Gwoza Media Forum

Gwoza Media Forum Barka da shigowa wannan gida mai albarka.

Yaddah Daliban Fudiyyah s**a gudanar da faretin girmamawar mauludin fiyayyen Halitta Annabi Muhammad(sawa)
02/09/2025

Yaddah Daliban Fudiyyah s**a gudanar da faretin girmamawar mauludin fiyayyen Halitta Annabi Muhammad(sawa)

MUZAHARAR ASHURAH A GARIN GWOZAAn Gabatar da muzaharar Ashura a Garin Gwoza, Borno State, taron an lapiyah kuma an tashi...
06/07/2025

MUZAHARAR ASHURAH A GARIN GWOZA

An Gabatar da muzaharar Ashura a Garin Gwoza, Borno State, taron an lapiyah kuma an tashi lapiyah.

Labbaika Ya Hussain
06-07-2025

04/05/2025

Dalilin tashin garin Mubi da Gwoza da akayi da sunan Wai Boko Haram.

-Sheikh Ibrheem Yaaqoub Al-Zakzaky (H)

Tiktok Team Of The Islamic
Movement
03/05/2025

Shugabannin kiristoci daga Lafiya Jihar Nasarawa sun bayyana gamsuwa mutuƙa bisa salon da'awar Jagora Sheikh Ibraheem Za...
04/05/2025

Shugabannin kiristoci daga Lafiya Jihar Nasarawa sun bayyana gamsuwa mutuƙa bisa salon da'awar Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) da ya ke bi wajen samun fahimta na zamantakewa tsakanin mabiya addinai daban daban a Nigeria.

Sun tabbatar da hakan ne jiya Asabat 03/04/2025, yayin da ya amshi baƙuncin su a gidansa dake Abuja.






03/04/2025

03/05/2025

Boko Haram de wani shiri ne kamar yadda America ba a nan ta fara ba a wurare da dama tayi, ta je ta kirkiro wadannan yan ta'adda din wani wuri ace musu Al qa'ida wani wuri ace musu Da'esh wani lokaci ace musu ISIS

_ Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) _

Tiktok Team Of The Islamic Movement.

11/04/2025

BABU ABUNDA ZAƁEN 2027 ZAI SAUYA MATUƘAR BA TSARIN ƘASAR NE YA SAUYA BA

Masu cewa Allah ya kaisu 2027 su sauya shugaban ƙasa, ko yaushe za su hankalta Oho. Sau nawa suna sauyawa amma a kullum sai ƙara masu masifa suke?

Kuskurensu shine sun ɗauka da gaske akwai demokradiyya ne a ƙasar, sannan sun ɗauka shugaban ƙasa na iya kawo sauyi mai ma'ana a cikin wannan tsarin da ake, basu san shima mai karɓar umurni ne daga sama ba.

Babu Demokradiyya a ƙasar nan, idan ma akwaita to sunanta military democracy ba representative democracy ba, har yanzu Decree ke jagorantar ƙasar nan ba consensus ba.

A wajen masu ikon ƙasa, ita demokradiyyar zaure ce da suke ratawa domin shiga wani gida da s**a tsara a cikinsa za su mulki ƙasar, ba a cikin zauren ba. Sunan gidan imperialism.

Don haka, ko za a sauya shugaba sau 1000 sau 1000, daga wannan kabilar zuwa waccan, daga wannan Addini zuwa wancan, matuƙar ba tsarin ne ya sauya ba, to abunda aka gani jiya, aka gani yau, na Zalunci da Danniya, shine dai za a gani gobe.

Sai an fara sauya "me ke mulki" (what is ruling) kafin sauya "wa ke mulki"(who is ruling ya amfani al'umma.

Wannan shine fahimtar malamimu Sayyid Ibraheem Zakzaky(H), kuma a kanta muke, domin tajriba ta nuna mana itace gaskiya.

System ɗin ƙasar ne matsala, ba a yishi domin yan ƙasa ba, ba zai taɓa amfanarsu ba. Shi za a haɗu a sauya kafin a fara ganin daidai.

