Bahsan online tv

Bahsan online tv Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Bahsan online tv, TV Channel, Zamfara, Gusau.

Bahsan Online tv kaface mai zaman kanta datake kawo maku labaran duniya da Rahotanni na gida da naketare, Muna tallata maku hajojinku da sauran shirye Shiryenku.

31/10/2025

“Gargadi da kira da babban murya!
Ga BARGAJA GUMMI da BALA SALEH NASARAWA— ku sani, siyasar ƙasar Bukkuyum ba filin hargitsi ba ce!
Jama’ar Bukkuyum sun tashi tsaye — sun san me suke so, sun san wanda ke tsayawa da su!
Mu na da labarin wanda ya ɗauki nauyinku, kuma muna cewa kusani,
Hon. Umar A. Faru – Kainuwa ne Dashen Allah!
Siyasar gaskiya ba ta buƙatar ruɗani… tana buƙatar jagora!”*

Inji Hon sani danbasha, Hon Umar Musa ,Hon surajo Salah, Hon Muhammad Niimatu Nasarawa.

Bahsan TV
Kainuwa Dashen Allah

31/10/2025

JAWABIN DAN TAKARAR GUSAU DA TSAFE A JAM'IYYAR ADC A FADAR MAI MARTABA SARKIN KATSINAN GUSAU HRH ALHAJI ABDULKADIR IBRAHIM BELLO

BAHSAN TV
KAINUWA DASHEN ALLAH

31/10/2025

HON.MAHARAZU SALIHU FARU YA KUMA JAM'IYYAR A.P.C DOMIN CIGABAN AL UMMAR YANKINSAHI DA WAI DAN ANFANIN SA KAWAI BAH

INJI HON.YAHAYA SAIDU GIDAN GOGAH

Bahsan tv
Kainuwa Dashen Allah

Kungiyar ZCCF ta soki Gwamna Dauda Lawal kan rashin kyakkyawan amfani da kudaden jihar Zamfara da tsauraran haraji ga ta...
31/10/2025

Kungiyar ZCCF ta soki Gwamna Dauda Lawal kan rashin kyakkyawan amfani da kudaden jihar Zamfara da tsauraran haraji ga talakawa

Kungiyar Zamfara Concerned Citizens Forum (ZCCF) ta bayyana damuwa mai yawa kan yadda ake tafiyar da kudaden jihar Zamfara cikin sakaci da kuma yadda ake kara jefa jama’a cikin wahala a karkashin mulkin Gwamna Dauda Lawal Dare.

A cikin wata sanarwa da Sakataren Kungiyar, Muhammad Ibrahim Marafa, ya sanya wa hannu, kungiyar ta bayyana matakin gwamnan na mika harkar tara kudaden cikin gida na jihar hannun Rakkiya Ahmad Dodo, ‘yar asalin Funtua a Jihar Katsina, a matsayin babban cin amana da kuma alamar nuna wariya da cin moriyar jama’a.
Kungiyar ta ce ana zargin gwamnati da biyan Naira biliyan 3.6 a duk shekara ga wannan mai kwangila, abin da ta bayyana a matsayin “wani mummunan tsarin satar dukiyar Zamfara a fili, alhali jama’ar jihar na fama da talauci da rashin tsaro.”

Kungiyar ta ce a karkashin mulkin Gwamna Dauda, jama’a na cikin matsanancin halin kunci, inda ake karbar haraji daga ‘yan dako, masu shayi da biredi, tukin keke napep, masu sayar da shayi da kananan ‘yan kasuwa, duk da cewa jihar tana karɓar fiye da Naira biliyan 35 daga gwamnatin tarayya a duk wata.
Ta ce irin wannan zaluncin wajen tara kudade ya kara tsananta rayuwar jama’a da ke fama da hare-haren ‘yan bindiga, rashin ayyukan yi da rashin tallafin jin kai.

A cewar sanarwar, “abin takaici ne sosai ganin cewa al’ummar jihar Zamfara da kyar suke samun abinci su ci, amma gwamnan yana jin daɗin ciyar da ‘yan'uwansa na Funtua da miliyoyin kudade. Wannan ba mulki ba ne, wannan wawurar dukiyar jama’a ce cikin fili.”

Kungiyar ZCCF ta kuma yi Allah wadai da kin ba da tallafi ga jami’an tsaro da gwamnan ke yi, tana kiran hakan wata rashin kulawa ta gangan da ke barazana ga rayuka da kuma kokarin dawo da zaman lafiya a jihar.
Ta bukaci gwamnatin jihar da ta mayar da kudaden da ake batarwa ba bisa ka’ida ba wajen tallafa wa kananan ‘yan kasuwa, taimaka wa wadanda rikicin ‘yan bindiga ya rutsa da su, tare da farfado da bangarorin ilimi da kiwon lafiya.

