
08/09/2025
Kungiyar Zamfara Good Governance Forum Ta yi Allah-wadai da yadda Gwamnan Dauda ke lalata dukiyar jama'a da siyasantar da matsalar tsaron jihar Zamfara
Kungiyar nan mai rajin tabbatar da shugabanci na gari wato Zamfara Good Governance Forum ta yi tir da kakkausar murya kan wasu kalaman da Gwamna Dauda Lawal Dare ya yi kwanan nan, inda ya bayyana cewa yana sane da inda ’yan bindiga suke, hanyoyin da suke bi da kuma maboyarsu.
Kungiyar ta bayyana wannan magana tasa a matsayin ta rashin tunani da raahin tausayi kuma abin kunya, inda ta ce idan har da gaske gwamnan yana da irin wannan muhimman bayanai, amma ya ki daukar mataki, hakan na nuni da gazawar shugabanci. Kungiyar ta jaddada cewa kare rayuka da dukiyoyin jama’a shi ne babban alhakin gwamna, don haka babu wani uzuri da zai dace a yi yayin da rayukan jama’a ke ci gaba da salwanta kullum.
Da yake jawabi a madadin kungiyar, sakataren ta, Kabiru Ibrahim Gusau, ya ce
“Idan Gwamna Dauda Lawal Dare na da sahihan bayanai kan inda ’yan ta’addar nan suke k**ar yadda ya yi ikirari, to me ya sa bai dauki mataki ba? Me ya sa bai mika bayanan ga jami’an tsaro domin su hallaka su ba? Sai kawai ya rika fakewa da cewa ba shi da ikon umartar sojoji ko ’yan sanda, alhali gwamnatinsa na kashe sama da Naira biliyan 3 a duk wata a kan tsaro. Ina kuɗin suke zuwa? Ana kashe mutanenmu, ana sace su, ana raba su da muhallansu, shi kuma yana siyasa da rayukan mutune.”
Kungiyar ta zargi gwamnan da rashin gaskiya, tana mai cewa da zarar jami’an tsaro sun yi nasara sai ya yi ta ikirarin cewa shi ne ya yi nasara, amma idan matsalar tsaro ta ta’azzara, shi ne farkon mai fara babatu a kafafen yada labarai yana maganganu na siyasa. Kungiyar ta ce hakan ya nuna cewa gwamnan ya fi sha’awar tallata kansa fiye da ceton rayuka.
Kungiyar ta tunatar da jama’a cewa kafin zaben 2023, Dauda Lawal ya yi kyamfe yana zargin tsohon gwamna Bello Matawalle da gazawa kan tsaro, tare da yin alkawarin kawo karshen ’yan bindiga cikin makonni biyu idan aka zabe shi. Sai dai fiye da shekaru biyu bayan hawan mulkinsa, matsalar tsaro ta kara tsananta, ana lalata kauyuka, hare-haren ’yan bindiga sun karu, kuma iyalai na ci gaba da rayuwa cikin tsoro.
Baya ga matsalar tsaro, kungiyar ta yi kakkausar s**a ga barnar kudade a gwamnatin Dauda. Kungiyar ta zarge shi da bayar da kwangiloli da sake bayar da su cikin tsada ta barna wadda ba ta kawo wani amfani ga jama’a, abin da ya haifar da asarar biliyoyin kudi da za a iya amfani da su wajen inganta ilimi, kiwon lafiya ko samar da ayyukan yi. Kungiyar ta kuma kawo misali da aikin filin jirgi, wanda a karkashin Matawalle aka tsara gudanar da shi kan kuɗin Naira bilyan 11.8 tare da kammala kashi 60%, amma Dauda ya sake bayar da kwangilar kan kuɗin Naira bilyan 62.9. Daga baya kuma ya kara wata Naira bilyan 30 a matsayin wasu sauye-sauye da jimillar kudin ta kai ta kai zuwa Naira bilyan 90.9, abin da s**a bayyana a matsayin dabara ta wawure kudaden jama’a da sunan ci gaba.
Kabiru Ibrahim Gusau ya ƙara jaddada cewa, “Wannan ba batun siyasa kawai ba ne, batun tseratar da rayukan mutane ne. Mutanen jihar Zamfara na cikin mawuyacin hali Maimakon Gwamna Dauda Lawal Dare ya yi shugabanci cikin tausayi, sai ya zaɓi yin siyasa da rayuwar mutanen da ba su ji ba su gani ba. Ya yi kyamfe da alƙawuran da bai cika ɗaya ba, yau kuma yana mulki da uzuri da yaɗa farfaganda, alhali jama’a na biyan kuɗin hakan da jinin su.”
Kungiyar Zamfara Good Governance Forum ta yi kira ga jama’a da su ƙi amincewa da yaudara su kuma nemi a riƙa dora wa gwamnan alhakin aiki na aikace-aikacen da ya gaza. Kungiyar ta bukaci hukumomin yaƙi da cin hanci, ƙungiyoyin farar hula da hukumomin tarayya da su binciki yadda ake yi wa kuɗaɗen jihar Zamfara rikon sakainar kashi.
“Mutanenmu sun cancanci zaman lafiya ba farfaganda ba. Sun cancanci kariya ba uzuri ba. Sun cancanci shugabanci ba wasa da siyasa ba. Dole ne a riƙa ɗora wa Gwamna Dauda alhakin siyasantar da rayukan da ya rantse zai kare,” in ji Gusau a ƙarshe.