Jaridar Shaho

Jaridar Shaho Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Jaridar Shaho, Media/News Company, Gusau.

Kungiyar matasan Arewacin Nijeriya ta yabi salon diflomasiyyar inganta tsaro da Matawalle ya bullo da ita .....Jagora ne...
19/09/2025

Kungiyar matasan Arewacin Nijeriya ta yabi salon diflomasiyyar inganta tsaro da Matawalle ya bullo da ita

.....Jagora ne na gudanar da aiki, ba na ba da uzurorin karya ba....in ji kungiyar

Kungiyar matasan Arewacin Nijeriya mai suna Northern Youth Concert Citizen ta bayyana jin daɗinta da nutsuwa ga ire-iren ayyukan da ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya, Dr. Bello Muhammad Matawallle ke aiwatarwa, tana mai kiran sa “jagoran gudanar da aiki tukuru, ba na ba da uzurorin babu gaira babu dalili ba” saboda jajircewarsa wajen ƙarfafa diflomasiyyar inganta tsaron Nijeriya.

Shugaban ƙungiyar, Dr. Ibrahim Garba daga Karamar Hukumar Birnin Gwari ta Jihar Kaduna, ya ce, “Matawalle ya sake fasalin diflomasiyyar inganta tsaro ta hanyar nuna batutuwan gyaran tsaro a aikace. Daga Turkiyya zuwa China, daga Pakistan zuwa Amurka, ƙoƙarinsa ya samar da kayayyakin aiki na zamani, inganta fasaha da kuma horo na zamani ga rundunar sojinmu.”

Sanarwar ta kuma nuna muhimmancin sababbin jiragen sintiri masu nisan zango, inda ta bayyana su a matsayin wani hangen nesansa da burin kare Nijeriya ta ƙasa, sama da ruwa da Minista Matawalle kebda shi.” Sanarwar ta ƙara da cewa hakan sadaukarwa ce wajen kare kima da martabar ƙasar.

Dr. Garba ya ƙara da cewa, “Ga matasan Arewacin Nijeriya da ke rayuwa a kullum da matsalar tsaro, jagorancin Matawalle ya dawo musu da cikakkiyar fata cewa Nijeriya za ta iya, kuma za ta shawo kan ƙalubalen tsaronta ta hanyar haɗin gwiwar dabaru da kuma ƙarfafa ƙarfin cikin gida.”

A ƙarshe, ƙungiyar ta sake tabbatar da cikakken goyon bayanta ga Ministan Matawalle, tana mai jaddada cewa
“Jajircewarsa na kara sanya kwarin gwiwa a zukatan miliyoyin ’yan kasa, musamman matasa, waɗanda ke fatan ganin ƙasa mai tsaro, ƙarfi da kuma cigaba.”

Kungiyar da ke rajin an gudanar da shugabanci nagari a jihar Zamfara ta ZGGF ta bukaci  Shugaba Tinubu ya daina ba jihar...
17/09/2025

Kungiyar da ke rajin an gudanar da shugabanci nagari a jihar Zamfara ta ZGGF ta bukaci Shugaba Tinubu ya daina ba jihar kudin dauni na tarayya, sannan ya kakaba dokar ta-baci bayan kalaman Gwamna Dauda Lawal

Kungiyar Zamfara Good Governance Forum ZGGF da ke rajin tabbatar da shugabanci na gari a jihar Zamfara ta roƙi Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya gaggauta dakatar da raba kuɗaɗen tarayya ga jihar Zamfara tare da kafa dokar ta-baci, bisa ga abin da ta bayyana a matsayin mummunar furucin Gwamna Dauda Lawal wanda ya bayyana cewa yana da masaniya kan matsugunnai da maboyar manyan ‘yan bindiga da ke addabar jihar.

Sakataren kungiyar, Muhammad Ibrahim Mafara, ya faɗa wa manema labarai a Gusau cewa wannan ikirarin gwamnan ya zama “cin amanar kasa da kuma babbar gazawa a shugabanci.”

Ya ce “ba wai kawai ganganci ba ne wannan; wannan furuci na nuna tsantsar masaniya dumu-dumu a cikin aikata laifukan ‘yan ta’adda. Idan gwamna mai ci ya fito fili ya ce yana da masaniya kan inda waɗannan ‘yan ta’adda ke rayuwa da yin ta’addanci, amma bai ɗauki mataki ba, to wannan kadai ya tabbatar da laifinsa a gaban jama’a kuma ya tabbatar wa da jama'a zarge-zargen da suke yi a kansa game da ta'addanci.”

Kungiyar ta nuna cewa duk da fiye da Naira miliyan 600 da ake ware wa kowane wata a matsayin kudin tsaro na "security votes" babu wata hujja da gwamna zai ba da cewa ba zai iya kare jama’a ba alhali ana kashe mutane kullum a jihar Zamfara. Mafara ya ce “abin da muke gani yanzu tamkar ciyar da ‘yan ta’adda daga gidan gwamnati ne. Wannan abin kunya ne ga sadaukarwar sojojinmu, kuma abin kunya ga gwamnati da ta gaza kare iyalai da sauran jama'ar da s**a rasa ‘yan uwansu a hannun ‘yan bindiga.”