Kungiyar ta kuma yaba wa mambobin Kungiyar ‘Yan Kasuwar Man Fetur ta Najeriya (IPMAN) saboda jinkirta yajin aikin da s**a shirya duk da tsananin haraji da ake kakaba wa a kansu.
“Haƙurinsu da fahimtarsu sun nuna sahihiyar jarumtar mutanen Zamfara, sabanin rashin tausayi da gwamnatin yanzu ke nunawa,” in ji sanarwar.

A ƙarshe, ZCCF ta kira hukumomin yaki da cin hanci da rashawa da sauran hukumomi masu alhakin bincike da su gudanar da cikakken bincike kan wannan yarjejeniya ta biliyan 3.6 da sauran mu’amaloli masu shakku a karkashin gwamnatin Gwamna Dauda.
Kungiyar ta jaddada cewa Zamfara ta cancanci mulki na gaskiya, adalci da nuna gaskiya, ba son kai da cin moriyar jama’a ba.

26/10/2025
Kalaman Sani Shinkafi ga Matawalle cike suke da hassada da bakin ciki Kungiyar matasan jam’iyyar APC ta jihar Zamfara ta...
26/10/2025

Kalaman Sani Shinkafi ga Matawalle cike suke da hassada da bakin ciki

Kungiyar matasan jam’iyyar APC ta jihar Zamfara ta bayyana cewa kalaman da Dr Sani Abdullahi Shinkafi ya yi kan Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya, Dr. Bello Muhammad Matawalle (MON), sun samo asali ne daga hassada da jin zafi da bakin ciki saboda rasa tasiri a siyasar jihar.

A wata sanarwa da kungiyar ta fitar, ta ce ta damu da irin yadda Shinkafi ke fitowa da maganganu marasa kan gado, inda take siffanta shi a matsayin mutum ma ci amana, hassada da neman suna ta kowace hanya. Kungiyar ta ce duk da irin taimakon da Matawalle ya yi masa a baya, yanzu kuma ba abin da zai saka masa da shi sai s**a da kazafi.

Kungiyar ta bayyana cewa kafin Matawalle ya zama gwamna a 2019, Dr Shinkafi ba shi da wani tasiri a siyasa, domin ko a mazaba bai taɓa lashe zaɓe ba, Matawalle ne ya ɗaga shi ya ba shi dama da mukamai, amma daga baya sai ya zama ma ci amana da neman kawo rarrabuwar kawuna a jam’iyyar.

A cewar kungiyar, maganganun Dr Shinkafi na baya-bayan nan kan Matawalle tamkar ihu ne na ɗan siyasar da ya rasa jama’a, domin yanzu babu wanda ke tare da shi, hatta wadanda s**a taɓa ruɗuwa da shi sun bar shi. Haka kuma tarihinsa na tsalle daga jam’iyya zuwa jam’iyya domin neman kuɗi da suna, ya tabbatar da cewa babu ainihin akida, nagarta a siyasarsa.

Kungiyar ta matasan APCn ta sake jaddada cikakken goyon bayanta ga Dr. Bello Muhammad Matawalle, tana mai cewa tsohon gwamnan jihar Zamfara kuma minista a ma'aikatar tsaron Nijeriya a halin yanzu ya nuna nagarta, kishin ƙasa da aminci ga jam’iyya.

Hakazalika, kungiyar ta kuma gargadi Dr Shinkafi da ya daina amfani da ƙarya da farfaganda don neman kulawa, tana mai cewa lokacinsa a siyasa ya ƙare. Sannan kuma kungiyar ba za ta lamunci irin waɗannan maganganu ba, kuma jam’iyyar ta APC a jihar Zamfara tana nan haɗe ƙarƙashin jagorancin Sanata Abdulaziz Yari Abubakar da Dr. Bello Matawalle.

Daga karshe, kungiyar ta kara da cewa, babu irin maganganu, bakin ciki daga wasu ‘yan siyasa da s**a gaza da za su hana jam’iyyar samun cikakkiyar nasara a zaɓen 2027.

20/10/2025

KAITSAYE TATTAUNAWA TARE DA ENGINEER AHMAD GARBAN YANDI KWAMISHINAN KANANAN HUKUMOMI DA SARAUTU NA JIHAR ZAMFARA DA HON MAMUDA MUHAMMAD DAN TAWASA KWAMISHINAN YADA LABARAI NA JIHAR ZAMFARA.

BAHSAN TV
KAINUWA DASHEN ALLAH

Yaƙin Kawar da Matsalar Tsaro Aiki Ne Na Haɗin Kai - Gwamna LawalGwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana cewa nas...
20/10/2025

Yaƙin Kawar da Matsalar Tsaro Aiki Ne Na Haɗin Kai - Gwamna Lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana cewa nasarar da ake samu wajen rage matsalar tsaro a jihar na samuwa ne sakamakon haɗin kai da jajircewar jami’an gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki.

Gwamnan ya bayyana haka ne a ranar Litinin yayin da ya jagoranci taron majalisar zartarwa ta jihar karo na 18 a fadar gwamnatin jihar da ke Gusau.

