
08/08/2025
Kungiyar Matasa 'Yan Gwagwarmaya Ta Jaddada Kudirinta Na Ci Gaban Al’umma
Kungiyar Matasa 'Yan Gwagwarmaya ta bayyana cewa har yanzu tana nan daram wajen jajircewa da sadaukarwa domin jin ƙorafe-ƙorafen al’umma da kuma tabbatar da ci gaban rayuwar al’ummar Najeriya.
Shugaban kungiyar matakin ƙasa, Comrade Nura Muhammad, ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da aka gudanar domin ƙarin bayani game da manufofi da shirye-shiryen kungiyar. Ya ce an kafa kungiyar sama da shekaru biyar da s**a wuce tare da nufin ƙarfafa matasa su tsaya tsayin daka wajen kare muradun jama’a da kuma sanya gwamnati da shugabanni su duba halin da talakawa ke ciki.
Comrade Nura ya ce kungiyar tana buɗe kofofinta ga dukkan matasa masu kishin ƙasa da ke son bada gudunmawa a fannonin ci gaban siyasa, ilimi, tattalin arziki da kare hakkin dan adam. Ya jaddada cewa kungiyar ba ta da wata alaƙa da kowace jam’iyyar siyasa, kuma a kullum tana yin aikin sa ido a cikin gaskiya da rikon amana.
A wani ɓangare na jawabin nasa, shugaban ya gargadi wasu gungun mutane da ke amfani da tambarin kungiyar a hanyoyin da ba su dace ba, yana mai cewa hakan babbar barna ce da kan iya sa mutum fuskantar matakin doka.
Ya ce kungiyar za ta ci gaba da zama muryar al’umma a kowane lokaci tare da kare muradun jama’a ba tare da tsoro ko son zuciya ba.
[email protected]
08133676020
08164949696
08031568637