Farin Wata News

Farin Wata News ONLY POST YOU CAN TRUST

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnatin Jihar Adamawa Ta Haramta Manna Fosta A Gine-Ginen Gwamnati Da Kayayyakin Jama’a A Faɗin JiharKwa...
14/11/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnatin Jihar Adamawa Ta Haramta Manna Fosta A Gine-Ginen Gwamnati Da Kayayyakin Jama’a A Faɗin Jihar

Kwamishinan Muhalli na Jihar Adamawa, Mohammed Sadiq, shi ne ya bayyana haramcin na manna duk wani nau’in hoto a kan gine-ginen gwamnati da sauran muhimman kayayyakin jama’a a fadin Jihar.

Ya bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis, 13 ga Nuwamba, 2025, a ɗakin taro na Ma’aikatar Muhalli da Albarkatun Ƙasa da ke Yola, k**ar yadda Dokin Ƙarfe TV ta ruwaito.

A cewar Kwamishinan, Ma’aikatar ta lura da yadda mutane, ƙungiyoyi, da cibiyoyi ke ƙara yawaita manna tallace-tallace, na siyasa da na kasuwanci, a wuraren gwamnati da tituna, wanda ya ce hakan na ɓata fasalin birane, na karya dokokin tsaftar muhalli, kuma yana kawo cikas ga ƙoƙarin gwamnati na tabbatar da tsafta da tsari a jihar.

Ya bayyana cewa daga yanzu an haramta manna fosta, tambari, ko banoni a kan gine-ginen gwamnati, sandunan hasken t**i, allunan bayanai, shataletale, da sauran wuraren jama’a a duk faɗin jihar. Ya kuma gargaɗi jam’iyyun siyasa, ƙungiyoyin addini, ƴan kasuwa da jama’a gaba ɗaya da su kauce wa wannan aiki da ya kira saɓawa doka.

Kwamishinan ya kuma yi gargaɗi cewa duk wanda aka k**a yana keta wannan sabon umarni zai fuskanci hukunci, tare da cire kayan tallan da kansa kuma a caje shi kuɗin aikin cirewar, bisa tanadin dokokin Kare Muhalli da Tsafta a Jihar Adamawa.

Ya ce Ma’aikatar na ci gaba da jajircewa wajen samar da muhalli mai tsafta, lafiya, da ɗorewa ga mazauna jihar, tare da neman goyon bayan jama’a domin kare martaba da ingancin mahalli a Adamawa.

Tsohon shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki, ya shawarci jam’iyyar PDP ta dakatar da shirin gudanar da babban taron...
13/11/2025

Tsohon shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki, ya shawarci jam’iyyar PDP ta dakatar da shirin gudanar da babban taronta na ƙasa a jihar Oyo sak**akon sabanin umarnin kotuna kan taron.

Saraki ya bayyana haka ne a shafinsa na X, inda ya ce umarnin kotuna huɗu masu karo da juna kan taron na iya jawo rikici da shakku kan sahihancin duk wani matakin da za a ɗauka daga baya.

A yanzu akwai ƙararraki uku a kotuna daban-daban da ke bayar da umarnin dakatarwa da ci gaba da taron, yayin da jam’iyyar ke shirye-shiryen gudanar da shi a ranakun 15 da 16 ga watan Nuwamba.

Ministan Abuja, Nyesom Wike, da tsohon gwamnan Jigawa, Sule Lamido, na daga cikin waɗanda s**a kai ƙarar jam’iyyar kan batun taron.

DA DUMI-DUMI: A yau Alhamis Gwamnan jihar Gombe ya gabatarwa da majalisar dokokin jihar Gombe Budget na shekarar 2026, k...
13/11/2025

DA DUMI-DUMI: A yau Alhamis Gwamnan jihar Gombe ya gabatarwa da majalisar dokokin jihar Gombe Budget na shekarar 2026, kimamin Naira biliyan 535,691,983,000.

Libya ta kora 'yan Nijeriya 80 gida saboda zama ba bisa ka'ida ba a kasar
13/11/2025

Libya ta kora 'yan Nijeriya 80 gida saboda zama ba bisa ka'ida ba a kasar

Gwamna Abba Ya Sake tura Daliba 'yan jihar  Kano karo karatu Zuwa ƙasar India.A yau Alhamis, 13 ga Nuwamba 2025, Gwamnan...
13/11/2025

Gwamna Abba Ya Sake tura Daliba 'yan jihar Kano karo karatu Zuwa ƙasar India.

