Albayan Media

Albayan Media Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Albayan Media, News & Media Website, Gusau.

27/08/2026

Kanason Sanin gaskiyar Labarai
Jeka Albayan Media

Kungiyoyi 100 sun goyi bayan Gwamna Dauda Lawal domin ya zarce a zaben 2027.Sama da ƙungiyoyi 100 masu zaman kansu da na...
26/08/2026

Kungiyoyi 100 sun goyi bayan Gwamna Dauda Lawal domin ya zarce a zaben 2027.

Sama da ƙungiyoyi 100 masu zaman kansu da na al'umma a faɗin Jihar Zamfara sun bayyana cikakken goyon bayansu ga Gwamna Dauda Lawal domin sake fitowa takara da zarcewa a ƙaragar mulki a zaɓen shekara ta 2027.

Taron gangamin wanda aka gudanar a ƙarƙashin tsara da jagorancin Mai Bawa Gwamna Shawara kan Al'amuran Siyasa, Hon. Nura Sani Abdullahi (Sarkin Samarin Tsafe), ya sami halartar shugabannin ƙungiyoyi daban-daban, gami da samari, mata, da ƙungiyoyin kasuwanci daga ƙananan hukumomi 14 na jihar.

Da yake jawabi a wurin taron, Hon. Nura Sani Abdullahi ya jaddada cewa wannan matakai da ƙungiyoyin s**a ɗauka ya biyo bayan kyakkyawan aiki, manufofi na gari, da kuma nasarorin da gwamnatin Dauda Lawal ta samu a ɓangarori daban-daban, musamman ta fannin tsaro, ilimi, aikin noma, da kuma inganta rayuwar al'umma.

Wannan haɗin gwiwa na ƙungiyoyi 100 alama ce a fili da ke nuna cewa al'amuran jihar Zamfara na tafiya a turba madaidaiciya. Jama'a sun gani da idon su, saboda haka s**a yanke shawara ba tare da shakku ba don gani an ci gaba da wannan tsari na bunkasa jihar mu," in ji Hon. Nura Sani.

Wakilan ƙungiyoyin da s**a haɗu sun amince su kafa maɗaukakin tsari a dukkan mazabu da ƙauyuka domin wayar da kan jama'a da haɗa kai waje ɗaya don tabbatar da nasarar gwamnan a babban zaɓen shekarar 2027 mai zuwa.

Albayan Media

26/08/2026
26/08/2026

BIDIYO: ‎Yadda ɗumbin magoya baya da masoyan Ministan tsaro Dr Bello Matawalle s**a tarye shi a birnin Abuja cikin shauƙi da ƙauna, bayan dawowarsa daga ƙasar waje a jiya Talata.

‎A jawabin da ya gabatar, Ministan ya ce ya dawo da ƙarfinsa da cikakken shirin yi wa shugaban ƙasa Tinubu yaƙin neman zaɓe a duk Jihohin Najeriya 36 da Abuja.

Albayan Media

26/08/2026

Kaitsaye a wajen Taron Bita da wayar dakai na kwana 2 na Kungiyoyi 100 da kuma nuna goyon bayansu ga Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara.

Albayan Media

Address

Gusau
632101

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Albayan Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share