Mairakumi

Mairakumi LABARAI DA DUMI-DUMINSU AKO YAUSHE

DA DUMI-DUMI: Gargaɗi ga ƙasashen Afirka musamman Najeriya da Arewa: A yi hattara da magungunan tari daga IndiyaGwamnati...
09/10/2025

DA DUMI-DUMI: Gargaɗi ga ƙasashen Afirka musamman Najeriya da Arewa: A yi hattara da magungunan tari daga Indiya

Gwamnatin Indiya ta gano wasu manyan matsaloli wajen gwajin magungunan tari da wasu kamfanonin ƙasar s**a ƙera, bayan da aka danganta mutuwar yara 17 da shan magungunan da s**a ƙunshi sinadarin diethylene glycol, wani guba mai haddasa lalacewar koda, jijiya da ma mutuwa.

Rahoton majiyar Muryoyi ta jaridar Reuters ya bayyana cewa magungunan da ake bincike sun haɗa da Coldrif, Respifresh, da RELIFE, waɗanda aka samu da sinadarin da ya fi na daidaitaccen ƙima sau 500.

Muryoyi ta ruwaito wannan matsala ta janyo hankalin Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) wadda ta yi gargadin cewa Indiya ba ta kula sosai wajen gwajin magungunan kafin su shiga kasuwa, abin da ke iya sa su yadu zuwa ƙasashen waje, ciki har da ƙasashen Afirka.

Masana sun ba da shawarar cewa jama’a su daina siyan magunguna ba tare da shawarar likita ba, kuma su tabbatar cewa kowanne magani da suke saya yana da rajista daga hukumar NAFDAC domin guje wa haɗarin guba da mutuwa.

KUN SAN MAGUNGUNAN?

ABIN KOYI: Yadda Wani Matashi Ya Kwashe Shekaru Sama Da 25 Yana Yi Wa Mahaifiyarsa Tallar 'Yar TsalaDaga Aji Kima Hadeji...
03/10/2025

ABIN KOYI: Yadda Wani Matashi Ya Kwashe Shekaru Sama Da 25 Yana Yi Wa Mahaifiyarsa Tallar 'Yar Tsala

Daga Aji Kima Hadejia

Mabo ɗan Mai Tsala matashi ne dan asalin karamar hukumar Hadejia da ya shafe sama da shekaru ashirin da biyar (25) yana taimakawa mahaifiyarsa wajen tallar tsala. Duk da cewa akwai damarmaki da dama da zai iya tsunduma cikinsu, ya zaɓi wannan sana’a saboda tarbiyya da biyayya da ya ke yiwa mahaifiyarsa.

Wannan lamari ya nuna irin darajar da ya baiwa mahaifiyarsa da kuma muhimmancin taimakon iyaye. A yau da yawa daga cikin matasa suna guje wa irin waɗannan ayyuka, suna ɗaukar su a raine. Amma Mabo ya zama abin koyi, domin ya fahimci cewa duk wata sana’a da ake yi da gaskiya da amana tana da daraja.

Abin da ya ke yi darasi ne ga sauran matasa:

(a) A taimaki iyaye domin albarkarsu ta tabbata.

(b) A yi koyi da juriya da biyayya.

A fahimci cewa ba'a raina sana'a komin kankantarta, sana’a ba laifi ba ce, illa ma hanyar samun halal da dogaro da kai.

Lamarin Mabo darasi ne da ya kamata matasa su ɗauka a matsayin izina wajen nuna kauna, biyayya da kuma taimakon iyaye.

Sheikh Bala Lau Ya Yi Kira da A Sasanta Rikicin Kano Cikin Lumana, Ya Yabi DSS Kan Rawar da Ta TakaShugaban Jama’atu Iza...
01/10/2025

Sheikh Bala Lau Ya Yi Kira da A Sasanta Rikicin Kano Cikin Lumana, Ya Yabi DSS Kan Rawar da Ta Taka

Shugaban Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS) ta tarayyar Nigeria, Ash-Sheikh Dr. Imam Abdullahi Bala Lau , ya yi kira da a kwantar da hankali da nuna haƙuri wajen tafiyar da rikicin addini da ke ci gaba a Kano, inda ya gargadi mutane da su guji amfani da lamarin don haifar da rarrabuwar kawuna a cikin al’ummar Musulmi.

