Hadejia Emirate

Hadejia Emirate Official Page of Hadejia Emirate

MOTTO: Majestic City of Stallion/Birnin doki
TWITTER
INSTAGRAM

Ya Allah, Ka jikanki Hon. Abba Anas Adamu (Laushi) da rahama, Ka gafarta masa zunubansa, Ka sa Aljannatul Firdausi ta za...
12/05/2026

Ya Allah, Ka jikanki Hon. Abba Anas Adamu (Laushi) da rahama, Ka gafarta masa zunubansa, Ka sa Aljannatul Firdausi ta zama makomarsa. Ya Allah Ka kawo zaman lafiya mai dorewa a Najeriya, Ka kuma kubutar da duk waɗanda ke hannun masu garkuwa da mutane.

Kwamitin Zakka da Waqafi na Masarautar Hadejia, ƙarƙashin jagorancin Mai girma Talban Hadejia Brr. Abdulwahab Tahir Fata...
10/05/2026

Kwamitin Zakka da Waqafi na Masarautar Hadejia, ƙarƙashin jagorancin Mai girma Talban Hadejia Brr. Abdulwahab Tahir Fatahu, sun karɓi baƙuncin Kwamitin Zakka na Masarautar Fika, waɗanda s**a kai wa Mai Martaba Sarkin Hadejia, Alhaji Dr. Adamu Abubakar Maje, CON, ziyarar girmamawa tare da neman ƙarin ilimi da musayar ƙwarewa a fannin gudanar da harkokin zakka.

Ziyarar ta kasance ne duba da yadda Masarautar Hadejia ke kan gaba a cikin masarautun ƙasar nan wajen tsara da kula da harkokin zakka da waqafi, musamman ta fuskar yadda ake tattarawa, sarrafawa da kuma rabon zakka ga waɗanda s**a cancanta.

A ƙarshe, Kwamitin Zakka na Masarautar Fika sun bayyana jin daɗinsu tare da godewa Masarautar Hadejia bisa kyakkyawar tarba da kuma muhimman bayanai da shawarwari da s**a samu, waɗanda s**a bayyana cewa za su taimaka matuƙa wajen inganta ayyukansu na zakka da waqafi.

Murnar Cika Shekara 40 A Karagar MulkiJiya Asabar 9th May 2026 Aka Gudanar Da Taro Tare Da Addu'oi Na Murnar Cika Shekar...
10/05/2026

Murnar Cika Shekara 40 A Karagar Mulki

Jiya Asabar 9th May 2026 Aka Gudanar Da Taro Tare Da Addu'oi Na Murnar Cika Shekara Arbin na Mai Girma Sarkin Ban Hadejia Hakimin Ayama. Alh. Haruna Muhammad Bashari.

Allah Ya Kara Lafiya Ameen

Mai Martaba Sarkin Hadejia, Alhaji Dr. Adamu Abubakar Maje, CON, ya karɓi bakuncin sabon Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar...
09/05/2026

Mai Martaba Sarkin Hadejia, Alhaji Dr. Adamu Abubakar Maje, CON, ya karɓi bakuncin sabon Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Jigawa, Haruna Yahaya, wanda ya kai masa ziyarar ban girma a fadarsa a yau.

CP Haruna Yahaya ya bayyana cewa ziyarar tasa ita ce domin gabatar da kansa ga Mai Martaba Sarkin a matsayin sabon Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar, tare da yi masa bayani kan dabarun da yake shirin amfani da su wajen ƙarfafa tsaro a faɗin Jigawa.

A nasa jawabin, Mai Martaba Sarkin Hadejia ya jaddada aniyar masarautar wajen ci gaba da bai wa rundunar ‘yan sanda cikakken goyon baya domin su gudanar da aikinsu yadda ya kamata wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Rayuwa tamkar tafiya ce mai gajeren zango. Duk wanda ka gani yau, wata rana ba zai kasance ba. Ka yi amfani da lokacinka...
09/05/2026

Rayuwa tamkar tafiya ce mai gajeren zango. Duk wanda ka gani yau, wata rana ba zai kasance ba. Ka yi amfani da lokacinka wajen aikata alheri, domin kalma mai dadi na iya warkar da zuciyar da ke ciwo, kuma murmushi naka na iya zama farin cikin wani.

Mai Martaba Sarkin Hadejia, Alhaji Dr. Adamu Abubakar Maje, CON, ya ziyarci Mai Girma Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Dr. Um...
08/05/2026

Mai Martaba Sarkin Hadejia, Alhaji Dr. Adamu Abubakar Maje, CON, ya ziyarci Mai Girma Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Dr. Umar A. Namadi, FCA, a gidan Gwamnatin Jigawa dake Dutse.

07/05/2026

Ada Mai Zamani 👑✊

05/05/2026

Mai Girma Dan Madamin Hadejia

Address

Emir's Palace Road
Hadejia
171101

Telephone

+2348033970270

Website

https://bit.ly/Hja22

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hadejia Emirate posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share