Zamfara Daily Updates

Zamfara Daily Updates life is simple,
(787)

Na kalubalanci duk wani mai mukami cikin tafiyar Dauda A garin kaura Namoda Tun daga chairman har commissioner da duk wa...
12/08/2026

Na kalubalanci duk wani mai mukami cikin tafiyar Dauda A garin kaura Namoda Tun daga chairman har commissioner da duk wani mukara bin gwamnatin dauda da ya nuna man Inda wani cikin su yayyi Abinda AA KAURA yayyi ko yake da jama'ar da AA KAURA yake dasu A garin kaura Namoda

AA KAURA yaraba motoci Ina cikin wadanda s**a Samu kyautar mota

AA KAURA ya raba masuna

AA KAURA ya raba inginin nika

AA KAURA ya raba Teloli

AA KAURA yaba matasa jari ciki

AA KAURA ya dauki nauyin matasa guda 25 zuwa makaranta domin su kammala degree Kuma sun kallama yanzu haka Alhamdulillahi

AA KAURA yakai mutun sama da Dari biyu Aikin HAJJI da UMRA

AA KAURA ya samama matasa Aikin yi sunfi mutun Dari A matsayin gwamnatin Tarayya

AA KAURA ya gyara ya Kuma Gina masallatai

AA KAURA ya Gina Kuma ya gyara islamiyoyi

AA KAURA yana kishin garin kaura Namoda

AA KAURA duk sallah karama, Azumi da babba sai ya raba kayan Abinci da Raguna da Atamfu da kudade ga Al'umma

Dan haka Inason Akawoman Wanda yayyi irin wadannan Ayukan cikin gwamnatin dauda A garin kaura Namoda

A takaice, Babu wani aikin jin kai, tausayi, tallafi, karfafawa da kuma ayukkan ci gaban gari Wanda Dan siyasa keyi komai girmansa a jahar Zamfara da Comrd AA Kaura bai zoma da alumma shi ba a halin yanzu 👌

Duk da kasancewarsa ba a ta6a za6ensa ba akan wata Kujerar Mulki har yanzu, duk wadan nan abubuwan jin qan yana aiwatar dasu ne aljihunsa bada lalitar Gwamnati ba 👌

Bisa haka AA KAURA ya wuce raini ga duk wani Dan siyasar Jahar zamfara wlh Dan ba KAURA kadai ba wlh duk fadin Jahar zamfara Babu LG din da Anas baida wadanda zaisa suyi suyi su bari su bari !

~ INJI WANI BABBAN JIGO KUMA SECRETARY NA AA KAURA FOUNDATION

WATO SULEIMAN SKETCH

MATSIN LAMBAR SOJOJI YA SA ƘARIN MUTUM 17 DAGA ƘUNGIYAR JAS SUN MIƘA WUYA GA JAMI'AN TSARO A BORNOMutum 17 daga cikin iy...
05/08/2026

MATSIN LAMBAR SOJOJI YA SA ƘARIN MUTUM 17 DAGA ƘUNGIYAR JAS SUN MIƘA WUYA GA JAMI'AN TSARO A BORNO

Mutum 17 daga cikin iyalan ƙungiyar Jama'atu Ahlis Sunna Lidda'awati wal-Jihad (JAS) sun miƙa wuya ga dakarun Operation HADIN KAI a wasu lokuta daban-daban a Jihar Borno, sakamakon ci gaba da matsin lambar da sojoji ke yi wa 'yan ta'adda a yankin Arewa maso Gabas.

A cewar wata sanarwa da Mukaddashin Jami'in Yaɗa Labaran Soji na Operation HADIN KAI, Kyaftin Mohammed Goni, ya fitar ranar Laraba, mutum 16 daga cikin waɗanda s**a miƙa wuya sun haɗa da mata 10 da yara shida.

Sanarwar ta ce mutanen sun miƙa wuya ne da misalin ƙarfe 9:15 na safe ranar 4 ga Agustan 2026 ga dakarun Bataliya ta 222 yayin da suke sintiri a yankin Gezuwa da ke Ƙaramar Hukumar Konduga ta Jihar Borno.

A yayin tambayoyin farko, waɗanda s**a miƙa wuya sun bayyana cewa hare-haren da sojoji ke ci gaba da kai wa maɓoyar 'yan ta'adda ne ya sa s**a yanke shawarar barin ƙungiyar. Haka kuma, an samu kuɗi Naira 92,000 daga hannunsu.

