Jaridar Shaho

Jaridar Shaho Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Jaridar Shaho, Media/News Company, Gusau.

Shinkafi Youth Mobilization Forum Ta Gabatar da Forms Ga Mata 110 a Sabon BirniSabon Birni, Sokoto — Ƙungiyar Shinkafi Y...
08/09/2026

Shinkafi Youth Mobilization Forum Ta Gabatar da Forms Ga Mata 110 a Sabon Birni

Sabon Birni, Sokoto — Ƙungiyar Shinkafi Youth Mobilization Forum ta kai Forms ga shugabannin Jam’iyyar APC a Ƙaramar Hukumar Sabon Birni, a wani sabon shiri na tallafa wa mata 110 da horar da su kan sana’o’in hannu domin ƙarfafa dogaro da kai da inganta rayuwar iyalai.

Shirin, wanda ƙungiyar APC Youth Mobilization Forum Shinkafi ke jagoranta, na da nufin bai wa mata damar samun ƙwarewar sana’o’in hannu da za su iya amfani da su wajen samar da kuɗin shiga, rage tasirin talauci, da kuma inganta walwalar iyalansu da al’umma baki ɗaya.

A cewar ƙungiyar, wannan shiri na daga cikin shirye-shiryen da take gudanarwa domin tallafa wa mata da matasa, tare da ƙarfafa haɗin kai da haɗin gwiwa a tsakanin al’umma.

Haka kuma, ƙungiyar ta bayyana cewa shirin na daga cikin ƙoƙarinta na nuna goyon baya ga tafiyar Alhaji Umaru Ajiyan Sokoto, musamman a ƙoƙarinsa na neman wakiltar al’ummar Sokoto ta Gabas a Majalisar Dattawa.

Ana sa ran cewa nan ba da daɗewa ba, ƙwararrun masu koyar da sana’o’i za su fara horar da matan 120 da s**a karɓi Forms, domin ba su ilimi da ƙwarewar da za su taimaka musu wajen inganta rayuwarsu da ta iyalansu.

Ƙungiyar ta bayyana fatan cewa shirin zai samar da kyakkyawan sak**ako, tare da buɗe sabbin damar tattalin arziki ga mata a yankin.

A ƙarshe, ƙungiyar Shinkafi Youth Mobilization Forum ta yi addu’ar Allah Ya sanya shirin ya zama sanadin alheri, ci gaba da sauƙin rayuwa ga waɗanda aka shirya tallafa wa, tare da ba wa masu gudanar da shirin ikon ci gaba da irin waɗannan ayyuka cikin nasara da aminci.

Shinkafi Youth Mobilization Forum

08/09/2026

DOLE NE MA'AIKATAN ZAMFARA SU BIYA BASHI YAZAMA WAJIBI KUMA TILAS DUK WANI MA'AIKACIN ZAMFARA YA ZABI GWAMNA DR DAUDA LAWAL A 2027.

Biyan Albashi kan kari
Biyan fansho kan kari
Karin Albashi ga ma'aikata
Kyakkawan yanayi na wurin ayukkanmu hujja ce ta sake zaben Gwamna DR DAUDA LAWAL kuma wajibi ne ga duk Ma'aikatan zamfara su bashi goyon baya _Inji COMRADE SANI HALLIRU Shugaban Kungiyar Kwadago ta jihar Zamfara a wata ziyara da s**a kaiwa Gwamna DR DAUDA LAWAL yau a fadar Gwamnati. Part 6

ALLAHU AKBAR: An Kammala Jana'iza Tareda Bizñe Gawàr Jarumar Fina Finan Hausa Ta Kannywood, Margayiya Zainab Zee Diamond...
08/09/2026

ALLAHU AKBAR: An Kammala Jana'iza Tareda Bizñe Gawàr Jarumar Fina Finan Hausa Ta Kannywood, Margayiya Zainab Zee Diamond Maman Bintalo Ta Shirin Labarina

Muna rokon Allah ya jikanta

08/09/2026

Lokacin da kuke gida a lokacin suna Daji domin kare Ƙasa da kakkaɓe Ƴan ta'adda

Dattijo Mai Shekaru 87 Ya Yanke Hannuwan Alƙali Da Adda A AdamawaWani abin mamaki ya faru a Kotun Yankin Mayo-Ine da ke ...
08/09/2026

Dattijo Mai Shekaru 87 Ya Yanke Hannuwan Alƙali Da Adda A Adamawa

Wani abin mamaki ya faru a Kotun Yankin Mayo-Ine da ke ƙaramar hukumar Fufore a jihar Adamawa, inda wani dattijo mai shekaru 87, Dahiru Garba, ya kai wa Alƙalin Kotun Yankin, Dauda Hamman, hari da adda har ya yanke masa hannuwansa.

Dahiru, ɗan ƙauyen Korawa da ke gundumar Mayo-Ine a ƙaramar hukumar Fufore, ya yi amfani da adda wajen kai wa Alƙalin hari ne a lokacin da yake sauraron shari’ar da ta shafe shi da wani mutum mai suna Ismail Yusuf.

Bayan k**a shi, an gurfanar da Dahiru a gaban Babbar Kotun Majistare ta Ɗaya da ke Yola a ranar Litinin. A lokacin da yake gaban kotun, dattijon ya ce “Shaiɗan ne ya jefa ni cikin wannan hali,” tare da nuna matuƙar nadama kan abin da ya aikata.

