Dan Bahaushe Tv

Dan Bahaushe Tv Dan Bahaushe Tv zai dinga kawo muku labarai sahihai na Najeriya da Afirka da ma duniya baki daya.

Muna matukar farin ciki da samun ku a cikin safin mu. Ibrahim Nadada, Nafiu Zaria Zazzau, Mohanmed Gambo Abdullahi, Yusu...
06/07/2023

Muna matukar farin ciki da samun ku a cikin safin mu.

Ibrahim Nadada, Nafiu Zaria Zazzau, Mohanmed Gambo Abdullahi, Yusuf A Idris, Aminu Wali, Sunkanmi Babalola, Phyno Moses Gyalange, Abdullahi Adams, Ajibola Dada Marvelous, Mustapha Sani, Yahaya Usman Saleh Karim, Gabriel Ajayi, Chika-Mmadu Eze

TAMBAYA DAGA TWITTER.....A Arewacin Najeriya akwai garuruwa masu yawa dake dauke da sunan TUDUN WADA tun daga Kano har J...
02/07/2023

TAMBAYA DAGA TWITTER.....

A Arewacin Najeriya akwai garuruwa masu yawa dake dauke da sunan TUDUN WADA tun daga Kano har Jos, shine ake tambaya waye WADA ko menene asalin WADA da yake da Tudu masu yawa...

Tudun wada, Kano.
Tudun wada, Zaria.
Tudun wada, Kaduna.
Tudun wada, katsina.
Tudun wada, Sokoto.
Tudun wada, Kebbi.
Tudun wada, Minna.
Tudun wada, Jos.
Tudun wada, Bauchi.
Tudun wada, Gombe.
Tudun wada, Lafia.
Tudun wada, Keffi.

Waye WADA mai Tudu....?

Anyi Nasarar k**a wani barawon naman layya.
30/06/2023

Anyi Nasarar k**a wani barawon naman layya.

Masha AllahSojojin Najeriya 🇳🇬 Sunyi Nasarar Kawarda Barayin Masu Satar Danyen Man 🛢️🪔 Ijaw South Local Government Jahar...
30/06/2023

Masha Allah

Sojojin Najeriya 🇳🇬 Sunyi Nasarar Kawarda Barayin Masu Satar Danyen Man 🛢️🪔 Ijaw South Local Government Jahar Bayelsa.

Bmm Oa Mofokeng Mofokeng, Aminu S Fawa Makuku, Waktu Tilo KñrMuna matukar farin ciki da biyo shafin mu da kukai, ku kasa...
30/06/2023

Bmm Oa Mofokeng Mofokeng, Aminu S Fawa Makuku, Waktu Tilo Kñr

Muna matukar farin ciki da biyo shafin mu da kukai, ku kasance tare da mun domin samun ingantattun labarai da nishadantarwa da kuma ilmantarwa.

21/03/2023

📢📢📢WATA DAMA TA KARA SAMUWA 📢📢📢

AVIVE AVIVE AVIVE AVIVE AVIVE

idan har ba ka samu dama kayi Mining din Satoshi Core ba to hakika ga wata damar ta samu.

AVIVE. wani sabon shiri ne k**ar na Satoshi Core, sun zo da wasu tsaruka wanda za a samu alkairi dasu in sha Allah.

Kamar haka,

Idan ka bude link din da zan ajiye a kasa zaka saka Email address din ka zasu tura maka otp a email dinka sai kaje kayi copy din lambar otp din kazo ka saka ta a layi na biyu.

Daga nan sai su nuna maka inda za ka yi downloading din application din na su, bayan kayi downloading application din sai kayi login.

Bayan kayi login kayi kokari ka biyo su a Twitter bayan ka biyo su a Twitter sai kazo ka cike wani guri a kasan application din da username dinka na Twitter bayan yan mintuna za su baka wata kyauta, sannan kuma za ka ci gaba da Mining ⚒ dinka.

Mining ⚒ din yana da round 24 bayan nan idan ba ka yi Claiming ba / ma'ana karɓar abun da kayi Mining ba to Mining din zai dakata.

Suna ba da BTC kyauta a kullum duk da bashi da yawa.

Zan yi bidiyon yadda za ku yi rijistar sa cikin sauki.