A lokacin da yake gabatar da wa’azi a makon jiya wajen taron ƙungiyar ‘Federation of Ahlusunnah Organization in Nigeria’ (FAFSON) da aka gudanar a Ibadan, Jihar Oyo, Sheikh Bala Lau ya yaba da hangen nesa da kwarewar Darakta Janar na Hukumar Tsaro na Farin kaya (DSS), Mista Tosin Ajayi, wajen tabbatar da lamarin zuwa hanyar zaman lafiya ba tare da zuwa kotu ba.

“Ina yabawa shugabancin DSS bisa tabbatar da cewa an tafiyar da wannan al’amari cikin hikima da lumana. Kai shi kotu zai iya tada jijiyoyin wuya kuma ya tsawaita rikicin. Abin da al’ummar Musulmi ke buƙata a yanzu shi ne hikima, haƙuri da haɗin kai,” in ji shi.

Malam ya kuma yi kira ga Gwamnatin Jihar Kano da ta ci gaba da zama tsaka-tsaki, yana jaddada cewa shiga gefen kowane ɓangare na iya ƙara rarrabuwar kai da lalata zaman lafiya a jihar.

“A irin wannan lokaci, bai kamata gwamnati ta nuna tana goyon bayan ɓangare guda ba. Adalci da gaskiya suna buƙatar a tsaya a tsaka-tsaki. Aikinmu a matsayin shugabanni shi ne kiyaye zaman lafiya, ba ƙara wa rikici wuta ba,” in ji Sheikh Bala Lau.

Jawabansa sun biyo bayan ƙorafe-ƙorafe da aka gabatar tare da mayar da martani ga Majalisar Shura ta Jihar Kano kan zargin kalaman batanci da ake alakanta Shi da Sheikh Lawan Shuaibu Abubakar Triumph. Majalisar ta bayyana cewa za ta saurari masu ƙorafi da kuma malamin kafin ta ba da wani shawari ga gwamnati.

Sai dai Sheikh Bala Lau ya yi kira ga Musulmi da kada su bari zarge-zargen su rinjaye su, yana gargadi cewa irin waɗannan muhawarori idan ba a kula ba za su iya bata sunaye kuma su kau

DA DUMI-DUMI: Sabon rahoto ya gargadi Najeriya kan raguwar buƙatar Mai a Duniya - An nemi ta mayar da hankali gun noma D...
30/09/2025

DA DUMI-DUMI: Sabon rahoto ya gargadi Najeriya kan raguwar buƙatar Mai a Duniya - An nemi ta mayar da hankali gun noma

Daga Muryoyi

Wani sabon rahoto da ƙungiyoyi Climate Strategies da Salzburg Global s**a wallafa ya bayyana cewa Najeriya na fuskantar matsin tattalin arziki sakamakon raguwar buƙatar mai a duniya, abin da zai iya jefa tattalin arzikin ƙasar cikin matsala.

Rahoton ya bukaci gwamnati ta mai da hankali kan fitar da kayayyakin da ba na mai ba kamar noma, masana’antu, ma’adanai da makamashi, da sauransu domin rage dogaro da mai da kuma kare ayyukan yi da kudaden shiga a nan gaba.

Muryoyi ta ruwaito rahoton, ya jaddada cewa dogaro da ƙarfin man fetur da gas yana sa Nigeria zama mai rauni yayin da kasashen duniya ke ƙara yin nisa

Da dumi'dumi: Gwamnatin Tarayya ta Samu Naira Biliyan 250bn Don Gina Jirgin ƙasa mai Anfani Lantarki a Kaduna da Kano.Gw...
29/09/2025

Da dumi'dumi: Gwamnatin Tarayya ta Samu Naira Biliyan 250bn Don Gina Jirgin ƙasa mai Anfani Lantarki a Kaduna da Kano.

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ta samu kimanin naira biliyan 250 don gina jirgin ƙasa mai sauƙi (Light Rail) a jihohin Kaduna da Kano. Wannan shirin, a cewar gwamnati, zai taimaka wajen rage cunkoson hanyoyi da kuma inganta sufuri a Arewa maso Yamma.

Gwamnati ta ce aikin zai inganta tattalin arziki da sauƙaƙa zirga-zirga ga al’umma, musamman ma tsakanin manyan biranen nan guda biyu.

Idan Zà A Kàshè 'Yañ Sandà Dari A Matsayin Hukuncin Kashe Danà Da Aka Yì, Bai Zai Yì Daidai Da Ran Dan Nawa Ba, Domin Ni...
29/09/2025

Idan Zà A Kàshè 'Yañ Sandà Dari A Matsayin Hukuncin Kashe Danà Da Aka Yì, Bai Zai Yì Daidai Da Ran Dan Nawa Ba, Domin Ni Ďànà Hafizin Kùr'anì Nè, Cewar Mahaifin Salim, Wanda Ya Mutu A Komar 'Yañ Sanda A Kano

Mahaifin nasa ya cigaba da cewa zai cigaba da bibiyar binciken da ake yi koda komai nasa zai kare ne, saboda an cutar da su.