Kotun ta bayar da umarnin tsare shi a gidan gyaran hali da ke Yola bisa zargin haddasa mummunan rauni, wanda ya saɓa wa sashe na 219 na dokar Penal Code ta jihar Adamawa ta shekarar 2018.

ASP Zakka Musa ne ya gabatar da ƙarar farko ta ‘First Information Report’ (FIR), inda Dahiru ya amsa cewa shi ne ya aikata laifin.
Mai gabatar da ƙara ya bayyana cewa an tura batun daga hedikwatar ‘yan sanda ta Fufore zuwa sashen binciken manyan laifuka na jihar (SCID) a ranar 4 ga Satumba, 2026.

A cewar mai gabatar da ƙarar, Alƙali Dauda Hamman ya kai rahoto ofishin ‘yan sanda na Mayo-Ine a ranar 31 ga Agusta, 2026, yana cewa yayin da yake gudanar da shari’a, Dahiru Garba, wanda yake ɗaya daga cikin waɗanda ake ƙara, ya kai masa hari da adda.
Ya ƙara da cewa Dahiru ya rika sare hannuwan Alƙalin da addar sau da dama a lokacin da yake sauraron shari’ar da Ismail Yusuf ya shigar, lamarin da ya jikkata Alƙalin sosai.

Bayan an karanta masa bayanan tuhumar tare da fassara masa su a gaban kotun, Dahiru ya amince da aikata laifin.
Daga nan ne kotun da Babban Alƙali Majistare, Ismail Bello Shelleng, ke jagoranta ta bayar da umarnin ci gaba da tsare Dahiru a gidan gyaran hali, sannan ta ɗage sauraron shari’ar zuwa 17 ga Satumba, 2026, domin ci gaba da sauraron ƙarar.

DA DUMI-DUMI: Yar Gwagwarmaya Hauwa Farouk Ta Ƙaddamar da Ƙungiyar Mata Masu Tallata Shugaba TinubuYar gwagwarmaya Hauwa...
07/09/2026

DA DUMI-DUMI: Yar Gwagwarmaya Hauwa Farouk Ta Ƙaddamar da Ƙungiyar Mata Masu Tallata Shugaba Tinubu

Yar gwagwarmaya Hauwa Farouk Ibrahim ta ƙaddamar da sabuwar ƙungiyar Women of Influence for Tinubu 2027, wadda aka kafa da nufin haɗa kan mata masu tasiri daga sassa daban-daban domin tallata manufofin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ƙarfafa goyon bayansa gabanin zaɓen 2027.

Ƙungiyar ta fito da manufar samar da wani faffaɗan dandali da zai haɗa mata masu tasiri daga jihohin Arewa 19 da kuma Babban Birnin Tarayya Abuja, domin su haɗa ƙarfi, ilimi, ƙwarewa da tasirinsu wajen wayar da kan jama’a da kuma tallafa wa manufofin Shugaba Tinubu.

A cewar Hauwa Farouk, akwai buƙatar mata su ƙara haɗin kai, su tallafa wa juna, tare da amfani da damar da suke da ita wajen taka muhimmiyar rawa a harkokin siyasa da ci gaban ƙasa.

Ta bayyana cewa ƙungiyar za ta mayar da hankali wajen ƙarfafa mata, inganta jagoranci, wayar da kan jama’a, ƙarfafa haɗin kai da kuma shirya mata domin su taka muhimmiyar rawa wajen ganin nasarar Tinubu a zaɓen 2027.

Hauwa Farouk ta ce mata suna da muhimmiyar rawa wajen gina al’umma da kuma tsara makomar siyasa, tana mai cewa haɗa kan mata masu tasiri zai taimaka wajen samar da ingantaccen tsari na wayar da kan jama’a da tallafa wa shugabanci.

A cewarta, Women of Influence for Tinubu 2027 ta faɗaɗa zuwa jihohin Arewa 19 da Babban Birnin Tarayya Abuja, inda aka gina tsarin jagoranci daga matakin jiha zuwa ƙananan hukumomi.

Ƙungiyar za ta kuma samar da dama ga mata domin musayar ra’ayoyi, ƙarfafa juna da samar da haɗin gwiwa, tare da wayar da kan jama’a kan manufofin gwamnati da muhimmancin ci gaba da goyon bayan Shugaba Tinubu a 2027.

Hauwa Farouk Ibrahim, wadda ita ce National Convener ta ƙungiyar, ta bayyana cewa wannan tafiya za ta kasance bisa haɗin kai, jagoranci, ƙarfafa mata da kuma aiki tukuru domin ganin nasarar Shugaba Tinubu a zaɓen 2027.

Ta yi kira ga mata masu tasiri da kishin ci gaban al’umma da su haɗa hannu domin gina ƙungiya mai ƙarfi wadda za ta zama babbar murya wajen wayar da kan jama’a da kuma tallafa wa nasarar Shugaba Tinubu a zaɓen 2027.

Sponsored

07/09/2026

Sanarwa ta musamman daga Kwamitin yakin neman zaben Hon Aminu Garba Gusau Shattiman Gusau.

06/09/2026

KAI TSAYE DAGA FILIN BAJE KOLI, INDA AKE BAJE KOLIN YAN KASUWA

06/09/2026

Allah ka kara bawa jami'an tsaron nasara

Address

Gusau
900271

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jaridar Shaho posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share