Bahsan online tv

Bahsan online tv Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Bahsan online tv, TV Channel, Zamfara, Gusau.

Bahsan Online tv kaface mai zaman kanta datake kawo maku labaran duniya da Rahotanni na gida da naketare, Muna tallata maku hajojinku da sauran shirye Shiryenku.

JAM'IYAR PDP BA TA SAN MUTUNCIN YAYANTA. DA DARAJAR AL'UMMA BA- Ƙungiyar Yan Takarar kansila na PDP a Zamfara Kungiya Su...
12/08/2025

JAM'IYAR PDP BA TA SAN MUTUNCIN YAYANTA. DA DARAJAR AL'UMMA BA- Ƙungiyar Yan Takarar kansila na PDP a Zamfara

Kungiya Sun tsofaffin yan takarar kansilolin zamfara na PDP ta yi kira ga jam'iyar PDP ta yi masu adalci ta dawo masu da kudadensu, na sayen form da ta yi masu alkawari tare da cika masu alkawarin da ta yi masu na yi masu supervisory kansila ko Sa, da kwangiloli da muk**ai . Amma har yanzu ba abin da aka yi masu.

Kungiyar ta bayyana cewa siyasa ce ake yi kuma ko yaushe neman al'umma ake yi ba korarsu ba. Don haka muna kira ga mai girma Gwamna da su dawo cikin. Hayacinsa ya taimaki al'umma inji shugaban kungiyar Buba Maigoro

Hon. Auwal Abdullahi Mairabi'a Gusau. Ya bayyana rashin jin dadinsa kan rashin biyan wasu daga cikin yan wannan ƙungiyar tasu. Don haka ya kara kira ga gwamna Dauda Lawal da fito ya taimaki yayan ƙungiyar ta su ta hanyar taimakonsu k**ar yadda ya yi alkawari. Wanda rasa su ga jam'iyar babbar illa ce ga PDP. Mairabi'a ya nuna rashin jin dadinsa da rashin cika dukkan alkawarin da aka yi masu

Hon.Tasi'u Abdullahi Gurusu, ya bayyana cewa duk da cewa an yi masu alkawari cewa za a mayar masa da kudinsa da aka yi masa alkawarin za abiya shi, har yanzu kusan shekara daya kenan ba a biya shi ba. Don haka Ya yi kira ga shugaban jam'iyar PDP Da ya ji tsoron Allah ya biya shi kudinsa ganin wahalar da ya sha wajen neman a biya shi kudinsa amma har yanzu dubu ɗari biyar kurrum aka ba shi saura miliyan daya da dubudari biyu da hamsin.

Gurusu ya kara da cewa Wadannan shuwagabannin jam'iyar PDP din ba su san mutuncin jam'iyar ba. Haka ba su san darajar al'ummarsu ba. Don haka ya yi kira ga gwamna Dauda Lawal da ya kafa kwamitin da zai taimake su.

Hon. Abdullahi Muhammad Gago ya yi kira ga mai daraja gwamna da ya ji tsoron Allah ya taimake su. Ganin cewa duk da alkawarin da ya yi masu har yanzu ba wani taimakon da ya yi masu.

Naziru Abdullahi Ɗankwangila ya yi kira ga gwamna Dauda Lawal ya ji tsoron Allah ya taimake su k**ar yadda s**a taimake shi. Ganin cewa babu wani mukarabinsa da ke taimakonsu. Ya kara da cewa don lada ake sallah in ba za a taimake su ba za su waiwaya wani wurin.

An ci zarafin al'ummarmu na Jimrawa a Gusau lokacin zanga-zangar matsalar tsaro.Aliyu Sani Jimrawa Mu al'ummar garin Jim...
09/08/2025

An ci zarafin al'ummarmu na Jimrawa a Gusau lokacin zanga-zangar matsalar tsaro.

Aliyu Sani Jimrawa

Mu al'ummar garin Jimrawa da ke Karamar Hukumar Kaura Namoda a Jihar Zamfara muna fuskantar daya daga cikin mafi muni a tashin hankali rayuwarmu. Shekaru da daya da rabi kenan tun da ‘yan bindiga s**a mamaye garinmu wanda a farko yake cikin zaman lafiya, s**a mai da gidajenmu filin yaki. A mummunan lamarin da ya fi kowane muni a baya-bayan nan, mazauna garinmu da dama an yi garkuwa da su,

An mamaye gidajenmu, gonakinmu sun lalace saboda an daina noma, kuma an rusa hanyoyin samun rufin asirin da muke bi domin mu rufa wa kanmu. A zahiri, ana neman goge Jimrawa a tarihi, amma gwamnatin Gwamna Dauda Lawal Dare ta ci gaba da kallon abin tana yin shiru don tana nuna k**ar ma babu abin da ya dame ta.

