Al akhyar TV

Al akhyar TV Assalamu alaikum, Muna yima dukkan musulmi fatan al-khairi.

16/09/2025

Idan Copy Na Alƙur'ani Ya Tsufa Ko Ya Yayyage To Sai A Ƙona Shi A Samu Guri Mai Tsafta Inda Baza Ana Takawa Ba A Binne Shi.
Dr. Bashir Aliyu Umar (Hafizahullahu)

13/09/2025

GIRMAN HAKKIN ABOKI

Wani daga cikin magabata ya zo gidan abokinsa, sai ya ce masa ana bina bashin Dirhami dari hudu. Sai abokin nashi ya shiga gida ya dauko masa su ya bashi. Bayan abokin ya tafi sai ya shigo gida yana kuka, sai matarsa ta ce masa: To ai da ka bashi hakuri ka gabatar masa da uzurinka idan har bashin da ka yi za ka takura sosai. Sai ya ce mata, ba dan bashi da na yi ba ne nake kuka, a'a ina kuka ne saboda ban iya gano halin da yake ciki ba har sai da ta kai ga ya furta min".

التبصرة لابن الجوزي ٢/٢٦٣

Wannan qissar tana kunshe da darussa masu muhimmanci sosai, kada ka karanta ka wuce ba tare da ka fitar da wani darasi akalla guda uku ba acikinsa.

Daga shafin 📄 Ash-sheikh Muhammad Awwal Maishago Zaria .

21/08/2025

Hatim al-Aṣamm (Rahimahullah ) ya ce:
Na kalli halittu;
sai na ga kowanne mutum yana da abin da yake ƙauna,
amma idan ya isa kabari, sai ya rabu da abin ƙaunarsa;
to ni sai na sanya ayyukana na alheri su zama abin ƙaunata,
domin su kasance tare da ni a cikin kabari.

📚 Mukhtaṣar Minhāj al-Qāṣidīn (shafi na 28).

17/08/2025

أحسنوٱ وضوئكم

17/08/2025
12/08/2025

Kun san menene gafala? 🌸

Gafala ita ce: Matashi yana aikata zunubi yana cewa “zan tuba”, amma mutuwa ta riske shi bai tuba ba... 🌸

Gafala ita ce: Masu zina cikin sirri, bala’i ya zo, kawai sai dai a riske su gawarwaki tsirara... 🌸

Gafala ita ce: Mai shan miyagun ƙwayoyi ya sha har zuciyarsa ta tsaya, ya mutu a cikin wannan hali... 🌸

Gafala ita ce: Wata tana sauraron wakoki, sai numfashinta ya tsaya, ta kasa faɗin Shahada — kalmar da ake so ta zama ƙarshen maganar dan Adam lokacin barin duniya... 🌸

Gafala ita ce: Wata ta fito da kwalliya da suturar fitina, sai ta fāɗi a hanya, mota ta karye jikinta... 🌸

Gafala ita ce: Matasa acikin maye suna tuki suna sauraron waka, hatsari ya hallaka su cikin wuta... 🌸

Gafala ita ce: Wata tana rawa, ta bugu, ta mutu nan take... 🌸

Gafala ita ce: Ka kwanta barci ba tare da ka yi salla ko ka yi zikiri ba, sai ka wayi gari a kabari ana yi maka hisabi... 🌸

Mutuwa ɗaya ce, amma hanyoyin gafala sun bambanta.

Ya Allah, Ka kyautata ƙarshenmu.
Ka tsare mu daga kunyar duniya da azabar lahira.
Ka sa mafi kyawun ranarmu ita ce ranar da muka haɗu da Kai. 🌸

08/08/2025

SALLAR NAFILA LOKACIN DA LIMAN YA HAU MINBARI RANAR JUMU'AH

1) Idan mutum ya shiga masallaci ranar Jumu'ah liman yana akan minbari, zaiyi sallah raka'ah biyu, amma ya gajarta. (Bukhari da Muslim)

2) Idan mutum ya taradda ana kiran sallah kafin a fara khutbah, zaiyi sallah lokacin da ake kira bazai jira a gama kiran sallah ba, saboda sauraron khutbah wajibi ne amma sauraron maikiran sallah Sunna ne. ( Ibn Uthaimeen)

3) Idan mutum bai samu shiga masallaci ba ya tsaya a harabar masallaci, bazaiyi sallah ba lokacin da liman ke khutbah, saboda sallar ta Tahiyyatul masjid ce, bata wajaba sai ga wanda ya shiga masallaci.

4) Mutane da yawa s**anyi kuskure sai su zata akwai wasu raka'ah biyu da akeyi kafin Jumu'ah, sai kaga mutum yazo yana wajen masallaci ya kabbarta sallah alhali liman yana khutbah. Wannan kuskure ne, matsayin sa kamar wanda ya tashi a cikin masallaci ya kabbarta sallah alhalin liman yana khutbah.

