Jaridar Shaho

Jaridar Shaho Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Jaridar Shaho, Media/News Company, Gusau.

Minti nawa ka ɗauka kafin ka gano banbanci ɗaya da ke jikin hotunan nan Biyu🤔
05/06/2026

Minti nawa ka ɗauka kafin ka gano banbanci ɗaya da ke jikin hotunan nan Biyu🤔

INEC da DSS sun fara binciken zargin fitar da bayanai daga rumbin bayanan masu zaɓeHukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa,...
03/06/2026

INEC da DSS sun fara binciken zargin fitar da bayanai daga rumbin bayanan masu zaɓe

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, (INEC), ta ce ta fara bincike kan zargin fitar da bayanan wani ɗan takara daga kundin rajistar masu kaɗa ƙuri’a (CVR), yayin da Hukumar Tsaro ta Farin Kaya, (DSS), ita ma ta fara nata binciken.

INEC ta bayyana cewa binciken farko ya nuna babu wani kutse daga waje ko harin na’ura mai kwakwalwa da ya shiga tsarin bayananta. Sai dai an samu damar shiga bayanan ne ta hanyar sahihan bayanan shiga da aka bai wa wasu jami’an rajistar masu zaɓe, amma aka fitar da bayanan ba tare da izini ba.

Hukumar ta ce ta gano asusun da aka yi amfani da shi wajen shiga bayanan, kuma tana binciken ko an karya dokokin tsaro da kariyar bayanai. Ta kuma tabbatar da cewa lamarin bai shafi bayanan sama da masu zaɓe miliyan 90 da ke cikin kundinta ba.

Sai dai ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya ce bayanin da INEC ta fitar ya ƙara haifar da tambayoyi fiye da amsoshi. Ya buƙaci a yi cikakken bincike domin gano yadda bayanan da ke cikin tsarin da aka killace s**a kai hannun wasu ‘yan siyasa.

Atiku ya ce rashin samun kutse daga waje ba ya rage girman lamarin, domin hakan na nuna yiwuwar matsalar ta fito daga cikin tsarin hukumar. Ya kuma yi maraba da binciken DSS, yana mai cewa dole ne a gudanar da shi cikin adalci ba tare da nuna son kai ba.

Takaddamar ta samo asali ne bayan mai taimaka wa Ministan Abuja kan harkokin yaɗa labarai, Lere Olayinka, ya wallafa bayanan rajistar zaɓe na fitaccen jarumin Nollywood, Emeka Ike. Jarumin ya yi zargin cewa an karya masa haƙƙin sirri, tare da barazanar ɗaukar matakin shari’a kan lamarin.

HANNUN KA MAI SANDA  Assalamu Alaikum Tare da girmamawa ga junan mu mabiya wannan Jam'iyya ta APC musammam marubuta dama...
02/06/2026

HANNUN KA MAI SANDA

Assalamu Alaikum

Tare da girmamawa ga junan mu mabiya wannan Jam'iyya ta APC musammam marubuta dama sauran magoya baya, Ina amfani da wannan dama in ankarar damu dimbin hadarin dake tattare da wannan wuta da muke kokarin rurawa tsakanin jagororin mu da kuma abinda zamu riska a lahira dama wannan duniyar.

Ina da tabbacin cewa wallahi wannan abin na rubuce rubuce da maganganu a cikin faya-fayin bidiyo babu abinda zai haifa muna daga karshe bayan nadama mai tarin yawa.

Mu sani cewa wadannan Jagorori da kuke labewa da sunan soyayyar su kuna aibata sashen su dukkan su suna bukatar juna a wurin nasarar bukatocin su musammam wannan Jam'iyya ta APC.

Da wannan nake rokon dukkan ya'yan wannan Jam'iyya a kowane bangare da su yiwa Girman ALLAH su daina wannan batanci ga Shugabannin mu.

Allah SWT Ya ganar damu Ya kuma bamu zaman lafiya.

Hon. Dr. Zannan Bungudu

Zaben 2027: Minista Matawalle da Sarkin Maradun Sun Jagoranci Addu’o’i Ga Tinubu.Ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Mohammed ...
02/06/2026

Zaben 2027: Minista Matawalle da Sarkin Maradun Sun Jagoranci Addu’o’i Ga Tinubu.

Ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Mohammed Matawalle, ya bayyana kwarin gwiwarsa cewa nasarorin da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai samu cikin wani wa’adin shekaru huɗu na gaba za su kai Najeriya matsayi mafi girma fiye da yadda gwamnatocin baya s**a taɓa yi.

Matawalle ya bayyana haka ne yayin wani taron addu’a na musamman da aka gudanar a Fadar Mai Martaba Sarkin Maradun da ke Jihar Zamfara bayan sallar Juma’a ta ranar 29 ga Mayu, 2026.

