Farin Wata News

Farin Wata News ONLY POST YOU CAN TRUST

An gano wasu muhimman bayanai dangane da dalilin da ya sa aka dage shirin ficewar Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ...
03/01/2026

An gano wasu muhimman bayanai dangane da dalilin da ya sa aka dage shirin ficewar Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, zuwa jam’iyyar APC mai mulki, duk da an riga an kammala shirye-shirye tun da farko.

A ranar Juma’a, jaridar DAILY NIGERIAN ta rawaito cewa gwamnan ya kammala dukkan shirye-shirye na sanar da ficewarsa zuwa APC a ranar Litinin.

Kafin dagewar shirin sauya shekar jam’iyyar, hedkwatar APC ta kasa ta shirya cewa gwamnan zai kasance mutum na farko da za a yi wa rajista a Kano a sabon tsarin rajistar jam’iyyar ta yanar gizo.

A cewar tsarin da aka tsara tun farko, tsohon Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ne zai raka gwamnan zuwa Mazabarsa ta Diso, domin yin rajista a shafin jam’iyyar tare da karɓar katin zama mamba.

Bayan kammala rajistar gwamnan, an tsara cewa shi kuma zai raka Ganduje kai tsaye zuwa garinsu na Dawakin Tofa, domin Ganduje ya sabunta rajistarsa a sabon tsarin rajistar APC.

Sai dai majiyoyi daga cikin jam’iyyar sun ce an dakatar da wannan tsari ne bayan an ja hankalin gwamnan cewa ya dace ya fara ganawa da manyan shugabannin APC a Kano, musamman Abdullahi Ganduje da Sanata Barau Jibrin, domin neman albarkarsu kafin sanar da ficewarsa daga jam’iyyar NNPP.

Wata majiya da ta san abin da ke faruwa ta ce:
“Idan gwamna ya fice ba tare da ya gana da Ganduje, Sanata Barau da sauran shugabannin APC ba, hakan zai nuna kamar ya raina su, kuma hakan ba zai yi masa kyau ba.”

Ko da yake jaridar Platinum Post ta ruwaito cewa gwamnan zai sanar da ficewarsa a ranar 12 ga Janairu, wasu majiyoyi sun ce ranar ba ta tabbata ba tukuna, kuma lamarin na iya faruwa “a kowace rana bayan ya gana da shugabannin APC na Kano.”

Wasu majiyoyi kuma sun bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ne ya bayar da umarnin a dakatar da shirin ficewar, har sai an yi kokarin karshe na shawo kan uban gidan siyasar gwamnan, Rabiu Musa Kwankwaso.

A cewar majiyoyin, shirin Kwankwaso na komawa jam’iyyar ADC ya sauya lissafin APC gaba daya.

“Fadar Shugaban Kasa na da bayanan sirri cewa Kwankwaso ya gana da Olusegun Obasanjo da Peter Obi, kuma akwai yiwuwar su hada kai domin kalubalantar Tinubu a zaben 2027.

Hadakar Obi/Kwankwaso hadaka ce mai karfi wadda za ta iya sauya tsarin siyasar APC.

“Kuma ba tare da Kwankwaso ba, karfin siyasar gwamnan yana raguwa sosai. Saboda haka Tinubu na sake tunani kan batun karɓar ficewar Gwamna Yusuf.

“A gaskiya, gwamnan ne ke neman shiga APC, ba APC ce ke nemansa ba. Shi ya sa har yanzu babu wani tsayayyen sharadi kan rabon matsayi ko iko bayan ficewarsa,” in ji wata majiya.

Sai dai wasu majiyoyi sun shaida wa wannan jarida cewa gwamnan da kansa ne ya nemi a kara masa lokaci, domin samun damar shawo kan karin ‘yan Majalisar Jiha da na Tarayya su bi sahunsa wajen sauya sheka.

Wasu majiyoyi da ba a tabbatar da sahihancinsu ba sun kuma ce tsananin martanin da gwamnan ke fuskanta daga bangarori daban-daban ya sanya shi cikin rudani, har ya fara tunanin janye shirin ficewar gaba daya, ya koma ya sasanta da uban gidansa na siyasa, Rabiu Musa Kwankwaso.

03/01/2026

A jaraba Tallafin $5000 na Tony Elumelu Foundation
👇👇👇

Uwar Jam’iyyar APC Ta Ƙasa Ta Nemi Dr. Abdullahi Umar Ganduje Ya Dawo Gida Nigeria Domin Jagorantar Karɓar Gwamnan KanoY...
02/01/2026

Uwar Jam’iyyar APC Ta Ƙasa Ta Nemi Dr. Abdullahi Umar Ganduje Ya Dawo Gida Nigeria Domin Jagorantar Karɓar Gwamnan Kano

Yanzu Haka Shugaban Jam’iyyar (APC) na Ƙasa Prof Yitwalde Nantawe Ya gayyaci Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya Gaggauta dawowa gida Najeriya domin jagorantar karɓar Gwamnan Jihar Kano H.E Abba Kabir Yusuf zuwa Jam’iyyar APC, wanda aka tsara zai gudana a ranar Litinin mai zuwa a Babban Birnin Tarayya Abuja.

