10/05/2026
Kwamitin Zakka da Waqafi na Masarautar Hadejia, ƙarƙashin jagorancin Mai girma Talban Hadejia Brr. Abdulwahab Tahir Fatahu, sun karɓi baƙuncin Kwamitin Zakka na Masarautar Fika, waɗanda s**a kai wa Mai Martaba Sarkin Hadejia, Alhaji Dr. Adamu Abubakar Maje, CON, ziyarar girmamawa tare da neman ƙarin ilimi da musayar ƙwarewa a fannin gudanar da harkokin zakka.
Ziyarar ta kasance ne duba da yadda Masarautar Hadejia ke kan gaba a cikin masarautun ƙasar nan wajen tsara da kula da harkokin zakka da waqafi, musamman ta fuskar yadda ake tattarawa, sarrafawa da kuma rabon zakka ga waɗanda s**a cancanta.
A ƙarshe, Kwamitin Zakka na Masarautar Fika sun bayyana jin daɗinsu tare da godewa Masarautar Hadejia bisa kyakkyawar tarba da kuma muhimman bayanai da shawarwari da s**a samu, waɗanda s**a bayyana cewa za su taimaka matuƙa wajen inganta ayyukansu na zakka da waqafi.