JIBIA MEDIA News

JIBIA MEDIA News JMCNews kafa ce ta Labarai mai cikakken Lasisin gudanar da aikin Jarida.

JMCNews ta dukufa wajen samar da sahihan Labarai tare da Ingantattun Rahotannin abubuwan dake faruwa a Najeriya da sauran kasashen Afrika da ma sauran kasashen Duniya baki daya.

Hukumar wannan kafa ta JMCnews na farincikin gayyatar masoya, 'yan'uwa da abokan arxiki zuwa daurin auren daya daga ciki...
09/02/2024

Hukumar wannan kafa ta JMCnews na farincikin gayyatar masoya, 'yan'uwa da abokan arxiki zuwa daurin auren daya daga cikin jiga-jigan da s**a assasa ta, Kuma Shugaban yada labarai da al'amurran yau da kullum na kafar, watau Yusuf Aminu Tinau.
Wanda zai gabata a gobe Asabar idan Allah ya kai mu. Zaa gudanar da daurin auren ne da misalin karfe 02:30 na yamma, a Unguwar Filin sale (Lungun gidan Alh. Ashiru Dan Masani dake garin Jibia.

Muna barar addua ga wadanda basu samu damar halarta ba.

Takardar tsarin biyan kudin rejista a Makarantar FUDMA study Centre dake garin Jibia. K**ar yanda daya daga cikin wakila...
22/01/2024

Takardar tsarin biyan kudin rejista a Makarantar FUDMA study Centre dake garin Jibia. K**ar yanda daya daga cikin wakilan Makarantar (Malam Mus'ab Ibrahim) ya wallafar a shafin jaridarmu ta Jibia Media a matsayin AMSA ga masu tambayar adadin kudin rejista

21/01/2024

Bayani a kan FUDMA Study Centre Jibia, Daga Haziƙin matashi.

Malam Mus'ab Ibrahim Jibia.

Kana iya yin tambaya a comment section.

*SHIN KANA DA MAFARKIN CIGABA DA KARATU TAREDA FULLY FUNDED SCHOLARSHIP A KASASHEN DUNIYA?*Muna yi maka albishir da cika...
31/12/2023

*SHIN KANA DA MAFARKIN CIGABA DA KARATU TAREDA FULLY FUNDED SCHOLARSHIP A KASASHEN DUNIYA?*

Muna yi maka albishir da cikar Mafarkin ka a tareda mu insha Allah. Muna cike scholarship na kowanne matakin karatu, Undergraduate, MSc da PhD.

Haka zalika Muna da qwarewa sosae wajen Samar da Academic CV, Job CV, Cover Letter, Statement of Purpose, Personal Statement, Recommendation letter, Scholarship Essay da duk abubuwan da scholarship ya qunsa.

Muna da tsari Mai kyau ga Daliban mu tareda guarantee akan scholarship din da zamu cikewa Dalibai, sannan Muna da tsari k**ar haka:-
1. Dalibi zai biya kaso 50% na kudin aikin mu, bayan admissions ya fito zai cika mana ragowar kaso 50% .

2. Zamu ba Dalibi guarantee na 75%, idan admissions ya fito Bai samu ba yana da zabi guda biyu: i) Ko mu dawo Masa da kudin sa cikin awanni 72hrs bayan fitar da admissions ko kuma ii) ka zabi wani scholarship din a cike maka.

Wannan babbar dama ce gareku Dalibai masu muradin cika burin rayuwarsu na cigaba da karatu a kasashen duniya.

Zaku iya tuntubar mu akan Whatsapp lambar mu #08062290008 #

Ina Iyaye da Makusanta masu bukata 'ya'yansu su samu Ingantaccen Ilimin Zamani da na Muhammadiyya hadi da Nagartacciyar ...
01/09/2023

Ina Iyaye da Makusanta masu bukata 'ya'yansu su samu Ingantaccen Ilimin Zamani da na Muhammadiyya hadi da Nagartacciyar tarbiyya bisa turba da koyarwar Addinin Islama.