Shamsudeen Hassan Zuru
11/4/2025

11/04/2025

Addu’ar Yaye Zalunci da Kau da Shi
Wacce Jagora Sayyid Zakzaky (H) ya umarci ’yan’uwa da su rika karantawa tun yana tsare

بِسْمِ اللهِ الرَّحْمنِ الرَّحِيمِ
اللّهُمَّ صَلِّ عَلى مُحَمَّدٍ وَآلِ مُحَمَّدٍ وَعَجِّلْ فَرَجَهُمْ يَا كَرِيمُ
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. Ya Allah! Ka yi salati ga Muhammad da iyalan Muhammad, kuma ka gaggauta farfadowarsu, Ya Mai karamci.

اَللَّهُمَّ اِنَّ ظُلْمَ عِبادِكَ قَدْ تَمَكَّنَ فِي بِلادِكَ،
حَتَّى اَماتَ الْعَدْلَ وَ قَطَعَ السُّبُلَ،
Ya Allah, lalle zaluncin bayinka ya mamaye ƙasarka, har ya kashe adalci, ya katse hanyoyi.

وَ مَحَقَ الْحَقَّ وَ اَبْطَلَ الصِّدْقَ،
وَاَخْفَي الْبِرَّ وَ وَاَظْهَرَ الشَّرَّ،
Ya shafe gaskiya, ya kawar da amana; ya ɓoye kyautatawa, ya bayyanar da sharri.

وَاَخْمَدَ التَّقْوَي وَ اَزالَ الْهُدَي،
وَ اَزاحَ الْخَيْرَ وَ اَثْبَتَ الضَّيْرَ،
Ya kashe tsoron Allah, ya kawar da shiriya; ya kore alheri, ya tabbatar da cutarwa.

وَ اَنْمَي الْفَسادَ وَ قَوَّي الْعِنادَ،
وَ بَسَطَ الْجَوْرَ وَ عَدَي الطَّوْرَ.
Ya watsa fasadi, ya ƙarfafa girman kai; ya shimfiɗa zalunci, ya ƙetare iyaka.

اَللَّهُمَّ يَا رَبِّ، لا يَكْشِفُ ذلِكَ اِلاَّ سُلْطانُكَ،
وَ لا يُجِيرُ مِنْهُ اِلاَّ امْتِنانُكَ،
Ya Allah, Ya Ubangiji, babu wanda zai iya kawar da hakan sai da mulkinka, kuma babu mai karewa daga gare shi sai falalarka.

اَللَّهُمَّ رَبِّ فَابْتُرِ الظُّلْمَ وَ بُثَّ جِبالَ الْغَشْمِ،
وَ اَخْمِدْ سُوقَ الْمُنْكَرِ وَ اَعِزَّ مَنْ عَنْهُ يَنْزَجِرُ،
Ka sare zalunci, ka bazar da azzaluman da s**a yi girman kai; ka kashe kasuwar mummuna, ka ɗaukaka masu nisantar shi.

وَاَحْصُدْ شَاْفَةَ اَهْلِ الْجَوْرِ،
وَاَلْبِسْهُمُ الْحَوْرَ بَعْدَ الْكَوْرِ،
Ka sare tushen masu zalunci, ka sanyasu cikin rikicewa bayan sun taɓa shiriya.

وَعَجِّلِ اللَّهُمَّ اِلَيْهِمُ الْبَيَاتَ،
وَ اَنْزِلْ عَلَيْهِمُ الْمَثُلاتِ،
Ka gaggauta musu azaba ba zato ba tsammani, ka saukar da hukunci a kansu.

وَاَمِتْ حَيوةَ الْمُنْكَرِ لِيُؤْمَنَ الْمَخُوفُ،
وَيَسْكُنَ الْمَلْهُوفُ وَيَشْبَعَ الْجائِعُ،
Ka kawo ƙarshen rayuwar mummuna domin masu tsoro su sami aminci, masu damuwa su huta, masu yunwa su ƙoshi.

وَيُحْفَظَ الضَّائِعُ وَيَاْوَي الطَّريدُ،
وَيَعُودَ الشَّريدُ وَيُغْنَي الْفَقيرُ،
A kare wanda ya ɓace, a ba mafaka ga wanda aka kore, a dawo da ɓatacce, a wadatar da matalauci.