A cewar wata sanarwa da Mataimakinsa na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai, Ahmad Dan-Wudil, ya fitar, dubban jama’a ne s**a halarci taron inda s**a yi addu’o’i domin Shugaba Tinubu, zaman lafiya, ci gaban ƙasa da kuma nasarar gwamnatin da ke mulki.

Da yake jawabi a wajen taron, tsohon gwamnan Jihar Zamfara ya ce mutane da dama sun yi imanin cewa Allah ne Ya zaɓi Tinubu domin ya sake gina da kuma gyara Najeriya, yana mai cewa zuwansa mulki ya nuna burin al’umma na samun sauyi mai ma’ana a ƙasar.
Matawalle ya bukaci ‘yan Najeriya su ci gaba da yi wa ƙasa da shugabanninta addu’a, tare da yin addu’ar kariya daga duk wata makarkashiya ta cikin gida ko ta waje da ake kitsa wa Najeriya da Shugaban Ƙasa.

“Dole ne mu ci gaba da yi wa Najeriya addu’ar ci gaba tare da yin addu’a a kan duk wata makarkashiya da ake yi wa ƙasa da Shugaban Ƙasa. Babu wani abu mai muhimmanci da ake samu cikin sauƙi,” in ji shi.

Ministan ya jaddada muhimmancin addu’a wajen ci gaban ƙasa, yana mai bayyana ta a matsayin wata babbar hanya da ke jawo taimakon Allah cikin harkokin shugabanci da rayuwar al’umma.

Ya ce ‘yan Najeriya a sassa daban-daban na ƙasar na ci gaba da yi wa ƙasa da shugabanninta addu’a, yana mai nuna fatan cewa irin waɗannan addu’o’i za su haifar da sakamako mai kyau ga Najeriya.

“Yanzu ana ganin bambanci a tafiyar da gwamnati a Najeriya. A ƙarƙashin jagorancin Shugaba Tinubu, ƙasar na samun sauye-sauye masu kyau, tare da goyon bayan addu’o’in ‘yan Najeriya,” in ji Matawalle.

Shi ma da yake jawabi, Sarkin Maradun, Muhammad Garba Tambari, ya bayyana Tinubu a matsayin ni’ima ga Najeriya, tare da kira ga jama’a da su ci gaba da yi masa da kuma ƙasar addu’a.

Sarkin ya ce ci gaba da addu’a yana da muhimmanci domin samun shiriya daga Allah ga shugabanni da kuma dorewar zaman lafiya a ƙasa.

Ya kuma yi kira ga Musulmai a faɗin Najeriya da su ƙara himma wajen yin addu’a domin tsaro, kwanciyar hankali da haɗin kan ƙasa, tare da ƙarfafa gwiwar jama’a su mara wa gwamnati baya wajen magance ƙalubalen da ƙasar ke fuskanta.

Hakazalika, ya buƙaci ‘yan Najeriya su gudanar da ayyukansu cikin gaskiya da tsoron Allah, yana mai cewa irin waɗannan kyawawan halaye za su jawo taimakon Allah wajen shawo kan matsalolin tattalin arziki.

An kammala taron addu’ar ne da addu’o’i na musamman daga malamai, waɗanda s**a roƙi Allah Ya ba shugabanni hikima, kariya da jagoranci wajen gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

02/06/2026

Ina mamaki kana Dan APC ka fito karara ka ce za ka yi Anti-party ya kamata shuwagabanninmu na APC a Sanya ido ga irin wadannan yan Jam'iya tare da hukunta wadanda s**a shirya haka-Husaini Abubakar Tafkin-Gazai Magoyi Bayan APC a Zamfara

SIYASAR ZAMFARA: Da ni da Abdulaziz Yari duk wanda ya kira kansa shugaba sai dai in na mahaukata, amma APC guda ɗaya ce ...
02/06/2026

SIYASAR ZAMFARA: Da ni da Abdulaziz Yari duk wanda ya kira kansa shugaba sai dai in na mahaukata, amma APC guda ɗaya ce a Jihar Zamafara kuma gwamna Dauda Lawal shi ne shugabanta, In ji Minista Bello M. Matawalle.

Me zaku ce?

"Takarar Gwaman Zamfara ga Barista Mahdi Aliyu Gusau ba gudu ba ja da baya a ADC, talakawan ne s**a zabi ya yi takarar, ...
02/06/2026

"Takarar Gwaman Zamfara ga Barista Mahdi Aliyu Gusau ba gudu ba ja da baya a ADC, talakawan ne s**a zabi ya yi takarar, in ya jaye sai talakawan jihar sun tsine mashi albarka- Umar Aminu Gusau"

Baban hadimi Ga Mahdi Aliyu
Dan Takarar Gwamnan Zamfara a ADC

Hotuna:- Daga fadar Gwamnatin jihar Zamfara Inda  ake Gudanar da walima tare saukar Alqu’arni Mai girma domin murnar cik...
30/05/2026

Hotuna:- Daga fadar Gwamnatin jihar Zamfara Inda ake Gudanar da walima tare saukar Alqu’arni Mai girma domin murnar cikar gwamnatin Dr Dauda Lawal shekaru ukku (3) a mulkin jihar Zamfara.