Hakazalika, da misalin ƙarfe 12:04 na rana a wannan rana, wani yaro ɗan shekara 11 daga cikin iyalan JAS ya miƙa wuya ga dakarun Bataliya ta 202 a Ƙaramar Hukumar Bama. Shi ma ya bayyana cewa matsin lambar da sojoji ke yi wa 'yan ta'adda ne ya sa ya miƙa wuya.

Operation HADIN KAI ta ce ana ci gaba da tantancewa da yi wa waɗanda s**a miƙa wuya tambayoyi kafin a miƙa su ga hukumomin da s**a dace domin ci gaba da bincike, shirye-shiryen gyaran hali inda ya dace, da sauran matakan da doka ta tanada.

Rundunar ta jaddada cewa za ta ci gaba da kai hare-hare kan maɓoyar 'yan ta'adda, tare da lalata hanyoyin sadarwarsu da na samar musu da kayan aiki, domin hana su ci gaba da gudanar da ayyukansu a yankin Arewa maso Gabas.

05/08/2026

To ga fa mutanen ya samu sabon babur, bayan an sace na Shi

Sojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Yi Garkuwa da Su, Sun Kwato Dabbobi 281 da ’Yan Bindiga S**a Sace a SakkwatoDaga Aliyu ...
05/08/2026

Sojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Yi Garkuwa da Su, Sun Kwato Dabbobi 281 da ’Yan Bindiga S**a Sace a Sakkwato

Daga Aliyu Samba

Dakarun Rundunar Sojin Najeriya ta 8 Division Garrison sun ceto mutum 14 da aka yi garkuwa da su tare da kwato dabbobi 281 da wasu ’yan bindiga s**a sace bayan sun kai hari ƙauyen Horo Birni da ke Ƙaramar Hukumar Shagari a Jihar Sakkwato.

Wata majiya mai tushe a rundunar sojin ta shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) cewa lamarin ya faru ne a ranar Talata, inda dakarun s**a gaggauta kai É—auki bayan samun kiran neman agaji daga mazauna yankin.

Majiyar ta ce da isar sojojin, sun yi arangama da ’yan bindigar da ke tafiya da mutanen da s**a yi garkuwa da su tare da dabbobin da s**a sace daga ƙauyen.

Ta bayyana cewa sojojin sun yi wa ’yan bindigar ruwan wuta, lamarin da ya tilasta musu tserewa cikin ruɗani bayan sun samu raunukan harbin bindiga, s**a bar mutanen da s**a sace da kuma dabbobin.

A cewar majiyar, sojojin sun yi nasarar ceto mutane 14 tare da kwato shanu 195, tumaki 84, rakuma biyu da kuma babura biyu.

Ta ƙara da cewa gaggawar da sojojin s**a yi wajen kai ɗauki ta taimaka wajen ceton rayuka da dukiyoyin al’umma, tana mai yabawa haɗin gwiwar jami’an tsaro da ya taimaka wajen nasarar aikin.

Majiyar ta jaddada cewa dakarun sojin na ci gaba da kasancewa cikin shiri domin yaƙi da duk wani nau’in ta’addanci da laifuffuka, tare da kira ga al’umma da su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro cikakken haɗin kai da kuma kai rahoton duk wani abin da ba su yarda da shi ba.

DA DUMI-DUMI: Hukumar EFCC ta Kulle asusun Gwamnatin Jihar Osun na  First Bank, kwanaki goma kacal kafin zaɓen gwamnan j...
05/08/2026

DA DUMI-DUMI: Hukumar EFCC ta Kulle asusun Gwamnatin Jihar Osun na First Bank, kwanaki goma kacal kafin zaɓen gwamnan jihar.

A 'yan sa'o'i da s**a gabata, Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke, ya yi zargin cewa EFCC na shirin daskarar da asusun gwamnatin jihar da kuma na manyan jami'an gwamnati.

Ya bayyana matakin a matsayin wani yunƙuri na kawo cikas ga ayyukan gwamnati gabanin zaɓen gwamna da za a gudanar ranar 15 ga Agusta, yana mai cewa babu wani tushen doka da ke bai wa EFCC damar daskarar da asusun gwamnatin jihar. A cewarsa, EFCC ba ta da hurumin doka na ɗaukar irin wannan mataki.
Rahotanni sun ce Gwamna Adeleke na duba yiwuwar gudanar da taron manema labarai domin yi wa al'ummar jihar bayani kan lamarin.

