Jaridar Shaho

Jaridar Shaho Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Jaridar Shaho, Media/News Company, Gusau.

Zauren kula da ilmi na jihar Zamfara ya yaba wa Matawalle da ya farfado bangaren ilmi a lokacin yana Gwamna duk da kudad...
08/07/2025

Zauren kula da ilmi na jihar Zamfara ya yaba wa Matawalle da ya farfado bangaren ilmi a lokacin yana Gwamna duk da kudade kalilan da yake samu a lokacin

Zauren da ke sa ido don cigaban Ilimi a Zamfara Zamfara Education Forum ZEF ya yaba wa tsohon Gwamna kuma Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya, Dr Bello Mohammed Matawalle, bisa kokarinsa na farfado da harkar ilimi a jihar duk da karancin kudaden da aka samu a lokacin mulkinsa.

A cikin wata sanarwa da Shugaban zauren Yusuf Ibrahim Maradun, ya fitar a ranar Juma’a, ta bayyana yadda gwamnatin Matawalle a wancan lokacin ta samu gagarumar nasara karkashin tallafin gyaran makarantu na 2017/2018, inda aka gina azuzuwa 900 a sassa daban-daban na jihar cikin shekaru biyu kacal.

Ya ce karkashin jagorancin Matawalle, harkar ilimi ta samu sauyi da tagomashi mai ma’ana duk da cewa gwamnatin ta karbi kason kudi 'yan kaɗan daga asusun tarayya idan aka kwatanta da gwamnatin yanzu.

“Dr Matawalle ya sauya fasalin ilimi a jihar Zamfara da kudi 'yan kadan. Wannan abin shaida kuma abin a yaba ne na hangen nesa da jajircewa,” in ji Maradun.

Zauren ya kara da bayyana cewa ban da sabbin azuzuwa, an gyara azuzuwa 375 da s**a lalace, tare da sabunta ofisoshi uku na Hukumar Ilimi ta Ƙananan Hukumomi (LGEA).

Maradun ya ce gyaran wadannan ofisoshi ya taimaka wajen samar wa ma’aikata da muhallin aiki mai kyau, wanda hakan ya kara kwazo da ingancin aiki a fadin jihar.

Ya kwatanta hakan da gwamnatin yanzu da ke karɓar fiye da Naira bilyan 19 a kowane wata daga asusun tarayya, amma har yanzu ba ta iya yin ababen da za a iya gani kamar na Matawalle ba.

“Da Matawalle ne aka ba irin wannan adadin kudi, da tsarin ilimin jihar Zamfara ya zama abin koyi a Nijeriya,” in ji shi.

Yayin da lokacin zaben 2027 ke karatowa, Zauren ya yi kira ga al’ummar jihar Zamfara da su gane irin jagorancin da ke kawo ci gaba.

“Muna kira ga jama’a da su kare kuri'arsu kuma su goyi bayan Matawalle. Komawarsa kan madafun iko zai dawo da fata da ci gaba ga jihar Zamfara,” in ji sanarwar.

Matawalle ya yi jinjina ga sojoji 'yan ajin NDA 18RC a taron cika shekaru 50 da s**a shiryaMinistan kasa a ma'aikatar ts...
06/07/2025

Matawalle ya yi jinjina ga sojoji 'yan ajin NDA 18RC a taron cika shekaru 50 da s**a shirya

Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya, Dr. Bello Muhammad Matawalle, ya yi yabo, jinjina da ban girma ga hafsan sojin da s**a karbi horo karo na 18 wato NDA 18RC a yayin taron tsoffin dalibai bayan cikarsu shekaru 50 da kammala samun horon.

An gudanar da taron ne a dakin taro na Command Officers’ Mess na Hedikwatar Sojojin Kasa da ke Asokoro, Abuja, inda tsofaffin sojoji, jagororin ƙasa, da manyan baki s**a hallara domin murnar shekaru 50 na haɗin kai, jagoranci da hidima ga ƙasa.

Da yake jawabi a matsayin Babban Bako na Musamman, Matawalle ya jinjina wa mambobin kwas ɗin bisa zumunci da haɗin kan da suke ci gaba da nunawa da kuma gudummawar da suke bayarwa wajen gina ƙasa.

