
08/07/2025
Zauren kula da ilmi na jihar Zamfara ya yaba wa Matawalle da ya farfado bangaren ilmi a lokacin yana Gwamna duk da kudade kalilan da yake samu a lokacin
Zauren da ke sa ido don cigaban Ilimi a Zamfara Zamfara Education Forum ZEF ya yaba wa tsohon Gwamna kuma Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya, Dr Bello Mohammed Matawalle, bisa kokarinsa na farfado da harkar ilimi a jihar duk da karancin kudaden da aka samu a lokacin mulkinsa.
A cikin wata sanarwa da Shugaban zauren Yusuf Ibrahim Maradun, ya fitar a ranar Juma’a, ta bayyana yadda gwamnatin Matawalle a wancan lokacin ta samu gagarumar nasara karkashin tallafin gyaran makarantu na 2017/2018, inda aka gina azuzuwa 900 a sassa daban-daban na jihar cikin shekaru biyu kacal.
Ya ce karkashin jagorancin Matawalle, harkar ilimi ta samu sauyi da tagomashi mai ma’ana duk da cewa gwamnatin ta karbi kason kudi 'yan kaɗan daga asusun tarayya idan aka kwatanta da gwamnatin yanzu.
“Dr Matawalle ya sauya fasalin ilimi a jihar Zamfara da kudi 'yan kadan. Wannan abin shaida kuma abin a yaba ne na hangen nesa da jajircewa,” in ji Maradun.
Zauren ya kara da bayyana cewa ban da sabbin azuzuwa, an gyara azuzuwa 375 da s**a lalace, tare da sabunta ofisoshi uku na Hukumar Ilimi ta Ƙananan Hukumomi (LGEA).
Maradun ya ce gyaran wadannan ofisoshi ya taimaka wajen samar wa ma’aikata da muhallin aiki mai kyau, wanda hakan ya kara kwazo da ingancin aiki a fadin jihar.
Ya kwatanta hakan da gwamnatin yanzu da ke karɓar fiye da Naira bilyan 19 a kowane wata daga asusun tarayya, amma har yanzu ba ta iya yin ababen da za a iya gani kamar na Matawalle ba.
“Da Matawalle ne aka ba irin wannan adadin kudi, da tsarin ilimin jihar Zamfara ya zama abin koyi a Nijeriya,” in ji shi.
Yayin da lokacin zaben 2027 ke karatowa, Zauren ya yi kira ga al’ummar jihar Zamfara da su gane irin jagorancin da ke kawo ci gaba.
“Muna kira ga jama’a da su kare kuri'arsu kuma su goyi bayan Matawalle. Komawarsa kan madafun iko zai dawo da fata da ci gaba ga jihar Zamfara,” in ji sanarwar.