Shafin Matasa 'yan Gwaggwarmaya

Shafin Matasa 'yan Gwaggwarmaya BARKA DA ZUWA SHAFIN MATASA YAN GWAGGWARMAYA. MASU FAFUTUKAR KAWO CHANJI MAI MA'ANA. A YANKIN AREWA Muna Alfahari da kasancewa daku a kowane lokaci

Kungiyar Matasa 'Yan Gwagwarmaya Ta Jaddada Kudirinta Na Ci Gaban Al’ummaKungiyar Matasa 'Yan Gwagwarmaya ta bayyana cew...
08/08/2025

Kungiyar Matasa 'Yan Gwagwarmaya Ta Jaddada Kudirinta Na Ci Gaban Al’umma

Kungiyar Matasa 'Yan Gwagwarmaya ta bayyana cewa har yanzu tana nan daram wajen jajircewa da sadaukarwa domin jin ƙorafe-ƙorafen al’umma da kuma tabbatar da ci gaban rayuwar al’ummar Najeriya.

Shugaban kungiyar matakin ƙasa, Comrade Nura Muhammad, ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da aka gudanar domin ƙarin bayani game da manufofi da shirye-shiryen kungiyar. Ya ce an kafa kungiyar sama da shekaru biyar da s**a wuce tare da nufin ƙarfafa matasa su tsaya tsayin daka wajen kare muradun jama’a da kuma sanya gwamnati da shugabanni su duba halin da talakawa ke ciki.

Comrade Nura ya ce kungiyar tana buɗe kofofinta ga dukkan matasa masu kishin ƙasa da ke son bada gudunmawa a fannonin ci gaban siyasa, ilimi, tattalin arziki da kare hakkin dan adam. Ya jaddada cewa kungiyar ba ta da wata alaƙa da kowace jam’iyyar siyasa, kuma a kullum tana yin aikin sa ido a cikin gaskiya da rikon amana.

A wani ɓangare na jawabin nasa, shugaban ya gargadi wasu gungun mutane da ke amfani da tambarin kungiyar a hanyoyin da ba su dace ba, yana mai cewa hakan babbar barna ce da kan iya sa mutum fuskantar matakin doka.

Ya ce kungiyar za ta ci gaba da zama muryar al’umma a kowane lokaci tare da kare muradun jama’a ba tare da tsoro ko son zuciya ba.

[email protected]
08133676020
08164949696
08031568637

Cikin Hotuna: Ɗan takarar Kansila ya gudanar da feshin maganin sauro a yankinsa a Zamfara  Wani mai neman a tsayar da sh...
16/09/2024

Cikin Hotuna: Ɗan takarar Kansila ya gudanar da feshin maganin sauro a yankinsa a Zamfara

Wani mai neman a tsayar da shi takarar kujerar Kansila a mazaɓar Galadima da ke ƙaramar hukumar Gusau a jihar Zamfara, Hon. Imrana Abdullahi Shagamu, ya ƙaddamar da aikin feshin maganin sauro a yankunan gundumar da yake neman wakilta.

Sahel24 Tv ya ruwaito cewar al'umma da dama a gundumar sun yi farin ciki da wannan aikin jinƙai da matashin ya gudanar, domin a cewar wasu daga cikinsu kusan babu gidan da ba a fama da cutar zazzaɓin cizon sauron sakamakon yawaitar sa a yankin.

A jawabinsa yayin ƙaddamar da wannan aikin, Hon. Imrana Abdullahi, ya jaddada aniyar da yake da ita ta ci gaba da inganta wannan gunduma, idan Allah ya ba shi nasarar zamewa Kansila mai wakiltarta.

Ba dai a kasafai ake samun ƴan siyasa masu tunani irin wannan ba, domin mafi yawancin lokuta al'umma kan nemi gwamnati mai ci da irin wannan jinƙai, to sai dai kuma haƙar ta su ta kan gaza cimma ruwa.

02/02/2024

Assalamu alaikum ƴaƴan wannan kungiya mai albarka muna yi maku barka da warhaka

Ƙungiyar Matasa Ƴan Gwagwarmaya Na Nuna Damuwa  Kan Halin Da Ƴan Najeriya Ke Ciki!!!Ƙungiyar Matasa Ƴan Gwagwarmaya ta t...
20/07/2023

Ƙungiyar Matasa Ƴan Gwagwarmaya Na Nuna Damuwa Kan Halin Da Ƴan Najeriya Ke Ciki!!!

Ƙungiyar Matasa Ƴan Gwagwarmaya ta tarayyar Najeriya na nuna takaici da damuwarta bisa halin ƙuncin rayuwa da al'ummar Najeriya ke ciki, sakamakon tsadar rayuwa wanda janye tallafi da kuma ƙarin farashin man fetur s**a haddasa.

A fili take a halin yanzu, al'ummar ƙasar nan suna ɗanɗana kuɗarsu a cikin rayuwar yau da kullum, musamman hauhawar kayan masarufi a ƙasar.

Wannan ƙungiyar tana kira ga shugabanni, musamman shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, da sauran ƴan majalisun dattijai da na wakillai, da kuma gwamnonin jihohi, da su yi duk mai yiwuwa wajen ganin sun fitar da al'umma cikin wannan yanayi da suke ciki.

Abu na farko, ya kyautu gwamnatin shugaba Tinubu ta gaggauta buɗe iyakokin ƙasar nan da s**a ɗauki shekaru a garƙame, domin ba da damar shigowa da abinci ta yadda ƴan ƙasa za su samu sauƙin rayuwa.

Ya kyautu gwamnatin tarayya ta ƙara ƙaimi wajen yaƙar ƴan ta'adda da s**a hana al'ummar ƙasar walwala, ta hanyar hana kasuwanci da noma da kuma kiwo, idan aka samu tsaro babu ko shakka ƴan Najeriya za su fita gonaki da kasuwanni su nemo abun sakawa bakin salati.

Gwamnatin tarayya ta ɓullo da shirin da zai tallafawa ƴan ƙasa masu ƙaramin ƙarfi, domin rage musu raɗaɗin tsananin rayuwa da janye tallafi da kuma tsadar man fetur s**a haddasa.

A ƙarshe, wannan ƙungiya tana kira ga al'umma masu hannu da shuni da su taimakawa ƴan uwansu da ke da ƙaramin ƙarfi a wannan yanayi da ake ciki na goro ko abun saye, domin Allah ya sanya wa dukiyoyin su albarka.

Allah maɗaukakin sarki ya kawo mana ƙarshen wannan halin matsi da wannan ƙasa take ciki, ameen *summa* ameen.🤲

📝 Ashiru Lawal Nagoma Ruwan-Ɓaure, Sakataren Ƙungiya Na Ƙasa, A Madadin Shugaba.

Address

Gusau
5550

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Shafin Matasa 'yan Gwaggwarmaya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Shafin Matasa 'yan Gwaggwarmaya:

Share

Category