Ka fara kawo karshen Ta'addanci a Nageriya Kafin Neman muƙamin tsaro a majalisar Dinkin Duniya -Jam'iyyar ADC ga Shugaba...
28/09/2025

Ka fara kawo karshen Ta'addanci a Nageriya Kafin Neman muƙamin tsaro a majalisar Dinkin Duniya -Jam'iyyar ADC ga Shugaba Tinubu.

Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta soki gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan yadda ta ke neman samun kujera ta dindindin a Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya (UN Security Council), alhali kuma ana fama da matsalar tsaro a cikin gida.

ADC ta ce kafin gwamnatin Tinubu ta nemi irin wannan matsayi a duniya, ya kamata ta mai da hankali kan magance matsalolin tsaro da tsare-tsaren da s**a addabi ‘yan Najeriya – musamman hare-haren ‘yan ta’adda, garkuwa da mutane da kuma matsalolin rashin tsaro a sassa daban-daban na ƙasar.

Jam’iyyar ta kuma yi kira ga gwamnatin Tarayya da ta zuba jari sosai a fannin tsaro, ta ƙarfafa dakarun tsaro, sannan ta samar da hanyoyin da za su kawo sauƙi ga rayuwar al’umma kafin ta yi irin wannan babban buri a matakin duniya.

"A Jigawa dai, lalacewar siyasata ba ta kai na kula gajiyayyen maula kamar Nafi'u Osamatu Kogga ba, ni Dankuda Kabo duk ...
28/09/2025

"A Jigawa dai, lalacewar siyasata ba ta kai na kula gajiyayyen maula kamar Nafi'u Osamatu Kogga ba, ni Dankuda Kabo duk girmanka a Jigawa, idan ka taba Danmodi, zan taba Iyayan gidanka duk girmansu" - Jamilu Dankuda Kabo.

Gwamnatin Tarayya Ta Karyata Ikirarin Kisan Kare-dangi Kan Kiristoci a Najeriya.Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta bayyana c...
28/09/2025

Gwamnatin Tarayya Ta Karyata Ikirarin Kisan Kare-dangi Kan Kiristoci a Najeriya.

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta bayyana cewa ba gaskiya ba ne kuma yaudara ce rahotannin da wasu kafafen ƙasashen waje ke yadawa cewa ana kisan kare-dangi na addini ga Kiristoci a ƙasar.

Gwamnatin ta ce waɗannan ikirari na ƙarya ne kuma suna nufin bata sunan Najeriya a idon duniya. Ta kuma bayyana cewa Najeriya ƙasa ce mai yawan al’umma daban-daban da addinai daban-daban waɗanda ke zaune tare cikin lumana, tare da samun kariya ta doka ga kowa ba tare da nuna bambancin addini ba.

Haka kuma gwamnatin ta yi kira ga ‘yan ƙasa da su guji yarda da irin waɗannan rahotanni marasa tushe kuma su ci gaba da zaman lafiya da juna domin ci gaban ƙasa.

DA DUMI-DUMI: An kori Rev. Sister Kinse bayan ta fallasa, Fastoci da shuwagabannin coci na kwana da suRev. Sister Annast...
28/09/2025

DA DUMI-DUMI: An kori Rev. Sister Kinse bayan ta fallasa, Fastoci da shuwagabannin coci na kwana da su

Rev. Sister Annastasia Kinse ta zargi wasu firistoci da shugabannin coci da zaluntar ‘yan’uwa mata (nuns), tana mai cewa "mu ba matan ku ko masoyanku ba ne, mata ne na Allah" wannan zargi nata ya jawo cece-kuce wanda, har kungiyar “Congregation of Mother of Perpetual Help” ta sallame ta, ta kuma ba ta Naira dubu ₦100,000 tare da kwace rigar addininta.

Sister Kinse ta ce duk da hakan, tana nan a matsayin Katolika mai kishin addininta "amma dai ba zata ki fallasa gaskiya ba"

A ganim ku ya dace a kore ta saboda ta yi fallasa?

27/06/2025

Address

Hadejia

Telephone

+2349030510709

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Mairakumi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Mairakumi:

Share