Ya yaba da irin gudummawar da Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar (wanda shi ma memba ne na 18RC), da sauran fitattun mambobi kamar su Laftanar Janar Azubuike Ihejirika (mai ritaya), da Manjo Janar Ike Nwachukwu (mai ritaya) ke badawa.

Ministan ya waiwayi tarihin kwas ɗin wanda ya fara a shekarar 1975 da dalibai 149 daga bangaren Regular Combatant da Short Service Course.

“Daga cikin 149 da s**a fara, mutum 47 ne kacal ke raye a yau,” in ji Matawalle. “Muna gode wa Allah bisa rahamarSa kuma muna addu’a ga wadanda s**a riga mu gidan gaskiya.”

Ya kuma yaba da shugaban kwas ɗin, wanda a halin yanzu shi ne shugaban Kwamitin Walwalar Tsofaffin Sojojin Ma’aikatar Tsaro.

Matawalle ya jaddada muhimmancin tsofaffin sojoji a cikin rayuwar farar hula bayan ritaya, yana mai cewa irin gudummawarsu bayan barin aiki abin yabo ne kuma ana yaba musu da shi.

Ministan ya bukaci sauran ƙungiyoyin tsofaffin ɗaliban NDA su kwaikwayi hadin kai da zumuncin NDA 18RC, yana bayyana zumuncinsu a matsayin abin koyi ga ɗorewar haɗin kan ƙasa.

“Wannan taro yana nuna abin da za a iya cimmawa ta hanyar haɗin kai tsakanin ‘yan kwas,” in ji shi, yana ƙarfafa shirya tarurrukan da ke ƙarfafa zumunci da hidima ga ƙasa.

Taron ya samu halartar manyan jami’ai ciki ha da Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Tsaro, Malam Nuhu Ribadu, da Babban Hafsan Tsaro, Janar Christopher Musa.

Kwas ɗin 18RC ya fara horar da hafsan soja a NDA da ke Kaduna ranar 30 ga Yuni, 1975, wanda yanzu ke cika rabin ƙarni na hidima ta kwarai da mambobinsa s**a bayar.

A ƙarshe, Matawalle ya yi addu’a ga mamatan tare da yi wa ragowar ‘yan kwas fatan lafiya mai inganci, zaman lafiya da ci gaba da kasancewa masu muhimmanci ga ƙasa.

Manufofin gwamnatin Shugaba Tinubu: Shugaban hukumar NAIC na goyon bayan ci gaban bangaren kiwoManajan daraktan hukumar ...
04/07/2025

Manufofin gwamnatin Shugaba Tinubu: Shugaban hukumar NAIC na goyon bayan ci gaban bangaren kiwo

Manajan daraktan hukumar Inshorar Aikin Gona ta Kasa NAIC, Hon. Yazid Shehu Danfulani, ya bayyana cikakken goyon bayansa ga kokarin Gwamnatin Tarayya na farfaɗo da bangaren kiwo a karkashin tsarin Renewed Hope Agenda na Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Hon. Danfulani ya bayyana hakan ne bayan wata muhimmiyar ganawa da Ministan Raya Bangaren Kiwo, Dr. Idi Mukhtar Maiha, a Abuja ranar Alhamis.

Tattaunawar ta mayar da hankali kan daidaita ayyukan inshorar hukumar NAIC da manufofin kasa na samar da isasshen abinci, dorewar aikin gona da kuma karfafa wa al’ummomin yankunan karkara.

“Bangaren kiwo na da matukar muhimmanci ga tattalin arzikinmu da kuma rayuwar jama’a,” in ji Hon. Danfulani. “Hukumar NAIC ta shirya tsaf wajen samar da sabbin hanyoyin inshora don kare manoma da tallafa musu wajen habaka yawan amfanin su.”

Hukumar NAIC, a matsayin cibiyar da ke jagorantar sarrafa kalubalen aikin gona a kasar nan, ta sake jaddada aniyarta ta rage illolin sauyin yanayi, tabarbarewar kasuwa da kuma sauran hadurran da manoma ke fuskanta.

A yayin ganawar, bangarorin biyu sun tantance hanyoyin haɗin guiwa ciki ha da kirkirar inshorar musamman ga dabbobi, horas da manoma, da amfani da fasahar zamani wajen inganta ayyuka.