NAIC Ta Kaddamar da Shirin Inshorar Fasinjoji Tare da Ƙungiyoyin SufuriHukumar Inshorar Noma ta Ƙasa (NAIC) ta bayyana s...
03/08/2026

NAIC Ta Kaddamar da Shirin Inshorar Fasinjoji Tare da Ƙungiyoyin Sufuri

Hukumar Inshorar Noma ta Ƙasa (NAIC) ta bayyana shirin ƙaddamar da Shirin Inshorar Haɗarin Fasinjoji (Passenger Group Accident Insurance Scheme) tare da haɗin gwiwar ƙungiyoyin sufuri domin ba da kariyar kuɗi ga fasinjojin da ke fuskantar haɗarin mota a faɗin Najeriya.

An bayyana wannan shiri ne a yayin wata ganawa da aka gudanar a hedikwatar NAIC da ke Abuja, inda shugabannin Ƙungiyar Direbobin Motoci ta Ƙasa (NURTW) s**a kai ziyarar girmamawa ga Manajan Darakta kuma Babban Jami'in Hukumar, Hon. Yazid Shehu Danfulani.

Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Manajan Hulɗa da Jama'a na NAIC, Dr. Lawal Umar Maradun, ya sanya wa hannu ranar Juma'a.

Da yake jawabi a taron, Danfulani ya bayyana cewa sabon shirin inshorar wata muhimmiyar dabara ce da aka ƙirƙira domin rage nauyin kuɗaɗen da haɗurran mota ke jefa a kan waɗanda abin ya shafa da iyalansu.

Ya ce ana tsara shirin ne tare da haɗin gwiwar NURTW da kuma Ƙungiyar Masu Motocin Sufuri ta Ƙasa (NARTO) domin tallafa wa ƙoƙarin Gwamnatin Tarayya na inganta tsaron hanyoyi da ƙarfafa tsarin kariyar jin daɗin al'umma.

A cewarsa, kimanin mutane 32,000 ne ke samun raunuka sakamakon haÉ—urran mota a Najeriya duk shekara, yayin da kusan mutane 5,200 ke rasa rayukansu a irin waÉ—annan haÉ—urra a kowace shekara.

Danfulani ya ce:
"Shirin Inshorar HaÉ—arin Fasinjoji wata muhimmiyar hanya ce da aka tsara domin rage nauyin kuÉ—aÉ—en da haÉ—urran mota ke jefa a kan waÉ—anda abin ya shafa da iyalansu."

Ya ƙara da cewa inshorar za ta ba da tallafin kuɗi ga waɗanda s**a ji rauni ko iyalan waɗanda s**a rasa rayukansu, domin rage matsin tattalin arziƙin da haɗurran ke haifarwa.

Danfulani ya sake jaddada kudirin NAIC na samar da sabbin hanyoyin inshora da za su taimaka wajen magance ƙalubalen ƙasa tare da inganta walwala da tsaron rayuwar 'yan Najeriya.

A nasu ɓangaren, wakilan NURTW, NARTO da masu ba da shawara kan aikin sun yi alƙawarin ba da cikakken haɗin kai domin tabbatar da nasarar aiwatar da shirin.

Sun bayyana kwarin gwiwarsu cewa wannan haɗin gwiwa zai taimaka wajen inganta tsaron hanyoyi, ƙarfafa tsarin kariyar al'umma, da samar da kariyar kuɗi ga miliyoyin fasinjoji a faɗin Najeriya.

Taron ya kuma haÉ—a da gabatar da tsarin aiwatar da sabon shirin inshorar, inda mahalarta s**a nuna tabbacin cewa zai kawo É—orewar alheri ga masu amfani da hanyoyin Najeriya.

Ministan Tsaro, Matawalle Ya Umurci Hadin Guiwar Rundunar Fansan Yamma Dasu Kara Kaimi Ga Yakar Ta'addanci a Arewa Maso ...
25/07/2026

Ministan Tsaro, Matawalle Ya Umurci Hadin Guiwar Rundunar Fansan Yamma Dasu Kara Kaimi Ga Yakar Ta'addanci a Arewa Maso Yamma,
- Ya YiWa Al'ummar Bungudu Jaje.

Ministan Kasa a Ma'aikatar Tsaro, Mohammed Bello Matawalle yayi jaje ga al'ummar yankin Bungudu da sauran al'ummar garuruwan da ayyukan ta'addanci s**a shafa a makon jiya nan, tare da kara baiwa shugabanin rundunar Fansan Yamma dake aikin yaki da ta'addanci umurnin kada su daga kafa ga aikin da suke yi na yaki da ta'addanci tare da sauran jami'an tsaro a wadanan wuraren.

