09/06/2026
Sanata Ali Ndume ya bayyana cewa fushin da ‘yan Najeriya ke yi kan matsin rayuwa da wahalhalun tattalin arziki na ƙaruwa, inda ya gargadi jam’iyyar APC da Shugaba Bola Tinubu cewa ba za su raina ƙarfin hamayya ba yayin shirin zaɓen 2027.
A lokaci guda, Ndume ya roki gwamnatin Amurka da ta kafa sansanin soja a Dutsen Mandara na Jihar Borno domin murkushe ragowar mayakan Boko Haram, yana mai jaddada bukatar haɗin kai tsakanin ƙasashen duniya da Najeriya wajen yaki da ta’addanci.
Sanata Ndume ya yi wannan bayani ne a daidai lokacin da ake tunkarar babban zaɓen 2027, inda ya nuna damuwarsa kan yadda rikicin tattalin arziki da tsaro ke shafar al’umma.