A nasa bangaren, Dr. Maiha ya yaba da hadin guiwar tare da bayyana cewa kofar ma’aikatarsa a bude take wajen aiki tare da masu ruwa da tsaki domin cimma manyan sauye-sauye don a daratta bangaren kiwo.

Wannan shiri na daga cikin muhimman matakai na tsarin gyaran aikin gona da Shugaba Tinubu ke jagoranta, wanda ke nufin farfaɗo da al’ummomin karkara da kuma tabbatar da wadatar abinci a kasa.

Hon. Danfulani ya tabbatar wa Ministan cewa hukumar NAIC za ta ci gaba da ba da gudunmuwa wajen kare jari a aikin gona da kuma tabbatar da daidaituwar ci gaban bangaren.

“Wannan hadin guiwar, mataki ne mai muhimmanci wajen gina makoma mai karfi da dorewa ga aikin gona a Nijeriya,” in ji shi.

04/07/2025

Majalisar dokokin jihar Zamfara na barazanar tsige Gwamna Dauda

Majalisar dokokin Jihar Zamfara ta bai wa Gwamna Dauda Lawal Dare wa’adin makonni biyu, tana mai gargadin yiwuwar tsige shi daga mukaminsa saboda tabarbarewar tsaro da kuma zargin almundahana da kudaden gwamnati.

’Yan majalisar sun bayyana matsananciyar damuwa a zaman majalisar da s**a gudanar, inda s**a ce gwamnatin Gwamna Lawal ta gaza kare rayuka da dukiyoyin al’umma a fadin jihar.

Sun ambaci yadda hare-haren 'yan bindiga ke karuwa, tare da kisan gilla da garkuwa da mutane, suna zargin gwamnan da jinkiri da rashin iya daukar matakan magance matsalar.

“Ba za mu ci gaba da zama shiru ba yayin da al’ummarmu ke rayuwa cikin fargaba,” in ji wani dan majalisa yayin zaman.

Majalisar ta ce idan har bangaren zartarwa ya gaza daukar matakin gaggawa da ya dace, to ba za ta yi wata-wata ba wajen amfani da hurumin kundin tsarin mulki don kare rayuwar al’umma.

Baya ga batun tsaro, 'yan majalisar sun nemi bayani kan yadda aka kashe kudi Naira bilyan 9 da aka ce an ware domin gyaran asibitoci.

Sun ce duk da kashe makudan kudaden, da dama daga cikin cibiyoyin kiwon lafiya a jihar na cikin halin kuncin da ba za a iya amfana da su ba, musamman a yankunan karkara.

“Asibitocin jihar Zamfara sun lalacewa, suna cikin halin kaka-ni-ka-yi,” in ji wani dan majalisa. “Muna bukatar cikakken bayani dalla-dalla kan yadda kudaden s**a tafi.”

Shirin tallafa wa al’umma da gwamnatin ta fi bayyanawa a kafofin watsa labarai, wanda aka ce yana bai wa mutane N250,000 don fara kananan sana’o’i, shi ma kwallaiya ba ta biya kudin sabulu ba.

’Yan majalisar sun ce shirin tamkar na bogi ne, s**a kuma nemi gwamnati ta fitar da sunayen wadanda s**a ci gajiyar shirin a baje ta a faifai a kowace karamar hukuma da mazaba.

Sauran s**a da caccakar da 'yan majalisar s**a yi wa Gwamnan jihar sun shafi nadin wasu wadanda ba 'yan asalin jihar ba a matsayin masu ba gwamna shawara na musamman.

’Yan majalisar sun bayyana matakin a matsayin rashin la’akari da jin dadin ’yan jihar, inda s**a ce an bai wa baki miliyoyin kudaden jihar yayin da ’yan asalin Zamfara da s**a cancanta ke ci gaba da zama a gefe, sun zama 'yan kallo.

“Ta yaya gwamnati za ta ce tana tallafa wa ’yan jiharta, amma a zahiri ta yi watsi da su wajen nadin mukamai?” in ji wani dan majalisa.

Majalisar ta jaddada kudurinta na tabbatar da gaskiya da rikon amana, tana mai cewa za ta yi duk mai yiwuwa ta hanyar doka don kare muradun al’ummar jihar Zamfara.

