farko da ya hau ginin Taipei 101 a Taiwan ba tare da igiya ko kayan kariya ba.

Ya kammala hawa benen mai hawa 101 cikin kusan mintuna 90, abin da ya jawo hankalin dubban masu kallo a duniya.

Kowane Wata, Tinubu na Cire Naira Biliyan 100 Daga Asusun Tarayya, Laifi Ne da Ya Cancanci Tsige Shi — El-RufaiTsohon Gw...
26/01/2026

Kowane Wata, Tinubu na Cire Naira Biliyan 100 Daga Asusun Tarayya, Laifi Ne da Ya Cancanci Tsige Shi — El-Rufai

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya zargi Shugaba Asiwaju Bola Ahmed Tinubu da cire Naira biliyan 100 kowane wata daga Asusun Tarayya na Najeriya ba tare da amincewar Majalisar Dokoki ba ko wata hujjar kundin tsarin mulki, yana bayyana hakan a matsayin laifi da ya cancanci tsige shugaban ƙasa.

A wata hira da ta yadu sosai a tashar Arise TV, El-Rufai ya ce ana yin wannan cire-cire ba bisa ƙa’ida ba tsawon fiye da watanni 15, wanda ya kai jimillar Naira tiriliyan 1.5. A cewarsa, wannan tsari na kwashe kuɗaɗe yana nuna karya Kundin Tsarin Mulki a fili da kuma ƙa’idojin kula da kuɗaɗen gwamnati.

El-Rufai ya ce:

> “Kowane wata, Shugaba Bola Tinubu na cire Naira biliyan 100 daga Asusun Tarayya. Wannan ya saɓa wa kundin tsarin mulki kuma laifi ne da ya cancanci tsige shi.”

Tsohon gwamnan ya kuma bukaci Majalisar Tarayya da sauran hukumomin sa ido da su binciki lamarin, yana gargaɗin cewa yin shiru kan irin wannan karya doka na iya kafa mummunan misali ga gwamnatoci masu zuwa. Kalaman nasa sun haifar da muhawara mai zafi a kafafen sada zumunta da kafafen watsa labarai, inda ake tambaya game da yadda ake tafiyar da kuɗaɗen jama’a da kuma iyakar ikon shugaban ƙasa.

Masana harkokin siyasa sun ce idan aka tabbatar da zargin El-Rufai, hakan na iya jawo manyan sak**akon shari’a da siyasa, ciki har da yiwuwar kiran tsige shugaban ƙasa, lamarin da ke nuna muhimmancin gaskiya da bayyana gaskiya a harkokin kuɗaɗen ƙasa na Najeriya.

Sauya Sheƙar Gwamnan Kano zuwa APC Babban Kuskure Ne — ArdoTsohon mataimaki na musamman ga tsohon Mataimakin Shugaban Ƙa...
26/01/2026

Sauya Sheƙar Gwamnan Kano zuwa APC Babban Kuskure Ne — Ardo

Tsohon mataimaki na musamman ga tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar, Jafar Sani Ardo, ya bayyana cewa sauya sheƙar da Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya yi zuwa jam’iyyar APC babban kuskure ne na siyasa.

Ardo, wanda ya taɓa riƙe mukamin Special Assistant kan Harkokin Kananan Hukumomi da Jihohi, ya ce wannan mataki na gwamnan ya nuna rashin fahimtar tarihin siyasar Kano da yadda ta bunƙasa tsawon lokaci.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, Ardo ya jaddada cewa siyasar Kano a tarihi ta fi karkata zuwa jam’iyyun adawa, kuma da wuya ta rungumi jam’iyyar da ke kan mulki a matakin tarayya.

Ya ce ya k**ata gwamnan ya sani cewa wannan yanayin siyasa na Kano abu ne da aka gada tun shekaru da dama, don haka sauya sheƙar zuwa APC ba zai masa amfani ba.