5) Duk wanda ya shiga masallaci wajibi ne (a kan zance mafi inganci) yayi sallah raka'ah biyu kafin ya zauna. Wannan hukuncin da ranar Jumu'ah da Assabar da sau ran ranaku duka daya ne. Dalili akan hakan shine, cewar da Manzon Allah S.A.W. yayi: Idan dayanku ya shiga masallaci kada ya zauna sai yayi sallah raka'a biyu. (Bukhari da Muslim)

Ya kamata ayi fadakarwa da mutane akan wannan hukuncin, saboda da yawa akan saba.

Allah yasa mudace da sunnah.

✍🏽 Dr. Jabir Sani Maihula

30/07/2025

Sheikh Ibn Uthaymeen (rahimahullah) yace :

"Lallai tasbihi guda daya a cikin littafin ayyukan mutum, ya fi dukkan duniya da abin da ke cikinta alkhairi; domin duniya da abin da ke cikinta suna gushewa kuma su bace, amma tasbihi da aiki nagari suna kasancewa har abada."

📚 Riyāḍuṣ-Ṣāliḥīn (juzu’i na 3, shafi na 478)

25/07/2025

✍️Ibnu al-Jawzī (rahimahullāh) ya ce:

"Na yi zurfin tunani a kan wani lamari mai girma: lallai Allah (Mabuwayi da ɗaukaka) yana jinkirta (azaba) har ka ga kamar yana barin (masu laifi) haka kawai! Za ka ga hannayen masu laifi na yawo cikin 'yanci, kamar babu wani mai hana su. Amma idan s**a ƙara wuce gona da iri, kuma hankula ba su dawo daidai ba; sai Allah ya ɗauki mataki kamar yadda Mai iko da ƙarfi yake ɗauka. Wannan jinkiri kuwa ba don komai ba ne, sai don Ya jarraba haƙurin mai haƙuri, kuma Ya ba wa azzalumi ƙarin lokaci... domin Ya ƙarfafa wannan akan haƙurinsa, kuma Ya saka wa wancan da mugun aikinsa."

Kada ka ji kunya ka ɗaga wandonka sama da idon sawun ƙafa (kamar yadda Sunnah ta koyar), domin akwai wasu da suke ɗaga t...
23/07/2025

Kada ka ji kunya ka ɗaga wandonka sama da idon sawun ƙafa (kamar yadda Sunnah ta koyar), domin akwai wasu da suke ɗaga tufafinsu har sama da guiwa suna jin girman kai kamar babu wanda ya kai su!.

⛔ Ga wanda ke cewa: "Ba ka yarda da 'yar uwarka ba!!" ⛔🌀 Wata mata ce ta zo Makka domin yin Hajj da Umrah. Tana daga cik...
06/07/2025

⛔ Ga wanda ke cewa: "Ba ka yarda da 'yar uwarka ba!!" ⛔

🌀 Wata mata ce ta zo Makka domin yin Hajj da Umrah. Tana daga cikin kyawawan mata. Yayin da ta je jifar jamar, sai Umaru dan Abi Rabi’ah – shahararren mawaki mai kaunar mata da yin waƙar soyayya – ya gan ta.

Sai ya yi mata magana, amma ta ƙi amsawa. A washe gari gobe, ya ƙara fitowa ya same ta, sai ta ce masa:
"Rabu dani! Ina cikin Haramin Allah, kuma muna cikin kwanakin da s**a daɗe da tsarki!"

Amma ya dage. Ta firgita saboda ta tsorata kada lamarinta ya bayyanu, sai ta guje shi ta koma tanti ɗinta.

A daren na uku, sai ta ce wa ɗan uwanta:
"Fito da ni ka koya min yadda ake ibadar nan."

Yayin da Umaru ya gan ta tare da ɗan uwanta, sai ya tsaya, bai kusance ta ba. Sai ta yi dariya, ta fadi wannan shahararriyar baitin:

✅تعدو الكلاب على من لا أسود له
✅وتتّقي صولة المستأسد الضاري

Karnuka na kai hari ne ga wanda ba shi da zaki,
Amma suna tsoron zaki mai karfi kuma mai ƙarfi sosai.

💠 Da Khalifa Abu Ja’afar Al-Mansur ya ji wannan labarin, sai ya ce:
"Da fatan dukkan 'yan mata na Kuraysh sun ji wannan labarin."

---

💢 A wani gari kuwa, wata mata saliha mai hankali ce, tana da yarinya. Duk lokacin da yarinyar za ta fita, sai ta ce wa ɗanta:

"Fita da ita, ka raki 'yar uwarka. Domin mace da babu namiji tare da ita domin ya kare ta, kamar tumaki ce tsakanin kyarkeci, duk da ƙarancin ƙarfin su sai su kusance ta."

🏵️ Saƙo zuwa ga iyaye, ’yan uwa maza, da mazaje:

🕋 An same ta har cikin Haramin Allah, wuri mafi tsarki – to me kuke tunani game da kasuwanninmu da titunanmu?

⚠️ Ku kula da mata da ’yan uwanku, ba wai saboda rashin yarda da su ba, sai don kare su da darajarsu.

📕 An samo daga: "Uyoonul Akhbar" 4/107 na Imamu Ibn Qutaybah

09/04/2025

Gaskiya sai an sake zama

Address

New Market Road
Gusau

Telephone

+2347067671267

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Al akhyar TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Al akhyar TV:

Share

Category