Bahsan online tv

Bahsan online tv Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Bahsan online tv, TV Channel, Zamfara, Gusau.

Bahsan Online tv kaface mai zaman kanta datake kawo maku labaran duniya da Rahotanni na gida da naketare, Muna tallata maku hajojinku da sauran shirye Shiryenku.

Kungiyar Zamfara Good Governance Forum Ta yi Allah-wadai da yadda Gwamnan Dauda ke lalata dukiyar jama'a da siyasantar d...
08/09/2025

Kungiyar Zamfara Good Governance Forum Ta yi Allah-wadai da yadda Gwamnan Dauda ke lalata dukiyar jama'a da siyasantar da matsalar tsaron jihar Zamfara

Kungiyar nan mai rajin tabbatar da shugabanci na gari wato Zamfara Good Governance Forum ta yi tir da kakkausar murya kan wasu kalaman da Gwamna Dauda Lawal Dare ya yi kwanan nan, inda ya bayyana cewa yana sane da inda ’yan bindiga suke, hanyoyin da suke bi da kuma maboyarsu.

Kungiyar ta bayyana wannan magana tasa a matsayin ta rashin tunani da raahin tausayi kuma abin kunya, inda ta ce idan har da gaske gwamnan yana da irin wannan muhimman bayanai, amma ya ki daukar mataki, hakan na nuni da gazawar shugabanci. Kungiyar ta jaddada cewa kare rayuka da dukiyoyin jama’a shi ne babban alhakin gwamna, don haka babu wani uzuri da zai dace a yi yayin da rayukan jama’a ke ci gaba da salwanta kullum.

Da yake jawabi a madadin kungiyar, sakataren ta, Kabiru Ibrahim Gusau, ya ce
“Idan Gwamna Dauda Lawal Dare na da sahihan bayanai kan inda ’yan ta’addar nan suke k**ar yadda ya yi ikirari, to me ya sa bai dauki mataki ba? Me ya sa bai mika bayanan ga jami’an tsaro domin su hallaka su ba? Sai kawai ya rika fakewa da cewa ba shi da ikon umartar sojoji ko ’yan sanda, alhali gwamnatinsa na kashe sama da Naira biliyan 3 a duk wata a kan tsaro. Ina kuɗin suke zuwa? Ana kashe mutanenmu, ana sace su, ana raba su da muhallansu, shi kuma yana siyasa da rayukan mutune.”

Kungiyar ta zargi gwamnan da rashin gaskiya, tana mai cewa da zarar jami’an tsaro sun yi nasara sai ya yi ta ikirarin cewa shi ne ya yi nasara, amma idan matsalar tsaro ta ta’azzara, shi ne farkon mai fara babatu a kafafen yada labarai yana maganganu na siyasa. Kungiyar ta ce hakan ya nuna cewa gwamnan ya fi sha’awar tallata kansa fiye da ceton rayuka.

Kungiyar ta tunatar da jama’a cewa kafin zaben 2023, Dauda Lawal ya yi kyamfe yana zargin tsohon gwamna Bello Matawalle da gazawa kan tsaro, tare da yin alkawarin kawo karshen ’yan bindiga cikin makonni biyu idan aka zabe shi. Sai dai fiye da shekaru biyu bayan hawan mulkinsa, matsalar tsaro ta kara tsananta, ana lalata kauyuka, hare-haren ’yan bindiga sun karu, kuma iyalai na ci gaba da rayuwa cikin tsoro.

Baya ga matsalar tsaro, kungiyar ta yi kakkausar s**a ga barnar kudade a gwamnatin Dauda. Kungiyar ta zarge shi da bayar da kwangiloli da sake bayar da su cikin tsada ta barna wadda ba ta kawo wani amfani ga jama’a, abin da ya haifar da asarar biliyoyin kudi da za a iya amfani da su wajen inganta ilimi, kiwon lafiya ko samar da ayyukan yi. Kungiyar ta kuma kawo misali da aikin filin jirgi, wanda a karkashin Matawalle aka tsara gudanar da shi kan kuɗin Naira bilyan 11.8 tare da kammala kashi 60%, amma Dauda ya sake bayar da kwangilar kan kuɗin Naira bilyan 62.9. Daga baya kuma ya kara wata Naira bilyan 30 a matsayin wasu sauye-sauye da jimillar kudin ta kai ta kai zuwa Naira bilyan 90.9, abin da s**a bayyana a matsayin dabara ta wawure kudaden jama’a da sunan ci gaba.

