Bahsan online tv

Bahsan online tv Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Bahsan online tv, TV Channel, Zamfara, Gusau.

Bahsan Online tv kaface mai zaman kanta datake kawo maku labaran duniya da Rahotanni na gida da naketare, Muna tallata maku hajojinku da sauran shirye Shiryenku.

03/10/2025
Ya zama wajibi hukumar kula da kasuwanci ta Zamfara Chamber of Commerce ta titsiye Gwamna Dauda Lawal har sai ya bayyana...
01/10/2025

Ya zama wajibi hukumar kula da kasuwanci ta Zamfara Chamber of Commerce ta titsiye Gwamna Dauda Lawal har sai ya bayyana gaskiyar inda aka kai Naira Biliyan 1.1 da aka ce na ’yan kasuwa ne a jihar

An bukaci hukumar kula kasuwanci, masana’antu, ma’adinai da aikin gona ta jihar Zamfara ZACCIMA da ta daina karkatar da zargi daga mai laifi a cikin badakalar karkatar da kudi fiye da Naira biliyan 1.1 da aka ware don tallafa wa kananan ’yan kasuwa a jihar.

Bisa umarnin gwamnatin jiha karkashin jagorancin Gwamna Dauda Lawan, an bukaci hukumar da ta tattara bayanan dukkan mambobinta domin samun wannan tallafi. Hukumar ZACCIMA ta gudanar da aikin cikin tsari inda ta mika bayanan fiye da ’yan kasuwa dubu ɗaya daga kananan hukumomi 14 na jihar. Amma abin takaici, daga baya da gwamnatin ta sanar da cewa an raba kudaden, ba a iya gano ko mutane goma daga cikin sahihan mutanen da s**a cika sharudda a matsayin waɗanda s**a ci gajiyar tallafin ba. Har ma ZACCIMA kanta ta kasa ambaton sunayen wadanda s**a amfana, abin da ya nuna an karkatar da tsarin rabon kudaden zuwa wata hanya ta daban.

Ya kamata hukumar ZACCIMA ta daina neman wanda za ta dora wa laifi, ta maida hankali kan Gwamna Dauda Lawal Dare da abokan aikinsa, ciki har da Barau da Mato, wadanda ake zargin sun karkatar da kudaden s**a raba wa mutanen da ba ma ’yan asalin jihar Zamfara ba. Wannan cin amanar mutane ce kuma mummunar gurgunta kokarin ’yan kasuwa masu neman ci gaban jihar Zamfara ne.

Muna kira da a gudanar da cikakken binciken gaskiya, a bayyane game da rabon wannan Naira biliyan 1.1. Dole ne hukumar ta wallafa jerin sunayen wadanda ta mika wa gwamnati da kuma wadanda ake cewa sun amfana da kudaden. Komai da ya gaza haka ba zai karbu ba a wajen dubban ’yan kasuwa sahihai da har yanzu suke jiran tallafin da bai kai gare su ba.

Ya kamata a tuna cewa kafin Bello Matawalle ya hau mulki a 2019, jihar Zamfara ce kadai jiha a Nijeriya da babu hukumar kula da 'yan kasuwa ta Chamber of Commerce da ke aiki yadda ya dace. Shi ne ya kafa ta a jihar, ya yi rajistarta da gwamnati, ya karfafa ta, ya kuma tabbatar da cewa ’yan kasuwa daga dukkan kananan hukumomi 14 sun amfana da tallafin gwamnati. Ya bayar da cikakken goyon baya ga ’yan kasuwa, abin da ya zama misalin shugabanci da ya fifita ci gaban tattalin arziki da karfafa ’yan kasuwa.

Don haka, ZACCIMA ya kamata ta daina kare masu mulki, ta jagoranci kira na neman lissafin keke-da-keke daga Gwamna Dauda Lawal Dare da gwamnatinsa. ’Yan kasuwar jihar Zamfara sun cancanci adalci, gaskiya da kuma tallafin da aka yi musu alkawari.

AKWAI SAKACIN GWAMNATI A HARIN MASALLACIN YANDOTO - MALAM MUSATsafe, Zamfara – Biyo bayan samun mummunan hari, ran 26 ga...
27/09/2025

AKWAI SAKACIN GWAMNATI A HARIN MASALLACIN YANDOTO - MALAM MUSA

Tsafe, Zamfara – Biyo bayan samun mummunan hari, ran 26 ga Satumba, inda wasu ƴan bindiga s**a kutsa cikin babban masallacin Yandoto, a karamar hukumar Tsafe ta jihar Zamfara, s**a bude wuta kan masu ibada a lokacin sallar Asuba, mazauna yankin sun fara tofa albarkacin bakin su.

