Hadejia Emirate

Hadejia Emirate Official Page of Hadejia Emirate

MOTTO: Majestic City of Stallion/Birnin doki
TWITTER
INSTAGRAM

Mai martaba sarkin Hadejia Alh. Dr. Adamu Abubakar Maje CON ya karbi bakuncin tsohon Dan takarar gwamnan jigawa karkashi...
30/07/2025

Mai martaba sarkin Hadejia Alh. Dr. Adamu Abubakar Maje CON ya karbi bakuncin tsohon Dan takarar gwamnan jigawa karkashin jam'iyar PDP Mustapha Sule Lamido (Santurakin Dutse) da mataimakin sa, da Shugabannin Jam'iyar da tsofin kwamishinini da sauran al'umma bisa masa ta'aziyar rasuwar 'Yar sa Khadija Adamu Maje.

Allah ya jikan tada Rahama Ameen🙏

Mai martaba sarkin Hadejia Alh. Dr. Adamu Abubakar Maje CON ya karbi bakuncin mai Girma gwannan Jigawa Malam Umar Namadi...
27/07/2025

Mai martaba sarkin Hadejia Alh. Dr. Adamu Abubakar Maje CON ya karbi bakuncin mai Girma gwannan Jigawa Malam Umar Namadi Danmodi bisa masa ta'aziyar rasuwar 'Yar sa Khadija Adamu Maje.

Allah ya jikan tada Rahama Ameen🙏

Allah yayiwa Khadijah Adamu Abubakar Maje rasuwa (Nana), 'Ya ga mai martaba sarkin Hadejia, Za a gabatar da sallar Jana'...
23/07/2025

Allah yayiwa Khadijah Adamu Abubakar Maje rasuwa (Nana), 'Ya ga mai martaba sarkin Hadejia, Za a gabatar da sallar Jana'iza a Kofar Fada Mai martaba Sarki 4:00pm a yau Laraba.

Allah yayi mata rahama yasa mai ceto ce Amin.

GAISUWAR TA'AZIYAMai martaba sarkin Hadejia Alh. Dr. Adamu Abubakar Maje CON ya ziyarci Mai martaba  sarkin Daura Alh. D...
18/07/2025

GAISUWAR TA'AZIYA
Mai martaba sarkin Hadejia Alh. Dr. Adamu Abubakar Maje CON ya ziyarci Mai martaba sarkin Daura Alh. Dr. Umar Faruq Umar, Mamman Daura da Iyalan marigayi tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari bisa yi musu ta'aziya rashin da akayi na tsohon shugaban kasar.

Muna Addua Allah ya jikan sa da Rahama yasa Aljannar fiddausi ce makomar sa Ameen.

Allah yajikan Tsohon Shugaban kasar Nigeria Muhammadu Buhari, Allah ya yafe masa kusakurensa, Allah yasa Aljanna ce mako...
13/07/2025

Allah yajikan Tsohon Shugaban kasar Nigeria Muhammadu Buhari, Allah ya yafe masa kusakurensa, Allah yasa Aljanna ce makomar sa Ameen 🙏

Mai Martaba Sarkin Hadejia Alh. Dr. Adamu Abubakar Maje CON ya halarci taron tseran dawaki na SAHEL SAVANNAH SERIES 2025...
12/07/2025

Mai Martaba Sarkin Hadejia Alh. Dr. Adamu Abubakar Maje CON ya halarci taron tseran dawaki na SAHEL SAVANNAH SERIES 2025 a Murtala Square dage Birnin Kaduna.

Wane Suna Ake Kiran Wannan Gini Na Cikin  Fada da Shekarar da aka Gina Shi?
10/07/2025

Wane Suna Ake Kiran Wannan Gini Na Cikin Fada da Shekarar da aka Gina Shi?