Kabiru Ibrahim Gusau ya ƙara jaddada cewa, “Wannan ba batun siyasa kawai ba ne, batun tseratar da rayukan mutane ne. Mutanen jihar Zamfara na cikin mawuyacin hali Maimakon Gwamna Dauda Lawal Dare ya yi shugabanci cikin tausayi, sai ya zaɓi yin siyasa da rayuwar mutanen da ba su ji ba su gani ba. Ya yi kyamfe da alƙawuran da bai cika ɗaya ba, yau kuma yana mulki da uzuri da yaɗa farfaganda, alhali jama’a na biyan kuɗin hakan da jinin su.”

Kungiyar Zamfara Good Governance Forum ta yi kira ga jama’a da su ƙi amincewa da yaudara su kuma nemi a riƙa dora wa gwamnan alhakin aiki na aikace-aikacen da ya gaza. Kungiyar ta bukaci hukumomin yaƙi da cin hanci, ƙungiyoyin farar hula da hukumomin tarayya da su binciki yadda ake yi wa kuɗaɗen jihar Zamfara rikon sakainar kashi.

“Mutanenmu sun cancanci zaman lafiya ba farfaganda ba. Sun cancanci kariya ba uzuri ba. Sun cancanci shugabanci ba wasa da siyasa ba. Dole ne a riƙa ɗora wa Gwamna Dauda alhakin siyasantar da rayukan da ya rantse zai kare,” in ji Gusau a ƙarshe.

06/09/2025
Shahararren ’dan ta’adda, Ado Aleru, ya kashe mayakansa bakwai a Zamfara bisa zarginsu da cin amana. Rahotanni sun nuna ...
04/09/2025

Shahararren ’dan ta’adda, Ado Aleru, ya kashe mayakansa bakwai a Zamfara bisa zarginsu da cin amana.

Rahotanni sun nuna cewa kashe-kashe sun faru a Takulawa, Turba, Bamamu da dajin Yamma, bayan da Aleru ya zarge su da aikata satar mutane ba tare da izini ba a kan hanyar Gusau – Yankara, abin da ya ce yana barazana ga iyakokinsa tare da jawo hankalin jami’an tsaro.

Wannan mataki nasa ya jefa tsoro da rashin jin daɗi cikin mabiyansa, inda ake ganin hakan alama ce ta karuwar rashin amincewa a cikin tawagar tasa.

Aleru, wanda Gwamnatin Tarayya ta ayyana shi a matsayin ’dan ta’adda da ake nema ruwa a jallo, ya dade yana da hannu a sace-sacen mutane, kisan kai da satar shanu a Zamfara, Katsina da wasu sassan Sokoto.

Duk da wannan mummunan tarihi, yana cikin tattaunawar sulhu da kwamitin gwamnatin tarayya yanzu domin kawo ƙarshen rikice-rikicen da ke addabar Arewa maso Yamma. Karanta rahoton Zagazola Mak**a a karkashin comment section.

Amincewa da gaza samar da tsaro da Gwamna Dauda ya yi a jihar Zamfara ta kara nunawa karara cewa ba zai iya kare rayuka ...
04/09/2025

Amincewa da gaza samar da tsaro da Gwamna Dauda ya yi a jihar Zamfara ta kara nunawa karara cewa ba zai iya kare rayuka da dukiyoyin al'ummar ba

Al'ummar jihar Zamfara sun shiga cikin firgici da takaici bayan maganar ban mamaki da gwamna Dauda Lawal Dare ya yi kwanan nan, inda ya rantse da Allah a fili cewa ya san maboyar kowane shugaban ’yan bindiga da ke a jihar Zamfara, kuma duk inda s**a shiga yana sane da su, ma'ana yana sane da dukkanin shige da ficensu. Wannan furuci ba kawai abin damuwa ba ne, amma babbar shaida ce da nuna hadin-baki da kuma gagarumar gazawar gwamnan wajen kare rayukan jama’ar da ba su ji ba, ba su gani ba.