🔨New Mining APP~
- The best mining app in 2023
Cliam free in referrals
Get $VV coin in mining
👉Click this link to register:

Hotuna 📷 Major Enzegwu Kaduna Da Kabarinsa A Kaduna. Patrick Chukwuma “Kaduna” Nzeogwu hafsan sojan Najeriya ne wanda ya...
16/01/2023

Hotuna 📷 Major Enzegwu Kaduna Da Kabarinsa A Kaduna.

Patrick Chukwuma “Kaduna” Nzeogwu hafsan sojan Najeriya ne wanda ya taka rawa a juyin mulkin farko na soja na 15 ga Janairun 1966, wanda a ka hambarar da jamhuriyar Najeriya ta farko. Wanda shi ne da kansa ya Kashe Sir Amadu Bello Sardauna.

An haifi Patrick Chukwuma Nzeogwu a Kaduna babban birnin yankin Arewa iyayensa al’ummar Anioma a Garin Okpanam na Yankin Tsakiyar Yamma (kusa da Asaba a Jihar Delta a yau ).

Nzeogwu Kaduna ya halarci makarantar firamare ta Katolika ta Saint Joseph da ke Kaduna in ya yi karatun firamare sannan kuma ya yi karatun sakandire a makarantar Saint John's College duka Dai A Kaduna.

A watan Maris na shekarar 1957, Nzeogwu ya shiga aikin sojan Najeriya rejiment na rundunar sojojin Afirka ta Yamma kuma ya ci gaba da samun horon sharar fage na watanni 6 a Ghana, sannan a kirata da (Gold Coast) Ya k**alla horonsa a Ghana a watan Oktoban 1957 sannan ya wuce Royal Military Academy, Sandhurst inda daga nan Ya zama sojan kasa a shekarar 1959.

Daga baya ya yi kwas na jami'an rundunar a Hythe da kwas na kwamandan runduna a Warminster. Max Siollun, wani masanin tarihi na soja ya bayyana Nzeogwu a matsayin Kirista dan Darikar "katolika mai kishin katolika, Wanda ko taba sigari baya sha.

Aikin soja

A lokacin da ya dawo Najeriya a watan Mayun 1960, Nzeogwu an tura shi zuwa Bataliya ta daya da ke Enugu inda Manjo Aguiyi-Ironsi ya kasance babban kwamanda na biyu a karkashin wani jami’in Birtaniya.

Daga baya aka tura shi bataliya ta 5 da ke Kaduna inda s**a yi abota da Olusegun Obasanjo. Abokan aikinsa Hausawa a cikin sojojin Najeriya ne sanya masa suna " Kaduna " saboda alakarsa da garin.

Bayan ya yi aiki kiyaye zaman Lafiya a Kongo a 1961, Nzeogwu ya zama jami'in horaswa na sojoji a Depot da ke Zariya na tsawon watanni 6 kafin a tura shi Legas. ya jagoranci sashin leken asirin soja a hedkwatar sojojin in da ya kasance jami'i dan Najeriya na farko, Wanda ya jagoranci rundunar leken asiri ta Sojojin Najeriya (NAIC) shi ne Sashen Tsaro (FSS) na Rundunar Sojojin Najeriya, wanda aka kafa a ranar 1 ga Nuwamba 1962 tare da Kyaftin PG Harrington (BR) a matsayin Babban Hafsan Soja na Grade Two (GSO2 Int). FSS da gaske kungiyar tsaro ce wacce ayyukanta s**a hada da tantance jami'an Sojojin Najeriya (NA), da daftarin tsaro da bayanan sirri.

Manjo Nzeogwu shi ne jami’in Najeriya na farko da ya rike wannan mukami daga watan Nuwamba 1962 zuwa 1964. A matsayinsa na jami’in leken asiri na soja, ya shiga cikin binciken manyan laifuka na cin amanar kasa da aka yi wa Obafemi Awolowo da jam'iyyarsa ta AG (Action Group) A cewar Olusegun Obasanjo , "Chukwuma yayi wasu zafafan kalamai game da tsaron kasa [Najeriya], da kuma wadanda ake bincike.

An ruwaito cewa Nzeogwu ya caccaki wasu abokan aikin soja a matsayinsa na jami'in leken asiri na soja har ma s**ayi musayar kalamai masu zafi da karamin ministan soji, Ibrahim Tako.

Saboda haka sai aka tura shi Kwalejin Horar da Sojoji ta Najeriya da ke Kaduna inda ya zama Babban hafsa.