Ku sani cewar: Shahararriyar Makarantar nan guda daya tilo wacce ta jajirce take ta hakilo tare da bayar da gudunmuwa wajen ganin Ilimi a karamar Hukumar Jibia ya bunkasa yayi fice ta yanda zamu goga da sauran kananan hukumomi Na cikin gida da na ketare, a Karkashin Jagorancin Cikakken Dan kishin Karamar Hukumar Jibia Kadi Makiyyu Adam Jibia, wato Gamayyar Rukunin Makarantun Madina (Madina Group of Schools) ta shirya tsaf tare da fara siyar da Fama Famai na shiga zangon karatun shekarar 2013/2024 a bangarori daban daban da take gudanarwa.

K**a daga matakin farko na Karatun Raino watau Nursery Classes. da kuma Matakin farko na Karatun Primary duk a karkashin jagorancin Makarantar su ta Baba Kudi Community Nursery and Primary school Madina.

Haka zalika ga masu Sha'awar Karatun boko tsantsa ko kuma karatun boko mai hade da na Muhammadiyya, kuma dama ta samu domin kuwa a karkashin Jagorancin Madina Community College of Arabic and Islamic studies Jibia duk dai a Rukunin Gamayyar Makarantun Madina sun tanadar maku bangarori daban daban wanda zaka Iya karatun ku a fannin boko tsantsa da kuma wani bangaren da zaka iya hadawa da karatun Muhammadiyya. K**a daga matakin Aji daya na karamar sakandire (JIS I), Aji daya a matakin babbar sakandire (SS I) sannan kuma har Ila yau ta bude daukar dalibai da suke da Sha'awar yo transfer domin cigaba da karatu a makarantarsu.

Ku hanzarta domin samun damar shiga wannan Makarantun don zabirar da 'ya'yanku wajen samun Ingantaccen Ilimi domin samun tsira a duniya da kiyama.

Zaku Iya samun wadannan Forms a Farfajiyar Makarantar a Unguwar Madina dake Tudunwada a cikin garin Jibia.
Ko kuma ku tuntubi lambobi K**ar haka
08066012908. 07033332647

30/08/2023
Sojoji Sun Sanar da yin Juyin Mulki a Kasar Gabon.Soji a Kasar Gabon sun Sanar da yin Juyin Mulki Wanda ya Kifar da Gwam...
30/08/2023

Sojoji Sun Sanar da yin Juyin Mulki a Kasar Gabon.

Soji a Kasar Gabon sun Sanar da yin Juyin Mulki Wanda ya Kifar da Gwamnatin Shugaban Kasar Ali Baggo.

K**ar watsa Labarai ta BBC ta rawaito cewa wasu Sojoji guda 12 sun bayyana a Gidan TV na Kasar inda s**a sanar da kibar da Gwamnatin Kasar tare da soki duk wasu tsare-tsaren Gwamnati.

Sojojin sun bayyana cewa sunyi Juyin mulkin ne domin kawo zaman lafiya a Kasar sak**akon Zaben da aka gudanar Wanda Hukumar zaben Kasar ta bayyana Shugaban Kasar Mai ci, Ali Baggo.

Sojojin sun bayyana zaben a matsayin wanda aka tafka Magudi Wanda hakan ka iya kawo rashin zaman lafiya a Kasar.

Wannan dai ya kawo karshen Mulkin shekaru 53 da iyalan gidan Shugaban su kayi suna mulkin Kasar ta Gabon.

An gudanar da Bikin Ranar Hausa a Garin Jibiya...Rubutawa: Yusuf Aminu Jby K**ar yadda majalisar dinkin duniya ta ware r...
27/08/2023

An gudanar da Bikin Ranar Hausa a Garin Jibiya...