Falalar Azumin Tasu'a Da AshuraGobe, Juma’a, 4 ga watan Yuli 2025, ita ce tara ga watan Muharram, rana da ake kira Tasu’...
04/07/2025

Falalar Azumin Tasu'a Da Ashura

Gobe, Juma’a, 4 ga watan Yuli 2025, ita ce tara ga watan Muharram, rana da ake kira Tasu’a a cikin harshen Larabci. Wannan rana na ɗaya daga cikin kwanaki masu albarka da Manzon Allah ﷺ ya nuna darajarsu cikin hadisai sahihai, musamman idan aka yi azumi a cikinta tare da ranar Ashura, wato ranar goma.

An karɓo daga Ibn Abbas (RA) cewa: “Lokacin da Manzon Allah ﷺ ya zo Madina, ya tarar da Yahudawa suna azumin ranar Ashura. Sai ya ce: Me yasa kuke yin hakan? S**a ce: Wannan rana ce da Allah ya ceci Musa da mutanensa, sai Musa ya yi azumi domin godiya. Sai Annabi ﷺ ya ce: Mu muna da cancanta fiye da su wajen bin Musa.” Sai ya azumta kuma ya umurci musulmi da su azumta. (Sahih Muslim: 1130; Bukhari: 2004)

Daga nan ne Manzon Allah ﷺ ya bayyana cewa yana da niyya idan ya rayu zuwa shekara mai zuwa, zai yi azumin Tasu’a da Ashura tare. Ya ce: “Idan na rayu zuwa shekara mai zuwa, lallai zan yi azumin ranar tara (Tasu’a).” (Sahih Muslim: 1134) Wannan yana nuni da hikimar bambanta musulmi da Yahudawa a ibada, da kuma ƙara daraja ga azumin.

Azumin Ashura da Tasu’a yana da girma matuƙa. A wani hadisi daga Abu Qatada, Manzon Allah ﷺ ya ce: “Ina fatan Allah zai gafarta zunuban shekara guda da ta gabata saboda azumin Ashura.” (Sahih Muslim: 1162). Malamai sun ƙara bayani cewa wannan falala na shafe zunuban saghā’ir – wato ƙananan zunubai – ne kawai, amma duk da haka yana nuni da girman wannan rana.

A mahangar fikihu, malamai kamar Imam Nawawi, Ibn Rajab, da Ibn Qudamah sun yi ittifaki cewa azumtar Tasu’a da Ashura tare ya fi daraja fiye da yin Ashura kawai, kamar yadda Manzon Allah ﷺ ya ƙudurta. Kuma wannan ya zamo hanya mai kyau ta sabunta ibada da tsarkake zuciya ga sabon shekara ta Hijira.

Musulmi da ya azumci gobe, ya tanadi tsarkakakkiyar niyya, kuma ya guji yin karya, zargi, ko munanan halaye. Ana kuma karfafa yin azumin Ashura (rana ta goma) a ranar Asabar, domin cikar sunnah da samun falala gaba ɗaya.

A ƙarshe, wannan wata ne da Allah Ya karrama, rana ce da Manzon Allah ﷺ ya fifita, azumi ne da ke gogewa da yafe zunubai. Ya kamata musulmi ya yawaita ibada, istighfar da kyautatawa. Allah Ya karɓi ibadunmu, Ya tsarkake zukatanmu, Ya tabbatar mana da falalar wannan muhimmiyar rana. Ameen.

Mai martaba sarkin Hadejia Alh. Dr. Adamu Abubakar Maje CON ya ziyarci iyalan marigayi Aminu Dantata bisa yi musu ta'azi...
03/07/2025

Mai martaba sarkin Hadejia Alh. Dr. Adamu Abubakar Maje CON ya ziyarci iyalan marigayi Aminu Dantata bisa yi musu ta'aziyar rashin da akayi na, Baba Aminun.

Muna addua Allah ya jikan sa da Rahama yasa Aljannar fiddausi ce makomar sa Ameen. 🙏

Address

Emir's Palace Road
Hadejia
171101

Telephone

+2348033970270

Website

https://bit.ly/Hja22

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hadejia Emirate posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share