Tsawon watanni, jihar Zamfara na fama da hare-haren ’yan bindiga masu dauke da mak**ai, wadanda ke kashe mutane, yin garkuwa, da tsoratar da jama’a kullum. Dubban mutane sun rasa matsugunansu, mata sun zama zawarawa, yara sun zama marayu, al’ummomi kuma na rayuwa cikin fargaba. A tsakiyar wannan azaba, gwamnan ya fito ya bayyana a zahiri cewa ya san inda mutanen da ke jagorantar wadannan manyan laifuka suke, amma bai dauki wani mataki ba don tabbatar da an k**a su da kawo su gaban shari’a.

Wannan babban cin amanar jama’a ne. Gwamna wanda ya san inda masu zubar da jinin bayin Allah suke amma ya ki daukar mataki, to ya zama cikin masu hannu a laifinsu. Maimakon ya hada kai da jami’an tsaro domin murkushe wadannan ’yan ta’adda, sai ya yi ikirarin cewa da saninsa, alhali jama’ar jihar Zamfara na ci gaba da shan wahala. Da bakinsa, gwamna Dauda Lawal Dare ya tuhumci kansa, tare da tabbatar da cewa gwamnatin sa ba ta da niyyar kawo karshen matsalar tsaro a jihar.

Wannan furuci abin cin zarafi ne ga iyalan wadanda s**a mutu sak**akon ta’addancin ’yan bindiga, saboda gwamna ya yi wadannan kalamai ne ba tare da daukar wani mataki na gaskiya ba. Haka kuma abin cin mutunci ne ga al'ummar jihar Zamfara wadanda s**a ba shi amanar mulki, amma ya mayar da shugabanci da yin shela marar amfani da maganganun banza. Shugabanci ba wai yin ikirari bane, shugabanci kare rayuka ne, tabbatar da adalci, da kawo zaman lafiya da tsaro ga jama’a ne.

Saboda haka muna kira ga hukumomin da abin ya shafa, jami’an tsaro, da ’yan Nijeriya masu kishin kasa su dauki mataki kan wannan mummunan kalami na Gwamnan da ya amince cewa ya gaza. Idan da gaske ya san inda shugabannin ’yan bindiga suke, to wajibi ne ya dauki mataki nan take don tabbatar da an k**a su kuma a gurfanar da su. Idan bai yi haka ba, to wannan hujja ce karara cewa yana kare miyagu ne a kan mutanen jihar.

Jama’ar jihar Zamfara sun cancanci zaman lafiya. Sun cancanci gwamnati da za ta kiyaye rayukansu, ba wadda za ta yi wasa da radadin da suke ciki ba. Amincewar Dauda Lawal Dare hujja ce mai karfi da ta tabbatar da cewa ya gaza wajen sauke nauyin da ke kansa a matsayin gwamna, kuma jihar Zamfara ba za ta iya jure karin shekaru na irin wannan gazawar shugabanci ba.

Al'ummar yankin karamar hukumar Gummi sun soki Gwamna Zamfara Dauda kan gazawa wajen samar da tsaro bayan hadarin kwale-...
01/09/2025

Al'ummar yankin karamar hukumar Gummi sun soki Gwamna Zamfara Dauda kan gazawa wajen samar da tsaro bayan hadarin kwale-kwale

Al'ummar yankin karamar hukumar Gummi a jihar Zamfara sun bayyana tsananin fushi, da Allah wadai da gwamnatin Gwamna Dauda Lawal Dare a jihar Zamfara, sak**akon mummunan hadarin kwale-kwale da ya auku a Nasarawar Kifi ranar 29 ga Agusta, 2025. Wannan hadari ya yi sanadin mutuwar akalla mutane 16, ciki har da mata bakwai da yara hudu.