Kungiyar ta kuma zargi gwamnan da zama bisa tsarin da ake wawushe kuɗaɗen kananan hukumomi, yayin da shugabannin kananan hukumomi ke zaune a Gusau maimakon yin hidima a yankunansu. Mafara ya bayyana furucin gwamnan a matsayin wata dabara ta karkatar da hankali daga gazawar gwamnatinsa da kuma tura laifin kan gwamnatin tarayya.

Saboda haka, kungiyar ZGGF ta goyi bayan kira da aka yi na gudanar da bincike daga hukumomin EFCC, DSS, da ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara kan tsaro, tare da binciken majalisar tarayya kan yadda gwamnan ke tafiyar da sha'anin tsaro da dukiyar jama’a.

Mafara ya ce idan binciken ya tabbatar da cewa Gwamna Lawal na da hannu wajen ba da dama ga ‘yan bindiga, to wajibi ne gwamnatin tarayya ta ɗauki matakin kafa dokar ta-baci domin dawo da zaman lafiya, tsari, da mutunci a jihar.

Ya ƙara da cewa “Jihar Zamfara ta zama filin zubar da jini a lokacin mulkin Gwamna Dauda Lawal. Ana kashe bayin Allah, ana rusa ƙauyuka, gonaki duk sun yi sabra, ba a iya nomawa. Ba za mu ci gaba da shan wahala yayin da gwamna ke buga siyasa da rayukan jama’a ba. Wannan kungiya za ta ci gaba da magana da muryar marasa ƙarfi har sai an ga an yi adalci.”

Kungiyar Arewa Forum ta yaba da jinjina ga shugaban hukumar NAIC Yazid Danfulani kan cikarsa kwanaki 100 a ofisKungiyar ...
15/09/2025

Kungiyar Arewa Forum ta yaba da jinjina ga shugaban hukumar NAIC Yazid Danfulani kan cikarsa kwanaki 100 a ofis

Kungiyar manoma ta Arewa Forum ta yaba wa shugaban hukumar inshorar noma ta kasa NAIC, Yazid Shehu Umar Danfulani, bisa abin da s**a bayyana a matsayin kyakkyawan farko a cikin kwanaki 100 na farko da ya yi a ofis.

Kungiyar ta lura cewa Danfulani ya shimfida sahihin jagoranci ga hukumar, yana daidaita shirye-shiryen NAIC da shirin noma na Renewed Hope na Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, wanda ya ba da fifiko kan samar da isasshen abinci, faɗaɗa noman rani da kuma inganta noma ta hanyoyin zamani.

A cikin wata sanarwa da aka fitar a Abuja, Shugaban ƙungiyar, Farfesa Hassan Muhammed, ya yaba da yadda Danfulani ya tunkari batun kawo sauyi a fannin noma, inda ya ambaci ƙoƙarinsa na farfaɗo da ƙarfin hukumar, ƙarfafa haɗin gwiwa da gwamnatocin jihohi, tare da jawo jarin kamfanoni masu zaman kansu cikin harkar noman rani da na damina da ma noma a zamance.

“Yazid Danfulani ya nuna cikin kwanaki 100 kacal cewa shugabanci da aka gina bisa hangen nesa da gaskiya na iya sake sanya hukumar NAIC a matsayin ginshiƙi wajen bunƙasar ƙasa,” in ji ƙungiyar.

“Himmarsa ta faɗaɗa filayen noman rani, tallafa wa manoma da kuma shigar da hanyoyin noma na zamani suna cike da daidaito da manufofin inganta noma na Shugaban Ƙasa Tinubu.”

Haka kuma, sun yaba da jajircewarsa kan gaskiya, ƙarfafa matasa da kuma ƙara wa mata shiga harkar noma, inda s**a nuna shirin horarwa da tallafa wa manoma da aka kaddamar a ƙarƙashin jagorancinsa.

A cewar shugabannin kungiyar Arewa Forum, gyare-gyaren da Danfulani ya fara sun riga sun ba manoma kwarin gwiwa tare da gina tubalin juyin juya halin noma na dogon lokaci a fadin Nijeriya.

Sun roƙe shi da ya ci gaba da ƙara ƙaimi ta hanyar faɗaɗa ayyukan hukumar NAIC a sassa shida na kasar nan, domin tabbatar da cewa al’ummomin karkara da ƙungiyoyin manoma sun amfana sosai daga noman rani da ci gaban noma a zamanance.

“Arewacin Nijeriya, da ma ƙasar baki ɗaya, na alfahari da nasarorin da Dr Yazid Danfulani ya cimmawa cikin wannan ɗan gajeren lokaci,” in ji sanarwar.

“Ƙoƙarin da ya fara na ba mu tabbacin cewa hukumar NAIC a ƙarƙashin jagorancinsa za ta taka muhimmiyar rawa wajen magance matsalar karancin abinci da kuma haɓaka samar da amfanin gona.”

Sakaci na karshe: Mutanen Zauma a karamar hukumar Bukuyum sun dora alhakin kara tabarbarewar tsaro a jihar Zamfara kan G...
15/09/2025

Sakaci na karshe: Mutanen Zauma a karamar hukumar Bukuyum sun dora alhakin kara tabarbarewar tsaro a jihar Zamfara kan Gwamna Dauda Lawal Dare.