A cewar Gwamna Lawal, gwamnatin sa ta samu ci gaba wajen dawo da zaman lafiya a yankunan da rikice-rikice s**a daɗe suna addaba, inda ya ce ta’addancin ’yan bindiga ya ragu sosai idan aka kwatanta da shekarun baya.

“Na so in tunatar da mu duka muhimmancin haɗin kai wajen yaki da matsalar tsaro. Mun samu nasarori masu yawa wajen dawo da kwanciyar hankali a yawancin yankunan jihar. Ina roƙon kowa ya kasance mai jajircewa da kusanci da al’umma, da kuma isar da rahotanni ga jami'an tsaro akai-akai,” in ji shi.

Ya kuma bukaci mambobin majalisar su ci gaba da yin aiki tare da sauran jami’an gwamnati da shugabannin siyasa domin samun ingantaccen tsarin aiki da gudanarwa.

Taron ya kuma tattauna batutuwan da s**a shafi tsaro, ilimi, kiwon lafiya da ci gaban gine-gine a faɗin jihar.

Rahoto daga: Ofishin Mai Magana da Yawun Gwamnan Jihar Zamfara,
Sulaiman Bala Idris.
20 Oktoba, 2025.

Malamai a jihar Zamfara sun cancanci girmamawa, ba amfani da su don cimma wata manufa ta siyasa ba — cewar kungiyar da k...
20/10/2025

Malamai a jihar Zamfara sun cancanci girmamawa, ba amfani da su don cimma wata manufa ta siyasa ba — cewar kungiyar da ke rajin samar da kyakkyawan shugabanci a jihar Zamfara.

Kungiyar rajin samar da kyakkyawan shugabanci ta jihar Zamfara, wato Zamfara Good Governance Forum, ta nuna damuwa kan yadda gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare ke kokarin amfani da manyan malamai na jihar domin cimma muradun siyasa yayin da ake dab da zaben 2027.
Kungiyar ta bayyana wannan mataki nasa a matsayin rashin gaskiya da neman amfani da addini wajen neman goyon bayan jama’a, abin da ya saba da tsarin mutuntaka da girmamawa da tsohon gwamnan jihar kuma ministan tsaro, Dr Bello Muhammad Matawalle, ya kafa tsakanin gwamnati da malamai.

A zamanin mulkin Matawalle, gwamnatin jihar ta bai wa malamai babban matsayi, ta kuma ba su muhimmanci a cikin tafiyar da mulki, tare da samar musu da ofishi na dindindin a gidan gwamnati. Haka kuma, ya gina musu katafaren ofishi mai dauke da ɗakin karatu na addinin Musulunci wanda ke cike da littattafai na addini da na zamani, tare da kula da jin dadinsu da ci-gaban iliminsu ta hanyar tallafa musu su yi karatu a cikin gida da waje.

A cikin nuna tawali’u da girmamawa ga ilimi, Dr Matawalle ya gayyaci fitattun malamai kamar Malam Aminu Daurawa da Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami domin kaddamar da sabon ofishin malamai, alamar da ta nuna jajircewarsa wajen inganta ilimin addini, zaman lafiya da kyakkyawan shugabanci a jihar Zamfara.

Sai dai bayan Gwamna Dauda Lawal Dare ya hau mulki, ya rusa wannan ginshikin alheri ta hanyar korar malamai daga ofishinsu a gidan gwamnati, sannan ya mayar da wurin ofishin uwargidan gwamna. Rahotanni sun nuna cewa an kashe miliyoyin kudaden jama’a wajen sake gyaran ofishin domin nuna alfarma da jin dadi, abin da ya zubar da mutuncin malamai da kuma tarihi na addini a jihar.

Yanzu kuma, wannan gwamna da ya raina malamai da ayyukansu shi ne yake sake gayyatarsu domin yin addu’a ga jihar, abin da kungiyar ta bayyana a matsayin wani yunkuri na siyasa domin amfani da tasirin malamai wajen neman goyon bayan jama’a kafin zaben 2027.

Kungiyar ZGGF ta bukaci malamai su tuna bambanci tsakanin gaskiya da nuna sha’awa ta siyasa. Dr Bello Matawalle ya kula da su cikin mutunci da girmamawa a matsayin abokan tafiya wajen kyautata shugabanci, ba kayan amfani a siyasance ba.

A cewar kungiyar, jama’ar Zamfara har yanzu suna tuna zamanin da girmamawa, zaman lafiya da hadin-kai na addini s**a mamaye gwamnatin Matawalle.

Daga karshe, kungiyar ta ce, Zamfara tana bukatar shugabanci na gaskiya, girmamawa da mutunci ba na yaudara, girman kai da son kai ba.

Address

Zamfara
Gusau

Telephone

+2349040067825

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Bahsan online tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Bahsan online tv:

Share

Category