13/08/2026
Mai Martaba Sarkin Hadejia, Alhaji (Dr.) Adamu Abubakar Maje, CON, ya kai ziyarar ta’aziyya ga Mai Martaba Sarkin Ringim, Alhaji Sayyadi Muhammadu, CON, bisa rasuwar matar sa Hajiya Aisha Sayyadi Mahmud.
A yayin ziyarar, Mai Martaba Sarkin Hadejia ya jajanta wa Mai Martaba Sarkin Ringim tare da iyalansa bisa wannan babban rashi.
Haka kuma, ya yi addu’ar Allah Ya jikanta da rahama, Ya gafarta mata kura-kuranta, Ya sa Aljannatul Firdausi ce makomarta, tare da bai wa iyalanta da ‘yan uwanta hakurin jure wannan rashi.
Amin Ya Allah.
13/08/2026