Haka kuma Daga Bisani zai yanki Katin Jam’iyyar a Mazabarsa ta Diso Dake Karamar Hukumar Gwale, wanda Yanzu Haka Dr Abdullahi Ganduje Zai Sauka Nigeria da Asubahin Gobe Asabar Domin Cigaba da Shirye shiryen Gudanar da Gagarumin Bikin a Ranar Litinin Mai Zuwa.

HASBUNALLAHU WA NI'IMAL WAKIL😭Barayin daji masu garkuwa da mutane sun afka wa garin Tungar-giwa dake karamar hukumar Sha...
01/01/2026

HASBUNALLAHU WA NI'IMAL WAKIL😭

Barayin daji masu garkuwa da mutane sun afka wa garin Tungar-giwa dake karamar hukumar Shanga jihar Kebbi s**a kaddamar da mafi munin ta'addanci wa mutanen garin

Sun yiwa mutanen garin ¥ankan rag0, s**a raba ka¥ukán mutane da $a$$an jikinsu, sun mayar da mutanen garin kamar kwata gurin ¥anka dabbobi, an ¥anka iyaye a gaban 'ya'yansu

Wallahi ban taba ganin ta'addanci barayin daji da yayi munin wannan ba, ku duba Telegram dina na saka bidiyo ta nan
👇
https://t.me/DattiassalafiyTech

Don Allah mutanen Arewa mu hada kai, mu bi duk wani mataki na doka mu dakatar da wannan ki$a na rashin imani da ake yiwa 'yan uwan mu
Innalillahi wa inna ilaiHi raji'uuun😭😭😭😭

Allah Ya isa bamu yafe ba😭😭😭

YANZU-YANZU: Sanata Abaribe ya fice daga jam'iyyar APGA zuwa jam'iyyar hadaka ta ADC.
31/12/2025

YANZU-YANZU: Sanata Abaribe ya fice daga jam'iyyar APGA zuwa jam'iyyar hadaka ta ADC.

31/12/2025

Yanzu haka an fara zaman majalissar zartarwa a gidan gwamnatin kano

Bankunan Nijeriya za su fara cire harajin N50 daga masu tura kudi ta banki da s**a kai N10,000
31/12/2025

Bankunan Nijeriya za su fara cire harajin N50 daga masu tura kudi ta banki da s**a kai N10,000

DA DUMI-DUMI: Ba zamu taba bari a murde mana zabe a 2027 ba, a cewar Peter Obi, a yayin jawabin shi na shiga jam'iyyar h...
31/12/2025

DA DUMI-DUMI: Ba zamu taba bari a murde mana zabe a 2027 ba, a cewar Peter Obi, a yayin jawabin shi na shiga jam'iyyar hadaka ta ADC.

Me za ku ce?

An gurfanar da wani Ɗan Majalisar dokokin ƙasar Mali Mamadou Hawa Gassama a Ivory Coast dake maƙotaka da ƙasarsa, bisa z...
31/12/2025

An gurfanar da wani Ɗan Majalisar dokokin ƙasar Mali Mamadou Hawa Gassama a Ivory Coast dake maƙotaka da ƙasarsa, bisa zarginsa da aikata laifin cin mutuncin shugaba Alassan Ouattara, kamar yadda lauyansa Mamadou Ismail Konate ya shaidawa maneman labari.

Ƙarin bayani: https://rfi.my/CJJc

31/12/2025

Matsa A Jaraba Tallafin Green Entrepreneurship Challenge

👇👇

Yanzu-yanzu daga gidan Gwamnatin Kano, inda Gwamna Engr. Abba Kabir Yusuf zai gana da 'yan jarida.Mene ne tsammanin zai ...
31/12/2025

Yanzu-yanzu daga gidan Gwamnatin Kano, inda Gwamna Engr. Abba Kabir Yusuf zai gana da 'yan jarida.

Mene ne tsammanin zai faru?

Masu zagi na su daina domin kuwa bisa umarnin jagora zan koma APC yau ɗin nan da misalin ƙarfe 11:00AM—Abba
31/12/2025

Masu zagi na su daina domin kuwa bisa umarnin jagora zan koma APC yau ɗin nan da misalin ƙarfe 11:00AM—Abba

Address

001
Jahun

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Farin Wata News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Farin Wata News:

Share