وَيُجارَ الْمُسْتَجيرُ وَيُوَقَّرَ الْكَبيرُ،
وَيُرْحَمَ الصَّغِيرُ وَيُعَزَّ الْمَظْلُومُ،
A tsare mai neman kariya, a girmama babba, a jiƙan ƙarami, a ɗaukaka wanda aka zalunta.

وَيُذَلَّ الظَّالِمُ وَيُفَرَّجَ الْمَغْمُومُ،
وَتَنْفَرِجَ الْغَمَّآءُ وَتَسْكُنُ الدَّهْمآءُ،
A ƙasƙantar da azzalumi, a sauƙaƙa wa mai damuwa, a warware ƙunci, a lafa bala’i.

وَيَمُوتَ الاِخْتِلافُ وَيَعْلُوَالْعِلْمُ،
وَيَشْمُلَ السِّلْمُ وَيُجْمَعَ الشَّتاتُ،
A kawar da sabani, a ɗaukaka ilimi, a yada zaman lafiya, a haɗa kawuna.

وَيَقْوِيَ الإيمَانُ وَيُتْلَي الْقُرْآنُ،
اِنَّكَ اَنْتَ الدَّيَّانُ الْمُنْعِمُ الْمَنَّانُ.
A ƙarfafa imani, a karanta Alƙur’ani. Lalle Kai ne Mai shari’a, Mai ni’ima, Mai yawan baiwa.

وَصَلِّ اللّهُمَّ عَلى مُحَمَّدٍ وَآلِهِ الطَّيِّبِينَ الطَّاهِرِينَ.
Ka yi salati, ya Allah, ga Muhammad da iyalansa masu tsarki, masu tsabta.

07/04/2025

Attempt to Invade Sheikh Zakzaky's Residence in Abuja.

KD-PRESS🌐

The general public is hereby informed that the Federal Government of Nigeria, under the directives of President Bola Ahmed Tinubu and chaired by Nuhu Ribadu, National Security Adviser (NSA), has planned to deploy security operatives to invade the residence of Sheikh Zakzaky in Abuja and other locations belonging to the Islamic Movement in Nigeria.

Notifications to Local and International Communities
We wish to notify the local and international communities that any harm or adverse consequences affecting Sheikh Zakzaky and his supporters will be attributed to President Bola Tinubu and Nuhu Ribadu, who will be held accountable.

Concerns about Accountability
This planned invasion raises concerns about the rule of law and the potential for human rights abuses. Given Nuhu Ribadu's past statements about President Tinubu's alleged wrongdoings, questions arise about the motivations behind this planned invasion.

Call to Action
We urge the international community to closely monitor this situation and ensure that the rights of Sheikh Zakzaky and his supporters are protected. The Federal Government of Nigeria must be held accountable for any actions taken against them.

KD-PRESS🌐
7th April, 2025

SHARUDDAN DA IRAN TA GINDAYAWA AMURKA AKAN SAKE YARJEJENIYAR NUKILIYA BA TARE DA TATTAUNAWA DA ITA KAI TSAYE BA.Ga wadan...
06/04/2025

SHARUDDAN DA IRAN TA GINDAYAWA AMURKA AKAN SAKE YARJEJENIYAR NUKILIYA BA TARE DA TATTAUNAWA DA ITA KAI TSAYE BA.

Ga wadanda ba su san sabbin sharudaddan da Kasar Iran ta gindayawa Kasar Amurka kafin su sake tattaunawa akan Shirinta na Samar da Fasahar Nukiliya ta zaman lafiya, wanda Amurka ke zargi Makaman Nukiliya Kasar Iran take son kerawa.

Abin na farko dai shi ne Kasar Iran ta bijerewa duk wata Barazanar abka mata da Farmakin da Amurka take cewa za ta yi idan ba ta rushe Shirinta ba, ko ta mikawa Amurka Wuya ta yi duk abin da ta umarceta.

Kasar Iran ta tsaya kyam akan cewa ba za ta sake tattaunawa da Amurka Kai tsaye ba sai dai ta bayan fage tare da shiga tsakanin wasu Kasashen da ba ruwansu da Rigimar.
Sannan ta shimfida wadannan Sharuddan da sai an cika su za su amince da fara tattaunawar. Sharuddan su ne kamar haka.