Sani Salisu kabiria Zauma

Al’ummar yankin Zauma a karamar kukumar Bukkuyum ta Jihar Zamfara sun bayyana bacin rai da takaicin da suke ji bisa gazawar da ake ta gani ta Gwamna Dauda Lawal Dare wajen magance tabarbarewar tsaro a jihar. Sabon harin da aka kai a Birnin Zarma, inda ’yan bindiga dauke da muggan mak**ai s**a kai farmaki da asuba, s**a halaka mutum ɗaya, s**a raunata matarsa, sannan s**a yi awon gaba da mata da yara su 18, ya zama abin takaici kan yadda rayuwar al’ummar jihar Zamfara ta koma cikin halin tsaka mai wuya.

Shaidun gani da Ido sun bayyana cewa maharan sun kutsa ƙauyen ne da misalin ƙarfe 5:00 na asuba a lokacin da jama’a ke shirin tashi sallar asuba. Sun harbe mutumin nan har lahira, s**a jikkata matarsa, sannan s**a sa mata da yara fita daga ƙauyen cikin firgici da tashin hankali. Rahotanni sun nuna cewa maharan sun fito daga yankin Anka, inda suke da sansanoni a dazukan da ke kusa, s**a aiwatar da wannan mummunan aiki ba tare da sun samu wata tirjiya ba. Sojojin da ke Bukkuyum sun kasa ketarawa zuwa Birnin Zarma domin ba da ɗauki saboda ruwa ya kawo kogin da ya raba ƙauyukan babu kuma jirgin da zai iya ɗaukar su. Wannan ya sake bayyana irin ƙarancin shiri, dabaru da kuma jajircewar gwamnatin jihar wajen kare yankunan karkara masu rauni.

Abin da ya kara tsananta wannan ibtila’i shi ne shiru da rashin nuna halin ko in kula daga Gwamna Dauda Lawal Dare da gwamnatin sa. Tun bayan faruwar lamarin, gwamnan bai je duba waɗanda abin ya shafa ba, haka kuma bai aiko wakilin sa domin ya tausaya ko ya tsaya tare da iyalan da abin ya rutsa da su ba. Wannan sakaci ya nuna ba wai kawai rashin jagoranci ba ne, har ma da rashin tausayi ga al’ummar jihar Zamfara da ke cikin halin ƙunci. Al’ummomin Bukuyum da sauran yankunan jihar sun bar wa ƙaddara rayuwarsu, babu wani taimako daga gwamnatin jihar da aka zaɓa domin kare su.

Mutanen Zauma sun jaddada cewa rayuwa a Birnin Zarma da sauran ƙauyukan da ke kewaye na kara zama cikin wahala. Idan ba gwamnatin tarayya ta sa baki ba, rayuwa a yankunan nan za ta gagara gaba ɗaya. Gaskiya tana da daci, gwamnatin jihar Zamfara a ƙarƙashin Dauda Lawal Dare ta gaza cika kundin tsarin mulki na kare rayuka da dukiyoyin jama’a. Maimakon nuna jarumta, jajircewa da dabaru na musamman wajen kawo ƙarshen rashin tsaro, gwamnan ya ma manta da rayukan mutanen karkara.

Wannan sanarwa na zama gargadi da kuma roƙo a lokaci guda. Na farko, tana zargin Gwamna Dauda Lawal Dare da barin ƙauyuka irin su Birnin Zarma da Zauma a hannun ’yan bindiga da ke kashewa, yin garkuwa, satar dukiya da lalatata. Na biyu, tana roƙon Shugaba Bola Ahmad Tinubu da gwamnatin tarayya su gaggauta kawo agaji a Jihar Zamfara. Sai dai matakan gaggawa na gwamnatin tarayya ne kawai za su iya ba wa jama’ar Bukuyum, Anka, Gummi da sauran wuraren da abin ya shafa damar samun sauƙi daga hare-haren da s**a mayar da rayuwarsu tamkar mafarki mai ban tsoro.

Mutanen jihar Zamfara sun sha wahala ƙwarai. Kisa, garkuwa da mutane da tilasta jama’a yin hijira. Gwamnatin Dauda Lawal Dare ta nuna gazawa wajen kawo ƙarshen wannan ibtila’i. Saboda haka, wajibi ne gwamnatin tarayya ta yi gaggawar ɗaukar mataki kafin a share dukkanin ƙauyukan jihar daga doron kasa..

Rikon sakainar kashin da Gwamna Dauda ya yi wa bangaren kiwon lafiya ya sa ma'aikatan jinya na 'nas' tsunduma yajin aiki...
12/09/2025

Rikon sakainar kashin da Gwamna Dauda ya yi wa bangaren kiwon lafiya ya sa ma'aikatan jinya na 'nas' tsunduma yajin aiki a jihar Zamfara, in ji wata kungiya mai rajin tabbatar da shugabanci na gari

Ƙungiyar mai rajin tabbatar da shugabanci na gari mai suna Zamfara Good Governance Forum ta bayyana matsananciyar damuwa da ɓacin rai kan yajin aikin da kungiyar ma'aikatan jinya ta 'nas' a jihar Zamfara ta tsunduma, inda ta danganta lamarin kai tsaye ga rikon sakainar kashi da Gwamna Dauda Lawal Dare yake gudanarwa a sashen kiwon lafiyar jihar.

A cikin wata sanarwa da Sakatarenta, Kabiru Ibrahim Gusau ya sanya wa hannu, Ƙungiyar ta la’anci ware malaman jinya a asibitoci daga cikin sabon tsarin albashi da aka amince da shi, wanda aka aiwatar ne kawai ga likitoci, duk da roƙo da gargaɗin da aka yi akai-akai daga ɓangaren waɗanda abin ya shafa.

