05/05/2026
Kungiyoyin Mata sun yi korafi kan yadda aka hana Mata Damar yin takara a zabukan 2027
Kungiyoyin mata a Najeriya sun bayyana damuwa matuƙa kan yadda ake ganin an rage wa mata damar shiga takara a zabukan fidda gwani na jam’iyyu daban-daban a ƙasar.
Wannan damuwa na zuwa ne bayan rahotanni sun nuna cewa a jihohi irin su Gombe, Borno da Yobe, jam’iyyu da dama ba su tsayar da mata a matsayin ‘yan takara ba, lamarin da ke kara bayyana gibin wakilcin mata a harkokin siyasa.
Masu ruwa da tsaki na cewa wannan yanayi na iya hana cimma daidaito a shugabanci, tare da rage damar mata wajen taka rawa a matakan yanke shawara.