04/07/2025

Me yasa mata ke jin haushín mata yan uwan su?

Bayan Sauka Daga Kujerar Shugabancin APC, Ganduje Ya Halarci Zama A Ofishinsa Na Hukumar Jiragen Sama Na Kasa (FAAN)Duk ...
04/07/2025

Bayan Sauka Daga Kujerar Shugabancin APC, Ganduje Ya Halarci Zama A Ofishinsa Na Hukumar Jiragen Sama Na Kasa (FAAN)

Duk da dai wata majiya ta bayyana cewa Ganduje ya ajiye mukaminsa na shugabancin APC ne sakamakon rashin lafiya, amma sai ga shi ya samu damar halartar taron hukumar FAAN.

Shin me kuke tuninin dalilin hakan?

Jami'ar Annahada international University of Niger ta karrama Shahararren matashin nan Dan siyasa Kuma Dan gwaggwarmaya ...
03/07/2025

Jami'ar Annahada international University of Niger ta karrama Shahararren matashin nan Dan siyasa Kuma Dan gwaggwarmaya COMRADE AA KAURA akan gagarumin kokarin da yayyi na daukar nauyin matasa 25 suyi karatun degree ta fannona daban daban Kuma cikin iyawar Allah mutun goma Sha Tara sun kammala degree dinsu

Suleiman sketch Mai magana da yawon Comrade Anas Abdullahi kaura wato AA KAURA yace irin wannan Abin ba sabon Abi bane ga wanann matashi yayi haka yafi A Kirga

Suleiman sketch ya bayyana irin nasarorin da Anas Abdullahi kaura ya Samu wajen taimakon Al'umma musamman matasa da mata, ya Kara da cewa Anas kaura Bai tsaya kawai wajen taimakon matasa ta hanyar sama masu makaranta domin su dogara da kaiba

Anas kaura ya dauki matasa ya sama masu gurabun Aiki A gwamnatin tarayya Wanda Nima Mai magana Ina cikin su sannan Kuma ya taimaki matasa da jari domin su dogara da kansu

Abinda kowa yasani ne cewa comrade Anas kaura mutun ne Wanda Al'umma ke Alfahari da samun shi musamman gyaran masallatai, Gina masallatai da islilamiyoyi A garin Kaura Namoda

Suleiman sketch ya rufe da Addu'ar ubangiji Allah ya saka ma da AA KAURA da mafificin Alkhairi bisa ga wanann dawainiya da yakeyi da Al'umma

MATASAN ZAMFARA SUN NEMI  SHAHARALIYYAR YAR SIYASAR NIGERIA HER. EXCELLENCY DR. ASLAM ALIYU( GIMBIYAR KAURA) TA FITO TAK...
03/07/2025

MATASAN ZAMFARA SUN NEMI SHAHARALIYYAR YAR SIYASAR NIGERIA HER. EXCELLENCY DR. ASLAM ALIYU( GIMBIYAR KAURA) TA FITO TAKARAR GWAMNA ZAMFARA A 2027 DON CETO SU DAGA KANGIN BAUTA.

Wasu kungiyoyin Matasan jihar zamfara daga kananan hukumomi jihar 14 ƙarƙashin Comrade Abba Bello Gusau, a yau sun yi gangamin da ya hada mata da matasa da dattijai, inda s**a rufe kofar gidan shahararriyar Yar siyasar Nigeria yar asalin zamfara Her EXCELLENCY Dr. Aslam Aliyu gimbiyar Kaura, domin mika kokensu ga MAMA MAI CAPACITY.

Kungiyar wadda ta zo dauke da allunan da ke dauke da hotunan Dr. Aslam Aliyu MAMA MAI CAPACITY ta Kaura tare da rubuce-rubucen da ke kiran da ta fito don ta ceci Zamfarawa daga ukubar da su ke ciki.