Ƙungiyar ta yi gargaɗin cewa irin wannan wariyar ba wai kawai tana keta mutuncin malaman jinya da sauran ma'aikatan lafiya ba, har ila yau tana jefa miliyoyin al’ummar Zamfara cikin haɗari, musamman a daidai lokacin da jihar ke fama da mummunar annobar kwalara wato amai da gudawa.

“Shirin gwamnatin na yin watsi tare da fifita likitoci kawai, babbar shaida ce ta amfani da mulki ba da gaskiya ba, kuma zalunci ne mai girma. Malaman jinya su ne ginshiƙin tsarin kiwon lafiyarmu, kuma yi musu wannan raini ba wai kawai rashin dattaku ba ne, illa ce kai tsaye ga rayukan al’ummarmu,” in ji Kabiru Ibrahim Gusau.

Ya ƙara da cewa rashin tausayi da nuna halin ko-in-kula na gwamnan yana jefa fannin kiwon lafiya na jihar Zamfara cikin hatsari. “A bayyane a fili, idan annobar kwalara ta ƙara muni kuma rayuka s**a salwanta sak**akon wannan yajin aiki, alhakin zai rataya ne a wuyan Gwamna Dauda Lawal Dare. Gazawarsa na gaggauta ɗaukar mataki cikin adalci cin amanar jama’ar da s**a ba shi amanar shugabanci ne,” in ji Gusau.

Ƙungiyar Zamfara Good Governance Forum ta yi kira ga Gwamna Dauda Lawal da ya gaggauta tsoma baki ta hanyar umartar Ma’aikatar Lafiya da ta gyara tsarin albashin da aka aiwatar cikin son rai, tare da haɗa malaman jinya a cikin biyan watan Satumba.

“Lokacin bayar da hujjoji ya wuce. Jama’ar jihar Zamfara ba za su iya jure rugujewar tsarin kiwon lafiya a daidai lokacin da aka fi bukatarsa ba. Dole ne Gwamna Lawal ya yi gaggawa yanzu, idan ba haka ba tarihi zai tuna da shi a matsayin mutumin da ya yi watsi da kiwon lafiyar jama'arsa a lokacin da s**a fi buƙatar sa,” in ji Kabiru Ibrahim Gusau.

Amincewa da gaza samar da tsaro da Gwamna Dauda ya yi a jihar Zamfara ta kara nunawa karara cewa ba zai iya kare rayuka ...
04/09/2025

Amincewa da gaza samar da tsaro da Gwamna Dauda ya yi a jihar Zamfara ta kara nunawa karara cewa ba zai iya kare rayuka da dukiyoyin al'ummar ba

Al'ummar jihar Zamfara sun shiga cikin firgici da takaici bayan maganar ban mamaki da gwamna Dauda Lawal Dare ya yi kwanan nan, inda ya rantse da Allah a fili cewa ya san maboyar kowane shugaban ’yan bindiga da ke a jihar Zamfara, kuma duk inda s**a shiga yana sane da su, ma'ana yana sane da dukkanin shige da ficensu. Wannan furuci ba kawai abin damuwa ba ne, amma babbar shaida ce da nuna hadin-baki da kuma gagarumar gazawar gwamnan wajen kare rayukan jama’ar da ba su ji ba, ba su gani ba.

Tsawon watanni, jihar Zamfara na fama da hare-haren ’yan bindiga masu dauke da mak**ai, wadanda ke kashe mutane, yin garkuwa, da tsoratar da jama’a kullum. Dubban mutane sun rasa matsugunansu, mata sun zama zawarawa, yara sun zama marayu, al’ummomi kuma na rayuwa cikin fargaba. A tsakiyar wannan azaba, gwamnan ya fito ya bayyana a zahiri cewa ya san inda mutanen da ke jagorantar wadannan manyan laifuka suke, amma bai dauki wani mataki ba don tabbatar da an k**a su da kawo su gaban shari’a.

Wannan babban cin amanar jama’a ne. Gwamna wanda ya san inda masu zubar da jinin bayin Allah suke amma ya ki daukar mataki, to ya zama cikin masu hannu a laifinsu. Maimakon ya hada kai da jami’an tsaro domin murkushe wadannan ’yan ta’adda, sai ya yi ikirarin cewa da saninsa, alhali jama’ar jihar Zamfara na ci gaba da shan wahala. Da bakinsa, gwamna Dauda Lawal Dare ya tuhumci kansa, tare da tabbatar da cewa gwamnatin sa ba ta da niyyar kawo karshen matsalar tsaro a jihar.

Wannan furuci abin cin zarafi ne ga iyalan wadanda s**a mutu sak**akon ta’addancin ’yan bindiga, saboda gwamna ya yi wadannan kalamai ne ba tare da daukar wani mataki na gaskiya ba. Haka kuma abin cin mutunci ne ga al'ummar jihar Zamfara wadanda s**a ba shi amanar mulki, amma ya mayar da shugabanci da yin shela marar amfani da maganganun banza. Shugabanci ba wai yin ikirari bane, shugabanci kare rayuka ne, tabbatar da adalci, da kawo zaman lafiya da tsaro ga jama’a ne.

