FVM Hausa

FVM Hausa Muna kawo muku sabbin labarai sahihai daga Najeriya da ma duniya baki ɗaya. Ku kasance cikin sani, ku kasance masu ƙarfi da ilimi. Stay informed, stay empowered.
(5)

Bringing you the latest, most reliable News from Nigeria and around the world.

05/05/2026

Kungiyoyin Mata sun yi korafi kan yadda aka hana Mata Damar yin takara a zabukan 2027

Kungiyoyin mata a Najeriya sun bayyana damuwa matuƙa kan yadda ake ganin an rage wa mata damar shiga takara a zabukan fidda gwani na jam’iyyu daban-daban a ƙasar.

Wannan damuwa na zuwa ne bayan rahotanni sun nuna cewa a jihohi irin su Gombe, Borno da Yobe, jam’iyyu da dama ba su tsayar da mata a matsayin ‘yan takara ba, lamarin da ke kara bayyana gibin wakilcin mata a harkokin siyasa.

Masu ruwa da tsaki na cewa wannan yanayi na iya hana cimma daidaito a shugabanci, tare da rage damar mata wajen taka rawa a matakan yanke shawara.

Da dumi-dumi: “Ya k**ata Iran ta mika wuya”—Trump.Shugaban Amurka Donald Trump ya ce ya k**ata Iran ta "daga tutar mika ...
05/05/2026

Da dumi-dumi: “Ya k**ata Iran ta mika wuya”—Trump.

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce ya k**ata Iran ta "daga tutar mika wuya" a yakin da suke yi.
Yayin da a hannu guda, Trump din ya zargi shugabannin Iran da sanya wasa a batun tattaunawa.
Ya kuma ce hauhawar farashin mai, bai kai matsayin Amurka ta janye daga hana Iran mallakar makamin nukiliya ba.

05/05/2026

Dalilin da Ya sa Sanata Danjuma Goje Ya ki Amincewa da Zaben Fidda na Jam'iyyar APC a jihar Gombe

Sabbin bayanai sun fito kan dalilan da s**a sa tsohon gwamnan Jihar Gombe, Danjuma Goje, ya ƙi amincewa da zaɓen fidda gwani na jam’iyyar APC a jihar.

A cewar Barista Mu'azu Sa'idu Kumo, akwai zarge-zargen rashin adalci da kuma saba ƙa’idojin jam’iyya a yadda aka gudanar da zaɓen, lamarin da ya sa ɓangaren Sanata Goje ya yi watsi da sak**akon.

Wannan batu na ƙara janyo cece-kuce a cikin jam’iyyar APC a Gombe, yayin da masu lura da al’amuran siyasa ke cewa rikicin na iya shafar haɗin kan jam’iyyar da kuma shirinta na zaɓe mai zuwa.

05/05/2026

Yadda Zaben fidda gwani na jam’iyyar APC a Jihar Gombe ya bar baya da kura

Zaɓen fidda gwamna na jam’iyyar APC a Jihar Gombe ya bar baya da ƙura, bayan da wasu daga cikin manyan ‘yan takara s**a yi fatali da sak**akon zaɓen, suna masu zargin cewa ba a yi musu adalci ba.

Daga cikin waɗanda s**a nuna rashin amincewa akwai Isa Ali Pantami, Sa'idu Ahmed Alkali da kuma Danjuma Goje, waɗanda s**a bayyana cewa akwai kura-kurai a yadda aka gudanar da zaɓen.

Lamarin na haifar da cece-kuce a cikin jam’iyyar, inda wasu ke ganin rikicin na iya shafar haɗin kai da kuma shirye-shiryen jam’iyyar gabanin zaɓe mai zuwa.

Masu lura da al’amuran siyasa na cewa, yadda za a warware wannan rikici zai taka muhimmiyar rawa wajen tantance makomar jam’iyyar APC a Jihar Gombe.

05/05/2026

Ga takaitattun labarai na FVM Hausa daga Sahura Usman

Muhimman labarai da s**a shafi tsaro, tattalin arziki da siyasa na ci gaba da daukar hankalin al’umma a Najeriya da ma sassa daban-daban na duniya. Haka kuma rikice-rikicen da ke faruwa a yankin Gabas ta Tsakiya da sauye-sauyen siyasar duniya na ci gaba da yin tasiri ga al’amuran kasa da kasa.

A cikin wannan shiri na takaitattun labarai daga FVM Hausa, za mu kawo muku manyan labaran da s**a fi daukar hankali kan batutuwan tsaro, tattalin arziki, siyasa da kuma abubuwan da ke faruwa a yankin Gabas ta Tsakiya da siyasar duniya, cikin takaitaccen lokaci.

Ku kasance tare da mu domin jin muhimman labaran da s**a faru a yau da kullum daga FVM Hausa

Ta faru ta Kare……Ganduje Ya Amince da Sanusi a Matsayin Sarkin Kano…Hakan na nufin Aminu Ado Bayero ya Tsohon Sarki kena...
05/05/2026

Ta faru ta Kare……Ganduje Ya Amince da Sanusi a Matsayin Sarkin Kano…Hakan na nufin Aminu Ado Bayero ya Tsohon Sarki kenan?