Ya nemi jami'an tsaron su ci gaba da amfani da dabarun zamani da na tsaro don ganin an ceto mutanen dake hannun yan ta'adda a cikin wannan yanayi na damina.

Haka ma Ministan Tsaro ya bayar da umurni ga rundunar Fansan Yamma da sauran masu aikin tsaro na soja a jihohin Zamfara, Kebbi, Katsina, Sokoto da Kaduna dasu kara kaimi da daukar matakai masu zafi wanda duk ya dace ga aikin dakile ayyukan ta'addanci tare da kira ga al'umma mussaman shugabanin al'umma dasu rinka tsegunta ma jami'an tsaro na bayanin masu baiwa yan ta'adda bayanai akan kai hare hare cikin yankunan karkara.

Ya kara da baiwa manyan kwamandojin dake kula da yankunan soja da abin yafi tsamari dasu sanya ido da yin patrol don rusa wuraren da ake zargin yan ta'adda na buya don aikata ta'addanci.

Ministan ya jijjina tare da yaba ma jami'an tsaro akan namijin kokarin da nasarar da s**a samu a baya akan rusa wasu manya da kananan yan ta'adda a Gummi, Anka, Tsafe, Faskari da sauransu. Ya nemi sojojin da su ci gaba da bayar da zafi wanda suke yi ga ganin an kai karshen mugayen mutane dake aikata ayyukan ta'addanci a sassa dabam dabam na kasarnan.

Sa hannun
Ahmed Dan Wudil,
Mataimaki na mussaman ga Ministan Tsaro,
Mohammed Bello Matawalle
25/7/2026

Dakarun Sojoji Sun Bankado Maboyar Masu Laifi, Sun Kwace Makamai a Yankin Kudu Maso GabasDakarun Rundunar Sojin Najeriya...
24/07/2026

Dakarun Sojoji Sun Bankado Maboyar Masu Laifi, Sun Kwace Makamai a Yankin Kudu Maso Gabas

Dakarun Rundunar Sojin Najeriya sun sake samun gagarumar nasara a ci gaba da farmakin da suke kai wa masu aikata laifuka a yankin Kudu maso Gabas, inda dakarun Sector 4, Joint Task Force South-East, Operation UDO KA (OPUK) s**a kwato tarin makamai da alburusai a wani samame na sirri da s**a kai a Jihar Rivers.

Wannan nasara ta nuna ƙudirin rundunar soji na rushe ƙungiyoyin masu aikata laifuka, hana su damar tayar da zaune tsaye, tare da samar da zaman lafiya, tsaro da bunƙasar tattalin arziki a yankin.

An gudanar da wannan samame ne da safiyar ranar 23 ga Yuli, 2026, inda aka kai farmaki wata maboyar da ake zargin masu laifi ke amfani da ita a bakin ruwa na Awara Community da ke ƙaramar hukumar Ohaji/Egbema, da kuma kan hanyar Omoku–Ogbaku–Ndoni a Jihar Rivers.

Bayan samun sahihan bayanan sirri, dakarun sun kutsa cikin dajin da ake zargin masu laifin ke amfani da shi a matsayin sansanin shirya sace mutane da kai hare-hare kan jami'an tsaro da fararen hula.

A yayin samamen, dakarun sun kwato:
Bindiga kirar Lee-Enfield MK I guda É—aya.
Bindiga kirar G3 guda É—aya.
Alburusai 116 na 5.56mm.
Alburusai 13 na 7.62mm.

Rundunar ta bayyana cewa har yanzu ana ci gaba da gudanar da aikin domin kawar da duk wani nau'in aikata laifi a yankin.

Sojojin sun ce wannan shi ne karo na huɗu cikin makonni biyu da s**a samu nasarar kwace makamai ba bisa ƙa'ida ba, lamarin da ke nuna tasirin ayyukan tattara bayanan sirri da kuma haɗin gwiwar da ke tsakanin Rundunar Sojin Najeriya, sauran hukumomin tsaro da kuma al'umma.

Rundunar Sojin Najeriya ta sake jaddada cewa za ta ci gaba da gudanar da hare-haren da s**a dogara da bayanan sirri tare da haÉ—in gwiwar sauran hukumomin tsaro har sai an kawar da dukkan masu aikata laifuka daga maboyarsu tare da gurfanar da su a gaban doka.

