
12/08/2025
JAM'IYAR PDP BA TA SAN MUTUNCIN YAYANTA. DA DARAJAR AL'UMMA BA- Ƙungiyar Yan Takarar kansila na PDP a Zamfara
Kungiya Sun tsofaffin yan takarar kansilolin zamfara na PDP ta yi kira ga jam'iyar PDP ta yi masu adalci ta dawo masu da kudadensu, na sayen form da ta yi masu alkawari tare da cika masu alkawarin da ta yi masu na yi masu supervisory kansila ko Sa, da kwangiloli da muk**ai . Amma har yanzu ba abin da aka yi masu.
Kungiyar ta bayyana cewa siyasa ce ake yi kuma ko yaushe neman al'umma ake yi ba korarsu ba. Don haka muna kira ga mai girma Gwamna da su dawo cikin. Hayacinsa ya taimaki al'umma inji shugaban kungiyar Buba Maigoro
Hon. Auwal Abdullahi Mairabi'a Gusau. Ya bayyana rashin jin dadinsa kan rashin biyan wasu daga cikin yan wannan ƙungiyar tasu. Don haka ya kara kira ga gwamna Dauda Lawal da fito ya taimaki yayan ƙungiyar ta su ta hanyar taimakonsu k**ar yadda ya yi alkawari. Wanda rasa su ga jam'iyar babbar illa ce ga PDP. Mairabi'a ya nuna rashin jin dadinsa da rashin cika dukkan alkawarin da aka yi masu
Hon.Tasi'u Abdullahi Gurusu, ya bayyana cewa duk da cewa an yi masu alkawari cewa za a mayar masa da kudinsa da aka yi masa alkawarin za abiya shi, har yanzu kusan shekara daya kenan ba a biya shi ba. Don haka Ya yi kira ga shugaban jam'iyar PDP Da ya ji tsoron Allah ya biya shi kudinsa ganin wahalar da ya sha wajen neman a biya shi kudinsa amma har yanzu dubu ɗari biyar kurrum aka ba shi saura miliyan daya da dubudari biyu da hamsin.
Gurusu ya kara da cewa Wadannan shuwagabannin jam'iyar PDP din ba su san mutuncin jam'iyar ba. Haka ba su san darajar al'ummarsu ba. Don haka ya yi kira ga gwamna Dauda Lawal da ya kafa kwamitin da zai taimake su.
Hon. Abdullahi Muhammad Gago ya yi kira ga mai daraja gwamna da ya ji tsoron Allah ya taimake su. Ganin cewa duk da alkawarin da ya yi masu har yanzu ba wani taimakon da ya yi masu.
Naziru Abdullahi Ɗankwangila ya yi kira ga gwamna Dauda Lawal ya ji tsoron Allah ya taimake su k**ar yadda s**a taimake shi. Ganin cewa babu wani mukarabinsa da ke taimakonsu. Ya kara da cewa don lada ake sallah in ba za a taimake su ba za su waiwaya wani wurin.