Taron ya gudanane karkashin jagorancin shugaban kwamitin addinin musulunci na bikin cika shakaru 3 na Mai girma Gwamna Dauda lawal Malam Muhammad Bello isah Almufty

Kungiyar Jajiyya, Mahaddatan Alƙur’ani da Wasu Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Tinubu Yayin Ziyarar Sallah ga MatawalleMini...
30/05/2026

Kungiyar Jajiyya, Mahaddatan Alƙur’ani da Wasu Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Tinubu Yayin Ziyarar Sallah ga Matawalle
Ministan Tsaro.

Bello Matawalle, ya sake jaddada aniyar gwamnatin Bola Ahmed Tinubu na dawo da zaman lafiya da tsaro a faɗin ƙasar nan, yana mai cewa ci gaba mai ɗorewa ba zai samu ba sai a cikin yanayi na kwanciyar hankali.

Matawalle ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis yayin da ya karɓi gaisuwar Sallah daga ƙungiyoyi daban-daban a gidansa da ke Maradun, Jihar Zamfara.

Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Mataimakinsa na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai, Ahmad Dan-Wudil, ya sanya wa hannu kuma aka rabawa manema labarai a Abuja ranar Asabar.

Tawagogin da s**a kai masa ziyarar sun haɗa da magoya bayan Jajiyya Movement, mahaddata da masu karatun Alƙur’ani, tsofaffin shugabannin jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), ƙungiyoyin siyasa da sauran masu ruwa da tsaki daga sassa daban-daban na jihar.
Daga cikin waɗanda s**a kai ziyarar akwai magoya baya daga Ƙaramar Hukumar Birnin Magaji, tawagar da ɗan majalisar dokokin jihar mai wakiltar mazaɓar Maradun II, Maharazu Salisu Faru, ya jagoranta, tsohon Kwamishinan Noma, Aminu Sulaiman Yarkufoji, Shugaban Ƙaramar Hukumar Maradun, Sanusi Ahmad Dosara, ƙungiyar mahaddata Alƙur’ani da kuma tsofaffin shugabannin PDP.

Da yake jawabi ga baƙin nasa, Matawalle ya bayyana gwamnatin Tinubu a matsayin gwamnati mai mayar da hankali wajen inganta rayuwar talakawan Najeriya.

Ya ce manyan ayyukan more rayuwa da gwamnatin tarayya ke aiwatarwa, musamman a Arewacin Najeriya, an tsara su ne domin rage wahalhalun tattalin arziki da kuma inganta hanyoyin sufuri da sadarwa.

A cewarsa, ayyuka kamar titin Zariya–Funtuwa–Gusau–Sakkwato, titin Sabon Birni–Lagos, titin Funtuwa–Kano da kuma titin Funtuwa–Katsina za su taimaka matuƙa wajen bunƙasa tattalin arziki da ci gaban al’umma.

Ministan ya kuma yi kira ga al’umma da su ci gaba da bai wa gwamnati goyon baya a ƙoƙarin da take yi na ƙarfafa zaman lafiya da tsaro a faɗin ƙasar nan.

Ya ce nasarar manufofin gwamnati na dogara ne da haɗin kan jama'a da masu ruwa da tsaki a kowane mataki.

“Manufar Renewed Hope Agenda ita ce fitar da jama’a daga talauci da kuma faɗaɗa ayyukan more rayuwa a faɗin ƙasa,” in ji shi.

Tun da farko, jagoran mahaddatan Alƙur’ani, Nura Isa Rara, ya yaba da jagorancin Matawalle tare da bayyana goyon bayan masu karatun Alƙur’ani na Zamfara ga nasarar gwamnatin Tinubu.

Haka kuma, tsohon Kwamishinan Noma, Dakta Aminu Sulaiman Yarkufoji, ya ce al’ummar Ƙaramar Hukumar Bakura na ci gaba da yaba wa Matawalle bisa ayyukan da ya gudanar lokacin da yake gwamnan jihar.
Shi ma Shugaban Ƙaramar Hukumar Maradun, Sanusi Ahmad Dosara, ya yabawa ministan kan rawar da yake takawa wajen yaƙi da matsalar ’yan bindiga a yankin.

A ƙarshe, Matawalle ya tabbatar wa tawagogin cewa gwamnatin tarayya za ta ci gaba da aiwatar da manufofin da za su inganta rayuwar ’yan Najeriya, musamman talakawa da marasa galihu.

Address

Gusau
900271

Opening Hours

Monday 09:00 - 17:00
Tuesday 09:00 - 17:00
Wednesday 09:00 - 17:00
Thursday 09:00 - 17:00
Friday 09:00 - 17:00
Saturday 09:00 - 17:00

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jaridar Shaho posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share