30/05/2026
Kungiyar Jajiyya, Mahaddatan Alƙur’ani da Wasu Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Tinubu Yayin Ziyarar Sallah ga Matawalle
Ministan Tsaro.
Bello Matawalle, ya sake jaddada aniyar gwamnatin Bola Ahmed Tinubu na dawo da zaman lafiya da tsaro a faɗin ƙasar nan, yana mai cewa ci gaba mai ɗorewa ba zai samu ba sai a cikin yanayi na kwanciyar hankali.
Matawalle ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis yayin da ya karɓi gaisuwar Sallah daga ƙungiyoyi daban-daban a gidansa da ke Maradun, Jihar Zamfara.
Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Mataimakinsa na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai, Ahmad Dan-Wudil, ya sanya wa hannu kuma aka rabawa manema labarai a Abuja ranar Asabar.
Tawagogin da s**a kai masa ziyarar sun haɗa da magoya bayan Jajiyya Movement, mahaddata da masu karatun Alƙur’ani, tsofaffin shugabannin jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), ƙungiyoyin siyasa da sauran masu ruwa da tsaki daga sassa daban-daban na jihar.
Daga cikin waɗanda s**a kai ziyarar akwai magoya baya daga Ƙaramar Hukumar Birnin Magaji, tawagar da ɗan majalisar dokokin jihar mai wakiltar mazaɓar Maradun II, Maharazu Salisu Faru, ya jagoranta, tsohon Kwamishinan Noma, Aminu Sulaiman Yarkufoji, Shugaban Ƙaramar Hukumar Maradun, Sanusi Ahmad Dosara, ƙungiyar mahaddata Alƙur’ani da kuma tsofaffin shugabannin PDP.
Da yake jawabi ga baƙin nasa, Matawalle ya bayyana gwamnatin Tinubu a matsayin gwamnati mai mayar da hankali wajen inganta rayuwar talakawan Najeriya.
Ya ce manyan ayyukan more rayuwa da gwamnatin tarayya ke aiwatarwa, musamman a Arewacin Najeriya, an tsara su ne domin rage wahalhalun tattalin arziki da kuma inganta hanyoyin sufuri da sadarwa.
A cewarsa, ayyuka kamar titin Zariya–Funtuwa–Gusau–Sakkwato, titin Sabon Birni–Lagos, titin Funtuwa–Kano da kuma titin Funtuwa–Katsina za su taimaka matuƙa wajen bunƙasa tattalin arziki da ci gaban al’umma.
Ministan ya kuma yi kira ga al’umma da su ci gaba da bai wa gwamnati goyon baya a ƙoƙarin da take yi na ƙarfafa zaman lafiya da tsaro a faɗin ƙasar nan.
Ya ce nasarar manufofin gwamnati na dogara ne da haɗin kan jama'a da masu ruwa da tsaki a kowane mataki.
“Manufar Renewed Hope Agenda ita ce fitar da jama’a daga talauci da kuma faɗaɗa ayyukan more rayuwa a faɗin ƙasa,” in ji shi.
Tun da farko, jagoran mahaddatan Alƙur’ani, Nura Isa Rara, ya yaba da jagorancin Matawalle tare da bayyana goyon bayan masu karatun Alƙur’ani na Zamfara ga nasarar gwamnatin Tinubu.
Haka kuma, tsohon Kwamishinan Noma, Dakta Aminu Sulaiman Yarkufoji, ya ce al’ummar Ƙaramar Hukumar Bakura na ci gaba da yaba wa Matawalle bisa ayyukan da ya gudanar lokacin da yake gwamnan jihar.
Shi ma Shugaban Ƙaramar Hukumar Maradun, Sanusi Ahmad Dosara, ya yabawa ministan kan rawar da yake takawa wajen yaƙi da matsalar ’yan bindiga a yankin.
A ƙarshe, Matawalle ya tabbatar wa tawagogin cewa gwamnatin tarayya za ta ci gaba da aiwatar da manufofin da za su inganta rayuwar ’yan Najeriya, musamman talakawa da marasa galihu.