Saboda rashin jure irin wannan wahala, mu mazaunan muka yi tattaki zuwa Gusau, babban birnin jihar, a yunkurin karshe na jawo hankalin Gwamnati kan halin da muke ciki tare da neman daukar matakin gaggawa. Amma maimakon a tarbe mu da tausayawa da alkawuran zahiri, sai aka tarbe mu da tashin hankali. Akan turo yan sara-s**a s**a tarwatsa mu da karfin tuwo, suna bugun dattawa da yara. Abin da ya fi tayar da hankali, s**a bar mutane da dama da raunuka da tozarci. Yanzu haka wasu daga cikin wadanda aka ji wa raunuka suna asibiti ana jinyar su.

Dole ne a rike Gwamna Dauda Lawal Dare da alhakin wannan abin kunya da rashin imanin da aka nuna wa wajen kare mu Maimakon kare wadanda ke cikin rauni.Wannan ba shugabanci ba ne, wani sashe ne na cin amanar babban nauyin kare rayuka da dukiyoyin jama'a da ya dauka shi Gwamna.

Jama’ar jihar Zamfara na bukatar amsa. Me ya sa aka bar manoma da aka raba da matsugunansu ba tare da tallafi ba, kuma ba su iya komawa gonakinsu? Kuma me ya sa shugaban da aka zaba ta dimokuradiyya zai bari a ci zarafin masu zanga-zangar lumana, wadanda da yawa daga cikinsu dattawa da yara ne?

Muna yin Allah-wadai da kakkausar murya kan wannan sakacin da raina 'yancin dan'Adam. Gwamna Dauda Lawal Dare dole ne ya nemi afuwa ga mutanen Jimrawa nan take, ya ba da umarnin k**awa da gurfanar da wadanda s**a kai musu hari, Duk abin da zai yi idan ba wannan ba, zai tabbatar da abin da ke cikin zukatan mutane cewa a karkashin jagorancinsa jihar Zamfara ta zama jiha da rashin tsaro ya yi kaka-gida, kuma Gwamna ya rasa wani katabus.

'Yan sanda sun k**a mai fafutuka Omoyele Sowore wanda a baya bayan nan ya jagoranci zanga-zangar kyatata ratuwar tsaffin...
06/08/2025

'Yan sanda sun k**a mai fafutuka Omoyele Sowore wanda a baya bayan nan ya jagoranci zanga-zangar kyatata ratuwar tsaffin 'yan sanda kuma yayi fice wajen gwagwarmaya kwatarwa wadanda aka danne wa hakkinsu.

Omoyele dan jarida ne mammalakin jaridar Sahara Reporters wanda a baya yake zaune a kasar waje amma ya dawo gida Najeriya domin gwagwarmaya, ya kuma tsaya takarar shugaban kasa a lokuta da dama.

Kuma a 'yan kwanakin nan yayi ta sa'insa da rundunar 'yan sandan Najeriya inda ya ke zargin kakakin rundunar da aiko wani mutum da ya dauke masa tabaron idonsa mai ganin har hanji.

Sowore dan fafutuka ne da baya tsoran yi wa kowa hawan kawara, kuma yana da alaka ta kud da kud da lauyoyin da sauran 'yan gwagwarmaya inda a baya bayan nan ya a alaƙa da su Dan Bello da Abba Hikima

Aikin gyaran makabartu na Kabiru Maipalace kaskanci ne da cin fuska ne ga al'ummar Gusau Tsafe: Daga Sani Salisu Danjibg...
06/08/2025

Aikin gyaran makabartu na Kabiru Maipalace kaskanci ne da cin fuska ne ga al'ummar Gusau Tsafe:

Daga Sani Salisu Danjibga

Wannan abu da Hon. Kabiru Maipalace ya aikata abin takaici ne kuma abin kunya! Dan majalisa da ake zargin ya kasa yin katabus, yanzu kuma yana wasa da hankalin jama’ar Gusau da Tsafe ta hanyar daukar gyaran makabartu 80 a matsayin babban aikin mazaba wato 'Constituency Projects'. Wannan aikin ba wai kawai ya saba wa bukatun al’umma ba ne, har ma nuna rashin tunani da rashin tausayi ne a daidai lokacin da jama’a ke bukatar agajin gaggawa da zai cetar da rayukansu.