Saboda haka muna kira ga hukumomin da abin ya shafa, jami’an tsaro, da ’yan Nijeriya masu kishin kasa su dauki mataki kan wannan mummunan kalami na Gwamnan da ya amince cewa ya gaza. Idan da gaske ya san inda shugabannin ’yan bindiga suke, to wajibi ne ya dauki mataki nan take don tabbatar da an k**a su kuma a gurfanar da su. Idan bai yi haka ba, to wannan hujja ce karara cewa yana kare miyagu ne a kan mutanen jihar.

Jama’ar jihar Zamfara sun cancanci zaman lafiya. Sun cancanci gwamnati da za ta kiyaye rayukansu, ba wadda za ta yi wasa da radadin da suke ciki ba. Amincewar Dauda Lawal Dare hujja ce mai karfi da ta tabbatar da cewa ya gaza wajen sauke nauyin da ke kansa a matsayin gwamna, kuma jihar Zamfara ba za ta iya jure karin shekaru na irin wannan gazawar shugabanci ba.

..Idan kura na da maganin zawo....to ta yi wa kanta....Daga, Salisu Aliyu Magami Idan har da gaske ne Kabiru Marafa na d...
04/09/2025

..Idan kura na da maganin zawo....to ta yi wa kanta....

Daga, Salisu Aliyu Magami

Idan har da gaske ne Kabiru Marafa na da karfin ikon hana Shugaba Tinubu kuri'u milyan 1, me ya sa ya gaza cin zaben Sanata a 2023? Maganar gaskiya Shugaba Tinubu ya ci zabensa, amma Kabiru Marafa ya sha kaye.

Maganganun da Kabiru Marafa ya yi kwanan nan na cewa zai yi aiki don ganin Shugaba Bola Ahmed Tinubu bai samu nasara a jihar Zamfara a 2027 ba, ba komai ba ne illa abin dariya da kuma nuna girman kai da cin amanar siyasa. Wannan kalamai cin mutunci ne ga wayewar jama’ar jihar Zamfara, wadanda kullum suke nuna biyayya ga jam’iyyar APC da shugabancinta. A fayyace komai yake, makomar jihar Zamfara tana hannun jama’arta, ba a hannun son zuciyar wani dan siyasa mara tasiri da ya riga ya rasa daraja ba.

Marafa, wanda yanzu yake ta ikirarin cewa shi ne “coordinator” din yakin neman zaben APC a jihar Zamfara a zaben da ya gabata, ya manta da gaskiya. ‘Yan Nijeriya sun sani cewa shugabancin APC tun da dadewa ya yanke hukunci cewa kowanne gwamna mai ci shi ne zai rike matsayin jagoran yakin neman zaben jam’iyya a jiharsa. A jihar Zamfara, wannan nauyi ya rataya a kan kafadun mai girma, Dr. Bello Mohammed Matawalle, MON, wanda ya samu nasarar tabbatar da APC ta yi galaba a jihar. Marafa ba shi da wani mukami a hukumance a wannan yakin neman zabe, kawai da tausayi irin na Matawalle ne ya ba shi wannan dama, amma babu ma wata gudunmuwa da ya bayar, ta hanyar saka shi cikin tsarin kyamfen. Marafa bai da wani tasiri a siyasance kuma tarihin zabubbukansa ya tabbatar da hakan.

Abin dariya, wai yaro ya tsinci hakori, wai a ce mutum da bai iya kare kujerarsa ta Sanata ba, duk da damar da ya samu, yanzu yana cewa zai iya hana Shugaba Tinubu sama da kuri’u miliyan daya a jihar Zamfara a 2027. Idan da gaske Marafa na da irin wannan karfin siyasa, me ya sa ya sha kaye a zabubbukansa na baya? Me ya sa bai iya samun amincewar jama’arsa lokacin da ya fi bukata ba? Gaskiya tana da sauki, tasirin Marafa ya tsaya ne kawai a bakinsa, ba a wajen masu kada kuri’a na jihar Zamfara ba.

Mafi muni kuma shi ne, Marafa ya fito yana zagin shugabanni masu daraja irin su Dr Bello Matawalle da Sanata Abdulaziz Yari. Wannan babban cin amanar siyasa ne, ganin cewa duk tushen siyasar Marafa ta hannun wasu ta fito. Kada a manta cewa Alhaji Ai Maradun ne ya fara shigar da Marafa siyasa ta jam'iyyar PDP, inda aka nada shi kwamishina. A wancan lokaci, Matawalle da Yari tuni sun kafa kansu a matsayin manyan jagorori a jihar Zamfara da ma wajen ta. Marafa dai ya hau kafadun wasu, amma yanzu ya juya yana neman yakusar wadanda s**a tallafe shi.

Maganganun banza na Kabiru Marafa ba hujjar da ke nuna yana da karfi ba ne, illa alamar rashin kwarin gwiwa. Mutum ne da yake kokarin neman a ci gaba da saninsa a tafarkin siyasar jihar Zamfara da ke ta canzawa. A yayin da nagartattun shugabanni irin su Bello Matawalle da Abdulaziz Yari ke ci gaba da samun mutunci, goyon baya da biyayya daga talakawa, Marafa ya koma wasan kwaikwayo irin na siyasa da barazanar banza.

Jama’ar jihar Zamfara sun cancanci shugabanni masu gaskiya, hangen nesa, da tarihi na nagarta, ba irin wadanda s**a dogara da cin amana, karya, da neman riba ta siyasa ba. Yayin da muke gab da 2027, APC a jihar Zamfara na nan daram a karkashin shugabancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, Rt. Hon. Bello Matawalle, da sauran nagartattun shugabanni masu kishin kasa, wadanda kullum ke bayar da gudummawa ga jama’a. Duk wani kazafi ko hayaniya daga ‘yan siyasa da s**a gaza, ba za ta taba girgiza wannan tsari ba.