A yau Alhamis, 13 ga Nuwamba 2025, Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya yi wa rukuni na biyu na daliban da gwamnatin Kano ke daukar nauyi rakiya a filin jirgin Malam Aminu Kano International Airport, yayin da suke tashi zuwa kasar India domin cigaba da karatun MSc ƙarƙashin Kano State Government Foreign and Domestic Scholarship Scheme.

Gwamna Abba ya yaba da jajircewa da himmar daliban, tare da tabbatar musu cewa gwamnati za ta ci gaba da saka hannun jari a ilimi domin gina sabuwar al’ummar Kano mai wayewa da ingantacciyar makoma.

Wadanda s**a soke ni a baya yanzu yabo na suke yi - Olusegun Obasanjo
13/11/2025

Wadanda s**a soke ni a baya yanzu yabo na suke yi - Olusegun Obasanjo

Wadannan hotuna sun janyo ce-ce-ku-ce musamman a shafukan sada zumunta a jihar Jigawa, saboda irin yadda s**a nuna mummu...
13/11/2025

Wadannan hotuna sun janyo ce-ce-ku-ce musamman a shafukan sada zumunta a jihar Jigawa, saboda irin yadda s**a nuna mummunan yanayin da makarantar ke ciki.

Tun da farko dai Mai Martaba Sarkin Hadejia, Alhaji Dr. Adamu Abubakar Maje, ne ya kai ziyarar bazata a makarantun yankin don ƙarfafa gwiwar ɗalibai da iyaye da malamai da zummar inganta ilimi, inda masu ɗaukar hoton Sarkin s**a wallafa hotunan.

Me za ku ce game da wadannan hotuna?

‎📸: Hadejia Emirate

WATA SABUWA: A Shari'ance An Fara Bayyana Irin Hukuncin Da Ka Iya Biyo Baya Akan Jami'in Sojan Ruwa Yarima Da Ya Hana Mi...
12/11/2025

WATA SABUWA: A Shari'ance An Fara Bayyana Irin Hukuncin Da Ka Iya Biyo Baya Akan Jami'in Sojan Ruwa Yarima Da Ya Hana Ministan Abuja Nyesom Wike Duba Wani Fili

Fitaccen lauya kuma masanin tsarin mulki Najeriya, Farfesa Sebastine (SAN), ya bayyana cewa jami’in rundunar ruwa, A.M. Yerima, ya karya doka a rikicin da ya faru tsakaninsa da Ministan Babban Birnin Tarayya, Barr. Nyesom Wike, a wani fili da ake gardama a Abuja.

A wata sanarwa da Farfesa ya fitar, ya ce jami’in ya hana Ministan shiga filin ne bisa hujjar “bin umarnin manya,” amma hakan ya sabawa doka da kuma tsarin mulki na ƙasa. Ya yi nuni da cewa Kotun Koli ta Najeriya ta taɓa yanke hukunci cewa babu wani jami’i da zai iya bin umarnin da yake bayyananne haramtacce ko rashin adalci.

Farfesan ya ƙara da cewa babu wata doka da ta amince da jami’in soja ya yi gadin wurin ginin mallakin tsohon shugaban sa, musamman a yanayi da ake zargi da rashin gaskiya wajen mallakan filin, Ya ce idan akwai barazanar ta take haƙƙi, abinda ya dace a hukumance shi ne a kira ’yan sanda na farar hula, ba a tura soja ba.

Ya kuma jaddada cewa, a matsayi na doka, Ministan Abuja na matsayin Gwamnan Jiha ne, kuma shi ne ke da ikon kula da dukkan filaye a Abuja bisa sashe na 297(2) da 302 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya.

“A wannan rana, Wike yana tsaye ne a matsayin wakilin shugaban ƙasa da kuma babban kwamandan rundunar soji. Saboda haka, ko da tsohon jami’in ruwan yana aiki ne baiyi ritaya ba, bai da ikon hana Minista Abuja shiga filin,” in ji shi.

Farfesan ya bayyana cewa ko da hanyar da Ministan ya bi tana da ƙarfi, duk abin da ya aikata yana bisa doka. Amma jami’in da ya hana shi ya aikata laifi wanda ya sabawa Dokar Rundunar Soja (Armed Forces Act), wacce ke cewa sojoji na iya fuskantar hukunci idan s**a aikata laifin farar hula.

