LENS TV

LENS TV An online TV channel that brings you reliable News and educative programs.

"National Union of Teachers" (NUT) reshen jihar Jigawa sun tabbatar da wannan takardar cewar tsoffin alkaluma ne da aka ...
22/02/2024

"National Union of Teachers" (NUT) reshen jihar Jigawa sun tabbatar da wannan takardar cewar tsoffin alkaluma ne da aka fidda sama da shekaru uku da s**a gabata tun kafin gwamnantin Jigawa ɗauki malaman J-TEACH, wadda ake shirin bawa takardun aikin din-din-din yanzu, sannan a sake daukar wasu 3,000 wadda za a sake turo su makarantu firamare da ke faɗin jihar Jigawa."

-Garba Muhammad

28/10/2023

An yabawa gwamnatin Jihar Jigawa bisa 6ullo da shirin tsaftar muhalli ta karshen wata a fadin Jihar Jigawa, masu amfani da shafukan sada zumunta a Jihar ne s**a nuna gamsuwarsu da shirin da yadda yake gudana.

Gudanar shirin na tsaftar muhallin dai ya biyo bayan sanya doka da kafa komitocin tsaftar Muhalli wanda gwamnan Jihar Mallam Umar Namadi ya kafa domin tsaftace Jihar.

Ana gudanar da wannan aiki a kowacce ranar Asabat ta karshen wata, kuma ko a yau shirin ya samu tallafin shugabannin kananan hukumomi, yan kwamati, jami'an gwamnati da kuma matasa da s**a bada gudunmawar lokacinsu da karfinsu.

06/10/2023

Join our WhatsApp channel

30/09/2023

J-TEACH PROGRAM

Jigawa State Ministry of Higher Education, Science and Technology wishes to inform the. J- teach applicants in the state that, the ministry has released the list of the successful applicants who will be posted to senior secondary schools across the state.

The announcement is therefore informing the successful applicants to check their names at the nearest zonal education offices.

Ministry of Higher Education is therefore inviting the successful. j-teach applicants to attend a one day training scheduled to take place
On Tuesday 3rd, October, 2023 .
Venue:: Manpower Development Institute. ( MDI ) Dutste.
Time::10:00am.

His Excellency, the Executive Governor, Jigawa State ,Malam Umar Namadi is expected to be the special guest of Hono,r who will also Flagg off the distribution of the engagement letter to the beneficiaries.

Announcer
Wasilu Umar Ringim
Public Relations Officer
Min. of Higher Education, Science and Technology
Jigawa State

01/08/2023

AN ƊAUKI MATAKI KAN SHUGABANNIN ASIBITIN GUMEL

Biyo bayan ziyarar bazata da Gwamna Mallam Umar Namadi ya kai babban asibitin Gumel a ranar Juma’ar da ta gabata, dangane da yadda gwamnan ya sami asibitin cikin wani mummunan yanayi, yanzu haka an ɗauki matakan ladabtarwa ga manyan jami’an gudanarwa na wannan asibiti.

Matakan sun haɗa da rushe hukumar gudanarwar asibitin nan take da kuma mayar da ɗaukacin manyan jami’an wannan asibitin zuwa hedikwatar ma’aikatar da ke Dutse inda za su jira hukuncin da zai hau kansu bayan an kammala bincike.

Jami’an da abin ya shafa sun haɗa da: Medical Director, Director Clinical Services, DAF, H.O.D Pharmacy, H.O.D Laboratory da kuma Accountant.

Idan ba a manta ba, a lokacin ziyarar Gwamnan, inda ya kewaya sassa daban-daban a cikin asibitin ya gane wa idonsa yadda ake tursasa wa marasa lafiya biyan kuɗin kayayyakin da ya kamata a samar da su a asibitin. Alal misali, Gwamnan ya tattauna da marasa lafiya da dama waɗanda s**a tabbatar masa da cewa ana tilasta musu biyan kuɗi har naira 7,000 kafin a ɗauki jinin da ‘yan uwansu s**a ba su gudunmuwar sa. Haka kuma ya gano cewa hatta auduga da ake amfani da ita asibitin marasa lafiyar ne suke saye da kuɗinsu, wanda kuma hakan ya saɓawa manufar gwamnatin jiha na samar da waɗannan abubuwa kyauta musamman ga yara ‘yan ƙasa da shekaru biyar da kuma mata masu shayarwa.

Baya ga wannan kuma Gwamnan ya gane wa idonsa yadda asibitin yake fama da matsalar isasshen ruwan famfo a duk kuwa da kuɗaɗen da gwamnati take samarwa asibitin a kowane wata. Bugu da ƙari kuma, Gwamnan bai sami shugabannin asibitin a bakin aikinsu ba a lokacin wannan ziyarar.

To a sakamakon haka ne Gwamna Mallam Umar Namadi ya yi taron gaggawa da manyan jami’an ma’aikatar lafiya da na hukumomin da ke ƙarƙashinta a safiyar litinin, inda nan take ya umarci kwamishinan ma’aikatar da ya ɗauki matakan ladabtarwa akan wannan halayya ta ma’aikatan kiwon lafiyar.

Government House Media Office

Address

Hadejia

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when LENS TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to LENS TV:

Share

Category