Tsaron sirrin Isra'ila yayi Rauni: Wani Abin mamaki, An sami wani soja me matsayin kaftin a Rundunar sojin Isra'ila.Duk ...
26/01/2026

Tsaron sirrin Isra'ila yayi Rauni: Wani Abin mamaki, An sami wani soja me matsayin kaftin a Rundunar sojin Isra'ila.

Duk da kwarewar Isra'ila a fagen tsaro da tattara bayanan sirri amma an sami babban soja me matsayin kafin na bogi wanda Ya shafe tsawon shekaru yana aiki a matsayin kaftin ba tare da an gano shi ba. Ana zargin yana daya daga cikin Yan leken asirin Hamas.

Kamar yadda Tashar Sky News Al-Arabiyya ta fitar da rahoto na musamman akansa.

𝗚𝗼𝗺𝗯𝗲 𝗜𝗚𝗥 𝘀𝘂𝗿𝗴𝗲𝘀 500% 𝘁𝗼 𝗡40𝗯𝗻 Gombe State's IGR skyrockets by 500% to a historic N40.8bn between 2019 and 2025, driven ...
26/01/2026

𝗚𝗼𝗺𝗯𝗲 𝗜𝗚𝗥 𝘀𝘂𝗿𝗴𝗲𝘀 500% 𝘁𝗼 𝗡40𝗯𝗻
Gombe State's IGR skyrockets by 500% to a historic N40.8bn between 2019 and 2025, driven by Governor Muhammadu Yahaya's strategic reforms....

𝗥𝗲𝗮𝗱 𝐟𝐮𝐥𝐥 𝐬𝐭𝐨𝐫𝐲 𝐢𝐧 𝐭𝐡𝐞 𝐜𝐨𝐦𝐦𝐞𝐧𝐭𝐬

Ana alaƙanta rikicin garin Pindiga da ke Ƙaramar Hukumar Akko a jihar Gombe da man fetur ne, sak**akon gano danyen mai a...
26/01/2026

Ana alaƙanta rikicin garin Pindiga da ke Ƙaramar Hukumar Akko a jihar Gombe da man fetur ne, sak**akon gano danyen mai a yankin (Kolmani River II) da ke kan iyakar jihohin Gombe da Bauchi a yankin Arewa maso Gabashin Najeriya.

Bincike ya tabbatar da cewa, gano man ya haifar da dambarwa a baya tsakanin al'ummomin da ke kan iyakar jihohin biyu, inda kowane ɓangare ke da'awar cewa rijiyoyin man suna cikin ƙasarsa ne domin cin gajiyar haraji da kuma kason kuɗaden da ake warewa yankunan da ake hako mai daga gwamnatin tarayya.

Bayan fara aikin bincike da hako mai da aka fara tun lokacin gwamnatin marigayi Shugaba Muhammadu Buhari, rahotannin ayyukan ƴan bindiga, garkuwa da mutane, da kashe-kashe a yankunan kusa da Kolmani s**a fara ɓulla.

Al'ummar yankin na ganin cewa darajar man ta janyo hankalin masu laifi zuwa yankin nasu, yayin da Shugabannin yankin, ciki har da, Mai Martaba Sarkin Pindiga, s**a bayyana damuwa kan yadda ake hako mai a yankin su, amma ba a samar musu da ayyukan raya ƙasa k**ar hanyoyi, asibitoci, da makarantu ba.

Haka kuma, an fara fuskantar barazanar gurɓatar ruwa da filayen noma, wanda hakan ke barazana ga rayuwar manoma da makiyaya a yankin lamarin da ke zama silar rikici.

Masana sun ce, masu hako ma'adinai ba bisa ƙa'ida ba, ƙungiyoyin daban-daban, har ma da ƙungiyoyin ta'addanci s**an mamaye irin waɗannan yankunan don samun kuɗin gudanar da ayyukansu, k**ar yadda ake gani a jihar Zamfara.