Haka kuma, rundunar ta buƙaci al'umma da su ci gaba da ba jami'an tsaro sahihan bayanai cikin lokaci, tana mai cewa haɗin kan jama'a na da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da dorewar zaman lafiya da tsaro a yankin Kudu maso Gabas da Najeriya baki ɗaya.

Matawalle Ya Yabawa Shugaba Tinubu Yayin Ƙaddamar da Gidajen Ma'aikatan DIAAbuja – Ministan Ƙasa na Harkokin Tsaro, Dr. ...
24/07/2026

Matawalle Ya Yabawa Shugaba Tinubu Yayin Ƙaddamar da Gidajen Ma'aikatan DIA

Abuja – Ministan Ƙasa na Harkokin Tsaro, Dr. Bello Mohammed Matawalle, ya yabawa Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, bisa ci gaba da ba da goyon baya wajen inganta jin daɗi da ƙarfafa ayyukan rundunonin tsaron Najeriya.

Matawalle ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis yayin da ya ƙaddamar da wani rukunin gidaje guda 20 na ɗaki ɗaya da Hukumar Leken Asirin Tsaro ta Najeriya (Defence Intelligence Agency – DIA) ta gina domin ma'aikatanta.

A cewar wata sanarwa da Mataimakinsa na Musamman kan YaÉ—a Labarai, Ahmad Dan-Wudil, ya fitar, ministan ya ce wannan aikin alama ce ta jajircewar Gwamnatin Tarayya wajen magance matsalar gidaje da kuma inganta walwalar jami'an tsaro.

Ya ce nasarorin da DIA ta samu sun kasance ne sakamakon cikakken goyon bayan Shugaba Tinubu, yana mai ƙara da cewa gwamnatin Renewed Hope ta himmatu wajen samar da ingantattun gidaje domin jami'an rundunonin sojin Najeriya.

Matawalle ya bayyana cewa sabbin gidajen za su taimaka wajen inganta rayuwar ma'aikata, ƙara musu ƙwarin gwiwa da kuma inganta ƙwarewarsu wajen gudanar da ayyukansu.

Ya ce:

"Muhalli da masauki na daga cikin muhimman buƙatun jami'anmu da ma'aikatanmu. Ingantaccen gida ba alatu ba ne, buƙata ce da ke ba mutum kwanciyar hankali, ƙara masa ƙwarin gwiwa da kuma inganta jajircewarsa wajen aiki."

Ministan ya kuma yaba wa Babban Daraktan Hukumar Leken Asirin Tsaro, Laftanar Janar Emmanuel Undiandeye, bisa ƙaddamar da wannan gagarumin aiki.

Ya ce hukumar na ci gaba da samun manyan nasarori ƙarƙashin jagorancinsa, tare da tabbatar da cewa Ma'aikatar Tsaro za ta ci gaba da ba DIA dukkan goyon bayan da take buƙata domin cika nauyin da ke kanta.

Har ila yau, Matawalle ya shawarci waÉ—anda za su amfana da gidajen da su kula da su yadda ya kamata domin tabbatar da É—orewarsu.

A nasa jawabin, Babban Daraktan DIA, Laftanar Janar Emmanuel Undiandeye, ya gode wa Ministan bisa halartar bikin da kuma ƙaddamar da gidajen da kansa, yana mai cewa hakan ya nuna irin muhimmancin da yake bai wa walwalar ma'aikatan hukumar.

Ya kuma miƙa godiya ga Shugaba Bola Tinubu bisa ci gaba da ba hukumar goyon baya, tare da jaddada cewa jami'an da ma'aikatan DIA za su ci gaba da kasancewa masu biyayya da sadaukar da kai wajen kare ƙasa.

Bikin ya samu halartar Mai Kula da Ƙungiyar Matan Jami'an DIA, Mrs. Jane Undiyandeye, daraktocin hukumar, manyan jami'an soja da farar hula, manyan hafsoshin runduna, sojoji da sauran ma'aikata.

22/07/2026

Kungiyar A.A YARI MEDIA TEAM Sun yi kira ga yan Social Media da su zama masu bin doka da oda tare da kira yayan jam’iyyar APC da su zabi dukkan yan takarkarin jam'iyar daga sama har kasa a zaben 2027 Part 51

Address

Gusau
Kano
880001

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zamfara Daily Updates posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share