
19/08/2025
SAURAN MAZAN JIYA
WANNAN SHINE ARC ABDULLAHI SA'IDU BELLO MNIA, FICEN.
An haifi Arc Abdullahi Sa'idu Bello a Tudun wadan Zaria , gidan Sarkin Tudun wada Sa'idu Doko a ranar 30 gawatan yuni 1957.
Yafara karatunsa Na Aji gutsure a Tudun wada Zaria, primary a LEA primary school dake Kofar Kuyanbana Zaria, ya kare a L E A Unguwan Rimi Kaduna a shekarar 1970 zuwa 1972 in da daganan yawuce Government College Kaduna a 1973 zuwa 1977.
Ya shiga jami'ar Ahmadu Bello Dake Zaria Yayi Karatun IJMB a SBS Shekarar 1977 zuwa 1978 daga bisani yafara karatun digirinsa Na Farko a Fannin Zane Wato (Architecture) a shekaran 1979 zuwa 1982.
NYSC a FCDA Abuja a 1982/83. Yafara karatunsa Na digiri Na Biyu a 1983 zuwa 1985.
Arc Abdullahi Sa'idu Bello Ya yi Aiki a wurare da dama a Gwamnatin Jihar Kaduna da Federal Capital Development Authority , Abuja (NYSC) a 1982 zuwa 1983.
Sannan New methods Design Associates a 1985 zuwa 1990.
Yazama mataimakin Darakta a hukumar tsara birane Na jihar Kaduna wato KASUPDA a 2002 zuwa 2010.
Sannan zama mataimakin Darakta a Ma'aikatar kula da Ayyuka da Sufuri Na jihar Kaduna wato MOWHAT daga 2010 zuwa 2015.
Arc Abdullahi Sa'idu Bello Yazama Overseer wato bubban mai saka ido hukumar KASUPDA Na jihar Kaduna a 2016, Yazama Darakta na Gine gine a Ma'aikatar ayyuka da sufuri Na jihar Kaduna daga 2015 zuwa 2016.
Arc Abdullahi Sa'idu Bello yayi ritaya a aikin gwamnati a 30th June 2016.
Arc Abdullahi Sa'idu Bello Yazama mamba a hukumomi kamar Nigerian Institute Of Architects. Shi Fellow nena Nigeria Institute Of Corporate Executives.
Yayi aikin Taswiran gine gine da dama kamar:-
1: Masallacin Juma'a na Sultan Bello dake unguwan Sarki kaduna .
2:Kofar gidan Sarkin Katsina da na Gwaram, Jigawa State.
3: Afribank PLC Abuja
4: Sabon Taswiran Masallacin Juma'a dake Maiduguri road kaduna.
5:Arc Abdullahi Sa'idu Bello shine Wanda yazana fadan Sarkin Birnin Gwari Kaduna Stateda90s da Fadar Galadiman Katsina Dake garin Malumfashi A Jihar katsina a Shekarar 2020
6: Arc Abdullahi Sa'idu Bello Shine Wanda yazana manyan Kofofin Taswiran shiga garin Kaduna a 2015.
Arc Abdullahi Sa'idu Bello Yanada Aure da Zuri'a.
Allah Ya Kara Lafiyan Da Nisan Kwana Da Jinkiri Mai Amfani Yasa A Gama Lafiya.