11/05/2026
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bukaci jam’iyyun adawa a Najeriya da su sake nazari kan batun mika tikitin takarar shugaban kasa na 2027 zuwa yankin Kudu, yana gargadin cewa hakan na iya raunana damar da suke da ita na kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a babban zabe mai zuwa.
A cikin wata sanarwa da kakakinsa, Olusola Sanni, ya fitar a ranar Litinin, Atiku ya bayyana kiran da ake yi na mayar da takarar shugaban kasa zuwa Kudu a matsayin mataki mai hadari kuma mara ingantaccen tsari na siyasa.
Ya ce duk da cewa jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na iya ci gaba da barin mulki a Kudu domin bai wa shugaban kasa mai ci damar sake tsayawa takara, bai dace jam’iyyun adawa su bi irin wannan tsarin ba tare da la’akari da ainihin yanayin siyasar kasar ba.