Juyin mulkin 15 Ga Watan Junairu 1966

Shirye-shiryen juyin mulkin ya fara ne da wasu gungun matasa masu ilimin jami'a wadanda s**a yi niyyar juyin juya hali na soja na kasa ta hanyar kwace iko a manyan biranen yankin Kaduna (yankin Arewa) da Ibadan (yankin Yamma), daga bisani kuma s**a kwace iko da Legas (Tarayya) An ba Nzeogwu alhakin jagorancin juyin juya hali a yankin Arewa wanda ya fara da Operation Damisa a ranar 15 ga Janairu 1966, sannan daga baya, Operation Kura, Operation Zaki da Operation Giwa wanda zai kai ga kisan gillar da aka yi wa manyan 'yan arewa.

Nzeogwu ya fara shirye-shiryensa ne ta hanyar shirya atisayen dare na kwana biyu "Damisa" (Operation Tiger) domin horar da sojoji sabbin dabarun yaki. Hukumomin hedikwatar Brigade ta daya ce ta amince da atisayen bisa dukkan alamu ba su san ainihin manufar Nzeogwu ba, da Brigade Manjo Alphonso Keshi ya aike da kasidu ga dukkan sassan da ke aiki a karkashin Brigade domin bayar da gudunmawar sojoji domin samun nasarar atisayen. A lokacin da Manjo Keshi ya fahimci cewa "Operation Damisa" wani makarkashiyar soji ne, Amma ina!! an Riga an makara wajen dakile aikin.

A safiyar ranar 15 ga watan Janairun 1966, Nzeogwu ya jagoranci wasu gungun sojoji a wani atisayen soji, inda s**a kai su farmaki kan gidan firayim ministan arewa, Sir Ahmadu Bello a wani juyin mulkin da ya yi sanadiyar mutuwar sa da mutane da dama.

Ciki harda Firimiyan Yammacin Najeriya Samuel Akintola, An kuma kashe firaminista ( Abubakar Tafawa Balewa ) da ministan tarayya ( Festus Okotie-Eboh ) da kuma manyan hafsoshin soja daga yankunan Arewa da yammacin kasar nan.

Firayim ministan yankin Gabas ( Michael Okpara ), shugaban tarayyar Najeriya ( Nnamdi Azikiwe ) da kuma shugaban sojoji ( Johnson Aguiyi-Ironsi).) Dukkanin Yan Kabilar ibo sun kasance sanannun waɗanda s**a tsira, Ba'a Kashesu ba.

A cewar wani rahoto na musamman na rundunar ‘yan sandan Najeriya, Nzeogwu ya kashe akalla sojoji 4 da jami’an tsaro na ‘yan sanda ciki har da daya daga cikin mutanen da ke cikin tawagarsa (Sajan Daramola Oyegoke). Nzeogwu ya kashe Kanar Raph Shodeinde, babban jami’insa a Kwalejin Horar da Sojoji ta Najeriya, kuma rahotanni sun ce ya harbe mata da kananan yara da s**ai Yunkurin gudu ba gaira ba dalili.

Bayan jiran sanarwar da aka yi da sanyin safiyar ta rediyo daga Manjo Adewale Ademoyega a Legas wanda hakan bai faru ba saboda gazawar juyin mulkin da aka yi a Legas, Manjo Nzeogwu ya yi sanarwar da tsakar rana, inda ya ayyana dokar ta-baci a Arewacin Najeriya.

An k**a Enzegwu Kaduna

Bayan sanarwar da aka samu daga Kaduna, da kuma bayanin cewa Nzeogwu na tattara sojoji domin kai hari Legas wanda hakan abu ne mai matukar yiwuwa a lokacin, Kwamandan rundunar, Sojojin Najeriya Manjo Janar Aguiyi Ironsi ya aika da jakadu karkashin jagorancin wani soja mai suna Col Conrad Nwawo, zuwa Kaduna domin tattaunawa da Maj. Nzeogwu da yiwuwar ya mika wuya.

Maj. Nzeogwu ya gindaya sharudda da Gen. Ironsi ya amince da su. Aguyi Ironsi ya karbi mulki, daga baya kuma an k**a Nzeogwu a Legas a ranar 18 ga Janairun 1966 sabanin yarjejeniyar da aka cimma a baya tsakanin Nzeogwu da Ironsi.