1- Dole Yarjejeniyar ta zama Daftarin hukuma na musamman Wanda Majalisun Dokokin Amurka s**a sakawa hannu yadda wani Shugaban Kasar Amurka a gaba ba zai bushi Iska shi kadai ya soke shi ba, kamar yadda Trump ya yi a baya ba.

2- Kafin wata Yarjejeniya ta fara dole ne Kasar Amurka ta cire takunkumi a fannin lafiya da wasu bangarorin.
Sannan bayan an Saka hannu akan Yarjejeniyar a cire dukkan sauran Takunkumomin da aka Kakabawa Iran a baya, ba wasu yan tsiraru ba.

3- A duk lokacin da Amurka ta janye daga Yarjejeniyar, Kasar Iran tana da hakki ta Dora daga wajen da ta tsaya. Ma'ana ta maye gurbin na'urorin tace Ma'adinin Uraniyom da sabbi mafi zama fiye da na baya. Ci gaba da tacewa da Adana Yuraniyom Gadangadan ba tare da wani Kaidi ba.

4- Dole a kyale Kasar Iran ta sake hadewa da Kafar Hada-hadar Kudi ta Duniya ta "SWIFT." Don ta ci gaba da Cinikayya da sauran Kasashen Duniya.

5- Za a kyale Iran ta ci gaba da shirinta na Nukiliya har da tace Uraniyom zuwa Mafi Kololuwar tacewa don 'ayyukan bincike'

6- Babu Yarjejeniya ko wata Ka'ida akan Shirinta na Makamai masu Linzami (Ballistic Missiles). Ko tallafawa Kungiyoyin gwagwarmaya da suke Yankin.

7- Dole a sakarwa Iran da Dukiyarta da aka daskarar a Kasashen Waje.

Idan daya daga cikin wadannan Sharuddan ba a amince da su ba, sake wata Yarjejeniyar Nukiliya zai yi matukar wahala a gaba.
Yawancin wadannan Sharuddan sun faru ne sakamakon rashin cika alkawari da Yaudarar Kasar Amurka a baya.


Ibrahim Daurawa

29/03/2025

Magana ta kare Nuhu Ribadu kaji Sheikh Ibrahim Al'Zakzaky (H) yace ko zakuyi harbi ko ba za suyi ba, baku isa ku hanamu yin addini a yadda muka fahimta ba.. * Allahu Akbar ✌️✊

"Except for Yemen, most Arab countries have remained silent about the massacre of Palestinians, fearing to show their su...
29/03/2025

"Except for Yemen, most Arab countries have remained silent about the massacre of Palestinians, fearing to show their support for Palestine. However, you can see how America and its allies openly stand with Israel, even directly assisting them in war without fear of anyone. In fact, because of Yemen’s support for Palestine, America itself is bombing Yemen! This is truly a disappointment for Muslim nations".

— Sayyid Ibraheem Yaqoub Zakzaky (H)

DAGA ZARIYA: an soma muzaharar Ƙudus a Nijeriya wanda Harkar Musulunci a ƙarƙashin jagorancin Shaikh Ibraheem Yaqoub Zak...
28/03/2025

DAGA ZARIYA: an soma muzaharar Ƙudus a Nijeriya wanda Harkar Musulunci a ƙarƙashin jagorancin Shaikh Ibraheem Yaqoub Zakzaky ke gudanarwa a duk shekara kamar yadda ta saba a garin Zariya ta jihar Kaduna.

Ya zuwa yanzu ƙarfe 2:49 na ranar Juma'a 28 ga watan Ramadan 1446 muzahar na ci gaba da gudana.

Maƙasudin fitowar shi ne domin nuna goyon baya ga al'ummar Falasɗinu, tare da Allah-wadai da ta'addanci da keta haddi da haramtacciyar Isra'ila ke yi wa al'ummar Falasɗinu.

Ga ƙarin hotunan gaggawa yanzu haka.

Address

Gwoza
610106

Telephone

+2348063703717

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Gwoza Media Forum posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Gwoza Media Forum:

Share