Da ya ke jawabi wajen gangamin shugaban gamayyar kungiyoyin Comrade Abba Bello Gusau ya bayyana cewa MAMA MAI CAPACITY ita dai ce talakan zamfara zai zaba ta iya fitar da talakawan jihar da ukubar da su ke ciki, na, ukubar da talakawan suke hannun yan sari

Haka zalika Comrade Gusau ya kara da cewa her excellency. Mama Mai CAPACITY yar siyasa ce wadda duk zamfara babu dan siyasa kamarta don ita ce kurrum tauraruwarta ke haskawa a tsakanin yan siyasar Zamfara, don haka ya yi kira shi da magoya bayan da ka da ta bari yan siyasa masu manyan riguna su bude mata ido domin yanzu yan siyasa masu kima ga idanun al'umma ake biya don haka ba wani abin da wani dan siyasa zai nuna mata. Don zamfara ta matasa ce a shekarar 2027

A cewarsa shi da magoya bayansa Wannan lokacin kaf zamfara ba dan siyasar da ake maganar alherinsa kamarta. Ita da ba ta taba wata kujerar zaben ba. Musamman ganin yadda take shiga lungu da sako a jihar tana taimakawa talakawan jihar.

Da su ke karbar kungiyar, jagoran tawagar manyan yaranta Hon. Auwal Musa Gusau (AMG) ya bayyana matukar jin dadinsa da wannan ziyarar goyon baya da matasan s**a kawo wa uwar dakinsa.

Tare ba su hakuri akan rashin ganin HER EXCELLENCY da ba su yi ba, wanda ya bayyana cewa MAMA mai CAPACITY tana wajen muhimmin aiki, tare da alkawarin isar da wannan muhimmin sakon da matasan su ke dauke da shi ga mai gidanmu MAMA MAI CAPACITY.

Hon. Auwal ya kara da cewa: " A matsayinmu na yaran her excellency Gwamnan Zamfara ta gobe insha Allahu, kullum muna kiraa gare ta shi ne ta fito takarar gwamnan Zamfara a 2027 don talakawan zamfara s**a kara amfanuwa da alherinta. Don haka wannan kungiyar ba ita ce ta farko da take neman Dr. Ta fito takara ba don haka muna sheda maku za mu isar da sakonku gare ta tare da kara rokonta da ta ji koken talakawan zamfara.

Zamfara ta cancanci samun masu CAPACITY Zamfara sai MAMA MAI CAPACITY 2027 a cewarsa"

03/07/2025

Yan majalissar dokokin Zamfara sun Baiwa gwamna Dauda mako 2 ya dawo cikin hayacinsa ko su akan matsalar tsaro farfado da jihar ko su tsige shi

Don kallon cikakken zaman majalisar

https://youtu.be/1QM-pfPycIA

Tv

YANZU-YANZU: Shugabannin jam’iyyun adawa sun hallara a cibiyar Shehu Musa Yar’Adua domin halartar taron haɗin gwiwa na k...
02/07/2025

YANZU-YANZU: Shugabannin jam’iyyun adawa sun hallara a cibiyar Shehu Musa Yar’Adua domin halartar taron haɗin gwiwa na kaddamar da sabuwar jam’iyya mai suna ADC.

Me za ku ce?

APC a jihar Zamfara ta taya Dalori murna, ta ce tana da yakinin zai kai jam’iyyar tudun mun-tsiraJam’iyyar APC a jihar Z...
02/07/2025

APC a jihar Zamfara ta taya Dalori murna, ta ce tana da yakinin zai kai jam’iyyar tudun mun-tsira

Jam’iyyar APC a jihar Zamfara karkashin jagorancin Hon. Tukur Umar Danfulani ta taya Hon. Ali Bukar Dalori murna bisa mukamin Shugaban riko na jam'iyyar APC kasa da ya samu.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun jam’iyyar a jihar, Yusuf Idris Gusau, ya fitar a yau Laraba, jam’iyyar ta bayyana wannan nadin a matsayin tabbacin yadda shugabannin jam’iyyar, karkashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da sauran magoya baya ke da cikakkiyar girmamawa da amincewa da cancantar Dalori wajen jan ragamar jam’iyyar zuwa tudun mun-tsira.

Sanarwar ta kuma ce, "Muna rokon Allah Ya ba ka kariya da jagora wajen amfani da gogewa da kwarewar da ka tara a matsayin shugaban jam’iyya a matakin jiha, mataimakin shugaban jam'iyya na kasa da sauran mukaman da ka rike, wajen kawo sabbin dabaru da za su tabbatar da cikar muradun sabuwar tafiyar Shugaba Tinubu."