Jihar Zamfara mallakin al'ummar ta ce, ba mallakin Kabiru Marafa ba.

Kwankwamin da Gwamna Dauda ya yi bayan PDP ta sha kaye a  zaben cike gurbin Kaura Namoda ta Kudu ya nuna karara yadda gw...
03/09/2025

Kwankwamin da Gwamna Dauda ya yi bayan PDP ta sha kaye a zaben cike gurbin Kaura Namoda ta Kudu ya nuna karara yadda gwamnatinsa ta gaza ta fuskar tsaro da yadda yake siyasantar da harkar a jihar

Irin kwankwamin da Gwamna Dauda Lawal Dare ya yi a kafafen watsa labarai, inda ya sake siyasantar da matsalar tsaron jihar, ya bayyana a fili zafin da jam’iyyarsa ta PDP ta ji, bayan kayen da ta sha a zaben cike gurbi na dan majalisar dokoki da aka kammala kwanan nan. Kamar yadda ya yi a zaben 2023, gazawar Gwamna Dauda ta sake fita fili wajen amfani da irin wahalhalun da al'ummar jihar Zamfara ke fama da su a matsayin domin yaudara, maimakon kawo ingantattun hanyoyin magance matsalolin da ke tunkarar jama'a.

Mutanen yankin Kaura Namoda ba su manta da alkawuran banza da ya yi a 2023 ba, lokacin da ya yi ikirarin cewa matsalar tsaro za ta kare cikin sati ɗaya ko biyu idan aka zaɓe shi. Yanzu fiye da shekara biyu da mulkinsa, matsalar tsaron ta ƙara ta’azzara. An rasa rayukan daruruwan mutane, iyalai da dama sun rasa matsugunnai, miliyoyin kuɗi aka karɓa daga hannun jama’a a matsayin kudin fansa, dukiyoyi masu daraja kuma sun salwanta. Duk da wadannan bala’o’i, Gwamna Dauda bai taɓa zuwa Kaura Namoda don jajanta wa waɗanda abin ya shafa ba, ko tsayawa tare da iyalan da ke cikin juyayi, b***e aika wakilin gwamnati don jajantawa.

Lokacin da aka sace mutum 53 a Banga, cikin karamar hukumar Kaura Namoda, ta jihar, Gwamna Dauda bai ce uffan ba, bai kuma mayar da hankali kansu ba. Lokacin da aka yi garkuwa da mutane a Kurya, Sabon Gari, Jimrawa, Kimadira, Kidaba, Sakajiki da Dan Isa, shiru ya yi, babu abin da ya ce k**ar dai an aiki bawa garinsu. Lokacin da ya je Kaura Namoda shi ne lokacin yaƙin neman zaɓen cike gurbi, ko a haka ma, bai je yankunan Galadima Dan Galadima, Dan Kaba, Kunkurki da Gabaki saboda babu su a jerin wuraren da za a yi zaɓe. Wannan ya tabbatar da cewa ya fi daraja kuri’u sama da rayukan al’ummarsa.

Wani ɗan asalin Kaura Namoda, Malam Yusuf Ibrahim, ya bayyana takaicinsa da ɓacin rai, inda ya ce, “Mun rasa ‘yan’uwanmu 53 a Banga, amma Gwamna bai zo ba. Mun yi juyayi mu kaɗai. Amma da aka tashi yin zaɓe, sai gashi ba kunya ba tsoron Allah ya yi gaggawar zuwa yaƙin neman zaɓe. Wannan ba shugabanci ba ne, cin amanar jama’a ne.”

Wata mata mai suna Aisha daga Sabon Gari, wadda ta rasa mijinta a hannun ‘yan bindiga, ta ce, “Mun zata Gwamna zai tsaya tare da mu, amma ya bar mu cikin kuka, juyayi da alhini. Ba mu samu taimako daga gwamnati ba, makwabta ne kaɗai s**a tsaya da mu a lokacin alhini. An watsar da mu.”

A yau, al'ummar Kaura Namoda sun tilasta kulla sulhu da ‘yan bindiga don samun zaman lafiya na wucin gadi. Wannan abin kunya ne daga gwamnatin da ta gaza kare rayukan al'ummarta.

Ta hanyar siyasantar da batun tsaro, an yi walkiya an gano inda Dauda Lawal Dare, ya dosa. Mulkinsa ya zama na gaba-gaba wajen karya alkawura, fifita abubuwan banza da watsi da waɗanda s**a ba shi amana.

Mutanen jihar Zamfara sun cancanci wanda ya damu da rayuwarsu, ba Gwamna mayaudari ba. Kwankwamin da Dauda Lawal Dare ya sake tabbatar da gazawarsa, rashin tausayi da kuma son kai na mulki fiye da kula da jin daɗin jama’arsa.