Wannan hadarin dai faru ne a yayin da jama’a ke tserewa daga harin ‘yan bindiga da s**a kawo musu farmaki a kauyukansu. Har yanzu ana cigaba da neman karin mutanen da s**a bace.

A cikin wata sanarwa, shugabannin al’umma da mazauna yankin sun bayyana cewa wannan mummunar masifa ta samo asali ne daga gazawar gwamnan wajen cika alkawuran da ya dauka a lokacin kamfen, da kuma kasa samar da tsaro ga jama’ar jihar Zamfara.

Sun tunasar da gwamnan cewa kafin zaben 2023, Gwamna Dauda Lawal ya kai ziyara Gummi inda ya yi alkawarin kawo karshen matsalar tsaro a yankin. “Wannan alkawari ne ya baiwa mutanenmu kwarin guiwa, kuma ya kasance babban dalilin da ya sa muka zabe shi. Amma abin takaici tun bayan hawansa kan mulki, Dauda Lawal ya juya mana baya. Duk da wannan ba sh ne karon farko da aka samu rasa rayukkan mutane saboda kifewar kwale-kwale a gumin ba. Amma hakan bai sa gwamnan ya taka Gummi ba domin ganin irin wahalhalunmu, bai turo wakilin gwamnati don ta’aziyya ga iyalan da s**a yi rashi ba, bai kuma yi wani abu mai gamsarwa wajen kare rayuwarmu da garuruwanmu ba,” in ji shugaban al’umma, Lukman Ibrahim Gummi.

Ibrahim Gummi ya kara da cewa wannan sakaci bai tsaya Gummi kadai ba, har da sauran kananan hukumomin da ke fama da hare-haren ‘yan bindiga k**ar Bukkuyum, Anka, Maru, Zurmi da Shinkafi. Ya nuna bakin ciki da cewa duk da tsanantar lamarin, gwamnan bai taba ziyartar ko daya daga cikin wuraren ba tun bayan darewarsa kan mulki.

“Abin da jihar Zamfara ta gani a mulkinsa shi ne rashin kulawa mai tayar da hankali. Yayin da matanmu da yaranmu ke nutsewa cikin ruwa suna gudun ‘yan bindiga, shi kuma gwamna yana gaggawar zuwa Kauran Namoda domin tarurrukan siyasa. Wannan ya nuna a fili abin da yake fifita siyasa da mulki na gabansa, rayuwar talakawa kuma ba ta da muhimmanci a wurinsa,” in ji Ibrahim Gummi.

Mazauna yankin sun soki abin da s**a kira “wannan rashin tausayi da kuma rashin kishi” daga gwamnan, suna mai jaddada cewa jagoranci na nufin daukar alhaki, tausayi da aiki, ba wai alkawuran banza na kyamfen ba. Sun ce shiru da gwamnatin jihar ta yi bayan hadarin jirgin ruwa ya sake tabbatar da cewa bata damu da rayuwar jama’a ba.

“Ba wannan ne karo na farko da muke binne ‘yan'uwanmu sak**akon rashin tsaro ba, amma wannan ne karo na farko da muke fuskantar gwamnati da ta dauki shiru da rashin bayyana kaico da wani katabus a duk lokacin da hakan ta faru a wurin al'umma. An bar jama’a cikin bakin ciki da kadaici, yayin da wadanda s**a rantse da kare mu suke kauda kai. Wannan gazawa abin kunya ce, ba za mu amince da ita ba, kuma ba za ta ci gaba ba,” in ji mazaunan.

Haka kuma sun roki hukumomin tsaro da gwamnatin tarayya da su gaggauta daukar mataki don kubutar da al’ummomin jihar Zamfara daga wannan halin ha'ula'i da suke ciki. A cewarsu, idan gwamnatin jihar a karkashin Dauda Lawal ta ci gaba da wannan sakaci, rayuwar duka al’ummomin na cikin hadari.

“Mutanen Gummi da sauran kananan hukumomin da abin ya shafa ba za su sake lamuntar da a dauke su a matsayin wadanda za a yi watsi da rayuwarsu ba. Muna bukatar daukar mataki na gaggawa, matakan tsaro masu karfi, da kuma kasancewar gwamnati kai tsaye a cikin al’ummominmu. Mutanenmu sun cancanci su rayu cikin mutunci da zaman lafiya, ba cikin tsoro da watsi ba,” in ji Lukman Ibrahim Gummi a karshe.