Rubutawa: Yusuf Aminu Jby

K**ar yadda majalisar dinkin duniya ta ware ranar 26 ga watan Ogusta a matsayin ranar Hausa ta duniya, dalibai da malamai masu nazarin harshen Hausa na karamar hukumar Jibiya Sun shiga sahun wadanda s**a gudanar da bikin zagayowar ranar.

Bikin wanda ya gudana a filin wasa na Firamaren Tudun Wada (Pilot) ya samu tagomashin samun mahalartan daban-daban. Daga cikin mahalartan akwai baturen 'yan sandar karamar hukumar, shugaban sashen nazarin harshen Hausa na kwalejin kimiyya ta Katsina, (Dr. Isah Dahiru) wanda yana cikin masu gabatar da makala, Akwai sanannen malamin malamin nan da ya yi fice wajen koyar da harshen Hausa a karamar hukumar, (Malam Mansur Mamuda). Daraktan Ta'asisul Qur'an kuma shugaban makarantar Makarantar gwamnati ta Daddara, Mai girma sarkin Arewa hakimin Jibiya ya shi ma ya amsa kiran taron ta hanyar wakilcin Yariman Jibiya, (Mubarak Rabe Rabi'u). Sarkin noma, da sarkin makera, da sarkin bakin Jibiya da sauran manyan mutane sun amsa katin gayyatar taron.

Malaman makaranta, da daliban makarantun gwamnati da masu zaman kansu, sun cika taro. Inda mafi yawancin abubuwan da s**a gudanar daliban makarantun ne s**a gudanar. Taron ba zai cika ba idan ba a ambaci masu kide-kiden gargajiya, da masu bushe-bushe.

Abubuwan da s**a gudana a wurin baya ga makaloli guda biyu masu taken, "Muhimmancin Rikon Al'adu Ga Hausa.", da "Yaduwar harshen Hausa a Duniya." Sannan akwai raye-rayen gargajiya, da wasan dambe, wasan 'Yar tsana, wasan tafa-tafa, wasan wargin fadawa, Al'adar bakar magana, Gasar Karin Magana, da sauran abubuwa masu kayatarwa.
Bayan kammala taron, al'ummar gari dai na ci gaba da tofa albarkacin bakinsu kan taron, da kuma yin tsokaci. Yayin da wasu suke korafin yadda aka ci aka tsire ba tare da sun ji duriyar taron ba, an yi babu su.

Gwamnan Katsina Ya Kar6i Bakuncin Kwamitin Majalisar Dattijai Ta Kasa Kan Ayyukan Jami'an Kwastan Musamman a Titin Katsi...
14/08/2023

Gwamnan Katsina Ya Kar6i Bakuncin Kwamitin Majalisar Dattijai Ta Kasa Kan Ayyukan Jami'an Kwastan Musamman a Titin Katsina-Jibia

Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, PhD, a ranar Litinin 14th Agusta, 2023 ya karbi bakuncin kwamitin majalisar dattawa kan ayyukan jami'an kwastam a gidan gwamnatin jihar.

Aikin da kwamitin ya zo yi a Katsina, shi ne na kyautata alaka tsakanin 'yan kasuwar da ke yankin Jibia da sauran yankunan da ke kan iyakar jihar Katsina da Jamhuriyar Nijar da kuma jami'an hukumar kwastam da ke aikin tabbatar da an bi dokar da kasa ta tanadar wajen shiga ko fitar da kaya.

Dama dai Gwamna jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD na bin duk wasu hanyoyin da s**a k**ata domin ganin al'ummar jihar Katsina sun samu hanyoyin gudanar da kasuwancinsu na halal ta yadda tattalin arzikin jihar zai bunkasa.

A lokacin ziyarar, Malam Dikko Umaru Radda ya yaba wa majalisar dattijai ta kasa da ta kafa wannan kwamitin da zai tabbatar da an tsaftace alaka tsakanin jami'an hukumar kwastam da al'ummomin da ke makwabtaka da iyakokin Jamhuriyar Nijar a jihar Katsina.