Tsohon gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana amincewarsa da Muhammadu Sanusi II a matsayin Sarkin Kano kuma Shugaban Majalisar Sarakunan jihar.
Ganduje ya yi wannan furuci ne a bainar jama’a yayin bikin rantsar da sabon mataimakin gwamnan jihar, Murtala Sule Garo, a fadar gwamnatin Kano, inda ya kira Sanusi da cikakken lakabinsa na sarauta—abin da ya jawo tafi da murna daga mahalarta taron.
Wannan ne karon farko da Abdullahi Umar Ganduje ya fito fili ya amince da Muhammadu Sanusi II tun bayan rikicin da ya raba su a baya.
A shekarar 2020 ne Ganduje ya tube Sanusi daga sarauta, inda daga bisani gwamnan Kano na yanzu, Abba Kabir Yusuf, ya mayar da shi kan karagar mulki bayan cire Aminu Ado Bayero wanda aka naɗa a madadinsa.
Lamarin dai ya dauki sabon salo a ‘yan kwanakin nan, musamman bayan sauye-sauyen siyasa da s**a faru a jihar, yayin da ake ganin wannan mataki na Ganduje na iya kawo sauyi a rikicin masarautar Kano.

Shekaru goma sha shidda da rasuwar tsohon shugaban Najeriya Ummaru Musa ‘Yar Aduwa.Shugaban ya rasu ne a ranar 5 ga wata...
05/05/2026

Shekaru goma sha shidda da rasuwar tsohon shugaban Najeriya Ummaru Musa ‘Yar Aduwa.

Shugaban ya rasu ne a ranar 5 ga watan Mayun 2010, bayan shafe tsawon lokaci yana fama da doguwar jinya, inda nan take ragmar tafiyar da Najeriya ta koma hannun mataimakinsa Goodluck Ebele Azikwe Jonathan.

Shin me kuke kewa game da gwamnatin ‘Yar Aduwa? Kuma wane fata kuke masa?

“Ka baro ADC ka zo mu hade a NDC”— Buba Galadima ga Atiku.Babban jigo a jam’iyyar (NDC), Buba Galadima, ya bukaci tsohon...
05/05/2026

“Ka baro ADC ka zo mu hade a NDC”— Buba Galadima ga Atiku.

Babban jigo a jam’iyyar (NDC), Buba Galadima, ya bukaci tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar da ya shiga jam’iyyar.

Galadima ya gargadi cewa idan Atiku bai mara wa NDC baya ba, ana iya dora masa alhakin gazawar hadin kan ’yan adawa gabanin zaben 2027.

Siyasar Najeriya: NDC na samun tagomashi, ’yan majalisa 16 sun fice daga ADC zuwa NDC.’Yan majalisar wakilai 16 na Najer...
05/05/2026

Siyasar Najeriya: NDC na samun tagomashi, ’yan majalisa 16 sun fice daga ADC zuwa NDC.

’Yan majalisar wakilai 16 na Najeriya sun sanar da ficewarsu daga jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) zuwa Nigerian Democratic Congress (NDC).

Sanarwar ta zo ne a hukumance a zauren majalisar wakilai, inda ’yan majalisar s**a bayyana cewa sun yanke shawarar ne bisa dalilai na siyasa da muradun mazabunsu. Wannan gagarumin sauyin na jam’iyya dai,na iya shafar daidaiton siyasa a majalisar.

’Yan sanda sun k**a masu garkuwa da mutane shida a Kaduna.Rundunar ’yan sandan Najeriya ta ce ta k**a mutane shida da ak...
05/05/2026

’Yan sanda sun k**a masu garkuwa da mutane shida a Kaduna.

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta ce ta k**a mutane shida da ake zargi da garkuwa da mutane a Kaduna, tare da kubutar da wasu da aka sace.

A cewar ’yan sanda, samamen ya kai ga tarwatsa wata ƙungiyar masu garkuwa da mutane da ake dangantawa da dajin Rijana Forest.
Rundunar ta ce za ta kuma ce za ta ci gaba da farautar sauran wadanda ke da hannu a laifukan sace-sace domin ƙara tabbatar da tsaro a jihar.

An gano wata jakar baya dauke da abin fashewa a Maiduguri.Yan sandan jihar Borno sun ce sun gano wani bam da aka ƙirar c...
05/05/2026

An gano wata jakar baya dauke da abin fashewa a Maiduguri.

Yan sandan jihar Borno sun ce sun gano wani bam da aka ƙirar cikin gida (IED) a cikin jakar baya a Maiduguri, babban birnin jihar.

A cewar rundunar, kwararru sun kwance bam ɗin cikin nasara ba tare da jikkata kowa ba. ’Yan sanda sun kuma yi kira ga jama’a da su ci gaba da ba da rahoton duk wani abu da ake zargin na barazana ga tsaro, domin kare rayuka da dukiyoyi a jihar.

Da dumi-dumi: Wani jami'in sojan Iran ya musanta cewa Iran ta kai hari kan tashar jiragen ruwa ta Hadaddiyar Daular Lara...
05/05/2026

Da dumi-dumi: Wani jami'in sojan Iran ya musanta cewa Iran ta kai hari kan tashar jiragen ruwa ta Hadaddiyar Daular Larabawa ko kuma Fujairah, yana mai zargin cewa sojojin Amurka ne s**a kai harin, a cewar kafofin watsa labarai na cikin gida.

Address

No 5 New GRA Along Ministry Of Education Gombe
Gombe
760101

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when FVM Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share