Daga karshe, jam'iyyar APC a jihar Zamfara ta bayyana cikakken goyon bayanta ga Dalori tare da fatan nasara a sabon aikin da aka dora masa.

Sanarwar ta ce a madadin shugabanninta na jiha, dattawa, jiga-jigai da sauran magoya a fadin jihar, suna da yakinin cewa jam'iyyar, za ta yi nasara a lokacin jagorancin Dalori.

Matawalle ya kaddamar da motoci masu amfani da makamashin CNG ga sojojin Nijeriya Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nije...
02/07/2025

Matawalle ya kaddamar da motoci masu amfani da makamashin CNG ga sojojin Nijeriya

Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya, Dr Bello Muhammad Matawalle, ya kaddamar da jerin sabbin motocin soji masu amfani da iskar gas na Compressed Natural Gas CNG.

Wannan wani babban mataki ne da ke nuna kokarin gwamnatin tarayya na kawo sauyi a fannin makamashi a harkokin tsaron kasa.

An gudanar da bikin kaddamarwar ne a sansanin sojoji na Mogadishu da ke birnin tarayya Abuja, lamarin da ke dauke da sakon goyon bayan shirin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na “Renewed Hope Agenda” wajen wanzar da tsabtace amfani da makamashi a fadin kasar.

A cewar wata sanarwa da mai taimaka masa kan kafafen yada labarai, Ahmad Dan-Wudil ya fitar a ranar Talata, Matawalle ya bayyana wannan mataki a matsayin gagarumar nasara wajen kirkire-kirkire, rage yawan kashe kudin aiki da inganta amfani da makamashi a harkokin sufurin rundunar soji.

“Wannan ba kawai sabbin motocin aiki bane,” in ji shi, “amma sauyi ne da zai mayar da rundunoninmu na tsaro tamkar abin koyi wajen kirkire-kirkire da dorewar ci gaba.”

Ministan ya bayyana cewa wannan shiri na amfani da CNG zai rage dogaro da man fetur, ya rage fitar da hayakin da ke gurbata iska, kuma zai taimaka wa Nijeriya wajen cimma kudirorinta na kare muhalli a matakin duniya.

Bisa rakiyar manyan jami'an tsaro ciki ha da babban sakatare na Ma'aikatar Tsaro, Amb Gabriel Aduda, da Shugaban Hafsoshin Tsaro, Janar Christopher Musa, Matawalle ya zagaya don duba motocin CNG har ma ya ja daya daga cikin motocin da kansa.

Ya kara da cewa wadannan sabbin motocin za su rage yawan kudin da ake kula da su a dogon lokaci tare da samar da kariya ga muhalli da kuma karfafa guiwar dakarun.

Ministan ya bukaci a gaggauta kafa tashoshin zuba gas na CNG a dukkan sansanonin soji domin tabbatar da ci gaba da amfani da motocin.

Haka zalika, ya jaddada bukatar horar da jami’an soji yadda ya kamata domin su iya kula da kuma gudanar da motocin CNG yadda ya dace.

Daga cikin manyan baki da s**a halarci bikin akwai Barrister Ismaeel Ahmad, Shugaban Hukumar Kula da Shirin CNG na Fadar Shugaban Kasa, da manyan hafsoshin soji da masana daga bangaren makamashi.

Matawalle ya tabbatar wa 'yan Nijeriya cewa rundunar soji na nan daram wajen yaki da ta'addanci, kuma Shugaba Tinubu na ci gaba da tallafa wa duk wani yunkuri na samar da tsaro.

Ya kuma bukaci al’umma su ci gaba da saka rundunonin tsaro cikin addu’o’insu tare da jaddada kudirin gwamnati na samar da Nijeriya mai tsafta, karfi da kuma ingantaccen tsaro.

Sponsored

Address

Gusau
900271

Opening Hours

Monday 09:00 - 17:00
Tuesday 09:00 - 17:00
Wednesday 09:00 - 17:00
Thursday 09:00 - 17:00
Friday 09:00 - 17:00
Saturday 09:00 - 17:00

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jaridar Shaho posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share