Malam Dikko Umaru Radda ya bukaci wannan kwamiti da ya yi dubar tsanaki game da korafe-korafen da 'yan kasuwar wannan yakunan s**a bijiro da su domin samowa tare da lalubo hanyoyin da za a bi a warware su cikin sauki da kuma kara kimar aikin na hukumar kwastam.

Ya bayyana matsayarsa ta kin nuna goyon baya ga ayyukan 'sumogal' sannan ya ce zai ba jami'an kwastam duk hadin kai da goyon bayan da suke nema na ganin an dakile dabi'ar 'fasa-kwauri' a kasar nan.

Shugaban kwamitin Sanata Francis ya ce dalilin wannan ziyarar shi ne don su binciki ayyukan jami'an hukumar kwastam a titin Katsina-Jibia domin samar da kyakkyawar alaka tsakanin jami'an da al'ummar da ke yankunan.

A cikin kwamitin akwai Sanatan Katsina ta tsakiya Abdulaziz Musa Yar'adua da na shiyyar Funtua Muntari Dandutse da sauransu.

MA SHA ALLAHMuna taya abokin aikinmu COE Jibia Media News (Abba Sani Danmowa) murnar samun karuwar 'ya mace da Allah ya ...
07/08/2023

MA SHA ALLAH

Muna taya abokin aikinmu COE Jibia Media News (Abba Sani Danmowa) murnar samun karuwar 'ya mace da Allah ya azurta shi da ita.

Ku yi mana fatan alkairi 🙏

Jibia Media New
05/08/2023

Jibia Media New

Danmajalisar Bichi Abba,Ya Biyawa Daliban BUK Yan Bichi Su 157 Kudin Registration Miliyan 16 Da Dubu 484 Da Dari 836.
04/08/2023

Danmajalisar Bichi Abba,Ya Biyawa Daliban BUK Yan Bichi Su 157 Kudin Registration Miliyan 16 Da Dubu 484 Da Dari 836.

Hukumar KAROTA Ta Jahar Kano Ta Gargadi Masu Amfani Da Iskar Gas A Ababen Hawa...Rubutawa: Yusuf Aminu Jibiya Hukumar ku...
02/08/2023

Hukumar KAROTA Ta Jahar Kano Ta Gargadi Masu Amfani Da Iskar Gas A Ababen Hawa...

Rubutawa: Yusuf Aminu Jibiya

Hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta jihar Kano, KAROTA, ta yi gargadi kan amfani da iskar gas maimakon man fetur a kekuna masu kafa uku.
Manajan Daraktan KAROTA, Faisal Mahmud-Kabir ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar, Nabilusi Abubakar, ya fitar ranar Laraba a Kano. A cewar Mista Mahmud-Kabir, amfani da iskar gas a madadin man fetur a kekunan masu kafa uku na da hadari, domin yana iya fashewa da kuma haddasa asarar rayuka.
“Gas din da ake amfani da shi don ababen hawa ya sha bamban da sauran iskar gas. "Hukumar za ta k**a masu yin amfani da iskar gas maimakon man fetur," in ji shi.

Amfani da iskar gas din dai ya biyo bayan cire tallafin mai da gwamnatin tarayya ta yi a kasar. Hakan ya tilasta wa jama'a aiki da gas din don samun saukin rayuwa duk da hatsarin da ke tattare da hakan.

31/07/2023

Marini community science and Technical school Jibia (Prize-giving Ceremony)

Makaranatar Al'umma ta kimiyya da fasaha ta Marini dake garin Jibia watau (Marini Community Science and Technical School...
31/07/2023

Makaranatar Al'umma ta kimiyya da fasaha ta Marini dake garin Jibia watau (Marini Community Science and Technical School Jibia) ta gudanar da taron Prize-giving Day

A ranar Asabar da ta gabata ne Makarantar ta gudanar taron Prize-given Ceremony a farfajiyar Makarantar dake bakin Kara Jibia.