An tsare shi a gidan yarin Kirikiri mafi girman tsaro a Legas kafin a kai shi gidan yarin Aba da ke yankin Gabas. Inda Gwamnan yankin Gabas kuma shugaban kasar Rushashshiyar Chukwuemeka Ojukwu ya sake shi a watan Maris 1967.

Yakin basasa da mutuwa

A ranar 30 ga Mayun 1967, Biyafara ta ayyana ‘yancin kai daga Najeriya; hakan ya samo asali ne sak**akon kashe-kashen da ake yi wa ‘yan kabilar Igbo a Arewacin Najeriya ba tare da kakkautawa ba, da kuma yadda shugaban mulkin soja na wancan lokacin Janar Yakubu Gowon ya ki sanya jami’an tsaro su dakile kashe-kashen.

A ranar 29 ga watan Yulin 1967 Nzeogwu - wanda aka kara masa mukami a Sojan Biafra zuwa Laftanar Kanar - ya makale a wani harin kwantan bauna a kusa da Nsukka a lokacin da yake gudanar da aikin leken asiri da daddare kan sojojin gwamnatin tarayya na bataliya ta 21 karkashin Captain Mohammed Inuwa Wushishi.

A lokacin ne a ka kashe shi, bayan an gano gawarsa; Duk da haka 'yar uwarsa ta dage cewa ya kashe kansa ne don gudun kada sojojin tarayya su wulakanta

Bayan an gano Gawar ta sa shugaban mulkin sojan Najeriya Janar Yakubu Gowon ya ba da umarnin a binne shi a makabartar sojoji da ke
Kaduna tare da cikakkiyar girmamawa ta soja.

Daga Saliadeen Sicey

An k**a Kwamishinan Ƴan Sanda na bogi da ya damfari wani dattijo naira miliyan 250Sashen Binciken Manyan Laifuka na Rund...
12/01/2023

An k**a Kwamishinan Ƴan Sanda na bogi da ya damfari wani dattijo naira miliyan 250

Sashen Binciken Manyan Laifuka na Rundunar Ƴan Sanda ta jihar Legas, ta k**a wani Oluwole Akande, dan shekara 55 da haihuwa, bisa zarginsa da laifin yin basaja a matsayin kwamishinan ƴan sanda, CP Yetunde Longe, ya kuma damfari wani tsoho mai shekaru 80 naira miliyan 250.

Kwamishinan, na yankin railway, CP Yetunde Longe, ya tabbatar wa kamfanin dillancin labarai na ƙasa k**a wanda ake zargin a jiya Laraba a Legas.

Longe ta ce ta samu kira daga CP Frank MBA, tsohon mai magana da yawun rundunar kan lamarin.

Ta ce matar wanda ake zargin ta kira Mba domin ta tsegunta masa shirin da wani CP Longe ke yi na neman mijin nata ya bashi miliyoyin Naira, domin ta kashe maganar wata kara da a ka kai mata a kan mijin ta.

"CP Frank Mba ya amsa wa matar wanda abin ya shafa cewa ya san CP Yetunde Longe ba za ta yi irin wannan mummunar bukatar ba, ya yi alkawarin zai kira ta ya tabbatar ya dawo wurin matar.

"CP Frank Mba ya kira ni don in ba da labarin lamarin kuma na tabbatar da cewa bayanan ba daidai ba ne. Na ce babu wani koke a gabana kuma ban ma san wanda abin ya shafa ba.

” A wannan lokacin ne aka sanar da CID Panti na jihar domin gano wanda ake zargin kuma an k**a shi. Ya furta cewa ya kwaikwaye ni,” in ji Longe.

Kwamishinan ta ce nan ba da jimawa ba za a gurfanar da shi a gaban kotu.

📷 Daily Nigerian

Innalilahi wa'inna'ilahinraji'un 😭😭Taren yanzu babu Amana wannan bawan Allah da kuke gani driver ne na dangote flour sun...
12/01/2023

Innalilahi wa'inna'ilahinraji'un 😭😭

Taren yanzu babu Amana wannan bawan Allah da kuke gani driver ne na dangote flour sunansa Ibrahim dayan wanda kuke gani Mai babbar Riga Shima tsohon driver ne na, dangote flour Amma yanzu bashida mota shiya kashe wannan bawan Allah maisuna Ibrahim dasunan ya ragemasa hanya hanyar Bida.

