20/10/2025
Malamai a jihar Zamfara sun cancanci girmamawa, ba amfani da su don cimma wata manufa ta siyasa ba — cewar kungiyar da ke rajin samar da kyakkyawan shugabanci a jihar Zamfara.
Kungiyar rajin samar da kyakkyawan shugabanci ta jihar Zamfara, wato Zamfara Good Governance Forum, ta nuna damuwa kan yadda gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare ke kokarin amfani da manyan malamai na jihar domin cimma muradun siyasa yayin da ake dab da zaben 2027.
Kungiyar ta bayyana wannan mataki nasa a matsayin rashin gaskiya da neman amfani da addini wajen neman goyon bayan jama’a, abin da ya saba da tsarin mutuntaka da girmamawa da tsohon gwamnan jihar kuma ministan tsaro, Dr Bello Muhammad Matawalle, ya kafa tsakanin gwamnati da malamai.
A zamanin mulkin Matawalle, gwamnatin jihar ta bai wa malamai babban matsayi, ta kuma ba su muhimmanci a cikin tafiyar da mulki, tare da samar musu da ofishi na dindindin a gidan gwamnati. Haka kuma, ya gina musu katafaren ofishi mai dauke da ɗakin karatu na addinin Musulunci wanda ke cike da littattafai na addini da na zamani, tare da kula da jin dadinsu da ci-gaban iliminsu ta hanyar tallafa musu su yi karatu a cikin gida da waje.
A cikin nuna tawali’u da girmamawa ga ilimi, Dr Matawalle ya gayyaci fitattun malamai kamar Malam Aminu Daurawa da Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami domin kaddamar da sabon ofishin malamai, alamar da ta nuna jajircewarsa wajen inganta ilimin addini, zaman lafiya da kyakkyawan shugabanci a jihar Zamfara.
Sai dai bayan Gwamna Dauda Lawal Dare ya hau mulki, ya rusa wannan ginshikin alheri ta hanyar korar malamai daga ofishinsu a gidan gwamnati, sannan ya mayar da wurin ofishin uwargidan gwamna. Rahotanni sun nuna cewa an kashe miliyoyin kudaden jama’a wajen sake gyaran ofishin domin nuna alfarma da jin dadi, abin da ya zubar da mutuncin malamai da kuma tarihi na addini a jihar.
Yanzu kuma, wannan gwamna da ya raina malamai da ayyukansu shi ne yake sake gayyatarsu domin yin addu’a ga jihar, abin da kungiyar ta bayyana a matsayin wani yunkuri na siyasa domin amfani da tasirin malamai wajen neman goyon bayan jama’a kafin zaben 2027.
Kungiyar ZGGF ta bukaci malamai su tuna bambanci tsakanin gaskiya da nuna sha’awa ta siyasa. Dr Bello Matawalle ya kula da su cikin mutunci da girmamawa a matsayin abokan tafiya wajen kyautata shugabanci, ba kayan amfani a siyasance ba.
A cewar kungiyar, jama’ar Zamfara har yanzu suna tuna zamanin da girmamawa, zaman lafiya da hadin-kai na addini s**a mamaye gwamnatin Matawalle.
Daga karshe, kungiyar ta ce, Zamfara tana bukatar shugabanci na gaskiya, girmamawa da mutunci ba na yaudara, girman kai da son kai ba.