Rashin samar da ayyukan ci gaba a yankunan da ake hako arziƙin, gurbatar muhalli, da kuma rashin adalci wajen raba kuɗaɗen shiga na janyo fushin matasa, abin da ya daɗe yana faruwa a yankin Niger Delta inda tsageru s**a kwashe shekaru suna fafatawa da gwamnati.

Kasancewar ɗanyen mai ko ma'adinai na kawo maƙudan kuɗaɗe, hakan na sa a samu rashawa da raunin hukumomin tsaro, wanda ke ba masu laifi damar kafa sansani a yankunan cikin sauƙi.

Ƙungiyoyin ta'addanci na duniya k**ar su IS da Al-Qaeda s**an yi amfani da albarkatun ƙasa k**ar man fetur a Iraƙi da Siriya, ko ma'ad

26/01/2026
Gombe records nearly 500 percent revenue growth in six years as reforms boost tax collection and fiscal performance. htt...
26/01/2026

Gombe records nearly 500 percent revenue growth in six years as reforms boost tax collection and fiscal performance. http://ow.ly/mbrs106tCh2

“Tinubu Deducts N100bn Monthly From Federation Account Without Approval” — El-Rufai Alleges, Says Action Deserves Impeac...
26/01/2026

“Tinubu Deducts N100bn Monthly From Federation Account Without Approval” — El-Rufai Alleges, Says Action Deserves Impeachment.

El-Rufai said the unauthorised deductions have been going on for over 15 months, amounting to a total of N1.5 trillion.

Gombe Government Chief of Staff Commends Public Support for APC, Reaffirms Governor Inuwa Yahaya’s Exemplary LeadershipT...
26/01/2026

Gombe Government Chief of Staff Commends Public Support for APC, Reaffirms Governor Inuwa Yahaya’s Exemplary Leadership

The Chief of Staff to the Gombe State Government, Alhaji Abubakar Inuwa Kari (Matawallen Nafada), has commended the people of Gombe State for their overwhelming loyalty and support for the leadership of His Excellency, Governor Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya, CON, as demonstrated by their massive turnout for the renewal of APC membership registration across the state.

Alhaji Abubakar Inuwa Kari stated that the impressive public response did not come by chance, but rather as a result of the Governor’s exemplary leadership style, anchored on integrity, transparency, accountability, and people-oriented governance since assuming office. According to him, the All Progressives Congress (APC) has gained wide acceptance in Gombe State because of its firm commitment to policies and programmes that promote development and improve the welfare of the people.

He emphasized that the renewal of party membership cards is not merely a partisan exercise, but a symbolic expression of public confidence in good governance, strengthening democracy and enabling citizens to actively participate in political decision-making. “When citizens come out in large numbers to renew their membership, they are clearly reaffirming their trust in the direction the government is taking the state,” Matawallen Nafada noted.

The Chief of Staff further praised Governor Inuwa Yahaya’s governance approach, describing it as one founded on justice, sincerity, vision, and inclusive leadership, which has significantly strengthened the APC at the grassroots level and fostered unity among the people, irrespective of political differences. He added that the Governor’s leadership style has become a model worthy of emulation by leaders at all levels.

In the same vein, Alhaji Abubakar Inuwa Kari called on politicians, traditional and community leaders, youths and women to seize the opportunity to join or strengthen their participation in the APC, stressing that the party requires collective commitment and unity to sustain its successes and consolidate future victories.

In conclusion, he assured the people of Gombe State that the administration of His Excellency, Governor Muhammadu Inuwa Yahaya, CON, remains fully committed to implementing people-centered policies and programmes that will continue to improve the living conditions of the জনগ, while ensuring that the APC remains firmly rooted in the principles of truth, trust, integrity, and sustainable development.

Address

Gadan Malale, Opposite Twin Filling Station, Sabon Layi
Gombe
760242

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ramfak RTV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share