yayi yunkurin kwace motarsa da lodin flour Allah baibashi nasara ba shida Abokinsa s**a dauko Adduna s**a dinga saransa yaruga cikin daji s**a bishi Har Saida s**a kasheshi yaron motar ya tsallake Rijiya da baya innalilahi wa'inna'ilahinraji'un rayuwa damu Ciki Kenan babu Amana babu Imani 😭😭😭

Jami'an tsaro sunyi nasara kwato motar Ibrahim Amma Ibrahim ya rigamu gidan gaskiya 😭😭

Yanzu haka Ana neman wanga Mai babbar rigar Wanda yakashe Ibrahim yayi yunkurin kwace motarsa Muna addu'a ubangiji Allah kajikan Ibrahim kasa aljannah fiddausi taxamo makoma Awajansa Allah shikarfi shahadarsa sukuma wadanda s**ayi wannan muguwar aika,aika Allah katona masu Asiri AMIN 🤲

Daga Munir Abdullah Visible

Wannan wata tsohuwar gada ce mai shekaru sama da 200 dari biyu da ginawa, angina wannan gada mai shekaru sama da dari bi...
12/01/2023

Wannan wata tsohuwar gada ce mai shekaru sama da 200 dari biyu da ginawa, angina wannan gada mai shekaru sama da dari biyu ne ba tare da ko da kusa guda daya ba, an samar da wannan gada ne a wani yanki na kasar Rasha wato Russia 🇷🇺 a wani gari mai suna Dagestan.

Wannan gada nada dumbun tarihin gaske kuma ya k**ata ace tana cikin abubuwan tarihin duniya k**ar irin su pyramids dake kasar Egypt 🇪🇬 CCewar mani tsoho kwararre wajen sarrafa katako a Kasar ta Rasha.

ANSAMU MUTUM NA FARKO DAN AFRIKA KUMA DAN BABBAN BIRNIN AFRIKA WATO LAGOS WANDA YA FARA MINING DIN BITCOIN DA COMPUTER K...
12/01/2023

ANSAMU MUTUM NA FARKO DAN AFRIKA KUMA DAN BABBAN BIRNIN AFRIKA WATO LAGOS WANDA YA FARA MINING DIN BITCOIN DA COMPUTER KIRAR TAFI DA GIDAN KA.

Mining din Bitcoin abune mai matukar wahala wanda yinsa ke bukatar tsayaryiyar wutar lantarki wanda mafi yawan cin kasashen Afrika ke fuskanta kalubale ta Fannin wutar lantarkin.

Mr Megasley mazaunin Lagos wanda ya fara mining din Bitcoin din ya shaida wa manema labarai cewa ya shirya tsaf domin tunkarar kalubalen na rashin wutar lantarkin, ya ce hakan ne yasa ya fara sayen jannareto mai amfani da man fetur domin samun wutar dun dun dun.

Ya ce yin hakan wani yunkuri ne na kawo karshe matsalolin karye war darajar kudi musamman akasar ta Najeriya, inda ya ce wannan yunkuri nasa zai taimaka wajan samun sauki na cinikayya da ku ma biya na tsarin layer-2.

© Metro.Ng Hausa

Ana sa ran Insha Allahu a cikin Makon nan za a bude Sabon Gidan Television Mallakin Mabiya Dariqar Tijjaniyya mai suna K...
11/01/2023

Ana sa ran Insha Allahu a cikin Makon nan za a bude Sabon Gidan Television Mallakin Mabiya Dariqar Tijjaniyya mai suna Khalifa TV wanda Khalifa Muhammadu Sunusi ya dauki Nauyin Gudanar wa karkashin Jagorancin Prof Ibrahim Maqari.

Gidan Television din zai fara aiki ne akan Babban Setlite daga bisani a fadada zuwa sauran Decorders.

Addu ar ku Masoya da fatan Alkhairi yana da Matukar muhimmanci bisa wannan cigaban.

Gwamnatin Najeriya ta biya zunzurutunkudi kimanin naira biliyan 173 domin daidaita farashin kudin man fetur a fadin ƙasa...
11/01/2023

Gwamnatin Najeriya ta biya zunzurutunkudi kimanin naira biliyan 173 domin daidaita farashin kudin man fetur a fadin ƙasar baki daya.

11/01/2023

Idan Ana maganar sanin aiki da ku ma I yawa to nan fa karshe ne.

Address

Jattu

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Dan Bahaushe Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Dan Bahaushe Tv:

Share