08/04/2026
Majalisar dokokin jahar Zamfara ta dakatar da shugabannin kananan hukumomi guda biyu da s**a hada da ba Kaura Namoda da kuma Bukkuyum.
Shugabannin dai sune Hon. Umar A. Faru Nasarawa na karamar hukumar Bukkuyum da kuma Hon. Mannir Mu’azu Haidara na karamar hukumar Kaura Namoda.
Majalisar dokokin ta kuma umurci mataimakan shugabannin majalisun biyu da su ci gaba da tafiyar da ragamar mulki har sai an kammala bincike.