14/09/2025
SARKIN HADEJIA NA GOMA SHA SHIDA YA CIKA SHEKARA ASHIRIN DA UKU A GADON SARAUTAR HADEJIA......
A ranar asabat 14/september/2002, aka nada Alhaji Adamu Abubakar a matsayin sarkin Hadejia na goma sha shida, bayan rasuwar Sarkin Hadejia Alh. Abubakar maje Haruna. Anyi wannan nadi ne karfe goma na safe a harabar fadar Hadejia, karkashin jagorancin Galadiman Hadejia na wancan lokacin marigayi Alh. Habibu Adamu.
A ranar Asabat 29/3/2003, akayi taron bada sanda ga mai martaba sarkin Hadejia, a lokacin gwamnatin wancan lokacin ta Ibrahim saminu Turaki, wadda taron ya samu halartar manyan Sarakuna na ciki da wajen kasar nan. wannan rana tana da matukar muhimmanci ga mutanen Hadejia, musamman a wannan zamani domin ba duk dan shekara kasa da Talatin bane zai adar lokacin da aka yi irin wannan taro a masarautar Hadejia.
Bayan an nada shi a matsayin Sarkin Hadejia na goma sha shida, hawan sa na farko a matsayin Sarkin Hadejia shine Hawan Sallar Azumi a watan December 2002, sannan a watan february 2003, bai samu damar Hawan Sallar Layya ba, domin shi aka baiwa Amirul-hajj na wannan shekarar.
A watan june na 2003 mai martaba Sarkin Hadejia Alhaji Adamu Abubakar yayi hawan Sallar Maulidi, wadda shine hawan maulidi na farko a matsayinsa na Sarkin Hadejia, ko zamu iya samun wadda zai fada mana ranar?
Mai martaba Sarkin Hadejia Alhaji Adamu Abubakar Maje shine ya nada Hakimai kamar haka....
1.Alhaji Baffa Adamu, a matsayin Dan Galadiman Hadejia Hakimin Waje
2. Alhaji Umar Ibrahim, a matsayin Sarkin Dawaki Hakimin Kirikasamma
3. Alh. Ilyasu S Ibrahim A matsayin Katuka na biyu Hakimin Turabu.
sannan ya nada Marigayi Chiroman Hadejia Alhaji Aminu Haruna da Tafidan Hadejia Alhaji Kaila Umar, Sardauna Alhaji Abdul-Aziz Umar. Wai ranar yaushe aka yi wannan nadin?
Madaki Alhaji Haruna Gauyama, Dokaji Alhaji Mohd. Saleh Hakimin Mallam Maduri, Sa'i na biyu Hakimin Garungabas
Magayaki Alhaji Muhammad Nabagara, Koguna Alhaji Haruna Idris.
Ranar Asabat 31/7/2004 Mai martaba Sarki ya nada Hakimai kamar haka...
1. Alh. Ibrahim Suleiman, a matsayin Wambai Hadejia Hakimin Bulangu
2. Alh. Adamu Haruna, a matsayin Sarkin Kudu Hakimin Kwatalo
3. Alh. Baffale Muhd,a matsayin Dan Ruwatan Hadejia Hakimin Atafi na biyu
4. Col. Jibrin Hassan, a matsayin Sarkin Yakin Hadejia
Ranar 5/August/2004, Mai martaba Sarkin Hadejia ya nada Baraden Hadejia Alhaji Haruna Ginsau
Wannan Hawan Maulidin shine Hawa na goma sha shida da Sarkin Hadejia Alhaji Adamu Abubakar yayi a matsayinsa na Sarkin Hadejia, a iya bincike na kuma ban ce ya taba kuskurewa Hawan Mauludi ba, ko zaku iya tuna akwai Maulidin da tazo Sarkin Hadejia bai samu Hawa ba?
Ranar Laraba 20/April/2005, Mai martaba Sarkin Hadejia Alhaji Adamu Abubakar Maje yayi hawan Maulidi, kuma a wannan Maulidin ne ya kara Hawa ya zama guda uku, wato hawan Sallah, hawan Bariki, da hawan Ziyara. daga lokacin da Sarki ya kara hawan ziyara zuwa yau hawan ziyara nawa yayi?
Dauda Shehu tare da me zaku iya tunawa game da shekara goma sha shida din nan? Allah ya daukaka masarautar Hadejia.