14/11/2025
DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnatin Jihar Adamawa Ta Haramta Manna Fosta A Gine-Ginen Gwamnati Da Kayayyakin Jama’a A Faɗin Jihar
Kwamishinan Muhalli na Jihar Adamawa, Mohammed Sadiq, shi ne ya bayyana haramcin na manna duk wani nau’in hoto a kan gine-ginen gwamnati da sauran muhimman kayayyakin jama’a a fadin Jihar.
Ya bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis, 13 ga Nuwamba, 2025, a ɗakin taro na Ma’aikatar Muhalli da Albarkatun Ƙasa da ke Yola, k**ar yadda Dokin Ƙarfe TV ta ruwaito.
A cewar Kwamishinan, Ma’aikatar ta lura da yadda mutane, ƙungiyoyi, da cibiyoyi ke ƙara yawaita manna tallace-tallace, na siyasa da na kasuwanci, a wuraren gwamnati da tituna, wanda ya ce hakan na ɓata fasalin birane, na karya dokokin tsaftar muhalli, kuma yana kawo cikas ga ƙoƙarin gwamnati na tabbatar da tsafta da tsari a jihar.
Ya bayyana cewa daga yanzu an haramta manna fosta, tambari, ko banoni a kan gine-ginen gwamnati, sandunan hasken t**i, allunan bayanai, shataletale, da sauran wuraren jama’a a duk faɗin jihar. Ya kuma gargaɗi jam’iyyun siyasa, ƙungiyoyin addini, ƴan kasuwa da jama’a gaba ɗaya da su kauce wa wannan aiki da ya kira saɓawa doka.
Kwamishinan ya kuma yi gargaɗi cewa duk wanda aka k**a yana keta wannan sabon umarni zai fuskanci hukunci, tare da cire kayan tallan da kansa kuma a caje shi kuɗin aikin cirewar, bisa tanadin dokokin Kare Muhalli da Tsafta a Jihar Adamawa.
Ya ce Ma’aikatar na ci gaba da jajircewa wajen samar da muhalli mai tsafta, lafiya, da ɗorewa ga mazauna jihar, tare da neman goyon bayan jama’a domin kare martaba da ingancin mahalli a Adamawa.