Jini na kwarara a jihar Zamfara, ‘yan bindiga na addabar al’umma, yara sun daina zuwa makaranta, asibitoci sun rushe, hanyoyi sun zama ramin mutuwa, kuma dubban iyalai na rayuwa cikin tsantsar talauci. A cikin wannan mawuyacin hali, Kabiru Maipalace yana ganin gyaran makabarta shi ne mafita ga jama’a? Wannan ba shugabanci ba ne, wannan cin fuska ne ga al'ummar Gusau da Tsafe da har yanzu ke da fatar samun shugabanci na adalci.

Abin da ya fi tayar da hankali shi ne, wannan Kabiru Maipalace din da ake magana akai na fuskantar bincike daga hukumomin EFCC, ICPC saboda zargin cin hanci, almundahana da amfani da ofis wajen cutar da al’umma. Ta yaya wanda ke cikin irin wannan zargi zai zo ya nuna ya damu da rayuwar jama’a ta hanyar zuba kudi a makabarta maimakon neman hanyoyin ceto rayuka?

Ya k**ata a fayyace: Gusau da Tsafe ba ta bukatar sabon fenti a kaburbura ko gyaran makabartu da aka lullube da sunan aikin mazaba. Abin da muke bukata shi ne shugabanni masu gaskiya, karfin hali, da zuciyar taimakon jama’a, domin ci gaba da wawashe dukiyar kasa ba.

Wannan ba kawai rashin amfani da kudin jama’a ba ne yadda ya dace, har ila yau, yana nuna rashin daraja ga mutane da ke da rai. Kabiru Maipalace dole ne ya girbi abin da ya shuka kuma ya wajaba ga al'ummar Gusau da Tsafe su farka su tunkari irin wannan shugabanci na yaudara da rashin amana da karfi da yaji.

03/08/2025
Sakon Taya Murna Kan Nadin Sarkin Gusau Na 16 – Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello Ƙungiyar Online TVs Proprietors Forum, k...
29/07/2025

Sakon Taya Murna Kan Nadin Sarkin Gusau Na 16 – Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello

Ƙungiyar Online TVs Proprietors Forum, karkashin jagorancin Comrade AbdulMalik Sa’idu (Mai Biredi), na mika sakon taya murna da fatan alheri ga Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello bisa nasarar da ya samu na zama Sarkin Gusau na 16, bayan rasuwar mahaifinsa, Marigayi Dr. Ibrahim Bello, wanda ya jagoranci masarautar Gusau cikin kwarewa da kima na tsawon shekaru goma.

Sabon Sarkin, wanda kafin nadin nasa yake da sarautar Bunun Gusau, ya fito daga zuriyar gidan sarauta na Malam Sambo Dan Ashafa, gida mai dogon tarihi na shugabanci da mutunci. Mun yi imani cewa wannan sabon nadin ya yi daidai da tanade-tanaden dokoki da kuma tsarin al’adar masarautar Gusau, tare da amincewar masu zaben sarki bisa sahihin tsari.

A madadin dukkan shugabanni da membobin wannan ƙungiya, muna fatan Allah ya ba sabon Sarki hikima, basira da ikon tafiyar da al’amuran masarauta cikin gaskiya da adalci, domin ci gaba da ɗorewar zaman lafiya da haɗin kai a Gusau da ma Zamfara gaba ɗaya.

Haka kuma muna yabawa Gwamnan Jihar Zamfara, Dr. Dauda Lawal, bisa sahihin jagoranci da goyon bayan da ya baiwa masarautar a lokacin wannan sauyi.

Comrade Nura Muhammad
Jami’in Hulɗa da Jama’a na ƙungiyar.

Address

Zamfara
Gusau

Telephone

+2349040067825

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Bahsan online tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Bahsan online tv:

Share

Category

Nearby media companies


Other Gusau media companies

Show All