Al'ummar yankin karamar hukumar Gummi sun soki Gwamna Zamfara Dauda kan gazawa wajen samar da tsaro bayan hadarin kwale-...
01/09/2025

Al'ummar yankin karamar hukumar Gummi sun soki Gwamna Zamfara Dauda kan gazawa wajen samar da tsaro bayan hadarin kwale-kwale

Al'ummar yankin karamar hukumar Gummi a jihar Zamfara sun bayyana tsananin fushi, da Allah wadai da gwamnatin Gwamna Dauda Lawal Dare a jihar Zamfara, sak**akon mummunan hadarin kwale-kwale da ya auku a Nasarawar Kifi ranar 29 ga Agusta, 2025. Wannan hadari ya yi sanadin mutuwar akalla mutane 16, ciki har da mata bakwai da yara hudu.

Wannan hadarin dai faru ne a yayin da jama’a ke tserewa daga harin ‘yan bindiga da s**a kawo musu farmaki a kauyukansu. Har yanzu ana cigaba da neman karin mutanen da s**a bace.

A cikin wata sanarwa, shugabannin al’umma da mazauna yankin sun bayyana cewa wannan mummunar masifa ta samo asali ne daga gazawar gwamnan wajen cika alkawuran da ya dauka a lokacin kamfen, da kuma kasa samar da tsaro ga jama’ar jihar Zamfara.

Sun tunasar da gwamnan cewa kafin zaben 2023, Gwamna Dauda Lawal ya kai ziyara Gummi inda ya yi alkawarin kawo karshen matsalar tsaro a yankin. “Wannan alkawari ne ya baiwa mutanenmu kwarin guiwa, kuma ya kasance babban dalilin da ya sa muka zabe shi. Amma abin takaici tun bayan hawansa kan mulki, Dauda Lawal ya juya mana baya. Duk da wannan ba sh ne karon farko da aka samu rasa rayukkan mutane saboda kifewar kwale-kwale a gumin ba. Amma hakan bai sa gwamnan ya taka Gummi ba domin ganin irin wahalhalunmu, bai turo wakilin gwamnati don ta’aziyya ga iyalan da s**a yi rashi ba, bai kuma yi wani abu mai gamsarwa wajen kare rayuwarmu da garuruwanmu ba,” in ji shugaban al’umma, Lukman Ibrahim Gummi.

Ibrahim Gummi ya kara da cewa wannan sakaci bai tsaya Gummi kadai ba, har da sauran kananan hukumomin da ke fama da hare-haren ‘yan bindiga k**ar Bukkuyum, Anka, Maru, Zurmi da Shinkafi. Ya nuna bakin ciki da cewa duk da tsanantar lamarin, gwamnan bai taba ziyartar ko daya daga cikin wuraren ba tun bayan darewarsa kan mulki.

“Abin da jihar Zamfara ta gani a mulkinsa shi ne rashin kulawa mai tayar da hankali. Yayin da matanmu da yaranmu ke nutsewa cikin ruwa suna gudun ‘yan bindiga, shi kuma gwamna yana gaggawar zuwa Kauran Namoda domin tarurrukan siyasa. Wannan ya nuna a fili abin da yake fifita siyasa da mulki na gabansa, rayuwar talakawa kuma ba ta da muhimmanci a wurinsa,” in ji Ibrahim Gummi.

Mazauna yankin sun soki abin da s**a kira “wannan rashin tausayi da kuma rashin kishi” daga gwamnan, suna mai jaddada cewa jagoranci na nufin daukar alhaki, tausayi da aiki, ba wai alkawuran banza na kyamfen ba. Sun ce shiru da gwamnatin jihar ta yi bayan hadarin jirgin ruwa ya sake tabbatar da cewa bata damu da rayuwar jama’a ba.

“Ba wannan ne karo na farko da muke binne ‘yan'uwanmu sak**akon rashin tsaro ba, amma wannan ne karo na farko da muke fuskantar gwamnati da ta dauki shiru da rashin bayyana kaico da wani katabus a duk lokacin da hakan ta faru a wurin al'umma. An bar jama’a cikin bakin ciki da kadaici, yayin da wadanda s**a rantse da kare mu suke kauda kai. Wannan gazawa abin kunya ce, ba za mu amince da ita ba, kuma ba za ta ci gaba ba,” in ji mazaunan.

Haka kuma sun roki hukumomin tsaro da gwamnatin tarayya da su gaggauta daukar mataki don kubutar da al’ummomin jihar Zamfara daga wannan halin ha'ula'i da suke ciki. A cewarsu, idan gwamnatin jihar a karkashin Dauda Lawal ta ci gaba da wannan sakaci, rayuwar duka al’ummomin na cikin hadari.

“Mutanen Gummi da sauran kananan hukumomin da abin ya shafa ba za su sake lamuntar da a dauke su a matsayin wadanda za a yi watsi da rayuwarsu ba. Muna bukatar daukar mataki na gaggawa, matakan tsaro masu karfi, da kuma kasancewar gwamnati kai tsaye a cikin al’ummominmu. Mutanenmu sun cancanci su rayu cikin mutunci da zaman lafiya, ba cikin tsoro da watsi ba,” in ji Lukman Ibrahim Gummi a karshe.

Matawalle ya sake jaddada goyon bayan Nijeriya ga hadin guiwar nahiyarMinistan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya Dr Bell...
29/08/2025

Matawalle ya sake jaddada goyon bayan Nijeriya ga hadin guiwar nahiyar

Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya Dr Bello Muhammad Matawalle, ya tabbatar da cewa kasar za ta ci gaba da mara baya ga hadin kan nahiyar Afrika a yunkurin samar da zaman lafiya da tsaro.