Yayin gudanar da taron Makarantar ta karrama tare da bayar da kyaututtuka ga dalibai da Malamai mafi hazaka da kuma dagewa don ganin makarantar taci gaba a kowane fanni.

Duk da cewar shekara daya kacal da bude makarantar, Shuwagabanni da Malaman Makarantar sunsha Alwashin cewar nan da shekaru kadan masu zuwa makarantar zata goga da duk wata makarantar Al'uma dama sauran makarantun kimiyya dake fadin Jahar.

An dai gabatar da da shirye-shirye masu kayatarwa da s**a hada da Muhawara (Debate), Spelling B na kananun aji watau Nursery Class dama na Manyan aji, wakokin yara(Nursery Rhymes), shiri domin wayar da kan iyaye su kula da karatun yaransu ba biyan kudin makarantar su kadaiba. Har ila yau sun gabatar da shirin da babu wata makarantar da ta taba yin irinshi yayin da aka dauko dalibai 'yan aji daya a bangaren kimiyya inda s**a gabatar da tun daga fandeshin gini (foundation) har zuwa dora bululuwa cos ukku duk a gaban mutane, yayin da daga karshe wasu daliban kuma s**a gabatar da wani shirin kimiyya da kuma fasaha.

Da yake Magantuwa a wajen taron Shugaban Ilimi na karamar hukumar wanda ya samu wakilcin shugaban gudanarwa na ilimi a karamar hukumar Malam Sani One Seven ya yabawa Malamai da shuwagabannin makarantar akan irin jajircewar da kokarin da s**ayi gurin ganin sun bada Ingantaccen ilimi ga daliban. Sannan yasha Alwashin zasuyi iya bakin kokarinsu don ganin sun tallafawa makarantar da kowane irin kayan aiki da basu dashi.

Yayin tofa Albarkacin bakinshi Alh Ibrahim Lawal Makiyayi (Sarkin Noman Jibia) ya jawo hankalin iyaye da su himmantu wajen kawo yaransu wannan makaranta domin ganin hasken gobensu, yayin da ha bayarda Kyautar naira dubu hamsin ga dukkan daliban da sunansu ya fito cikin shirye-shiryen da aka gabatar a ranar domin burgeshi da s**ayi a cewarsa.

Taron ya samu halartar manya manyan mutane da s**a hada da Sarakuna, ma'aikatan gwamnati, 'yan kasuwa, 'yan siyasa, iyayen yara, dama yaku bayi.
Wadanda s**a halarci taron sun hada da;

*Shugaban Karamar Hukumar Jibia wanda ya samu wakilcin Alh. Babangida BS

*Mai girma Sarkin Arewan Katsina Hakimin Jibia Alh Rabe Rabi'u Jibia

*Sakataren ilimi na karamar hukumar Jibia. Wanda ya samu wakilcin Mal. Sani One Seven

*Sarkin Noman Jibia Alh. Ibrahim Lawal Makiyayi

*Hon. Nura Yunusa Oga tsohon dan takarar dan majalisar jaha na karamar hukumar Jibia

*Hon. Nasiru One Boy. Shugaban Kamfani Who is Free Nigeria Ltd

*Alh Abu Mai zare shugaban Kamfanin Rauda Traveling agency

Da dai sauran manyan mutane, Attajirai da 'yan kasuwa

Ikon Allah!Tagwaye masu suna Sa'id da Sa'ad wadanda s**a auri tagwaye, kowane matarsa ta haifar masa tagwaye su ma.
25/07/2023

Ikon Allah!

Tagwaye masu suna Sa'id da Sa'ad wadanda s**a auri tagwaye, kowane matarsa ta haifar masa tagwaye su ma.

Address

Jibiya

Telephone

+2348032969739

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when JIBIA MEDIA News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to JIBIA MEDIA News:

Share