Dan majalisa mai wakiltar Funtua a zauran majalisar dokokin jahar Katsina yayima Al'ummar Funtua Emporment na bundugu do...
25/08/2025

Dan majalisa mai wakiltar Funtua a zauran majalisar dokokin jahar Katsina yayima Al'ummar Funtua Emporment na bundugu domin kare kansu Amina Isyaku da Sada Suleiman Usman

Kungiyar matasa magoya bayan jam’iyyar APC a jihar Zamfara sun soki gwamnonin PDP kan gudanar da taron siyasa duk kuwa d...
25/08/2025

Kungiyar matasa magoya bayan jam’iyyar APC a jihar Zamfara sun soki gwamnonin PDP kan gudanar da taron siyasa duk kuwa da irin matsalar tsaron da ke addabar jihar

Kungiyar matasan jam’iyyar APC a jihar Zamfara ta soki gwamnonin jam’iyyar PDP kan gudanar da taron siyasa a jihar, kwanaki kadan bayan kashe-kashen da s**a rutsa da al’ummar jihar.

Rahotanni sun nuna cewa ‘yan bindiga sun ci gaba da kai hare-hare a jihar Zamfara, inda a kwanan nan aka rawaito cewa an sace mutane 144, an kashe 24, sannan an ji wa 16 munanan raunuka a sassa daban-daban na kananan hukumomin jihar.

Gwamnonin jam'iyyar PDP sun gudanar da taronsu a jihar a ranar Asabar, 23 ga watan Agusta cikin galatsi da nuna rashin damuwa da halin da mutanen jihar ke ciki.

A cikin wata sanarwa da sakataren yada labaran kungiyar, Muhammad Ibrahim, ya fitar a ranar Litinin, ta bayyana taron da cewa an gudanar da shi babu tausayi a zukatan mahalartansa kuma wata alama ce ta raina mutanen da s**a rasa rayukansu.

“Maimakon gwamnonin su taru domin taimaka wa takawaransu da ke fama da hare-hare da kashe-kashen jami'arsa, sai s**a fi son gudanar da taron siyasa a inda aka yi kisan gilla ba tare da wani alhini ko ba da shawarar yadda za a magance matsalar ba, sai don su tattauna batun siyasa da zai amfane su, su kadai da iyalansu.,” in ji sanarwar.

“Hotunan gwamnonin jam'iyyar PDP cikin rigunan alfarma irin na sarautar Hausa mai daraja suna shewa da dariya a gaban kyamara ba su dace da yanayin da ake ciki ba, musamman a wurin da har yanzu ake cike da zubar da jini da al'ummomin jihar na cikin bakin ciki.”

“Wannan abin da s**a aikata ya sake tabbatar da cewa jam'iyyar PDP da ke mulki a jihar Zamfara da sauran gwamnonin PDP da s**a "taya bera bari" ba au damu da talakawa da wahalar da suke fuskanta ba. Abin da ya fi damunsu shi ne mulki da siyasa.”

Kungiyar ta soki lamirin gwamnonin PDP, inda ta zarge su da gaza mara baya ga kokarin gwamnatin Bola Tinubu na kawo karshen matsalolin tsaron da ke addabar yankin Arewa maso Yammacin Nijeriya da ma sauran sassan kasar.

25/08/2025




HON KAMILU SAIDU WAMBAN KASUWAR DAJI ZAI ANSHI CERTIFICATE A HEAD QUATER INEC TA JIHAR ZAMFARA

21/08/2025

Tattaunawa da Zannan Bungudu Akan zaben dake gudana a yankin kaura yanzu haka

16/08/2025

Muna collection center yanzu haka

Kucigaba da bibiyarmu domin Jin sak**akon zaben

Address

Zamfara
Gusau

Telephone

+2349040067825

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Bahsan online tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Bahsan online tv:

Share

Category