Da yake jawabi a Abuja, yayin bikin girmamawa da aka shirya wa mahalarta taron shugabannin hafsoshin tsaron Afrika na shekarar 2025, ministan ya ce hadin kai da kuma aiki tare sune manyan ginshikan nahiyar wajen yaki da matsalolin tsaro.

A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Ahmad Dan-Wudil, ya fitar a ranar Alhamis, Matawalle ya ce: “A daren yau ba don yaki muka taru ba, sai don murna da biki. Mun zo ne domin tunawa da irin dogon zangon da muka ci, girmama sadaukarwar da muka yi don zaman lafiya, da kuma tunasar da kanmu irin aikin da ya rage wajen gina nahiyar Afrika mai aminci.”

An gudanar da taron daga ranar 25 zuwa 27 ga watan Agusta, inda ya hada shugabannin tsaro daga sassan nahiyar.Tattaunawar ta mayar da hankali kan tsaron iyakoki, yaki da ta’addanci, tsaron teku da kuma amfani da sabbin fasahohi a ayyukan soji.

Matawalle ya yaba wa hafsoshin da s**a halarci taron bisa abin da ya kira jajircewarsu wajen kare mulkin kasashe da kuma tabbatar da daidaito a yankin. Ya ce zuwansu Nijeriya alama ce ta zumuncin da ke tsakanin kasashen Afrika.

Ya kara da cewa “Tare za mu iya gina Afrika inda kowane ɗan kasa zai rayu cikin tsaro da mutunci.” Ministan ya bukaci shugabannin tsaro su rungumi hadin kai tare da tsayawa kan dabi’un dimokradiyya, adalci da mutunta hakkin ɗan'adam.

Taron ya kuma tattauna hanyoyin karfafa hulda tsakanin farar hula da soji, musamman wajen sayen kayan inganta tsaro da harkar sufuri. Mahalarta taron sun jaddada muhimmancin hadin guiwar yankuna wajen tabbatar da tsaron manyan ruwan tekun Afrika.

Matawalle ya daga tare da jijjiga wani kofi a matsayin addu’ar samun nahiyar da za ta kasance cikin zaman lafiya, inda ya roki shugabannin tsaron su ci gaba da rike zumuncin da s**a kulla a taron. “Allah ya sa hadin gwiwar da muka yi a nan ya samar da sak**ako fiye da wannan taron,” in ji shi.

Ministan Tsaro Matawalle ya yi kira da a rungumi fasahar zamani wajen yaki da ta’addanciMinistan kasa a ma'aikatar tsaro...
26/08/2025

Ministan Tsaro Matawalle ya yi kira da a rungumi fasahar zamani wajen yaki da ta’addanci

Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya Bello Matawalle, ya yi kira da a rungumi amfani da fasahar zamani don yaki da ta’addanci da sauran matsalolin tsaro da s**a addabi nahiyar Afrika.

Matawalle ya bayyana haka ne a Abuja, yayin bude taron shugabannin hafsoshin tsaro na Afrika, inda ya ce dole Afrika ta rungumi kirkire-kirkire domin magance abin da ya bayyana da “manyan barazanar tsaro masu tsanani kuma masu ci gaba da sauyawa.”

“Wadannan kalubale suna da sarkakiya, suna da nasaba da kasashe da dama, kuma suna kara zama daban da na baya. Magance su ba kawai yana bukatar juriya ba ne, har ila yau yana bukatar hadin gwiwa mai karfi a tsakanin kasashen nahiyar,” in ji shi.

A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Ahmad Dan-Wudil, ya sanya wa hannu, aka kuma raba wa manema labarai a ranar Talata, ministan ya jaddada cewa kasashen Afrika ba za su iya dogara kacokam da tsoffin hanyoyin ba wajen shawo kan kungiyoyi masu tayar da kayar baya.

Ya bukaci kasashen su zuba jari a fannin sabbin fasahohi, ciki ha fasahar zamani ta AI da kariyar tsaro ta yanar gizo (Cyberdefence), domin tunkarar kungiyoyi irin su Boko Haram, ISWAP, Al-Qaeda da Al-Shabaab.

“Hanyoyim gudanar da yaki nan gaba za su kasance na zamani. Mu a matsayin ministocin tsaro, dole mu zuba jari a fannin fasahohin zamani, kariyar tsaro ta yanar gizo, da fasahohin soja na cikin gida,” in ji Matawalle ga mahalarta taron.

Ya nuna cewa Nijeriya ta dade tana taka muhimmiyar rawa a harkokin zaman lafiya na yankin, yaki da ta’addanci da kuma ayyukan jin kai, sannan ta ci gaba da jajircewa wajen karfafa hadin gwiwar tsaro a nahiyar.

Matawalle ya yi gargadin cewa babu wata kasa guda daya da za ta iya shawo kan matsalolin tsaron Afrika ita kadai, yana mai jaddada bukatar hadin kai, samar da bayanan sirri da kuma amincewa tsakanin cibiyoyin tsaro.

“Afrika ba kawai za ta tsaya ne wajen bin sahun duniya ba, dole mu kasance a gaba wajen tsara makomar wadannan abubuwa,” in ji shi.

Address

Gusau
900271

Opening Hours

Monday 09:00 - 17:00
Tuesday 09:00 - 17:00
Wednesday 09:00 - 17:00
Thursday 09:00 - 17:00
Friday 09:00 - 17:00
Saturday 09:00 - 17:00

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jaridar Shaho posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share