“Jami’in soja ko ɗan sanda na rantsuwa ne wajen kare tsarin mulki, ba wai bin kowanne umarni ba. Idan ya bi umarni da ya sabawa doka, shi ke ɗaukar alhakin aikinsa,” in ji Farfesa.

Ya gargadi cewa rashin hukunta jami’in na iya ƙara haifar da ƙarfin guiwar sojoji su raina fararen hula, su kuma yi ikirarin cewa “mun yi wa Wike haka, babu abin da ya faru.”

Menene ra'ayinku?

DAƊUMI-ƊUMI: Sanatoci A Najeriya Sun Amince Wa Sugaban Ƙasa Tinubu Ya Ciwo Bashin Naira Tiriliyan 1.15Majalissar Dattawa...
12/11/2025

DAƊUMI-ƊUMI: Sanatoci A Najeriya Sun Amince Wa Sugaban Ƙasa Tinubu Ya Ciwo Bashin Naira Tiriliyan 1.15

Majalissar Dattawan Najeriya ta amince da buƙatar Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na ciwo bashin Naira tiriliyan 1.15 a cikin gida domin ciki giɓin kasafin kuɗin shekarar 2025.

Amincewar ta biyo bayan karɓar rahoton kwamitin majalisar kan basuss**an cikin gida da na ƙasashen waje a zaman majalisar da aka gudanar ranar Laraba, k**ar yadda Dokin Ƙarfe TV ta ruwaito.

Kwamitin ya bayyana cewa Dokar Kasafin Kuɗi ta 2025 ta tanadi jimillar kashe kuɗi har Naira tiriliyan 59.99, wanda ya ƙaru da Naira tiriliyan 5.25 daga Naira tiriliyan 54.74 da Fadar Shugaban Ƙasa ta gabatar tun farko.

Me zaku ce?

YANZU-YANZU: Chief of Naval Staff tare da A.M Yarema a bayan shi ya ziyarce filin tsohon Chief of Naval staff wanda Wike...
12/11/2025

YANZU-YANZU: Chief of Naval Staff tare da A.M Yarema a bayan shi ya ziyarce filin tsohon Chief of Naval staff wanda Wike yake so ya kwace.

Nura Ahmad

'Yan Majalisar wakilan Nijeriya biyu sun sauya sheka zuwa APCDan majalisar tarayya Amos Daniel daga PDP, da Sagir Ibrahi...
12/11/2025

'Yan Majalisar wakilan Nijeriya biyu sun sauya sheka zuwa APC

Dan majalisar tarayya Amos Daniel daga PDP, da Sagir Ibrahim Koki daga NNPP, sun sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki bisa dalilin rikice-rikicen cikin gida a jam’iyyunsu.

Kakakin majalisar Abbas Tajudeen ne ya karanta wasikar da Amos Daniel ya aike wa shugabancin majalisar yayin zaman ta na Larabar nan, inda ya bayyana cewa ya koma APC ne bayan yin shawara da shugabanni, malamai, da dattawan yankinsa na Jema’a/Sanga a jihar Kaduna.

Kazalika, a yayin zaman ma aka tabbatar da ficewar Sagir Ibrahim Koki, dan majalisar da ke wakiltar Kano Municipal, daga jam’iyyar NNPP zuwa APC, yana mai cewa rashin jituwa da rashin tsari a jam’iyyarsa s**a sa ya yanke wannan shawara.

Barawon mota ya kutsa cikin gidan gwamnatin Kano, ya yi awon gaba da daya daga cikin ayarin motocin mataimakin gwamnaWan...
11/11/2025

Barawon mota ya kutsa cikin gidan gwamnatin Kano, ya yi awon gaba da daya daga cikin ayarin motocin mataimakin gwamna

Wani barawon mota ya shiga cikin Gidan Gwamnatin Kano da safiyar Litinin, ya yi awon gaba da wata motar Toyota kirar Hilux wacce ta ke daya daga cikin ayarin motocin mataimakin gwamnan jihar.

Jaridar Daily Nigerian ta ruwaito barawon ya arce da motar ne da misalin ƙarfe 5 na asuba. Bidiyoyin CCTV da aka duba sun tabbatar da lamarin.

Har ya zuwa yanzundai jami’an tsaro na bincike kan lamarin domin kamo mai laifin.

Address

001
Jahun

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Farin Wata News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Farin Wata News:

Share