Shaidu sun bayyana cewa akalla mutum biyar ne s**a rasa rayukansu a wajen, yayin da wasu kuma aka yi garkuwa da su. Lamarin ya jefa al’ummar yankin cikin firgici da alhini, inda aka ce jinin waɗanda s**a mutu ya bata dardumar masallaci.

Wani mazaunin yankin, Malam Musa Tsafe, wanda ya yi magana da manema labarai a madadin jama’ar Yandoto, ya bayyana cewa akwai alamun sakacin gwamnati, yana mai karawa da cewa harin ya girgiza su matuƙa. “Mutane sun rasa rayuka a gaban mahaliccinsu yayin da suke ibada. Wannan abin bakin ciki ne da ya bar yara da mata cikin tsananin tashin hankali,” in ji shi.

Ya ce al’ummar yankin na kira ga hukumomi da su dauki matakai na gaggawa wajen ƙara tsaro a Tsafe da kauyukan da ke makwabtaka. Ya kuma bukaci a gudanar da bincike kan yadda maharan s**a shigo masallaci ba tare da wani shamaki ba, tare da samar da taimako ga waɗanda abin ya rutsa da su.

A cewarsa, abin da jama’ar ke bukata a halin yanzu shi ne “kariya ta hakika daga jami’an tsaro, taimakon gaggawa ga wadanda s**a tsira, da kuma matakan doka da za su tabbatar da tsaro a nan gaba.”

Wannan hari, kamar yadda rahotanni s**a nuna, na cikin jerin hare-haren da ake ta kaiwa a yankin Tsafe da wasu sassan jihar Zamfara, wanda s**a hada da sace-sacen mutane da kuma kai farmaki a masallatai.

A halin yanzu, hukumomin tsaro ba su fitar da cikakken bayani kan lamarin ba, sai dai al’ummar Yandoto na kira da a dauki matakin gaggawa don dakile irin wannan tashin hankali da ke ci gaba da addabar jihar.

Ƙungiyar Shugabannin Kafafen Yaɗa Labarai na Yanar Gizo a Zamfara Ta Sayi Mota Don Sauƙaƙa AyyukaƘungiyar Shugabannin Ka...
20/09/2025

Ƙungiyar Shugabannin Kafafen Yaɗa Labarai na Yanar Gizo a Zamfara Ta Sayi Mota Don Sauƙaƙa Ayyuka

Ƙungiyar Shugabannin Kafafen Yaɗa Labarai na Yanar Gizo a Zamfara, mai suna Zamfara State Online TVs Proprietors Forum, ta sanar da siyan sabuwar mota domin sauƙaƙa zirga-zirga da inganta gudanar da ayyukanta a fadin jihar.

Yayin ƙaddamar da motar, Shugaban ƙungiyar, AbdulMalik Sa’idu Maibiredi, ya bayyana cewa wannan mataki wani shiri ne na ƙarfafa aikin ƙungiyar wajen tabbatar da yaɗa sahihan labarai cikin gaggawa.

Ya ce, matsalar sufuri ta dade tana kawo tsaiko ga ’yan jarida musamman a fagen kafafen zamani. Wannan mota, in ji shi, za ta taimaka wajen ɗaukar nauyin jigilar aiki, bayar da damar bin diddigin abubuwan da ke faruwa, da kuma isar da labarai cikin lokaci ga al’umma.

Maibiredi ya ƙara da cewa wannan nasara alama ce ta jajircewar ƙungiyar wajen bunƙasa aikin jaridancin zamani, tabbatar da gaskiya da kuma bayar da gudunmawa ga cigaban aikin jarida a Zamfara.

Ƙungiyar ta gode wa mambobinta bisa haɗin kai da jajircewa da ya kai ga cimma wannan buri, tare da sake jaddada kudirinta na ci gaba da bin ƙa’idojin aikin jarida na gaskiya.

Address

Zamfara
Gusau

Telephone

+2349040067825

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Bahsan online tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Bahsan online tv:

Share

Category